Tag: yadda ake

  • Kwanakin Da Mahaifa Ke Yi Kafin Ta Rufe Bayan Gama Al’ada

    Kwanakin Da Mahaifa Ke Yi Kafin Ta Rufe Bayan Gama Al’ada

    Kuskuren da mutane suke yi shi ne suna ɗaukar cewa mahaifar mace buɗewa take yi kuma ta zamo a wangale lokacin da take yin jinin al’ada. A a, abinda yake faruwa shi ne, jinin yana fitowa ne ta bakin mahaifa (cervix), wacce ‘yar ƙaramar ƙofa ce mai kewayayyar siffa (circular shape), faɗinta yana kamawa daga 0.5cm zuwa 1.5cm.

    Ƙofar takan buɗe ne kaɗan a daidai lokacin da mahaifar ta takure (compression) domin turo jinin da yake cikinta zuwa waje. Takurewar ita ce take haifar da ciwon mara ko ciki. Da zarar jinin ya gama fita, to, bakin mahaifar zai tsuke, ya jira sai idan jinin ya sake taruwa kuma mahaifa ta sake takurewa domin ya fito, sa’annan ta sake buɗewa.

    Misali gwari-gwari yadda za ki gane shi ne yadda ƙofar duburar mutum take buɗewa idan kashi zai fito. Da zarar kashin ya fito, za ta tsuke sai ki sake yin yunƙuri kuma. Daga wannan bayanin za ka iya fahimtar cewa ba maganar kwana nawa ne mahaifa za ta rufe bayan gama al’ada ba. A a, ko yaushe bakin mahaifarta a rufe yake, sai idan jinin al’ada zai fito take buɗewa.

    Sa’annan ya rufe da zarar ya gama fitowa, sai kuma wani lokacin. Game da shigar ƙyanƙyasasshen ƙwan haihuwa zuwa cikin mahaifa kuwa, ga yadda abin yake: Jakunkunan ƙwan haihuwa (ovaries) sukan saki ƙwayayen haihuwa (ova) a lokacin da zangon al’adar mace ya kai tsakiya (middle of menstrual cycle). Idan ƙwan ya fito, zai tsaya a cikin bututun ƙwan haihuwa (fallopian tubes) ya jira zuwan ‘ya’yan maniyyin namiji domin su ƙyanƙyashe shi (fertilization).

    A cikin ‘ya’yan maniyyin, za a sami guda ɗaya ne wanda zai ƙyanƙyashe ƙwan. Idan kuwa ba a yi sa’ar samun ɗan-maniyyin da ya ƙyanƙyashe shi ba, to, kwan haihuwar zai iya rayuwa ne na tsawon kimanin awoyi 24. Daga nan zai lalace.

    Idan kuwa an ƙyanƙyashe shi, shi ake kira “zygote” ko “blastocyst” a likitance. Daga nan ƙyanƙyasasshen ƙwan zai gangara a hankali daga cikin bututun fallopian tube zuwa bakin mahaifa (cervix). Yadda tafiyar take zamowa kuwa shi ne ta hanyar takurewar tsokar bangon bututun fallopian tubes ɗin (fallopian tubes muscular contractions).

    Abinda yake sauƙaƙawa tafiyar a lokacin da tsokar take takurewar shi ne bangon bututun yana da waɗansu halittu masu santsi kamar gashi (cilia), wanda santsinsu zai riƙa ingiza ƙwan gaba-gaba (ciliary motion) har zuwa bakin mahaifa.

    Don haka, idan ƙwan ya Isa bakin mahaifa, zai tarar da majinar bakin mahaifa (cervical mucus) tana jiransa. Majinar ita ce ruwan ni’ima na bakin mahaifa. To, da zarar ƙwan ya Iso, sai bakin mahaifar ya ɗosano isowarsa. Hakan zai aikewa ƙwaƙwalwa saƙon cewa ana buƙatar ta bayar da umarnin bakin mahaifar ya buɗe domin ƙyanƙyasasshen ƙwan ya shiga cikin mahaifa.

    Saboda haka bakin mahaifar zai buɗe, daga nan sai santsin majinar ya taimakawa ƙwan ya shiga cikin mahaifar. Da zarar ya shige, bakin mahaifar zai sake rufewa. Wannan shi ne ake kira “cervical os” wanda sakamakon awon ultrasound scan yakan nuna.

    Idan ƙwan ya shiga cikin mahaifa, to zai yi ƙoƙarin maƙalewa a jikin bangon mahaifar (implantation), kuma hakan yana haifarwa mace zubar jini kaɗan-kaɗan (implantation bleeding), wanda yake ɗaukar ‘yan kwanaki. Amma jinin zai daina zuba da zarar ƙwan ya yi nasarar maƙalewa yaddà ya kamata. Duk waɗannan ayyukan suna faruwa ne cikin kwanaki 6 zuwa 10. 

    Maƙalallen ƙwan zai cigaba da yin girma ta hanyar zuƙo jinin jikin mace mai juna biyun a daidai inda ya maƙale. Kuma maƙalewarsa za ta sanya jikin mai juna biyun ya fara samar da sinadarin “human chorionic gonadotropin-hCG”, wanda tsinken awon ciki na PT, ko awon ciki na jini suke ɗosanowa, har su nuna cewa tana da ciki. Sa’annan daidai wurin da ƙwan ya maƙale, to, a nan ne uwa (placenta) take tsirowa. U.S

    Danna nan don karanta hawan jini

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Marigayi Nuhu Baushe Kudan

    Tarihin Marigayi Nuhu Baushe Kudan

    An haife shi a garin Kudan, sunan mahaifinsa shi ne malam Bala, mahaifiyar sa kuma Hassana, ya shahara wajen iya harbi, wanda waɗansu mutane suka ce tun da suke, ba su taɓa ganin ya auna ko ya saita wani abu ba.

    Amma kuma ya ƙasa bugo abin, wanda hatta ma maganin bindiga an sha kawo su wajen sa, amma da ya saita, sai kawai ka ji bindigar ta tashi, kamar yadda muka tattauna da ‘ya’yansa (Suleman da Shitu mai aski) suka ce ba a taɓa kawo masa maganin bindiga ya harba ta ƙi tashi ba a iya tsawon rayuwar sa.

    Saboda haka ne ma yasa ake yi masa laƙabi da Nuhu mai bindiga, duk da yake an yi wasu a can baya, amma kuma su da kwari da baka suke yi kamar wata mace wacce ake iya kira da suna Madidi mace mai kamar maza, wadda ta kashe ɓarawo a daji ita kaɗai, ga sarkin Kudan Sambo, ga Mika na sari, ga Garba na Ode da sauran su.

    Bugu da ƙari kuma,  ya iya sana’ar wanzanci da ƙira da mafarauci da allura da ɗori da ba da magungunan gargajiya da gyaran keke da kuma harbi. Saboda a harkar faruta mafi yawanci shi kaɗai yake fita daji, ya tafi ya yi farautarsa a cikin dare ya dawo da safe, haka kuma wani lokacin ma yakan yi kwanaki uku ko sama da haka a daji bai ya dawo gida ba, sai dai kawai abin da ya farauto ya aiko da shi gari a siyar.

    Shahararsa 

    Ya shahara wajen iya sarrafa bindiga ta yadda yake so kuma a lokacin da yake so, misali idan  yana ɗaki a kwance a kan gadonsa, sai ya hango wata tsuntsuwa a kan wata bishiya, to zai iya auna ta daga nan inda yake zaune ya kuma harbo ta. Haka kuma akwai wani lokaci da ya tafi barikin sojoji na Fatakwal, wanda yake a Ohode ya dawo gida da wata adda, wanda wannan addar duk ƙafar da aka sara da ita ,sai dai kawai mutum ya ga ƙarfan ta gutsire ko ya noƙe ko ya lauye.

    Sannan kuma ya tafi Nassarawa wajen wani gari wanda ake kira da suna Toto ya yi kwana da kwanaki a can, ya kuma tafi jihar Sokoto wajen garin Moriki, ya tafi jihar Taraba wajen garin Zink, waɗannan su ne kaɗan daga cikin dajujjukan da  ya halarta daga cikin ƙasar nan banda su irin Katsina da Jigawa da dai sauran su.

    Bugu da ƙari kuma, akwai wata rana ya tafi daji akan ɗan wani gajeren mashin ɗin sa, bayan ya tafi dajin sai ya samu wani waje ya ajiye shi, can sai wani mutum ya lallaɓo ya taho zai ɗauke masa mashin ɗin nasa, ai ko yana zuwa kusa da inda mashin ɗin yake, sai kawai ya ga mashin ɗin ya koma kamar  Gada, sai ko ya tsaya ya ciro bakar sa wai zai harbe shi.

    Can sai ga Nuhu Baushe nan ya taho ya dafa mashin ɗin sa ya hau ya kara gaba, kawai abin nan  ya ba shi mamaki, kamar yadda duk wanda yake garin Kudan ko ƙaramar hukumar Kudan, ya san wane ne Lado, wanda shi Lado ɗa ne ga Nuhu Baushe, sannan kuma shi Lado idan mutane sun kai guda ɗari ko sama da haka, to ba su isa su hana shi ya wuce ba ko da ko sun kewaye shi baki ɗayansu.

    A lokacin da yake ganiyarsa, da zarar ya yi wani yunƙuri, sai dai kawai a ga ya wuce, kamar yadda an sha samun waɗansu zuga a garin Kudan, sun taho domin su yi masa lahani, amma kuma da zarar ya yi wani yunƙurin, sai kawai a ga ya fice.

    Saboda haka idan mutum ya yi nazari sosai, zai ga abin mamaki sosai akan sha’anin, domin kuwa kowane mutum a wannan zamanin zai iya shaidawa cewa masana na ɓangaran lafiya ne kaɗai suke yin allura ko kuma wanda ya yi ilimin zamani (boko) mai zurfi su ne kaɗai ne suke yi allura, amma  kuma shi  sai ga shi almajiri ne, wanda ya yi karatun allo, amma kuma sai ga shi yana yi wa mutane allura, wanda har ma ni kai na mai wannan rubutun na shaida ya yi min allura.

    Haka kuma akwai mutane da yawa waɗanda suka koyi allura, saboda yawan zama da suke yi da shi misali kamar ɗansa Nuhu mai aski a kuka, wanda ya shaida mana cewa dukkanin ‘ya’yan sa da shi kan sa, idan ba shi da lafiya, to da kansa yake yin allura, amma kuma almajiri ne.

    (Mun samu wannan jawaban ne ta hannun ‘ya’yan sa wato Suleman da Shittu a ranar lahadi 16/03/1442 Hijira=01/11/2020 da misalin ƙarfe goma na dare a shagon Shitu mai aski wanda yake Kuka Kudan).

    Danna nan don karanta tarihin hakimin Kudan

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

  • Tarihin Dakta Alhaji Gambo Kudan

    Tarihin Dakta Alhaji Gambo Kudan

    An haifi  Dr. Alh Gambo a garin Kudan a ƙofar gabas a ranar 01/01/1954, sunan  mahaifinsa shi ne Khalid, ya yi karatun Allo, sannan kuma ya yi karatun zamani a makarantar firamare ta garin Kudan a 1960-1967, sai ya tafi makarantar gaba da fimare, wacce take Maƙarfi a 1967-1973, sai ya wuce makarantar ilimin lafiya, wacce take jihar Katsina (School of Nursing) a 1976-1980.

    Bugu da ƙari kuma, ya fara aiki ne a asibitin Ikara (General Hospital Ikara) daga 1980-1994,ya yi kuma aiki a asibitin maƙarfi 1994-2015, wanda a wannan asibitin na Maƙarfi, ya yi ritaya na aiki kamar yadda dokar ƙasa ta tsara, wanda mutum ba zai haura shekara 35 ba, yana aikin gwamti ba, wanda ya yi ritaya ne yana da matsayin chief nursing officer.

    Sannan kuma ya buɗe asibitin sa a garin Kudan, wanda yake kan hanyar zuwa Doka daga Kudan, a shekara ta 1985 mai suna Rahama Nursing Home har zuwa yau (shekarar asibitin  36 ke nan daga wannan shekarar ta 2021).

    Sannan kuma, ya samu lambobin yabo da dama, amma ga kaɗan daga ciki;

    Arewa Trusted Youth initiative Forum of Nigeria 2016.

    Association of General Private Nursing practitioners 06/11/2015.

    (Mun samu wannan bayanin ne daga bakin sa,wanda ya umarci ma’aikacin sa wato Dr. Mu’azu ya rubuto akan takarda, ya ba Mubarak Idris a kawo min)

    Domin karanta shinkafa mai ƙwai danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Yadda Za Ki Inganta Halayyarki Da Ɗabi’u Masu Kyau

    Yadda Za Ki Inganta Halayyarki Da Ɗabi’u Masu Kyau

    A matsayinki na mace kuma uwar gida (mai zaman aure); Ya kamata ki san irin halayya da ɗabi’u masu kyau da za saba da su.

    1. Ƙwarin Gwuiwa

    Zaman Aure -Idan ya kasance ba ki da ƙarfin gwuiwa akan kanki ƙarfin zuciya hakan zai sa ki zama ba kya birge mijinki. Kuma zai hana ki samun jituwa da kyautata mu’amala, ki dinga faɗawa kanki cewa ke kyakkyawa ce, kina da kyakkyawan ɗabi’u. Kuma mijinki na sonki ne saboda halayyarki masu kyau.

    2. Kula Da Kanki

    Kulawa ba wai ta wanka da kwalliya ba a a ki ɗauki al’amuran da ya shafi yadda kike ji a zuciyarki da muhimmanci, farin ciki ko baƙin ciki saboda a duk lokacin da mijinki ya ɓata miki ba zai sa alaƙarku ta lalace ba. Kuma yana da kyau ki rage ɗaurawa kanki laifi akan komai. Hakan na da wahala amma idan kina samun lokaci da ‘yan uwanki ko kawayenki ko kuma kina iya koyon wasu abubuwan sababbi, da kuma wasu abubuwan da kike son yi kamar zane, rubutu ko karance-karance.

    3. Tarayya

    Kar ki ɗau mijinki ba a bakin komai ba, ki nuna masa muhimmanci da girmansa a rayuwarki. Ki samar masa da lokaci a cikin ranakun aiki da za ki dinga tattauna abubuwan da suke faruwa da ku. Ko ki dinga tura masa saƙo ko kiran waya sau ɗaya ko sau biyu wanda zai nuna masa cewa kina tare da shi kuma kina tunaninsa a ranki.

    4. Neman Taimako

    A kan aikin gida yana da matuƙar wahala kula da miji da kuma larurar gida musamman idan kina da yara. Hakan zai sa ki gaji kuma ki kasa samun lokacin kanki. Za ki iya samun sauƙin abubuwan ta hanyoyi kamar haka: Nuna masa yadda ake aikace-aikacen gida da kula da yara, samun mai kula da yara ko kuma mai gyaran gida.

     

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Zaku Gyara Zamantakewarku Ta Aure danna nan

  • Hattara Maza

    Hattara Maza

    Wasu lokutan mukan karanta ko mu ji labaran da kan ce wani ya mutu yayin jima’i  ko yayin gasar wauta akan hakan, musamman daga wani yanki na ƙasar nan ko ƙasashen ƙetare…  har wasu cikin mu su yi ta dariya, wasu na mamaki, wasu kuma na faɗin albarkacin bakinsu.

    Toh amma a zahiri na lura da yawa ba su fahimci me ke jawo hakan ba, illa iyaka wasu kan yi amfani da slang cewa; Matar ta ƙarar da shi, ko ta fi ƙarfinsa. Iya abinda mutane kan kawo ransu kenan…. Ga layman wanda bai san komi ba shi zai tafi akan ƙila ruwan maniyyi ne mutum ya yi ta zubarwa…har ya ƙare ya kai ga duk ƙarfinsa ya tafi ƙarshe ya mutu. Amma inaaa ba haka karatun yake ba.

    Abinda ba ku sani ba ko a tsakanin mata da miji da ke auren sunna jima’i ya kai magidanta da yawa lahira ba tare da sun shirya ba. Kurum wani lokacin matan ne ba sa gane al’amarin, ko kuwa ba su san ya za su bayyana ba, ko kuma su zaɓi rufe sirrin a tsakaninsu. 

    Shi yasa wani za ka ji ana lafiya ƙalau aka rabu da mutum amma kashe gari da safe ake sanar da rasuwarsa. Amma da za ka bincika wataƙil a daren da zai mutun har kwanciya da iyalinsa ya yi. Don haka maza ku buɗe kunnuwanku da kyau, ku shiga taitayinku, ku san me yake muku ciwo.

    BAKI ƊAYA ZAN MAGANA NE AKAN WANNAN JARABAR TA TALLAN MAGUNGUNAN MAGIDANTA

    Shan Magungunan ƙara ƙarfin Jima’i walau na Hausa, Islamic chemist ko na Bature haka siddan hauka ne. Wannan maganin ba ya ƙarawa mutum jin sha’awa, shauƙi, ko daɗin jima’i. Abinda kurum yake ma shi ne miƙar da azzakari, sai kuma  kan haɗa da jinkirta muku Inzali wato Delay Ejaculation. Wato ya zamto ka jima jikin mace.

    Jimawa jikin Mace ko ba shi ne daɗin jima’i ba, Infact a lokacin an sauka ma daga ainihin dalilin jima’in, kurum yanzu kuna yi ne cikin fargabar kar iyalinku, ko farkarku ta yi ƙorafi ba ma don kuna jin daɗin al’amarin ba.

    Toh amma abinda ba ku sani ba shi ne gwargwadon yadda kuka jinkirta ba ku kawo ba.. gwargwadon matsi da takurar da kuke sanyawa zuciyarku. A yayin da mutum ke jima’i dama a lafiyayyen yanayi ma adadin bugawar zuciyar mutum na ƙaruwa wato Heart rate. 

    Normal takan buga sau 60–100bpm a duk minti yayin da ake harkokin rayuwa…. Amma yayin jima’i bugunta kan iya ƙaruwa da kaso arba’in zuwa hamsin wato 40-50% ka ga kenan bugun zuciyar mutum na iya kai wa 140-150bpm wanda gudun ba kaɗan ba ne, tana bugawa tamkar sanda abin tsoro ya rarako ka a guje kake neman tsira.

    Shi yasa ka taɓa tambayar kanka me yasa mafi yawan mutane ke mutuwa bayan jima’in?Yayin da ka sha maganin ƙara kuzarin jima’i za ka sami kanka a yanayin da kai kanka za ka ji ƙwaƙwalwarka na nusar da kai cewa ya isa haka, ba abinda kake so illa kai release amma kuma ya ƙi zuwa…

    Don haka wannan buƙatar ta ka samu ka kawo don ka huta ba za ta yiwu ba har sai ka ƙarawa zuciyarka matsi wato stress akan matsin da already cikinsa take dalilin maganin da ka sha. Stress kan stress kenan… Dole sai ka sa ta ta yi aiki ɗoriya akan wanda ya wuce wanda take yi…. Toh ka ga a yanayin ne sai dai a ji zuciyar ta tsaya cak wato CARDIAC ARREST.

    Sai dai a ce Allah ya ji ƙanka kurum, da safe aiki ya ga makwabta na shirye-shiryen zuwa jana’izarka, kuma wallahi. Wanda kuma zuciyar ta ɗauke pressure ɗin toh shi kuma wajen inzali yake haɗuwa da massive stroke, jijiyar jini cikin kwanyarsa ta fashe.

    Don haka ba zancen dole sai ka birge mace, nutsu ka san me kake ciki.

    Gara ta kira ka da duk sunan da za ta kira ka, kar ka ji ƙasƙanci, minti 2, minti 3 ya wadatar. Ba gasar cin kofin Olympics ba ne da za ka nuna bajintar burge mutane, wannan abu ne daga kai sai ita, ko awa 2 kake babu wanda ya sani, ba kuma me buƙatar ya sani, amma ran da ka mutu a sama kowa sai ya ji.

    Sannan ɗoriya akan haka musamman ga wanda suke sama da shekara 50 ina gargadinku da kar ku kuskura ku ce wai ku sai kun birge mace da har za ku je kuna ɗebe-ɗebe musamman yadda hawan jinin nan ya lalata mutane da yawa, za ku haɗu da mummunan bugun zuciya.

    Ko matar da ka je ka hallaka kanka a kanta wallahi daga baya wani za ta je ta aura, in ma kai sa’a dama kai kaɗai ɗin ta tsarewa mutuncinta kenan tun kana raye. Don haka ku yi nazari kan wannan.

    Don karanta rashin jini a jiki danna nan

    ABIN DA BA KWA LURA 

    Mafi yawan mata daga cikin mu nan  gamsuwar su ba a tsawon lokacin da ka ɗauka jikinmu ba ne, Eh kana iya jimawa mu ji daɗi amma ba ta hanyar shan magunguna ba, kwai hanyoyi da yawa da za ka jima ba lallai Sai ka sha magani ba, ku lura da ita, ka saurare ta, ka laƙanci duk wani sashi da take da rauni in ka taɓa ta ta nan, da haka za ka birge ta, ka yi tsafta, ka iya magana, ya zamto ana haɗa gado wajen bacci ba lallai sai yayin da ake buƙatar juna ba, banda fushi, banda ƙullata a rai, duk sanda ake da matsala a tattauna kar ku ɓoye alhalin a ranku kuna jin haushin juna, in kuka kiyaye wannan ba ku da matsala.

    Uwa uba wani raunin azzakarin daga hormone ɗinsa ne, don haka hormone replacement therapy yake buƙata ya magance matsalar sa in ma gaban ne bai miƙewa da sauransu, wani ciwon suga gare shi ya lalata nerves da blood supply na mararsa… Shi yasa ba ya iya jima’i…ka ɗebi wannan shirmen magungunan ka ba shi ba dole ya mutu ba dama ga zuciyarsa kullum danƙare da sigar.

    In kana da matsala tafi asibiti likita ya ganka ya duba ka ya ba ka maganin da ya dace shi ne zaman lafiya, amma kiyaye zuwa Chemist da ka, ko wajen masu maganin gargajiya ko Islamic chemist, Ku kiyayi kanku tun kafin zuciyarku ta zamo WEAK ku mutu a banza.

    Allah yasa mu dace. A yi hattara.

    Danna nan don karanta mata ku ba ni kunnenku

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Ra’ayin Wani Masani Game Da Tasirin Bincike A Rubutu

    Ra’ayin Wani Masani Game Da Tasirin Bincike A Rubutu

    Wani masani na cewa zuzzurfan bincike ba shi ne abinda ke samar da kyakkyawan littafi ba. Hanyar da ka bi wajen sa binciken naka a littafi shi ne muhimmin abu. A nan akwai wasu abubuwa da ya dace mu kula da su.

    1) Ba kowanne irin sakamakon bincike ake sa wa a rubutu ba. Wani abin rashin bayyana shi ya fi zama maslaha fiye da bayyanawa.

    Lokacin da Bala Anas ke bincike kan littafin Zinaru na ‘yan Kano to Jidda, ya ci karo da wani labari mai tayar da hankali. Akwai wasu ‘yan daba da ake cewa ‘yan agulla da ke zaune a Jidda. Su har maza suke yi wa fyade. Yaranmu ne da aka haifa a can suka taso ba kulawa. Da gangan ya ƙi kawo labarinsu.

    Ko a kwanakin nan mun je bincike hukumar NDLEA sun faɗa mana yadda ake haɗa alawar Tom Tom da wasu lemuka ana cakewa. To ka ga ba za ka saka irin wannan a labari ba, don wani sai ya koya.

    2) Ko da ka tara sakamakon binciken naka, idan ka ce za ka zuba shi haka zai iya gundurar mai karatu.
    Akwai hikimar da za ka yi. Sai ka raba bayanin a ɓangare daban daban na cikin labarin. Irin yadda Amira Souley ta yi a cikin littafinta na kallo ya koma sama. Hirar da ta gudana tsakanin ma’aurata kan abinda ya shafi zuciya da ƙwaƙwalwa.

    Danna nan don karanta amfanin bincike a rubutu

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Bikin Karrama Gwarazan Gasar Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano

    Bikin Karrama Gwarazan Gasar Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano

    Hukumar tace fina-finai da ɗab’i ta jihar Kano ta ayyana Zubairu Musa Balannaji a matsayin wanda ya zo na farko a gasar gajerun labarai ta shekarar 2024.

    Da take bayyana sakamakon gasar a ɗakin taro na Malam Aminu Kano da ke Mambayya, Farfesa Halima Abdulƙadir Ɗangambo wanda Shugaban kwamitin gasar ya bayyana a madadin ta ya bayyana labarin Bahaushiyar Al’ada wanda marubuci Zubairu Musa Balannaji ya rubuta a matsayin wanda ya yi nasara Kuma ya zama na farko cikin labarai 50 da suka fafata a cikin gasar.

    Haka kuma, ya bayyana labarin gadon gida saida Horo wanda Danladi Haruna (Zakariyya) ya rubuta a matsayin wanda ya zo na biyu, Sai labarin Hauwa Shehu Mai taken Bahaushe Mai arziƙi ne a matsayin wanda ya zo na Uku cikin labarai 50 da suka fafata a gasar.

    Dubban marubuta, da mawaka, da taurarin fim ne suka halarci taron, yayin da mawaƙa da dama suka nishaɗantar da taron da waƙoƙin masu sanyaya rai.

    A nashi jawabin shugaban hukumar Abba El-mustapha ya bayyana farin cikinsa kan yadda gasar ta gudana tare da taya wanda suka yi nasara murna. Ya yi fatan alhairi ga mahalarta taron tare da addu’ar Allah ya bar zumunci ya sa kowa ya koma gida lafiya. Haka nan shugaban hukumar ya ayyana 31 ga watan Disambar kowacce shekara a matsayin ranar marubutan jihar kano, ko bayan ya bar kan kujerar shi.

    Hukumar ta ba wa wanda ya zo na farko kyautar Naira dubu ɗari biyar sai na biyu Naira dubu ɗari uku a yayin da ta uku ta samu kyautar Naira dubu ɗari biyu.

    Don karanta manufar rayuwar duniya danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Sha’iri Aliyu Sani (na annabi) Kudan

    Tarihin Sha’iri Aliyu Sani (na annabi) Kudan

    An haifi Aliyu Sani a garin Kudan kuka wanda aka fi sani da suna “na annabi”  a ranar talata 12/4/1982, ya taso a cikin garin Kudan, ya yi karatun firamare da sakandire duk a garin Kudan, sannan kuma ya yi karatun allo a Zaria, bayan ya yi sauka, sai ya wuce makarantar koyar sana’o’i  wacce take birnin gwari  a Dogon dawa a cikin  jihar Kaduna, wacce take koyar da ilimin noma da kiwon dabbobi (Agric Training School). A yanzu kuma yana aiki a hukumar Kastelea ta jihar Kaduna.

    Dalilin da ya sa ya fara bege shi ne, wata rana a makarantar allo yana bacci, sai ya yi mafarki an tara masa mutane da yawa sai aka ba shi amsakuwwa (lasafika) yana rera waƙa, amma kuma ba zai iya tuna irin waƙar da yake rerawa ba, bayan ya farka daga baccin, sai ya roki Allah ya cika masa burin sa, aiko Allah ya amsa muradin sa, saboda ya rera bege da yawa daga cikin su akwai ;

    1.Na riƙe Mustafa annabi Ɗaha.

    2.Lale-lale mauludi.

    3.Ni dai gaskiya  ina ƙaunar manzo.

    4.Mai daraja da muƙami.

    5.Almukhtari.

    6.Almadani.

    7.Ba zan bari ba.

    8.Oyo-oyo maulidi ya zo.

    9.Mu muna son manzonmu.

    10. Maulidin annabi sai mun yi.

    11.Marhaba ɗan Amina shugaba.

    12. Ya Muhammadu shugaba na.

    13. Rasulu bege a gunka soyayya ce.

    14. Azzahara’u ‘yar ma’aiki.

    15. Halin rayuwa.

    16. Mu yi nazari.

    17. Mai ilimi.

    A ƙarshe kuma, ya yi aure yana da mata guda ɗaya da ‘ya’ya guda huɗu.

    (Mun samu wannan bayanin ne daga Aliyu Sani na annabi Kudan, wanda ya turo min ta waya ta  a ranar Alhamis 17/06/2020 da misalin ƙarfe 6;33 na dare).

    Danna nan don karanta tarihin marigayiya Hajiya Gude

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

  • Tarihin Salman Khan Salim

    Tarihin Salman Khan Salim

    An haifi Abdurrashid Salim, wato Salman Khan a ranar 27 ga watan Disamba ta shekara 1965, a garin  Mumbai, sannan kuma ɗa ne ga fitaccen marubucin nan wato Salim Khan, wanda ya yi shura sosai  a fina-fina na shekarun baya, kamar Sholay (1975), Deewaar (1975), da Don (1978).

    Haka kuma,sunan mahaifiyarsa  furodusa fim Sushila Charak (wacce  aka fi sani da Salma Khan), kuma sau da yawa yana ba da labarinta a cikin hirarrakinsa.

    Salman Khan shi ne babba a cikin ‘ya’yan da mahaifinsa ya haifa guda biyar, daga cikinsu akwai  Sohail Khan da Arbaaz Khan, waɗanda su ma ‘yan wasa ne kuma mashirya fina-finan Indiya (Producer), sai kuma ‘yan uwansa mata guda biyu, wato Alvira Agnihotri Khan, wacce ta kasance mai shirya fina-finai kuma mai tsara kayan sa wa a cikin fina-finan Indiya, da kuma Arpita Khan Sharma, mai zanen cikin gida a cikin fina-finan Indiya.

    Salman Khan ya fara aikin wasan kwaikwayo ne ta hanyar yin rawa a cikin fim ɗin “Biwi Ho To Aisi” (1988). Har ila yau, ya samu  babban matsayi a cikin  ofishin romantic hit Maine Pyar Kiya (1989). Daga nan ne ya zama mai son kallon fina-finan Indiya.

    Salman Khan ɗan wasan Indiya ne, mai shirya fina-finai, kuma mai watsa shirye-shiryen talabijin, wanda fitattun ayyukansa da kuma fitattun jarumai gami da farin jini a wajen  jama’a, suka ba shi matsayin zama megastar a Bollywood.

    A cikin shekarun da suka wuce, ya zama wani yanki mai ban sha’awa na al’adun gargajiya a Indiya. Salman Khan, wanda ya fara a matsayin abin koyi kuma jarumi a ƙarshen shekarun 1980, ya fito a fina-finai sama da 100.

    Har ila yau, Salman Khan yana alfahari da sana’arsa, wanda  ya shafe kusan shekaru arba’in a cikinta. Ya yi shura da jarumai kamar su Shah Rukh Khan da Aamir Khan, Salman Khan yana ɗaya daga cikin jaruman maza uku da suka samu nasara a harkar fina-finai ta Bollywood tun daga shekarar 1990. Sannan kuma magoya bayansa, suna mutuƙar ƙauna gami da alfahari da shi, har sai suka sanya masu suna da  “Bhai” (Hindi: “Brother”) ko Bhaijaan (adireshin girmamawa da nuna ƙauna ga “ɗan uwa” a harshen Urdu).

    Bugu da ƙari kuma, Salman Khan ya yi shura a cikin fina-finai guda goma sha biyu, waɗanda suka shahara a ƙasar Indiya (ko a duniya baki ɗaya). Kamar su; Maine Pyar Kiya, Andaz Apna Apna, Hum Aapke Hain Koun..!, Hum Saath-Saath Hain, da Prem Ratan Dhan Payo.

    Khan ya yi aiki a matsayin abin koyi ga  kayayyakin talla irin su Limca (abin sha mai laushi), kafin ya sauko da rawar fim ɗinsa na farko, a cikin Biwi Ho To Aisi (“Matar ya kamata ta kasance kamar wannan”), a cikin 1988. Matsayinsa ya fara shahara ne tun daga  1989, wanda a cikin Fim ɗin soyayya nan “Maine Pyar Kiya” (“I have Loved”), wanda ya yi nasara a soyayyarsa, ya samu  kyautar Filmfare a matsayin mafi kyawun fitowar maza.

    Sunansa a cikin fim ɗin, Prem (“Love”), ya zama wani abu mai ban sha’awa a gare shi, kuma ya buga haruffa da wannan sunan a cikin fina-finai na gaba. Waƙoƙin Maine Pyar Kiya, irin su “Kabootar Ja Ja Ja” (“Fly Away, Pigeon!”), “Dil Deewana” (“Crazy Heart”), da “Mere Rang Mein Rangne Wali” (“Wanda Yake) Coloured in My Colours”), su ma sun kasance manyan ginshiƙai tare da masu sauraro kuma ana ci gaba da lissafa su a matsayin wasu fitattun waƙoƙin soyayya daga fim din Khan.

    Duk da yabon da ya samu na rawar da ya taka a fim ɗin “Maine Pyar Kiya”, aikin Khan ya ci gaba da riƙe kambunsa har zuwa fitowar fim ɗin “Hum Aapke Hain Koun” a 1994! (HAHK; “Wane ni a gare ku?”). Acikin fim ɗin ya fito ne a matsayin  Prem Nath, wanda ya kasance yaro mai fara’a, rashin laifi, iya  soyayya ga Nisha Choudhury, wanda hakan ya sa ya mamaye zukatan miliyoyin mutane da sauri.

    Har ila yau, kimiyyar sinadarai na Khan da Dixit ta kasance cikakkiyar abin farin ciki ga jama’a, kuma fim ɗin ya zama babban matsayi a wannan shekarar. A cewar mai bin diddigin kasuwancin fim Box Office India, HAHK ya zama fim ɗin Hindi da ya fi samun kuɗi a kowane lokaci, inda ya karya tarihin shekaru 19 da Bollywood classic Sholay (1975; “Embers”) ta yi.

    Ana la’akari da shi ɗaya daga cikin abubuwan da aka tsara na Bollywood da ingantaccen wasan kwaikwayo na iyali. HAHK ya riƙe rikodin akwatin ofishin har zuwa 2001, lokacin da Gadar: Ek Prem Katha (“Tawaye: Labarin Soyayya”) ya sauke shi, wanda jarumi Sunny Deol ya fito. Khan ya yi amfani da nasarar HAHK don ɗaukar sabbin ayyuka iri-iri daban-daban,don ganin ya riƙe kambunsa.

    Bugu da ƙari kuma, daga kan 1994-2010: Salman Khan  ya fito a cikin wasan barkwanci kamar Andaz Apna Apna (1994; “Kowa yana da nasa salon”) da babu shiga (2005); rawar da ya taka a fim ɗin  “Karan Arjun” (1995); da kuma soyayya, irin su fim ɗin “Kuch Kuch Hota Hai” (1998; “Wani abu ya faru”), wanda hakan ya ba shi damar lashe kyautar Filmfare Award, don jarumta da ya nuna a cikin fim ɗin, sai kuma fim ɗin  “Hum Dil De Chuke Sanam” (1999; ” madaidaiciyar zuciya”), Hum Saath-Saath Hain (1999; “We Stand United”), da Tere Naam (2003; “A cikin Sunan ku”).

    A shekarar 1999 fina-finan Khan guda uku ne suka shiga cikin fina-finan da suka fi samun kuɗi a Bollywood a waccan shekarun su ne; Hum Saath-Saath Hain, Biwi No. 1 (“Mace No. 1”), da Hum Dil De Chuke Sanam.

    Har ila yau, aikin Salman Khan ya samu karɓuwa sosai a shekarar 2009 ta fim ɗin Wanted, wanda har sai da ya kafa tarihi a duniyar Bollywood. A cikin 2010 Khan ya samu rawar tauraruwar Chulbul (“Robin Hood”) Pandey, ɗan sanda mafi girma fiye da rayuwa, a cikin blockbuster Dabangg (“Fearless”). Fim ɗin ya ƙayatar sosai gami da nishaɗantarwa,fim ɗin ya ɗauki hankulan masu kallo. A wannan lokacin, shahararsa ta sake bayyana a idon duniya sosai fiye da baya.

    A shekara ta 2012 jarumin ya sake mayar da matsayinsa na Chulbul Pandey a cikin Dabangg 2, wanda kuma ya kasance blockbuster. A shekarar 2019 ya dawo fagen kasuwanci tare da Dabangg 3. Fina-finan Tiger guda biyu na farko na Khan—Ek Tha Tiger (2012; “There Once Was a Tiger”) da Tiger Zinda Hai (2017; “Tiger Is Alive”)—wanda Khan ya taka Avinash Singh Rathore, jami’in leƙen asirin Indiya, sun yi nasara sosai.

    Don karanta yadda za a gabatar da aiki mafi muhuimmanci danna nan

    Tiger Zinda Hai ya karya tarihin daga cikin fina-finan Hindi da suka fi samun kuɗin shiga a kowane lokaci, inda ya ci gaba da lashe fim ɗin da ya fi ɗaukar hankali a Filmfare Awards. An saita ikon amfani da Tiger a cikin duniyar ɗan leƙen asiri , wanda kamfanin samarwa Yash Raj Films ya ƙirƙira.

    Salman ya kammala karatunsa a St. Stanislaus High School da ke Bandra, Mumbai, kamar yadda ƙaninsa Arbaaz da Sohail suka yi. Tun da farko, ya yi karatu a The Scindia School, Gwalior na wasu shekaru tare da ƙaninsa Arbaaz. Ya halarci Kwalejin Elphinstone kuma ya fita bayan shekara ta biyu.

    Abubuwa 10 masu ban sha’awa game da Salman Khan

    1. Jaruman da ya fi so su ne Sylvester Stallone & Hema Malini.

    2. Yana son tafiya Landan.

    3. Yana da tarin motoci kuma yana sha’awar tuƙin BMW, Mercedes-Benz da Land Cruiser.

    4. Salman yana son abincin ƙasar China kuma lambun China da ke Mumbai an ce shi ne abincin da ya fi so.

    5. Yawanci ya fi son saka  jeans kuma yana sanye da abin hannu na dutse turquoise a ciki da waje.

    6. Jarumin ya fi sha’awar tara sabulai iri-iri a banɗakinsa na gida, musamman sabulun da ke ɗauke da ‘ya’yan itatuwa da kayan marmari.

    7. Yana gudanar da wata ƙungiya mai suna “Being Human”.

    8. Jarumi ne mai son ganin ya nishaɗantar da mutane.

    9. Zai iya zama ƙwararren ɗan wasan linƙaya. Ya kasance zakaran linƙaya a makaranta har ma an sa shi a matsayin wanda yake wakiltar Indiya, don taron linƙaya.

    10. Baya ga wasan kwaikwayo, ya kuma gwada sauran  basirarsa a Bollywood: rubutu na Baaghi, kamar su ; A Rebel for Love, Chandra Mukhi and Veer. Sannan kuma mai gabatarwa a cikin Chillar Party, Jarumi kuma Dr Cabbie; Singer in Hello Brother, Chal Mere Bhai, Yuvaraj.

    Lambobin girmamawa da Salman Khan ya samu

    Salman Khan, ya samu lambobin girmamawa da yawa a cikin sana’arsa, ga wasu daga cikin nan;

    A. Filmfare Award

    1.  Salman Khan ya lashe jarumi  mafi kowa ƙwazo a ɓangaran maza a fim ɗin “Maine Pyar Kiya” ta 1990.

    2. Salman Khan ya lashe jarumi  mafi himma a fim ɗin “Kuch Kuch Hota Hai” ta 1999.

    B. Nomination for Filmfare Award

    1. Salman Khan  ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Mene Pyar Kya” ta 1990.

    2. Salman Khan ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Karan Arjun” ta 1996.

    3. Salman Khan ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Jeet” ta  1997.

    4. Salman Khan ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin ” Pyar Kya To Darna kya” ta 1999.

    5. Salman Khan ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Hum Dil De chuke Sanam” ta 2000.

    6. Salman Khan ya lashe jarumin barkwanci  mafi kowa ƙwazo a fim ɗin ” Bwi No. 1″ ta  2000.

    7. Salman Khan ya lashe jarumi mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Tere Naam”  ta  2004.

    8. Salman Khan  ya lashe jarumin mafi kowa ƙwazo a fim ɗin ” Baghban” ta 2004.

    9. Salman Khan   ya lashe jarumin barkwanci mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “No Entery” ta  2006.

    10. Salman Khan  ya lashe jarumin barkwanci mafi kowa ƙwazo a fim ɗin “Dabangg” ta 2011.

    C. Zee Cine Award

    1. Salman Khan an zaɓe shi a matsayin jarumi  mafi kowa ƙwazo a ɓangaren maza,wanda ya samu kyautar “Zee Cine Award”  a fim ɗin “Tere Naam” ta 2004.

    2. Salman Khan   an zaɓe shi a matsayin jarumi mafi kowa ƙwazo a ɓangaren maza, wanda ya samu kyautar “Zee Cine Award”  a fim ɗin  “Mujhse Shaadi Karogi” ta 2005.

    3. Salman Khan an zaɓe shi a matsayin jarumi mafi ƙwazo a ɓangaren maza, wanda ya samu kyautar “Zee Cine Award”  a fim ɗin “Entry” ta 2006.

    4. Salman Khan an zaɓe shi a matsayin jarumi mafi ƙwazo a ɓangaren maza, wanda ya samu kyautar “Zee Cine Award” a fim ɗin ” Dabangg” ta  2011.

    D. Star Screen Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar “Stardust Award”, a matsayin jarumi mafi ƙwarzon shekara na ɓangaren maza a fim ɗin “Dabangg” ta 2011.

    E. Nomination

    1. Salman Khan an zaɓe shi a matsayin wanda ya lashe kyautar “Star Screen Award” ɓangaren jaruma na fim ɗin “Tere Naam”  ta 2004.

    2. Salman Khan an zaɓe shi a matsayin wanda ya samu kyautar “Star Screen Award”  a fim ɗin “Pride and Honour”  ta  2005.

    F. Bollywood Movie Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar mai taken ” Most Sensational Actor”, a fim ɗin “Chori Chori Chupke Chupke”  ta 2002.

    G. International Indian Film Academy Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar IIFA a matsayin “Habitat Humanity Ambassadorship”  ta 2010.

    H. Stardust Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar “Stardust Award” a matsayin gwarzon shekara na ɓangaren maza a fim ɗin “Dabangg” ta  2011.

    I. Big Star Entertainment Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar “Most Entertaining Film Actor Award” a fim ɗin “Dabangg” ta 2010.

    J. Indian Television Award

    1. Salman Khan ya lashe kyautar “Best Anchor”, a fim ɗin “Ka Dum” ta 2008 (Zagaye na farko).

    2. Salman Khan ya lashe kyautar “Best Anchor” a fim ɗin “Ka Dum” ta  2008 (zagaye na biyu).

    Danna nan don karanta waƙar bikin ƙaddamar da manhajar WikiHausa

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

  • Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma

    Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma

    Mai Huɗuba:
    Sheikh Dr Saleh Bin Abdullahi Bin Humaid

    Mai Fassara:
    Dr Abdullahi Yunusa Machina

    Shugaban Sashi
    Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Huɗubar Masallaci Mai Alfarma
    Mai Girma Sheikh Salih Bin Humaid 26/06/1446H
    Yekuwar jahiliyya ce, ku bar ta, domin ita abar ƙyama ce

    HUƊUBA TA FARKO
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Ya kaɗaita da halitta da jujjuya al’amura, (Yanzu wanda ya yi halitta ba zai san ta ba, Alhali Shi ne mai tausasawa Masani?) (Suratul Mulk: 14).

    Ina gode masa, tsarki ya tabbata a gare Shi, Ya bayar da yawa, Ya nemi kaɗan.
    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba shi da abokin tarayya, shaidawar da ke tseratarwa daga azabar wuta.

    Kuma ina shaidawa lallai shugabammu kuma Annabin mu Muhammadu bawan Allah ne kuma manzonsa, mai bushara da kuma gargaɗi, kuma fitila mai haskakawa, tsira da aminci da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa waɗanda suka kasance mataimaka kuma mashawarta na ƙwarai ga Annabinsu, da tabi’ai da waɗanda suka biyo su da kyautatawa, kuma Ya yi daɗin sallama mai yawa a gare su.

    Bayan haka, Ya ku mutane! Ina mana wasiyya da jin tsoron Allah, saboda haka, ku ji tsoron Allah, Allah Ya muku rahama, kuma ku sai sani cewa lallai mu’amalantar masoyi da tausasawa tana dawwamar da ƙauna, ga baƙo kuma tana haifar da soyayya, ga maƙiya kuma tana tunkuɗe sharri, ga mai fushi kuma, tana kashe wutar fushi.

    Mafiya daraja cikin mutane su ne mafiya saurin nuna ƙauna, mafiya jinkiri wajen nuna ƙyama. Amma marasa daraja cikin mutane, su ne mafiya jinkiri wajen nuna ƙauna mafiya gaggawa wajen bayyana adawa. Kuma ana rigegeniyar samun kusanci da Allah ne da zuciya da kuma ayyuka, ba da ababen hawa ko ƙafafu ba. (Ranar da dukiya ko ƴaƴa ba sa amfani, sai wanda ya zo wa Allah da lafiyayyar zuciya (Suratush-Shu’ara: 88-89).

    Ya ku Musulmi!
    Akwai wata cuta mai hatsari cikin zamantakewa, wacce ke gadar da ƙiyayya, take haifar da gaba, take tarwatsa alaƙoƙi, take dasa ƙiyayya a zukata, take rarraba kawuman jama’a, take barazana ga zaman lafiya, take yaɗa yanke zumunta. Cuta ce abar ƙyama, wacce ke gina katangar ƙarfe tsakanin wanda aka jarabe shi da ita da sauran mutane, take hana fahimtar juna, take rufe ƙofar tattaunawa, take sa mutum yin hukunci na gama-gari, take sanya shi ya raina masu saɓawa ra’ayinsa, wannan cuta ita ce cutar ta’assubanci da ƙabilanci.

    Ya ku bayin Allah!
    Ta’assubanci cuta ne mai fatattakawa, shi ne sababin duk wani bala’i, kuma daƙushewar ƙwaƙwalwa ne da toshewar basira, yana makantarwa daga ganin gaskiya, kuma yana katangewa daga bin shiriya, yana ingiza faɗace-faɗace, kuma yana jawo yaƙe-yaƙe, yana rura wutar jayayya, kuma yana tsawaita saɓani.

    Ta’assubanci tsauri ne, kuma nisantarwa ne, Ta’assubanci yana jawo ɓoye gaskiya da lulluɓe ta, saboda ma’abocinsa yana ganin cewa gaskiyar, hujja ce ga abokin saɓaninsa. Ta’assubanci yana rage damar isa zuwa ga ingantacciyar mafita, kuma yana yaɗa zalunci da danne haƙƙoƙi, yana raunata al’umma kuma yana yaɗa fitintinu da yaƙe-yaƙen cikin gida.

    Ta’assubanci wuce iyaka ne game da mutane, da gidaje, da mazhabobi, da al’umma, da ƙabila, da gari, da ra’ayi, da al’ada, da kafafen yaɗa labarai, da wasanni, da dukkan wani lamari na zamantakewa.

    Ya ku Musulmi!
    Ku yi duba cikin wannan miƙaƙƙiyar matsaya ta Annabi, haƙiƙa Imamu Muslim ya rawaito a Sahihinsa, daga Hadisin Jabir ɗan Abdullahi Allah Ya ƙara musu yarda, ya ce: Mun kasance tare da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai wani mutum cikin Muhajirai ya bigi wani mutum cikin Ansarawa, sai Ba’ansaren nan ya ce: Ya ku Ansarawa ku taimake ni. Sai shi ma Almahajirin ya ce: Ya ku Muhajirai ku taimake ni, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Me ya sa ake irin wannan yekuwar jahiliyya?” Sannan sai ya ce: “Ku bar ta saboda ita abar kyama ce”. Allahu Akbar!

    Ya ku bayin Allah!
    Hijira da taimako sifofi ne biyu masu daraja, Muhajirai da Ansarawa kuma su ne mutanen farko ‘yan gaba-gaba, Allah Ya ƙara musu yarda. Amma lokacin da waɗannan mutane biyu suka nufi amfani da waɗannan laƙubba masu daraja kuma siffofi masu girma wajen ƙabilanci, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya zabura ya yi gaggawan shawo kan wannan matsaya da faɗinsa: “Yanzu yekuwa irin ta jahiliyya kuke yi?”.

    Wato lallai matsayin Hijira da darajar taimako sun koma siffofin zargi saboda ƙabilanci, bari dai, sun ma zama hanya abar ƙyama abar ƙi, kuma sun zama yekuwa irin ta jahiliyya: (Ku bar ta saboda ita abar ƙyama ce), babu inkari da ya kai wannan siffa tsanani, kuma babu zargi da ya kai wannan siffa girma.

    Ya zo a Hadisi ingantacce daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa: “Duk wanda ya yaƙi mutane a ƙarƙashin makauniyar tuta, yana fushi don ƙabilanci, ko yana kira zuwa ga ƙabilanci, ko yana taimakon ƙabilanci, sai aka kashe shi, to, ya mutu irin mutuwar jahiliyya”. A wani lafazi, “Ba ya cikin al’umma ta”. Muslim ne ya rawaito.

    Ku saurari wannan kalma mai hikima daga ma’abocin hikima Amru ɗan Aas Allah Ya ƙara masa yarda, an tambaye shi: Me ya sa ka yi jinkirin shiga Musulunci alhali kai mutum ne mai kaifin hankali? Sai ya ce: Lallai mu mun kasance muna tare da wasu mutane da suka fi mu shekaru, hankulansu sun kai duwatsu tabbatuwa, ba su taɓa bin wata hanya ba, da muka bi bayansu a cikinta, face mun same ta mai sauƙi.

    Amma yayin da suka ƙaryata Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai muka ƙaryata shi tare da su, kuma ba mu yi tunani cikin lamarinmu ba, sai muka girmama su, amma yayin da suka shuɗe, lamari ya dawo gare mu, sai muka yi duba cikin lamarin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, muka yi tunani game da shi, sai ga shi lamari ne bayyananne, sai Musulunci ya ɗarsu a zuciya ta”. Allah Ya kiyaye ku!

    Tabbas babu abin da zai katange gaskiya sai ta’assubanci, da makauniyar biyayya ga iyaye da kakanni, (Yayin da waɗanda suka kafirta suka sanya kishi irin kishin jahiliyya a cikin zukatansu) Alfath: 26, (Lallai mu mun sami iyayenmu a kan wani addini, kuma lallai mu hanyarsu muke kwaikwayo (23) Ya ce da su: Yanzu ko da na zo muku da abin da ya fi zama shiriya a kan abin da kuka sami iyayenku a kansa?” Suka ce: Lallai mu masu kafircewa abin da aka aiko ku da shi ne). Azzukhruf: 23-24.

    Ya ku taron Musulmi!
    Daga cikin siffofin mai tsananin ta’assubanci a ra’ayi da daskarewar tunani, da karkata zuwa ga kausasa wa abokin saɓani akwai cewa: Shi mai ta’assubanci yana raya cewa shi ne a kan gaskiya, da hujja ko babu hujja, kuma duk wanda ya saɓa masa, to, a kan ɓata yake, yana da hujja ko ba shi da ita, mai ƙabilanci ba ya gani sai abin da yake so ya gani.

    Mai ta’assubanci yana rarrabe mutane kuma yana ƙimanta su bisa dangance-dangancensu na addini, da na ƙabila, da yanki da mazhaba da ƙungiya da siyasa. Mai ta’assubanci yana jingina kura-kuransa da aibukansa ga wasu, mai ta’assubanci yana gane gaskiya ne ta hanyar mutane, amma ba ya gane mutane ta hanyar gaskiya.

    Mai ta’assubanci ba ya so gaskiya ta kasance tare da ɓangaren da ba nasa ba, domin shi ya taƙaita ne da ra’ayoyinsa da kuma ƙuntataccen hangen nesansa, damuwarsa ita ce gardama da kuma ɗaga kai bisa sauran abokanansa.

    Ya ku ‘yan uwa!
    A cikin yanayin ta’assubanci, murya tana ɗagawa, ana musayar zargi, za ka ga hakan a bayyane a cikin tarurrukan mutane da dandulansu da wajen haɗuwarsu da tattaunawar su a kafafen watsa labarai da hanyoyin sadarwa, ba tare da mutunta tsarin tattaunawa ko lura da dokokin ɗabi’a da bin tafarkin hikima da ladabi ba.

    Kuma an tabbatar da cewa wannan ba zai taɓa zama hanyar da ta dace don warware matsaloli ko haɗuwar zukata ko haɗin kai ba, kuma ba za a iya cimma kyawawan manufofi ta wannan hanyar ba.

    Ya ku ‘yan uwa a tafarkin Allah!
    Mutum ba a haifarsa da ta’assubanci, sai dai yana koyan ta’assubanci ne daga danginsa da abokansa da makarantarsa da kuma yanayin da yake ciki. Daga nan! Za mu gane cewa domin magance matsalar ta’assubanci to, dole ne a tabbatar da daidaito tsakanin mutane tare da yaɗa al’adun tattaunawa da zaman lafiya da karɓar ra’ayi daban-daban da ƙauna da neman uzuri da yin alheri ga wanda ka sani da ma wanda ba ka sani ba.

    Da izinin Allah, abubuwan da za su kare mutum daga ta’assubanci sun haɗa da: Ƙudurcewa ta gaskiya da kuma yaƙinin cewa babu abin da ya ke da kariya daga kuskure sai Littafin Allah, kuma babu wani mutum da ke da kariya daga zunubi sai Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

    Sai kuma kallon malamai da dattawa a matsayin masu nuni zuwa ga gaskiya, masu isar da saƙon Allah gwargwadon ijtihadinsu da iyawarsu, ba su da kariya daga kuskure, kuma ba su tsira daga yin kuskure da yin ba daidai ba.

    Allah Ya kare ku!
    Daga cikin hanyoyin guje wa ta’assubanci akwai ƙarfin zuciya da niyya ta gaskiya wajen watsi da al’adun da ba su dace ba da kuma ɗabi’un da suke nesa da gaskiya da adalci.
    Dukkan wannan, nauyi ne da ke kan ma’abota ilimi da falala da nagarta da alfarma da masu kula da tarbiyya, da kuma waɗanda suke da kishin al’umma da yin ƙoƙari tuƙuru don gina mutum cikakke da yaɗa nagarta da gyara da kuma yaƙar ɓarna da dukkan nau’ikanta, Kuma kafin komai ma, wajibi ne a samu tsarkin niyya da kyawun zuciya da kaucewa son rinjaye, da cin nasara, da tsere wa fitinar neman yabo da muƙamai, da kuma yaɗa soyayya a cikin gida da makaranta da kasuwa da kafofin yaɗa labarai ta dukkan hanyoyinsa.

    Da tsarkakar zuciya daga hassada da kuma kuɓuta daga sonkai. Wannan duk yana tattare cikin kalmar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi mai cike da ma’ana: (Imanin ɗayanku baya cika har sai ya so wa ɗan uwansa abin da yake so wa kansa). Auzu billahi minash shaiɗanir rajim.

    (Kuma aboki ba ya tambayar aboki []Alhali kuma ana nuna musu junansu, mai laifi ya riƙa buri ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ƴaƴansa[] Da matarsa da ɗan uwansa[] da danginsa waɗanda suke kare shi[] dama duk wanda yake a bayan ƙasa baki ɗaya, sannan fansar ta tserar da shi) (Suratul Ma’arij: 10-15)

    Allah Ya amfanar da mu da shiriyar LittafinSa, da sunnar AnnabinSa Muhammadu -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da sauran Musulmi daga kowanne zunubi da kuskure. Saboda haka, ku nemi gafararSa, domin Shi ne Mai gafara, Mai jin ƙai.

    Danna nan don karanta rayuwa

    HUƊUBA TA BIYU
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda ya ɗaga sama ba tare da ginshiƙi ba, kuma ya tabbatar da ƙasa da turaku. Ina gode masa tsarki ya tabbata a gare Shi. Ni’imominSa sun fi ƙarfin iyakancewa da kuma ƙidayawa.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, shaidawa ta gaskiya da yaƙini wanda nake adana ta domin ranar lahira, kuma ina shaidawa lallai shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu bawan Allah ne kuma ManzonSa wanda ya ɗaga tutar addini kuma ya yi jihadi matuƙa a kan tafarkin Allah.

    Allah Ya yi daɗin tsira da aminci da albarka gare shi da Alayensa da Sahabbansa masu nagarta da ɗaukaka, da Tabi’ai da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa ranar ƙarshe. Bayan haka,

    Ya ku Musulmi!
    Ma’abota ilimi suna cewa: Duk wanda ya riƙe wani mutum ko ma wane ne, sai ya ɗauke shi a matsayin ma’aunin soyayyarsa da ƙiyayyarsa cikin furuci da aiki, to, yana daga cikin waɗanda suka rarrabe Addininsu suka kasance ƙungiya-ƙungiya, kowace ƙungiya suna fahari da abin da ke tare da su.

    Suka ƙara da cewa: Kuma wannan hanya ce ta ma’abota bidi’a da son zuciya ababen zargi, duk wanda ya yi ta’assubanci ga wani ayyananne, to, akwai shubuhar cewa shi ma yana cikinsu. Dukkan wani abu da ya kauce wa da’awar musulunci da Alƙur’ani na dangantaka, ko gari, ko jinsi, ko mazhaba, ko wata ɗariƙa, to, shi yana daga dangogin jahiliyya.

    “Kuma duk wanda aikinsa ya jinkirta shi, to, dangantakarshi ba za ta gaggauto da shi ba”, kamar yadda ya zo a Hadisi ingantacce, (Sannan idan aka busa ƙaho to fa babu wata dangantaka (mai amfani) a tsakaninsu a wannan ranar, kuma ba za su tambayi juna ba). Almu’minun 101

    Allah Ya kiyaye ku!
    Tabbas ta’assubanci shamaki ne mai kauri da yake shiga tsakanin ma’abocinsa da gaskiya, da kuma tsakaninsa da soyayya. Ta’assubanci shamaki ne mai kauri da yake katangewa daga ilimi mai amfani, da aiki nagari, kuma katanga ce mai tsauri da take hana amfanuwa da wasu, kuma yana hana fasahar ƙirƙira.

    Kuma babu abin da zai ga bayan ta’assubanci sai yalwan zuci, saboda yalwan zuci shi ne girmama bambance-bambance, da karɓar saɓani. Kuma duk wanda damuwarsa ita ce isa zuwa ga gaskiya, ba wai ba da kariya ga kai ko mazhaba ko ƙungiya ba, to, zai kuɓuta daga ta’assubanci.

    Ya Allah ka haɗa kan Musulmi a kan gaskiya da shiriya, ya Allah ka yi albarka ga malamansu, da shugabanninsu, Ka haɗa zukatansu, Ka haɗa zukatunsu da ayyukansu a kan abin da zai yardar da Kai.

    Ku yi salati da sallama ga Annabin rahama da aka ba ku, da ni’imar da aka kwaranyo muku, Annabinku Muhammadu Manzon Allah. Haƙiƙa Ubangijinku Ya umurce ku da hakan, kamar yadda ya ce: (Lallai Allah da Mala’ikunSa suna salati ga Annabi, ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa) Al’ahzab: 56.

    Ya Allah Ka yi daɗin salati da sallama da albarka ga BawanKa kuma ManzonKa Annabinmu Muhammadu, da Alayensa da Matansa da Zuriyarsa. Ka ƙara yarda da halifofi shiryayyu guda huɗu: Abubakar da Umar da Usmanu da Ali, da sauran Sahabbai gabaɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyatatawa har zuwa ranar sakamako, Ka haɗa mu tare da su cikin afuwarKa da baiwarKa da kyautatawarKa ya mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da majiɓinta lamuranmu, ya Allah Ka ƙarfafi shugabanmu majiɓincin lamuranmu hadimin Masallatai biyu masu alfarma da gaskiya da dace, kuma Ka datar da shi ga abin da Kake so kuma Ka yarda da shi, Ka azurta shi da mashawarta nagari, Ka ƙarfafi AddininKa da shi, kuma Ka ɗaukaka kalmarKa da shi, Ka sanya shi ya zama taimako ne ga Musulunci da Musulmi, kuma Ka haɗa kan Musulmi da shi a kan Gaskiya da shiriya.

    Ya Allah Ka datar da shi da yarimansa da ‘yan’uwansa da mataimakansa ga abin da Kake so kuma Ka yarda da shi, Ka yi riƙo da hannunsa zuwa ga ayyukan nagarta da taƙawa, kuma Ka taimake shi ga abin da yake gyara ne ga bayi da ƙasa. Ya Allah! Ka datar da Shugabannin Musulmi bisa aiki da LattafinKa, da Sunnar AnnabinKa tsira da amincin Allah su tabata a gare shi, kuma Ka sanya su masu tausayi ga bayinKa Muminai, Ka haɗe kawunansu a kan shiya, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka kiyaye ‘yan’uwanmu a Falasɗinu, ya Allah! Ka kare su da kariyarKa, kuma Ka kewaye su da kulawarKa, Ka ɗora karayarsu, Ka kwance ɗaurinsu, Ka yafe laifinsu, Ka warkar da marasa lafiyarsu, Ka jiƙan mamatansu, Ka karɓe su a matsayin shahidai a wurinKa.

    Ya Allah! Ka ‘yanta Masallacin Ƙudus daga ‘yan mamaya da ƙwace, ya Allah! Ka ɗaukaka al’amarinsa, kuma Ka ɗaga matsayinsa, Ka ƙarfafa gininsa, Ka tabbatar da sasanninsa, ya Maji roƙo. Ya Allah! Ka taimaki sojojinmu masu dako a kan iyakoki, ya Allah! Ka daidaita ra’ayinsu, Ka ƙarfafa musu gwiwa, Ka ƙarfafi niyyarsu, Ka tabbatar da digadiginsu, Ka ƙarfafa zukatansu, Ka taimake su a kan wanda ya zalunce su, ya Allah! Ka jiƙan shahidansu, Ka warkar da maraunata daga cikinsu, Ka kare iyalansu da zuriyarsu, lallai Kai Maji roƙo ne.

    Ya Allah! Ka kare mu daga sharrin masu sharri, da makircin fajirai, da sharrin masu aukowa cikin dare da rana. Ya Ubangijinmu! Ka ba mu mai kyau da duniya da Lahira, Ka kiyashe mu azabar wuta. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Mazanni, dukkan godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai.

    Domin karanta kakannin manzon Allah SAW danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu