An rawaito daga Abu Sa’eed Allah ya ƙara masa yarda yace: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan ya yi sabon tufa ya kan kira shi da sunan shi sannan yace:
اللَّهمَّ لك الحمدُ أنت كسوْتنِيهِ أسألُك من خيرِه وخيرِ ما صُنِعَ له ، وأعوذُ بك من شرِّهِ وشرِّ ما صُنِعَ له
Allahumma lakal hamdu Anta kasautanihi, As’aluka min khairihi wa khairi ma suni’a lahu, wa A’uzu bika min sharrihi wa sharri ma suni’a lahu
Abu dawud: 4020 Turmidhi: 1727
Sharhin Addu’ar:
Ubangijina ina maka godiya kai ne ka azurta ni da wannan tufafi, ba tare da iyawa ta ba, ina roƙon ka ka sanya wannan tufafi ya zamto mai taimako na wurin aikata alheri, Ka haɗa ni da alherinsa, ina kuma neman tsarinka daga sharrinsa sa: ka kiyaye ni kada ya zamto wannan tufafi ya zamto sanadiyyar saɓa maka.