Tarihin Dakta Alhaji Gambo Kudan

0
57

An haifi  Dr. Alh Gambo a garin Kudan a ƙofar gabas a ranar 01/01/1954, sunan  mahaifinsa shi ne Khalid, ya yi karatun Allo, sannan kuma ya yi karatun zamani a makarantar firamare ta garin Kudan a 1960-1967, sai ya tafi makarantar gaba da fimare, wacce take Maƙarfi a 1967-1973, sai ya wuce makarantar ilimin lafiya, wacce take jihar Katsina (School of Nursing) a 1976-1980.

Bugu da ƙari kuma, ya fara aiki ne a asibitin Ikara (General Hospital Ikara) daga 1980-1994,ya yi kuma aiki a asibitin maƙarfi 1994-2015, wanda a wannan asibitin na Maƙarfi, ya yi ritaya na aiki kamar yadda dokar ƙasa ta tsara, wanda mutum ba zai haura shekara 35 ba, yana aikin gwamti ba, wanda ya yi ritaya ne yana da matsayin chief nursing officer.

Sannan kuma ya buɗe asibitin sa a garin Kudan, wanda yake kan hanyar zuwa Doka daga Kudan, a shekara ta 1985 mai suna Rahama Nursing Home har zuwa yau (shekarar asibitin  36 ke nan daga wannan shekarar ta 2021).

Sannan kuma, ya samu lambobin yabo da dama, amma ga kaɗan daga ciki;

Arewa Trusted Youth initiative Forum of Nigeria 2016.

Association of General Private Nursing practitioners 06/11/2015.

(Mun samu wannan bayanin ne daga bakin sa,wanda ya umarci ma’aikacin sa wato Dr. Mu’azu ya rubuto akan takarda, ya ba Mubarak Idris a kawo min)

Domin karanta shinkafa mai ƙwai danna nan

Edita; Rumasa’u M. Kallamu

labarin da ya wuceYadda Za Ki Inganta Halayyarki Da Ɗabi’u Masu Kyau
Labarin na GabaTarihin Marigayi Nuhu Baushe Kudan