Islamiya Daɗi

0
350

Ko ka san wanda ya fara harba kibiya a tafarkin Allah shine Sa’ad Bin Abi Waqqas..

Amintaccen Al’ummar Annabi (SAW) shine Abu Ubaidatu bn Jarrah.

Annabi (SAW) Yace: wanda yake so yaga ɗan aljannah yana yawo a bayan ƙasa ya kalli Dalha bn Ubaidullah.

Wanda yafi kowa tausayi a alummar Annabi (SAW) shine Sayyadina Abubakar.

Wanda yafi kowa tsananin kishin addinin musulinci shine Sayyadina Umar.

Wanda yafi kowa tsananin kunya a alummar Annabi (SAW) shine Sayyadina Usman.

Wanda yafi kowa sanin hukunci a alummar Annabi (SAW) shine Sayyadina  Aliyu.

Wanda yafi kowa sanin halal da haram shine Mu’azu bn Jabal.

Wanda yafi kowa iya karatun Ƙur’ani shine Ubayyu bn Ka’ab.

Wanda yafi kowa sanin ilimin rabon gado shine Zaidu bn Thabit

Wanda yafi kowa sanin ma’anar ALƘUR’ANI shine: ABDULLAHI BN ABBAS.

Ya Allah Kayi tsira da rahama ga Annabinmu Muhammad, da iyalansa, da sahabbansa, da duk wanda yayi aiki da saƙonsa har zuwa ranar tashin ƙiyama. AMEEN.

Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Sahabbai Suka Yi Koyi Da Annabi Muhammad (S.A.W) danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai danna nan.

labarin da ya wuceHalayen Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Siffantu Da Su
Labarin na GabaJan Hankali Game Da Sallar Asuba