An haifi Dr. Murtala Shehu a garin Kudan a ranar 01/01/1960, ya yi karatun allo, sannan kuma ya yi karatu a makarantar firamare wacce take Kudan, haka kuma ya yi karatun gaba da firamare, kazalika kuma ya yi karatu a jami’ar Ahmadu Bello ɓangaran ilimin lafiya (wato CHO) a 1982. Sunan mahaifinsa shi ne Alhaji Shehu Turaki, mahaifiyar sa ita ce Hajiya Khadija mai Gauda.
Sannan kuma ya yi aure ya haifi ‘ya’ya maza da mata kamar haka;
1. Usman
2. Abduljalali
3. Ahmad
4. Abdullahi
5. Sani
6. Isah
7. Yahaya
8. Abdulhadi
9. Mubarak
10. Hauwa
11. Amina
12. Bilkisu
13. Shafa’atu
14. Suwaiba
15. Maimuna
16. Khadija
17. Salima
18. Halima
19. Na’ima
20. Asiya
21. Fatima
22. Nusaiba
Sannan kuma ya buɗe asibiti a garin Kudan a shekara ta 1982 mai suna “Nakowa nursing and maternity home Kudan” (yau kimanin shekara 39 ke nan) wanda dubbunan mutane suke amfani da shi (asibitin).
Domin karanta yadda ilimi zai zama hasken rayuwarka danna nan
Edita; Rumasa’u M. Kallamu