Tag: yadda ake

  • Auren Annabi SAW Da Nana Khadija

    Auren Annabi SAW Da Nana Khadija

    1. Bayan da wowar su da wata biyu daga tafiyarsu ta biyu zuwa Sham (ita ce Siriya a yanzu) ya auri shugaba Khadija (ita ce wadda ta nemi auransa da kanta).

    2. Shekarunta sun kasance arba’in (40) na daga rayuwarta, shi kuma (annabi) shekarunsa ashirin da biyar (25) na daga rayuwarsa.

    3. Ta kasance kafin ta aure shi (annabi) ta auri Abi-Halata, haƙiƙa ya mutu yana da ɗa guda ɗaya (1), sunan ɗan Halata.

    4. Haƙiƙa ta zauna tare da annabi, shekara ashirin da biyar (25), bai auri wata macen ba bayanta, har sai da ta rasu.

    Sharhi;

    Yayin da ya shiga garin Makkah, sai shugaba Khadija ta ga ya dawo mata da riba mai yawan gaske, sai ta yi farin ciki da ganin haka, sai ta aika masa tana neman izinin auransa idan zai amince, daman ita shugaba Khadija ta samu labarin sa, sai ta yi yunƙuri ta aure shi, amma ba ta samu ikon yi masa magana ba, sai can ta yi wani tunani, tace eh, to, tunda ina ɗaukar mutane kasuwanci, sannan kuma shi mutum ne mai sauƙin kai, mai zai sa ba zan ɗauke shi aikin ba, idan ya so daga baya sai na sanar da shi abin yake cikin zuciyata.

    Hakan kuwa aka yi, saboda albarkar da ke tattare da annabin ne da kuma irin gaskiyarsa da riƙon amanarsa. Waɗannan abubuwa dai sun faranta wa Khadijah rai ƙwarai da gaske da kuma ƙaunar annabi.

    Sai ko ta ɗauke shi aiki, bayan ya yi shirin tafiya kasuwanci, sai ta nemi ɗan aikinta mai suna Maisara, ta sanar da shi cewa, tana so za ta haɗa su kasuwanci da wannan babban mutum, amma abin da nake so da kai kawai shi ne, ka lura duk abin da yake yi na ɗabi’unsa haɗi da mu’amalarsa baki ɗaya.

    Sannan aka ɗora kayan kasuwanci akan dabbobi, sai suka kama hanya suka tafi, har suka tafi suka dawo, sai ta haɗawa annabi (Sallallahu alaihi wasallam) liyafa mai kyau, ta samar masa da waje mai kyau, ta ajiye masa kaya, sai ta kira Maisara take tambayarsa game da halayensa, sai Maisara yace, a gaskiya tun da muke tafiya kasuwanci, ban taɓa ganin mutum irin wannan ba ga tausayi, ga haƙuri, ga riƙon amana ga gaskiya, ga sanyin hali, ga kunya, da dai sauransu sai ta ji ya kamata ta sanar da shi abin da yake cikin ran ta.

    Saboda Hausawa sun ce: “A bari ya huce shi ke kawo rabon wani” sai kuwa ta fara tunanin yadda za ta sanar da annabi (Sallallahu alaihi wasallam), saboda ta san annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) Balarabe ne, Sannan kuma ka san Larabawa farare ne su, kuma annabi Yusuf (Alaihis-salam) wanda muka ji labarinsa haɗi da abubuwan da suka faru a tsakaninsa da matan wannan zamanin duk da haka shi fa rabin kyau ɗin manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) aka ba shi, amma ga abin da yaka faru da shi a wancan zamanin.

    Sai shugaba Khadija ta ga fuskarsa ta fi farar audiga, ta zarce madara irin ta ruga, Sannan da girman da kyawun tsaga, fuskarsa tana walwali, ta fi walƙiya haskakawa, ga haƙoransa fes ko tar sun fi wata haskakawa, goshinsa ya yi lub-lub baƙi sitil ga sansti, idan ya yi murmushi haske ne ke fitowa daga bakinsa saboda kyawunsa da kuma girmansa a wajen Allah (Subhanahu wata`ala).

    Sannan gashin kansa kamar gashin gada, ga idanunsa gada-gada zancensa akwai da fa’ida daɗin ƙamshin sa wa zai kwada, kowa na son sa cikin mutane, Sannan ga lallausan lafazi wanda ke ratsa zuciyar mutane ko ƙarfe ne a cikin zukatan mutane sai ya narke, saboda jin wannan lallausar hamshaƙiyar muryarsa.

    Bugu da ƙari zuciyarsa tar ce ko fes kuma ga haƙuri da hankali a gunsa gami da nutsuwa tamkar a ce mutane su yi murɗiya, saurin fushi ko faɗa ko ha’inci babu guda a gunsa gwanin gaskiya, sai shugaba Khadija ta ji ta gani, sannan ta tsuduma a cikin kogin madarar ƙaunarsa, sai ta samu Baffanta Amru ɗan Asdu ta ba shi labarin duk abin da yake tafe da ita, sannan ya samu Baffan annabi (Sallallahu alaihi wasallam) daga ƙarshe sai annabi ya amince zai aure ta.

    Haka kuma a wata faɗar an ce lokacin da annabi ya dawo daga kasuwanci, sai Maisara ya sanar da ita cewa sun dawo, sai sayyada Khadija ta saurari shigowar annabi, bayan ya shigo cikin gidan ta ga ya dawo mata da riba mai albarka, ashe lokacin da yake yi ma ta bayanin yadda kasuwancin nasu ya kasance, ita ko tsayawa ta yi tana kallon sa yadda yake yi ma ta jawabi cikin nutsuwa da yadda yake magana haɗi da sunkuyar da kan sa ƙasa tare da lallausar muryarsa mai ɗankaran daɗi, wadda dole mutum ya saurara, idan kuma ya yi shiru sai kwarjinin sa ya mamaye zuciyar mutum, sai ko sayyada Khadija ta shiga cikin wani hali na faɗawa cikin kogin zumuɗin ƙaunar sa (sallallahu alaihi wasallam), amma kuma sai ta kasa faɗa masa.

    Daga ƙarshe sai sayyadina Hamza da Abdul-Muɗallib suka tafi gidan su Nana Khadija aka nemo waliyyin ta (a lokacin ma mahaifinta ya rasu), sai Abdulmuɗallib ya sanar da shi (waliyyin na ta) abin yake tafe da su, sannan sai ya tashi ya yi huɗuba yake cewa “ duk wanda aka haɗa shi annabi akan ma’auni, to sai ɗan mu ya rinjaye shi, sannan kuma ba shi da dukiya a hannun sa, ita ko dukiya inuwa ce yanzu za ka iya samun ta zuwa anjima kuma a rasa ta”.

    Sai aka amince aka ɗaura musu aure da annabi (Sallallahu alaihi wasallam), sai aka yi shagalin aure, can sai ga wata tsohuwar mace nan da tumaki arba’in ashe Halimatus-Sadiya ce ta kawo su ta ce a yi shagalin bikin ɗan ta, saboda haka malamai suka ce babu wata mace wacce ta kai Nana Khadija zaɓin miji.

    Saboda haka a lokacin da annabi ya auri Nana Khadija sai ta share masa baƙin cikin da yake cikin zuciyarsa na tunanin rasuwar mahaifiyar sa da Baffan sa, sannan kuma ita ce wacce ta auri annabi tun kafin ya zama annabi.

    Haka kuma Shugaba Khadijah ta kasance kafin ta auri annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ta auri wasu mazajen guda daga cikinsu akwai Abu-Halata shi ne wanda Allah (Subhanahu wata’ala) ya ba su ikon samun rabo na da guda miji guda ɗaya sunansa Halata. Sannan kuma ta zauna tare da annabi (Sallallahu alaihi wasallam) shekara shekara ashirn da biyar (25) saboda haka idan muka haɗa da shekarunsa sa aure shi ya kama shekarun Annabi (Sallallahu alaihi wasallam) Hamsi (50) kafin shugaba Khadija ta yi Wafati ita kuma shekarun sittin da biyar (65) ko hamsin da uku (53) ko hamsin (50):

    Saboda haka Shugaba Khadija ta yi Wafati a shekara ta goma bayan annabta, amma annabi (Sallallahu alaihi wasallam) bai taɓa auren wata mace ba, har sai da ta yi wafati sannan ta haifa masa ‘ya’ya mata guda huɗu (4), wanda Babbarsu ita ce Zainab, sai Ruƙayya, sai Ummul-khursum sai Nana Faɗima wanda annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yasa mata Fatima, Saboda sunan Mahaifiyar Mahaifinsa ne Abddullahi ɗan Abdul-Muɗallib.

    Sannan dukkansu sun rayu kuma sun yi aure wacce sayyadina Usman Bin Affan ya auri guda biyu (2), daga cikinsu akwai sayyada Ruƙayya, bayan ta rasu sai ya auri sayyada Ummul-khursum, sai sirikin annabi (Sallallahu alaihi wasallam), na biyu shi ne Abul-as ɗan Rabi’a wanda ya auri sayyada Zainab wacce ta haifi ‘ya’ya daga cikin su akwai wacce ake kira da Umaima, wacce wani lokaci annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yake fitowa da ita yake riƙe ta yana Sallah da ita, sai sirikin annabi (Sallallahu alaihi wasallam) na uku (3) shi ne sayyadina Aliyu ɗan Abu-ɗalib (Karramallahu Wajjahahu) wanda ya auri sayyada Fatima , sannan kuma sayyada Nana Fatima tana da sunaye da yawa kamar su; Zakiyya, Batula, Ma’asuma, Alawiyya, da dai sauransu.

    Saboda haka menene dalilin da yasa Khadija ta zauna Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) shekara ashirin da biyar (25), kuma annabi (Sallallahu alaihi wasallam) bai taɓa auren wata macen ba har sai da ta rasu? Maganar gaskiya dalilan suna da yawan gaske, amma dai sayyada Khadija mace mai yawan ibada da haƙuri da juriya, sannan kuma ta iya zamantakewar auratayya haɗi da sanin kalaman da za su sanyayawa annabi zuciya.

    Bayan annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya fito daga shinge (wata kariya ce da ya shiga, a lokacin mutanen Najrana suka Zo wajen annabi (Sallallahu alaihi wasallam) su ashirin (20) ko kusa da ashirin sai annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya karanta musu Alƙur’ani, suka yi Imani da shi) kafin Hijira daga Makkah zuwa Madinah da shekaru uku (3) a shekara ta hamsin).

    Sai Sayyada Khadija ta rasu ‘yar Khuwailid matar annabi (Sallallahu alaihi wasallam), ya kasance yana yawan tunawa da ita saboda Imam Bukhari (3,818), Babi na (20) yace,; “Annabi ya auri sayyada Khadija yana daga fifikonta daga Hadisin da aka ruwaito daga Nana A’isha tace: ‘’ban taɓa kishi da wata mace ba daga cikin matan annabi (Sallallahu alaihi wasallam), sai sayyada Khadija, saboda irin abubuwan da na gani da irin son da annabi (Sallallahu alaihi wasallam) yake yi mata.

    Sai dai da na ga annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya cika yawan ambaton ta har ma (bayan ta rasu) yana yanka akuya (fata) sai ya ba ƙawayenta da ‘yan uwanta (Sayyada Khadija), sannan annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance wani lokaci yana cewa, kamar bai taɓa ganin wata ‘ya mace a wannan duniyar kamar sayyada Khadija ba, yace: ita (sayyada Khadija) ta kasance kaza da kaza haka kuma a tare da ni da ita akwai ‘ya’ya (Nurul Yaƙin shafi na 53).

    Danna nan don karanta Sunayen Annabi Muhammad (S.A.W)

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

  • Nasiha Mai Tsoratarwa

    BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM.

    Tsira da aminci su tabbata bisa Annabin ƙarshe, da dukkan iyalansa da sahabbai baki ɗaya.

    Yazeedur Raqqashiy ya karɓo Hadisin daga Anas bn Malik (R.A) yana cewa:
    Watarana Mala’ika Jibrilu (A.S) ya zo wajen Manzon Allah (S.A.W) a wani lokacin da bai saba zuwa masa ba. Ya zo, gaba ɗayan launin fuskarsa ya canza. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa “MAI YASA NA GA LAUNIN FUSKARKA DUK YA CANJA HAKA?”

    Yace “Ya Muhammadu (S.A.W) na zo maka ne a wannan lokacin da Allah ya yi umarni da masu hura wuta su ci gaba da hura ta. Duk wanda ya san cewa Jahannama gaskiya ce, wuta gaskiya ce, azabar kabari gaskiya ce, kuma azabar Allah ita ce mafi girma, to bai kamata ya yi wani farin ciki ba har sai ya tabbatar da cewa ya samu tsira daga wannan”.
    Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa “YA JUBREELU INA SO KA SIFFANTA MUN YADDA
    JAHANNAMA TAKE”.

    Sai yace “Na’am. Haƙiƙa Allah maɗaukakin Sarki yayin da ya halicci Jahannama, ya sa an hura ta tsawon shekaru DUBU. Har sai da ta zama JA -JAWUR. Sannan aka sake hura ta tsawon Shekaru DUBU har sai da ta zama FARI – FAT!! Sannan aka sake hura ta tsawon shekaru DUBU har sai da ta zama BAƘA – ƘIRIN!!! Tana nan har yanzu BAƘA ƘIRIN ce, mai tsananin duhu ce. Harshen balbalinta ba su mutuwa ballantana garwashinta.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya, da a ce za a buɗe misalin ƙofar allura daga wutar Jahannama, Wallahi sai dukkan ma’abotan doron duniyar nan sun ƙone baki ɗayansu saboda tsananin zafinta.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya, da a ce za a ratayo tufafi guda ɗaya tufafin ‘Yan wutar Jahannama a maƙalo shi a tsakanin Sararin Samaniya, da sai dukkan ma’abotan doron ƙasa sun mutu baki ɗayansu saboda tsananin warin wannan tufafin. Da kuma zafin da ke tattare da shi. Babu wanda zai yi saura a cikinsu don tsananin abinda za su riska na zafin wannan tufafin.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya a matsayin Annabi, da a ce za a ɗauko zira’i guda na Sasarin nan na ‘yan wuta (wato sarƙa ɗin da ake ɗaure su da shi sannan a riƙa jan su akan fuskarsu). Wannan wanda Allah ya ambata a cikin Alqur’ani, a ɗora shi bisa wani dutse daga duwatsun duniyar nan, da sai dutsen ya narke ya zagwanye har zuwa ƙasa ta bakwai.

    Na rantse da girman Ubangijin da ya aiko ka da gaskiya a matsayin Annabi, da a ce za a ajiye wani mutum a mafaɗar rana ana yi masa azaba, da sai wanda yake mahudar rana ma ya ƙone ƙurmus saboda bala’in zafinta. Zafinta mai tsanani ne. Zurfinta mai nisa ne.
    Tufafin cikinta na ƙarfe ne. Abin shan cikinta HAMIMU ne (tafasasshen ruwan azaba) da kuma ruwan gyambo.

    Mayafan cikinta kuma an yanko su ne daga Wutar”. Tana da ƙofofi guda bakwai, kowacce ƙofa tana da wani yankin cikinsu da aka tsaga mata (za su shiga ta cikinta) daga mazaje da mataye. Sai Manzon Allah (saww) yace: “SHIN KOFOFIN NAN IRIN NAMU NE?”
    Sai Jibrilu yace: “A a sai dai ita ƙofofin a buɗe suke, wata ƙofar tana ƙasan wata.
    Tsakanin kowacce ƙofa da wata ƙofar, tsawon tafiyar shekara SABA’IN ne.

    Kowacce ƙofa ta ninka wacce take sama da ita a tsananin azaba har ninki SABA’IN.
    Za a riƙa kora maƙiyan Allah cikinta. Kuma duk sanda aka koro wasu (‘Yan wuta) zuwa wata ƙofa, Zabaniyawa ne za su tarbe su da sarƙoƙi da sasarai. Za a zira musu sasari (chains) ta cikin bakinsu sai ya fito ta duburarsu. Sannan za a ɗaure hannunsa na hagu a jikin wuyansa, hannunsa na dama kuma za a fasa ƙirjinsa da shi a turo shi ta cikin zuciyarsa sai ya fito ta bayan kafaɗarsa. Sannan a haɗa a ɗaure da waccan sarƙar.

    Kowanne ɗan Adam za a haɗa shi tare da shaitani guda a cikin sarƙar sasarin, Sannan a riƙa jan sa akan fuskarsa (a cikin garwashin wutar da kuma dagwalonta) mala’iku kuma suna jibgar su da gudumomin baƙin ƙarfe. Duk lokacin da suka nemi fita daga cikinta saboda baƙin ciki da wahala, sai a sake dawowa da su cikinta. Sai Annabi (S.A.W) yace ma Jibreelu (R.A) “SHIN SU WANENE MAZAUNAN CIKIN WAƊANNAN ƘOFOFI?”

    Sai Mala’ika Jibreelu yace: “Ka ga amma ƙofar nan wacce take can ƙarƙashin ƙasa, ita ce mazaunar munafukai da kuma waɗanda suka kafirce daga mutanen Annabi Isa (A.S) (Waɗanda aka ce kar su ɓoye abinci amma suka yi taurin kai suka ɓoye). Da kuma mutanen Fir’auna. Ita wannan wutar sunanta “HAAWIYAH”.

    Sai kuma ƙofar nan ta biyu, waɗanda za su shiga cikinta su ne MUSHRIKAI. Kuma sunanta “AL-JAHEEM”. Ƙofar ta uku kuwa masu bautar taurari ne za su shiga ta cikinta. Su ne mazaunan cikinta. (a wani wajen an ce za su zauna tare da masu wasa da sallah). Kuma sunan wannan wutar “SAƘAR”.

    Ƙofar wuta ta huɗu, ta nan ne IBLIS (L. A.) zai shiga cikinta tare da mabiyansa da kuma
    Majusawa masu bautar Wuta. Kuma sunanta “LAZAA”. Kofa ta biyar kuwa ta cikinta YAHUDAWA za su shiga. Kuma sunanta “ALHUTAMAH”. Kofa ta shida kuwa, NASARA ne za su shiga ta cikinta. kuma sunanta “SA’EER”.

    Daga nan kuma sai Mala’ika Jibrilu ya sunkuyar da kansa ya yi shuru, ya kasa ci gaba da magana saboda jin kunyar Manzon Allah (S.A.W). Sai Manzo (S.A.W) yace masa “SHIN BA ZA KA BA NI LABARIN KO SU WAYE MAZAUNAN CIKIN WANNAN KOFAR TA BAKWAI ƊIN BA?” Sai Jibrilu yace: “Su ne ma’abotan manyan zunubai daga cikin al’ummarka. Idan har suka mutu ba su tuba ba” Nan take Sai Sayyidina Rasulullahi (S.A.W) ya faɗi YA SUMA!!!
    Sai Mala’ika Jibrilu ya ɗauki kansa ya ɗora akan cinyoyinsa har sai da ya farfaɗo sannan
    yace:

    “YA KAI JIBRILU LALLAI MUSIBA-TA TA GIRMA! KUMA BAKIN CIKINA YA TSANANTA!!! YANZU ASHE AKWAI WANDA ZAI SHIGA WUTA DAGA CIKIN AL’UMMATA?” Sai yace “Eh amma ma’abotan manyan zunubai daga cikinsu”. Daga nan Sai Manzon Allah (S.A.W) yasa kuka, Mala’ika Jibrilu ma yana kuka…!!!” Ibnu Katheer ya kawo wannan hadisin da ruwayoyi daban-daban a cikin littafinsa mai suna AN-NIHAYAH FIL FITAN WAL MALAHIM. A cikin babin da ke magana akan wuta da azaba cikinta.

    Allah (S.W.T) Ya yafe mana zunuban mu manya da ƙanana. Amin. Manzon Allah (S.A.W) ya na cewa mutanen da ke kusa da ni a ranar tashin Alƙiyama su ne masu yawan yi min salati! Allahumma salli Ala Muhammad wa sallim!

    Domin karanta Nasiha Tsakanin Musulmi danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Sunayen Watanni Da Hausa (Gargajiya)

    Sunayen Watanni Da Hausa (Gargajiya)

    1. Watan cika ciki (Almuharram).

    Bahaushe, yana yi masa wannan laƙabi ne, saboda abinci da ake ci a ƙoshi sosai, bayan an gama bikin sallah babba, Bahaushe yana ajiye awazar (ƙugun naman dabba) nama ko jela, har sai watan ya kama, sai ya ɗauko naman (raguwar naman layya), ya dafa shi sosai, a yi abinci sosai, sai taru a ci, a sha, sosai, shi ne yake yi masa suna da bikin sallar cika ciki.

    2. Bawan watan cika ciki (Safar).

    Shi kuma, wata ne wanda yake bin watan da aka yi cika ciki a cikinsa, idan akwai ragowar nama, wanda mutum bai cinye ba, to a watan ake gama cinyewa, saboda akwai wani bikin ma a gaba, wato watan maulid.

    3. Tagwai “watan maulid” (Rabbiyul-auwal).

    Shi kuma watan murnan maulidi ne, kuma ya yi masa laƙabi ne da “Tagwai”, saboda ma’anar sunansa ta tagwaye (wato watanni biyu masu suna a ɗaya a jere, Hassan da Usaini), wato Rabbiyul-auwal da kuma Rabbiyul-thani.

    4. Tagwai “watan bawan maulid” (Rabbiyul-thani).

    Wata ne, wanda yake bin watan da aka yi shagalin bikin maulidi a cikinsa.

    5. Gambon wata (Jumada Auwal)

    Wata ne, watan yake bin tagwaye (Rabbiyul-auwal da kuma Rabbiyul-thani).

    6. Tankon wata (Jumada Thani).

    Wata ne ,wanda yake bin gambo, shi kuma a cikinsa ana yin tanajin fara azumi ga tsofaffi.

    7. Watan azumin tsofaffi (Rajab).

    Wata ne, wanda tsofaffi suka fi yin azumi a cikinsa, saboda ƙara samun kusanci ga Allah gami da jure wahalar azumi, saboda yin azumin watan Ramadan lafiya. Amma yara ma suna yin azumi, sai dai tsofaffi sun fi yin azumi a cikinsa.

    8.  Watan sallar tsofaffi (Sha’aban).

    Wata ne, wanda ake yin bikin sallah, saboda an gama azumin tsofaffi lafiya, sai a shirya kayan liyafa ta musamman, don warware gajiya.

    9. Watan azumi (Ramadan)

    Wata ne, wanda ake yin azumin farilla a cikinsa, wanda mafi yawan Hausawa musulmai ne bayan an rushe maguzanci daga gare su.

    10.  Watan ƙaramar sallah (Shauwal).

    Wata ne, da ake yin bikin sallah, za a shirya kayan abinci na musamman da ziyarce-ziyarce da bukukuwa daban-daban, don murnar kammala azumi lafiya.

    11.  Watan bawan sallah ƙarama (Zulƙida)

    Wata ne, wanda yake bin watan da aka yi bikin sallah a ciknsa, kuma wata ne wanda ake yin tanajin dabbar da za a yanka da babbar sallah.

    12. Watan babbar Sallah (Zulhaj).

    Wata ne, wanda ake yin bikin sosai, saboda wata ne na ƙarshe daga cikin jeren watanni, kuma Bahaushe yana yanka dabbobi sosai, don samun abin da za a ci gami da rabawa abokanan arziki. Saboda a cikin al’adar Bahaushe babu rowa a ciki, Bahaushe ya samu rowa ne daga Turawa, saboda shigowar ilimin boko.

    Danna nan don karanta hanyar korar aljanu da kariya daga dawowarsu

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma

    Mai Huɗuba:
    Sheikh Dr Saleh Usama Bn Abdullahi Alkhayyaɗ

    Mai Fassara:
    Dr Usman Muhammad Ahmad (Azzuhri)

    Shugaban Sashi
    Dr Abdurrahman Muhammad Sani YYakubu

    Huɗubar Juma’a ta Masallaci Mai Alfarma 3/7/1446H
    Dr. Usama bin Abdullahi Khayyaɗ

    (Kiyaye Rassa Tare Da Tozarta Asali)
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya yi wa bayinSa ni’ima da Musulunci, ina gode masa tsarki ya tabbata a gare Shi, idanuwa ba sa riskar Sa kuma hankula ba sa kewaye Shi da fahimta.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Mai cikakken sarauta da tsarkaka da aminci. Kuma ina shaidawa lallai Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu Bawan Allah ne kuma ManzonSa, Ya bayyana wa al’umma asalin wannan Addini da rassansa, da manyan ginshiƙansa.

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga BawanKa kuma ManzonKa Muhammadu, da Alayensa da Sahabbansa manyan jagorori masu taƙawa da nagarta, da waɗanda suka bi bayansu da kyatatawa muddin darare da yini na bibiyan juna.
    Bayan haka:

    Ya ku bayin Allah!
    Ku ji tsoron Allah, saboda tsoron Allah shi ne tafarkin ankararrun mutane, kuma hanyar ma’abota hankali, sannan kuma gwadaben ma’abota basira. Cikinsa akwai aminci daga faɗawa kuskure, da rabauta da Aljanna, da kuɓuta daga wuta, ((Kuma duk wanda ya yi wa Allah da ManzonSa biyayya, kuma yake tsoron Allah kuma yake kiyaye dokokinSa, to waɗannan su ne masu rabauta)).
    Ya ku Musulmi!

    A lokacin da matsaloli suke mamaya, illoli suke yaɗuwa, kuma cututtuka suke yawaita, to, hankula za su ɗimauce, zukata kuma za su rikice, fahimtu za su ruɗe, sai hakan ya nisantar da mutum daga bin miƙaƙƙiyar hanya, ya karkatar da shi daga tafarki, ya kawo ɓarna mai girma a cikin tsarin rayuwa, saboda matsaloli za su yaɗu, karkata kuma za ta bazu, ma’aunan rayuwa su lalace, lamura su babbauɗe, sai a wayi gari an fara gabatar da na baya, kuma a jinkirta na gaba, a ƙasƙantar da manya, kuma a girmama ƙasƙantattu, a kiyaye ƙananan rassa, tare da tuzarta asali.

    Ya ku bayin Allah!

    Lallai a duniyarmu ta yau akwai misalai mabambanta da ba za su ƙirgu ba na kiyaye rassa da tozarta ginshiƙai, sai ka ga wani cikin mutane yana ƙoƙari wajen aikata ayyuka masu kusantarwa zuwa ga Allah dare da yini, don ya samu kusanci zuwa ga Majiɓincinsa Allah da su, kuma ya samu matsayi mai girma da ni’ima dawwamammiya a wajenSa, amma kuma za ka same shi yana haɗa hakan da abin da zai ɓata masa ƙoƙarinsa da wahalarsa, da abin da zai lalata masa aikinsa da jajircewarsa, a lokacin da zai yi wa Allah shirka da waninSa, a addu’a, ko neman taimako, ko neman agaji, ko yanka, ko bakance, ko karkatar da wani abu cikin nau’ikan bauta, wanda haƙƙi ne keɓantacce ga Allah, ba ya halatta a karkatar da wani abu cikinsu ga waninSa tsarki ya tabbata a gare Shi.

    A lokacin da zai je wajen wani boka ko ɗan duba ya tambaye shi kuma ya gaskata shi, da kuma lokacin da yake rataya laya ko ɗanwuri, yana riya cewa zai tunkuɗe cuta daga kansa da iyalinsa ko ‘ya’yansa, alhali kuwa Allah Maɗaukaki Ya bayyana wa bayinSa a cikin LittafinSa da fayyataccen bayani cewa: Lallai sakamakon wannan shirka shi ne lalacewar aikin mutum da rushewarsa, kuma ba zai amfani ma’abocinsa ba a Lahira, da kuma haramta masa shiga Aljanna, da kuma sanya wuta ta zama makomarsa.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: Haƙiƙa kuma an yi maka wahayi kai da waɗanda suka gabace ka cewa: “Tabbas idan ka yi shirka, to, lalle aikinka zai ɓaci, kuma tabbas za ka kasance daga cikin asararru. (Suratuz-Zumar: 65).

    Bayani mai daraja wanda ba ya buƙatar wani ƙari, ya zo daga Annabi a cikin ingantaccen Hadisi game da makomar wannan lamari. Haƙiƙa Imam Ahmad ya rawaito a cikin Musnadinsa, da Hakim a cikin Mustadrak ɗinsa da isnadi ingantacce daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Duk wanda ya je wurin mai duba ko boka, kuma ya gaskata shi a kan abin da yake faɗa, to, lallai ya kafirce wa abin da aka saukar wa Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi).

    Haka kuma Imamu Ahmad ya rawaito a cikin Musnadinsa, da Al-Hakim a cikin Mustadrak ɗinsa da isnadi ingantacce daga Uƙba ɗan Amir Allah ya ƙara masa yarda, cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Duk wanda ya rataya laya, to, lallai ya yi shirka).

    Daga cikin misalan kiyaye rassa da kuma tozarta ginshiƙan addini, akwai abin da za ka ga wasu daga cikin masu mayar da hankali wajen karanta AlƘur’ani da Tajwidinsa da kyautata sautinsu wajen tilawa, sannan kuma suna yin sakaci wajen kiyaye iyakokin da aka gindaya a cikinsa, kuma suna yin sakaci wajen aiki da abin da aka saukar game da su, kuma suna kau da kai daga yin tuntuntuni a cikin ma’anoninsa, da tasirantuwa da wa’azozinsa, da ɗaukar darasi daga labarai da misalai da ke cikinsa.

    Haka nan, cikin mutane akwai wanda yake nisantar najasa don kada ta taɓa tufafinsa, amma ba ya kauce wa yin gulma da annamimanci da yin karya. Akwai kuma wanda yake yawaita yin sadaka, amma ba ya nisantar dukiyar haram. Haka kuma, cikin mutane akwai wanda zai tashi ya yi sallolin dare yayin da mutane ke barci, amma yana jinkirta sallar farilla a kan lokacinta.

    Akwai kuma wanda yake azumtar yini, amma yana cutar da makwabtansa, yana take haƙƙoƙinsu, yana cin mutuncinsu, har maƙwabtaka da shi ya zama damuwa matsananciya, da sharri mai yawa, da bala’i mai girma a gare su. Akwai kuma wanda yake faranta wa abokan hulɗarsa da danginsa na nesa ta hanyar ƙulla alaƙoƙi masu ƙarfi da su, amma kuma sai ka ga yana munana wa iyayensa da ‘yan’uwansa, yana yanke zumunci, yana nisantar makusantansa da mutan gidansa.

    A cikin mutane, akwai wanda yake sakin hannu ga talaka na nesa, amma yana barin iyalinsa cikin yunwa, suna neman taimako a hannun mutane, ko kuma yana ƙuntata musu a kan kuɗin da ya zama wajibi ya ba su, kuma ba ya kyautatawa wajen ba su abin da zai ishe su. Akwai wanda kuma yake tsare tufafinsa da abin hawansa da shimfidarsa daga datti da ƙazanta, amma ba ya kiyaye kunnuwansa da idanuwansa daga gani ko jin abin da aka haramta masa.

    Haka nan, akwai wanda yake bin ƙananan lamura, amma yana yin sakaci game da manyan lamura, kuma yana bin abin da yake masa sauƙi, amma ba ya bin abin da yake da nauyi a gare shi. Ibnul Jauzi Allah Ya masa rahama ya ce: “Abubuwan da muka gani daga mutane a wannan babi, wato dangane da kiyaye ƙananan lamura da kuma tozarta manya, akwai ababen al’ajabi waɗanda za a shafe lokaci mai tsawo wajen ambatonsu”.
    Ya ku bayin Allah!

    Lallai babu shakka cewa tushen wannan karkacewa da asalin wannan kaucewa yana cikin barin muhimman tushe da kiyaye ƙananan rassa. Wannan kuwa ba komai ba ne face tsagwaron rinsinawa ga al’adu da kuma bin ɗabi’un gargajiya, nesa da hasken wahayi biyu wato Alƙur’ani da Sunna, kuma nesa da ƙa’idojinsu, tare da bin son zuciya ba tare da shiriya daga Allah ba, da kuma rashin ilimi game da Addinin Allah, da ƙarancin masu nasiha, da rashin tallafin masu taimako.

    Ku saurara! Lallai mafita daga duk waɗannan abubuwa, ba ta samuwa sai da magani na ilimi da kuma aiki. Game da ilimi kuwa, yana nuna wa ma’abocinsa ƙa’idoji da tushe da kuma ginshiƙai da ake gina rassa a kansu, ƙananan sassa kuma su samu ginuwa daga su. Hakan yana ba shi tsararren tunani mai kyau sai ya dinga sanya abubuwa a inda suka dace, kuma ya fahimci matsayi da darajar ayyuka.

    Shi kuma aiki a ɓangarensa, yana kasancewa mai inganci daidai da abin da Allah ya shar’anta, yana tafiya a bisa tafarkin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mai rabauta da samun karɓuwa a wajen Allah, tare da kaiwa ga dukkan burin da ake fata.

    Haka kuma, lallai ƙin bin son zuciya da ƙoƙarin tsara al’adu da ɗabi’un gargajiya bisa dokokin shari’a yana daga cikin abin da ake fatan za a gyara wannan karkacewa da tsayar da wannan kaucewa da shi, wanda zai dawo da Musulmi zuwa ga tafarkin Addininsa madaidaici.

    Allah ya amfanar da mu da shiriyar LittafinSa da Sunnar ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah mai girma da ɗaukaka a gare mu da dukkan Musulmi daga kowanne zunubi, lallai shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai.

    Huɗuba ta biyu:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mai hukunci, Mai adalci, Mai tausasawa, Mai cikakken sani. Ina gode Masa -tsarki ya tabbata a gare Shi, Shi ne Mamallakin duniya da Lahira, kuma zuwa gare Shi ne makomar ƙarshe take.

    Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu BawanSa ne kuma ManzonSa, mai bishara da kuma gargaɗi, fitila mai haskakawa. Ya Allah, ka yi daɗin salati da sallama ga BawanKa kuma ManzonKa Muhammad, da Alayansa da Sahabbansa. Bayan haka:

    Ya ku bayin Allah!
    Lallai babbar asarar da wanda ya tsare ƙananan rassa ya bar muhimman tushe zai samu, musamman idan waɗannan tushen sun kasance Tauhidi da Imani ne, ya dace ya sanya masu hankali su ba da cikakkiyar kulawa a kan wannan al’amari, su nisanci faɗawa cikin raminsa, su kuma nisanci kowace hanya da ke kaiwa gare shi..

    Ya ku bayin Allah!
    Wace iriyar asara ce mafi girma fiye da lalacewar aikin mai aiki, ko rage ladansa, ko ninka laifinsa? Ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, ahir ɗinku da barin muhimman tushe, ku san ƙimar kowane abu, ku ajiye shi a matsayinsa, al’amuranku za su daidaita, rayuwarku za ta inganta, kuma ku samu yardar Ubangijinku.

    Kuma a kodayaushe, ku tuna cewa lallai Allah Ya umurce ku da salati da sallama ga Mafi alherin talikai, a inda Maɗaukakin Sarki Yake cewa, ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga BawanKa kuma AnnabinKa Muhammdu, Kuma Ka ƙara yarda da Halifofinsa guda huɗu shiryayyu, Abubakar da Umar da Usman Ali, da sauran Alaye da Sahabbai da Tabi’ai, da Matansa iyayen Muminai, da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa Ranar Sakamako, ka haɗa mu tare da su cikin afuwarKa da karamcinKa da kyautatawarKa ya mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinKa masu Tauhidi, Ka haɗa kawunan Musulmi da zukatansu, Ka daidaita sahunsu, Ka gyara Shugabanninsu, Ka haɗa kalmarsu a kan gaskiya ya Ubangijin talikai, kuma Ka sanya wannan ƙasa ta zamto mai aminci da lumana da sauran ƙasashen Musulmi.

    Ya Allah Ka amintar da ƙasashenmu Ka gyara shugabanninmu da masu jagorancin mu, Ka taimaki shugabanmu Hadimin Masallatai biyu masu alfarma, Ka sanya masa nagartattun mashawarta, Ka datar da shi a kan abin da Kake so kuma Ka yarda da shi Ya Maji roko.
    Ya Allah Ka datar da shi da Magajinsa ga abin da alheri ne ga Musulunci da Musulmi, da abin da yake gyara ne ga ƙasa da kuma bayinKa, ya Wanda komai zai dawo gare shi a Ranar ƙarshe.

    Ya Allah Ka kare wannar ƙasa, Ka ba ta kowane irin alheri Ka tsare ta daga kowane irin sharri, da sauran ƙasashen Musulmi. Ya Allah, ka ‘yanta Masallacin Ƙudus, Ka kiyaye Musulmi a Falasdinu. Ya Allah Ka kiyaye su ta gabansu da bayansu, da damansu, da hagunsu, da kuma samansu, kuma muna neman tsarinKa kada a shammace su ta ƙarƙashinsu.

    Ya Allah Ka kasance musu Mai taimako kuma Mai goyon baya, Mai ƙarfafa su kuma Mai basu nasara, Ya Allah Ka sauko wa maƙiyanKa kuma maƙiyansu da bala’i, ya Ma’abocin ɗaukaka da karamci. Ya Allah Ka inganta mana Addininmu wanda shi ne kariyar lamuranmu, Ka kyautata mana duniyarmu wacce a cikinta muke rayuwa, kuma Ka gyara mana Lahirarmu wacce zuwa gare ta za mu koma, Kuma Ka sanya rayuwa ta zama ƙari ga duk wani alheri a gare mu, Ka sanya mutuwa ta zama hutunmu daga dukkan wani sharri.

    Ya Allah Ka sanya wa zukatanmu tsoranKa, Ka tsarkake su Kai ne Mafi alherin Mai tsarkakewa, Kai ne Masoyinsu kuma Majiɓincinsu. Ya Allah Ka kyautata ƙarshen lamuranmu gabaɗaya, Ka tsare mu daga kunyar duniya da azabar Lahira. Ya Allah muna neman tsarinKa daga gushewar ni’imarKa da sauyawar amincinKa, da uƙubarKa ta bazata, da kuma dukkan fushinKa.

    Ya Allah, muna roƙon Ka Ka bamu ikon yin ayyuka nagartattu, da barin munanan ayyuka, da ƙaunar talakawa. Kuma Ka gafarta mana, Ka yi mana rahama, kuma idan Ka ƙaddara aukuwar wata fitina ga bayinKa, Ka karɓi rayukanmu ba tare da mun shiga cikin fitinar ba.
    Ya Allah, Ka isar mana kan maƙiyanKa kuma maƙiyanmu da abin da Ka ga-dama, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah, Ka yi maganin maƙiyanKa kuma maƙiyanmu, kuma muna neman tsarinKa daga sharrinsu. Ya Allah ka warkar da marasa lafiyanmu, Ka ji ƙan mamatanmu, kuma ka cika mana burikanmu cikin abin da Ka yarda da shi, kuma Ka sa ayyukanmu na ƙarshen su zama kyawawa.

    ((Ya Ubangijinmu! Mun zalunci kawukammu, idan ba Ka gafarta mana kuma Ka yi mana rahama ba, to, tabbas za mu kasance cikin hasararru)).
    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu kyakkyawa a duniya da kuma Lahira kuma ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Tsira da aminci su tabbata ga BawanKa kuma ManzonKa Annabi Muhammadu da Alayensa, da Sahabbansa baki ɗaya.
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Don karanta Tarihin Dutsen Dala danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Matsayin Sanya Baƙaƙen Kaya

    Matsayin Sanya Baƙaƙen Kaya

    ‘Yan shi’a suna sanya baƙaƙen kaya ranar ashura; waɗansu ma tun daga farkon watan Muharram har tsakiyar watan Safar suna fama da baƙaƙen kayan da baƙaƙen tutoci; tare da cewa Imamai sun ce baƙaƙen kaya shigar ‘yan wuta ce, kuma shiga ce irin ta Fir’auna.

    Ga wasu daga cikin waɗannan ruwayoyi:

    1-An tambayi Imamu Sadik akan hukuncin yin salla da baƙar hula sai ya ce; “kada ka yi salla da ita saboda (sanya baƙaƙen kaya) shiga ce irin ta ‘yan wuta.

    2-An rawaito daga Amirul Mumini Aliyu (Radiyallahu Anhu) ya koyawa almajiransa cewa; “Kada ku sa baƙaƙen kaya saboda shiga ce irin ta Fir’auna” 2.

    3-An rawaito daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya hana sanya baƙaƙen kaya sai dai rawani da huffi da mayafi.

    Wani shaihin malami na shi’a mai suna; Alhaji Muhammad Rida AI-Husaini Aha’iri ya tabbatar da Ijma’in maamansu akan wannan mas’ala; wato babu wani saɓani a shi’anci akan haramcin sanya baƙaƙen kaya; ya yi wannan magana ne a littafinsa mai suna “Najatul Umma fi Ikamatil aza’i ala! Husaini wal a imma”. Sh.83.

    To saboda Allah sanya baƙaƙen kayan nan ba kangarewa umarnin imamai ba ne? To mazhabin su wa ake bi ke nan?

    Domin karanta cikakken bayani akan Haramun Ne Mata Su Halarci Husainiyya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Haramtaccen Laƙani Ko Asiri danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Addu’ar sanya sabon Kaya A Musulunci

    Addu’ar sanya sabon Kaya A Musulunci

    An rawaito daga Abu Sa’eed Allah ya ƙara masa yarda yace: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan ya yi sabon tufa ya kan kira shi da sunan shi sannan yace:

    اللَّهمَّ لك الحمدُ أنت كسوْتنِيهِ أسألُك من خيرِه وخيرِ ما صُنِعَ له ، وأعوذُ بك من شرِّهِ وشرِّ ما صُنِعَ له

    Allahumma lakal hamdu Anta kasautanihi, As’aluka min khairihi wa khairi ma suni’a lahu, wa A’uzu bika min sharrihi wa sharri ma suni’a lahu

    Abu dawud: 4020  Turmidhi: 1727

    Sharhin Addu’ar:

    Ubangijina ina maka godiya kai ne ka azurta ni da wannan tufafi, ba tare da iyawa ta ba, ina roƙon ka ka sanya wannan tufafi ya zamto mai taimako na wurin aikata alheri, Ka haɗa ni da alherinsa, ina kuma neman tsarinka daga sharrinsa sa: ka kiyaye ni kada ya zamto wannan tufafi ya zamto sanadiyyar saɓa maka.

  • Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Halayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su

    Akwai waɗansu muhimman halaye da ya kamata mai azumi ya siffanta da su, a gan su da gaske a tattare da shi. Cikin halayen akwai:

    i. Haƙuri, wato mai azumi ya siffantu da haƙuri wanda shi zai zama jagaba a cikin lamuransa, ya hana shi bin son zuciya da saɓa wa Allah. Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Idan ɗayan ku yana azumi, kada ya yi maganganun fasiƙanci. Idan wani ya zage shi, ya ce Ni mai azumi ne” (Sahihul Bukhari 1894, Sahih Muslim 1151).

    ii. Riƙon amana, yana da kyau mai ya zama mai riƙon amana, domin tana daga cikin abar da za ta taimaka masa wajen kiyaye azuminsa.

    iii. Rahama, ana son mai ya siffantu da rahama, da sakin hannu da karamci, da kuma yalwar zuciya. Manzon Allah (S.A.W) ya ce “Duk wanda ya ciyar da mai azumi, yana da kwatankwacin ladan wanda ya ciyar ba tare da an rage ladan wanda aka ciyar ɗin ba” (Sunan al-Tirmizi 647, Sunan Ibn Majah 17).

    iv. Nasiha, yana da kyau mai azumi ya kasance mai yin nasiha da kuma umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna.

    v. Sulhu, mai azumi yana da kyau ya kasance mai yin sulhu da sasanta mutane, musamman la’akari da cewa ƙiyayya da gaba na kawo tsaiko wajen karɓar ibada da addu’a.

    vi. Kame harshe, ya kamata mai azumi ya kame harshensa daga maganganu na shirme da shashanci, sannan ya nesanci giba, zagin mutane da yi musu ƙage ko sharri da ƙarya ko musu marar dalili, musamman abin da ya shafi siyasa ko wasan ƙwallo ko wanin waɗannan.

    An karbo hadisi daga Abu Huraira (R.A) cewa, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Wanda duk bai bar faɗin magana ta zur da aiki da ita ba, to Allah ba shi da buƙatar ya bar cinsa da shansa”. (Bukhari 4/99).

    Haka nan wani hadisin dai daga Abu Huraira (R.A) dake cewa: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ba azumi ba ne barin ci da sha, shi azumi shi ne na yasasshen zance da batsa, ko da wani ya zage ka, ko ya yi maka wauta, to ka ce: “Ni mai azumi ne”. (Ibn Khuzaima 1996). Ibnu Majah ya fitar da hadisi mai ɗauke da razani ga mai yin maganganun banza a yayin da yake azumi, ya ce: “Sau da yawa wani mai azumin ladansa shi ne yunwa da ƙishirwa”.

    vii. Rintse ido da kame farji, yana da kyau mai ya rintse idanuwansa daga kallon haramun, ya kuma kare farjinsa daga dukkanin haramtattun abubuwa. A nan muna jan hankalin waɗanda ke ganin kallon fina-finai ko tashoshi na gusar musu da yunwa, haƙiƙa wannan kuskure ne babba da kuma munana zato ga Allah, da kuma keta iyakokinSa.

    Su ma masu sanya fina-finai a tashoshi wajibi su ji tsoron Allah, sani ribar rayuwa da albarkar abin da suke so shi ne ginawa bisa tafarkin Musulunci.

    viii. Iklasi, ya kamata mai Azumi ya ƙudurce cewa lalle yana yin wannan azumin ne saboda Allah, kuma domin neman yardar Allah, ba domin mutane su yabe shi ba. A nan, ana jan hankalin yan’uwa masu yin sadaka ko ciyar da masu Azumi da masu tafsirin Alku’ani, da limamai masu rera tilawa, da masu zuwa Umarah, da sauran aiyuka nagari, wajibi su sanya iklasi kada shaiɗan ya lalata musu ayyukansu.

    ix. Bin sunnar Manzon Allah (S.A.W), wajibi ne mai azumi ya nesanci bidi’o’i, ya tsaya kan sunna ka’in da na’in, domin kyakkyawan aiki yana cikin koyi da Fiyayyen Halitta (S.A.W).

    x. Tarbiyya, wajibi ne mai azumi ya tsaya wajen ƙoƙarin tarbiyyantar da kansa da ‘ya’yansa ko ‘yan’uwansa ko waɗanda yake da iko a kansu. Kuma iyaye su ɗauki wannan wata a matsayin lokacin roƙarwa ‘ya’yansu shiriya.

    Domin Karanta Abubuwan da Suke bata Azumi danna nan

  • Tarihin Marigayi Dakta Murtala Kudan

    Tarihin Marigayi Dakta Murtala Kudan

    An haifi Dr. Murtala Shehu a garin Kudan a ranar 01/01/1960, ya yi karatun allo, sannan kuma ya yi karatu a makarantar firamare wacce take Kudan, haka kuma ya yi karatun gaba da firamare, kazalika kuma ya yi karatu a jami’ar Ahmadu Bello ɓangaran ilimin lafiya (wato CHO) a 1982. Sunan mahaifinsa shi ne Alhaji Shehu Turaki, mahaifiyar sa ita ce Hajiya Khadija mai Gauda.

    Sannan kuma ya yi aure ya haifi ‘ya’ya maza da mata kamar haka;

    1. Usman

    2. Abduljalali

    3. Ahmad

    4. Abdullahi

    5. Sani

    6. Isah

    7. Yahaya

    8. Abdulhadi

    9. Mubarak

    10. Hauwa

    11. Amina

    12. Bilkisu

    13. Shafa’atu

    14. Suwaiba

    15. Maimuna

    16. Khadija

    17. Salima

    18. Halima

    19. Na’ima

    20. Asiya

    21. Fatima

    22. Nusaiba

    Sannan kuma ya buɗe asibiti a garin Kudan a shekara ta 1982 mai suna “Nakowa nursing and maternity home Kudan” (yau kimanin shekara 39 ke nan) wanda dubbunan mutane suke amfani da shi (asibitin).

    Domin karanta yadda ilimi zai zama hasken rayuwarka danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Mawaƙi Ashir San Kudan

    Tarihin Mawaƙi Ashir San Kudan

    An haifi Ashiru Hamisu a garin Kudan a gidan Tattibu, ɗa ne ga Malam Adamu wanda aka fi sani da Malam Bala, sunan mahaifiyar sa ita ce Maryam Yusha’u wacce aka fi sani da suna Dogora an haife ta a ƙofar Arewa gidan Malam Tanko, ta rasu a shekara ta 2019. Ashiru an fi sanin sa da suna Ashir San, wanda yake amfani da sunan yayan sa, wato Sani, wanda shi ne babban yayan sa.

    Ashir San ya yi karatun allo a hannun Malam Abdullahi, wanda shi ne ƙanin mahaifiyar sa, tun yana karatun allo ya fara tunanin yadda zai rubuta waƙa, saboda yawan jin wani shiri da yake yi a Kano a Freedom Radio, wato shirin Taskira sai ya samu takarda ya fara rubuta waƙa, amma da ajami (rubutun harafan larabci) sai mutane suke yi masa dariya, saboda su ba su taɓa ganin inda aka rubuta waƙa da ajami a lokacin su ba.

    Bayan ya dawo gida daga makarantar allo, sai ya shiga makarantar zamani (boko) a inda har yanzu yana fafatawa. Sannan kuma Allah ya yi masa baiwar waƙa har muryar Naziru sarkin waƙa yanayi, wanda ya fara koyo masa waƙa shi ne Shu`aibu army na ƙofar Arewa Kudan.

    A fannin waƙa har sai da ta kai an kulle shi a police station har sai ya yi kwana uku a can, saboda wata waƙa da ya yi mai suna Kutara-kutara ɓarayi, daga ƙarshe sai uban gidan sa wato Salisu Ten-ten ya fito da shi, tun lokacin da aka kama shi sai ya ƙara samun magoya baya sosai, yana fitowa sai ya yi wata waƙa mai suna kainuwa dashen Allah, domin nuna godiyar sa ga mutanan sa suka ba shi gudunmawar su a lokacin da aka kulle shi, a ƙarshe kuma ya yi waƙoƙi da dama ga kaɗan daga cikin waƙoƙinsa;

    1. Duniya .

    2. Ita gaskiya.

    3. Nusaiba.

    4. Ashir San Salisu M. Rana.

    5. Yayyafin kuɗi.

    6. Kainuwa dashen Allah.

    7. Ku tara ɓarayi.

    8. Sarkin dole.

    9. Tinjim.

    10. Mazurai.

    11. Sarkin Zazzau.

    12. Fatima.

    13. Baƙar masarauta.

    (Mun samu wannan bayani ne daga bakin Ashir San wanda ya turo min ta waya ta a ranar Talata 13/06/2020 a misalin ƙarfe 5;03 na yamma).

    Danna nan don karanta ƙa’idoji sha shida na samun nasara a rayuwa

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Mawaƙi Labaran Adam Kudan

    Tarihin Mawaƙi Labaran Adam Kudan

    An haifi Labaran Adamu Shu’aibu a ƙofar Arewa Gidan Malam Tanko Kudan, a Ƙaramar Hukumar Kudan jihar Kaduna, ya fara karatun allo a wajen Alaramma Aliyu Labaran Ƙofar Arewa Kudan, sai kuma ya wuce jihar Kano wajen Alaramma Hamisu wanda yake  Ƙaramar Hukumar Nassarawa Tudun Murtala a wannan makarantar ne ya samu damar sauke Alƙur`ani mai girma, sai kuma ya koma gida ya fara karatun littattafai a wajen malam Magaji na-umma wanda yake ƙofar Arewa, ya yi aure yana da ‘ya mace mai suna Nazifa, amma kuma Allah ya yi wa matarsa  ta farko rasuwa bayan ta haifa masa waccan ɗiyar.

    Bayan waɗansu lokuta ne sai kuma ya dawo jihar Kano ya kama harkar kasuwanci a ƙaramar hukumar Kumbotso jihar Kano. Sai kuma ya ci gaba da karatun addini a wajen marigayi Malam Adamu Azare limamin Juma’a na Panshekara da kuma Alaramma Misbahu Tsaure. Sannan kuma ya yi karatun boko a Yakubu firamare school wacce take jihar Kaduna a shekara 2001-2007, ya yi karatu a Annur Institute for Islamic education Shahuci a shekara ta 2011, yana yin waƙar bege da waƙar siyasa da dama ga kaɗan daga cikin su;

    1. Gari mai albarka (bege)

    2. Nana Aminatu (bege)

    3. Hajiya Mariya (waƙa ga mahaifiyar Ɗangote)

    4. Farin gani Kumbotso (waƙar siyasa ga Sadau)

    5. Isah Ashiru  (waƙar siyasa ga Rt. Hon. Isah Ashiru Kudan)

    6. Mudassir (waƙar siyasa ga Ɗanmajalisa Mudassir) da dai sauran su.

    (Mun samu wannan bayani ne daga Labaran Adamu wanda ya rubuto min a ranar Laraba 24/06/2020 da misalin ƙarfe 11;30 na safe).

    Domin karanta tarihin Dakta Alhaji Gambo Kudan danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu