Yadda Ilimi Zai Zama Hasken Rayuwarka

0
1460

Ma’anar Ilimi Da Matakansa

1. Ma’anar Ilimi

A wannan gaɓar za mu yi magana a kan ma’anar Ilimi a madarar lughah (a harshe Larabci) da kuma Isdilahi (mahangar yaren shari’ar musulunci) a taƙaice.

2. Ma’anar Ilimi A Lughah

Kalmar Ilm a lughah tana nufin duk abin da yake warware jahilci ya kawar da shi.

2.1. Ma’anar Ilimi Isdilahan

Ilimi a mahangar shari’ah shi ne, duk abin da za a riska a haƙiƙanin yadda yake ta fuskar karatu ko binciken nazari ko gwaji ko ƙwarewa da taimakon wahayi ko hankali ta ɗayan hanyoyin riska guda biyar na ɗan Adam.

2.2. Matakan Ilimi

Wasu ma’abota ilimi suna kallon ilimi ta nahiyar yadda ake riskar shi, sai su raba shi gida biyu Ilmud Daruriy ad-dabi’iy da Ilmun Nazariy al-Muktasab. Wasu kuma suna kallon shi ta fuskar addini da rayuwa, su ce akwai Ilmus Shar’iy da Ilmul Kauniy, wasu kuma ta nahiyar addini kaɗai su ce.

Akwai Ilmul Ghayah (Aqeedah, Qur’an, Hadith) da kuma Ulumul Wasa’il (Ulumul Qur’an, Usulul Fiqh, Musdalahul Hadeeth, Usulut Tareekh, Lughawiyyat d.s).

Ibnu AbdulBarr (Allah ya masa rahma) yana cewa: “Matakan ilimi a wajen dukkanin masu addini Uku ne; (a) Ilimi mafi ɗaukaka shi ne na addini da babu wanda ya halatta ya yi Magana a cikin sa ba tare da abin da Allah ya saukar ba a littafinsa ko  harsunan manzanninsa -Tsira da amincin Allah su tabbata a gare su- (b) Ilimi na tsakiya wanda ya ƙunshi sanin ilimin duniya ta hanyar nazari da bincike kamar Ilmud Dibb da Handasah da makamantan su (c) Ilimi na ƙasa wanda yake da alaƙa da koyan kyautata wata ƙwarewa ta iya zaman duniya kamar koyan zane, tsalle-tsalle, motsa jiki, iya ruwa da sauransu.

Ibnu Hajar (Allah ya kara masa rahma) ya ce: “Abin da ake nufi da Ilimi shi ne na shari’ah da mukallafi zai san abin da ya wajaba a kansa na al’amuran ibadah, mu’amalah da sanin Allah (Tauhidi).

____________

  1. Atthaqafah al-Islamiyyah na Prof. Shaukat Muhd Ulayyan sh108.
  2. Al-Fawa’id na Ibnu Qayyim sh137.
  3. Lisanul arab na Ibnu Manzur al-Ifrikiy 6/145.

Domin karanta cikakken bayani akan Islamiya Daɗi danna nan.

Labarin na GabaYadda Ake Amfani Da Na’urar Gwajin Ciki (Juna Biyu)