Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar Biri Da Kare

    Tatsuniyar Biri Da Kare

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kare yana yawo a cikin gari, sai ya haɗu da Biri. Sai Biri ya tambaye shi inda za shi, ya ce: “Ina yawo ne ko zan sami ɗan abin da zan ci.” Shi ma Kare ya tambayi Biri inda za shi, ya ce: “Ai ni kullum a daji nake wuni, in ci abinci in ƙoshi.” Biri ya ce da shi: “Ko za ka bi ni ne?” Kare ya ce: “Ni ban taɓa zuwa daji ba.”

    Daga nan Biri ya tambayi Kare: “Shin kai ma kana da wayo irin nawa?” Kare ya mayar da jawabi da cewa: “Wayona goma ne.” Biri ya ce: “Ka ga ni wayona ɗaya ne, amma kullum a daji nake wuni, ballantana kai babba mai wayo goma, shi ne ka zauna a gida? Haba, kada ka ba ni kunya mana.” Sai Kare ya ce: “To, bari in shirya mu tafi.”

    Biri da Kare suka kama hanyar daji. Suna cikin tafiya sai suka isa wani lambu. Ba tare da ɓata lokaci ba, Biri ya tsallake shingen lambu, ya dinga cin kayan marmari, sai da ya ƙoshi. Kare kuwa yana jin yunwa amma tun da ba ya cin kayan lambu sai ya ce: “Kai Biri ni fa yunwa nake ji.” Biri ya ce: “To, shi ke nan mu je gaba, ko ma sami abin da za ka ci.” Haka suka ci gaba da tafiya.

    Can sai Kare ya hango wata jaɓa ta fito daga rami; sai ya bi ta, ya kama ya cinye ya ce da Biri: “Yanzu kam na ɗan sami ƙarfi, mu ƙara gaba.”Suka ci gaba da tafiya. Can sai suka hango ‘ya’yan Kura su biyu, sai Kare ya ce wa Biri: “Kai ni fa zan koma na ga ‘ya’yan Kura.” Biri ya ji haka, kuma ya gane Kare ya tsorata, sai ya ce masa: “Haba, kada ka ba ni kunya mana.

    Yanzu da girmanka kake tsoron ‘ya’yan Kura?” Sai Kare ya ɗaure suka ci gaba da tafiya. Da ‘ya’yan Kura suka ga Biri da Kare, sai ɗaya daga cikinsu ya ce da ɗayan: “Je ka kira iya, ka ce mata ga nama ya zo har guda biyu.” Ɗan Kurar ya sami uwarsu a rami ya ce mata: “Iya, mun ga nama har biyu suna yawo.” Nan take Kura ta yaƙe baki, yawu ya zubo, ta yi miƙa, ta tambayi ɗan ta ce: “Me da me kuka gani?”

    Ya ce: “Biri da Kare.” Da ta ji haka sai ta ce: “Ka je ka kira ɗan’uwanka ku dawo gida.” Sai ya fita da gudu ya kira shi suka koma rami, uwarsu ta ce: “Ku je ku hura wutar da za mu dafa namansu idan sun zo.” Nan da nan’ya’yan Kura suka samo itace, suka hura wuta. Shi kuma Biri sai ya ce wa Kare ya raka shi zuwa wurin abokinsa.

    Sai suka tafi, ba su tsaya ko’ina ba sai bakin ramin Kura sai ya ce: “Bari in shiga ka jira ni a nan.” Biri ya shiga, ya gai da Kura, kuma ya ce: “Yau na zo tare da wani amini na ne domin mu gaishe ki.” Da Kura ta ji haka sai ta yi murna, Biri kuma ya leƙa, ya kirawo Kare. Da ya shiga ya ga Kura a tsugune, sai nan take ya faɗi a sume.

    Biri kuma da ya ga haka sai ya yayyafa masa ruwa, ya farfaɗo. Da Kare kuma ya lura an hura wuta, sai ya sake ƙifewa, ya ƙara suma. A nan ma dai Biri ya sake ta da shi ya ce da shi: “Ka je ka taya su hura wuta.”Da Kare ya je ya hura wuta sai ya riƙa yin waƙa yana cewa: “Biri ya kawo ni gidan mutuwa, Biri ya kawo ni wurin halaka, Da Biri ya ji haka, kuma ya tabbatar Kura ma ta ji, sai ya ce: “Kai Kare ba ka iya hura wuta ba; ba ni ka gani.”

    Da Biri ya karɓi hura wuta, sai ya kama wannan waƙa: “Na kashe Kura tara, Yau zan kashe ta goma, Ni da Kare mu sha nama, Na hura wutar dafa Kura ta goma, Yau zan kashe Kura ta goma.” Da Kura ta ji haka sai tsoro ya kama ta; sai ta ce: “To, ashe sun zo kashe ni ne?” Sai wata dabara ta faɗo mata, yadda za ta gudu tare da ‘ya’yanta.

    Sai ta kira ‘ya’yanta ta ce: “Ku je ramin kawuna ku gani ko ya dawo daga farauta. Maza ku dawo ku gaya mini fa; kada ku tsaya wasa a hanya.” Da suka fita suka ɗan daɗe, sai Kura ta ce: “Biri, ka ga fa yaran nan sun daɗe, bari in bi sawunsu in gani ko sun tsaya wasa a hanya.” Kura na fita ta hango ‘ya’yanta suna dawowa, sai ta yi sauri ta sha gabansu ta ce su gudu, idan ba haka ba Kare da Biri za su kashe su.

    Da Kare da Biri suka gane abin da ya faru, sai suka fito daga ramin Kura suka ci gaba da neman abincinsu; ba sauran wani tsoro kuma, domin Biri ya yi wayo ya kori Kura da dabara. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Girman kai rawanin tsiya.
    • Durƙusa wa wada ba kasawa ba ne, ba ya hana ka tashi da tsawonka.
    • Ƙarfin hali da juriya suna karya gwiwar abokin gaba kome ƙarfinsa.
    • Haɗama da rashin godiya ga Allah sukan sa a yi da-na-sani.
    • Igiya ba ta ɗaure kaya, sai dabara.
    • Banza ta kori wofi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta tatsuniyar Ɗan Kutungayya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Arɗo Da Ndoffiwa

    Tatsuniyar Arɗo Da Ndoffiwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani makiyayi wai shi Arɗo a can kusa da wani baƙin daji da ake kira Dajin Gafiya. Yana zaune da matarsa ɗaya, wai ita Hodanego. Shi Arɗo kullum yakan yini a daji ne wurin kiwo, amma ita matarsa ta ha’ince shi, domin tana da kwarto mai suna Ndoffiwa.

    Kullum idan mijinta ya tafi kiwo, sai ta kama kaza daga cikin kajin gidan ta yanka wa kwartonta, ta shirya abinci mai daɗi su ci tare. Ana nan, wannan abu yana tafiya, har dai wata rana wata maƙwabciyar Arɗo ta kira shi ta ce da shi: “A gaskiya Arɗo duk lokacin da ka tafi kiwo sai matarka ta kira kwartonta, ta kama kajinka ta ɗebi hatsinka ta yi abinci, su ci tare.

    Idan kana son ka kama su, ka yi kamar ka tafi kiwo, sai ka dawo jim kaɗan ka gani.” Sai Arɗo ya amince da shawarar. Rannan sai ya yi yadda ya saba, ya fita kamar ya tafi kiwo, amma sai ya laɓe a gidan maƙwabciyar nan tasa, ya shiga fako. Can sai ya ga matarsa ta kama kazarsa ɗaya ta yanka ta gyara ta kuma ɗora girki sai ƙamshin daɗi ke tashi.

    Da ta gama abinci, ta zuba a akusa, ta rufe da faifai ta ɗauka ta fita, ta kama hanyar gidan kwarton nan tiryan-tiryan, ba tsoro, ba shakka. Sai da ta ɗan yi nisa, sai ya bi ta a baya. Ba ta tsaya ko’ina ba sai gidan kwartonta; amma ta tarar ba ya gida. Arɗo kuma yana daga inda ya raɓe ya ga ta shiga, ta ajiye abincin ta fita daga gidan, amma shi Arɗo sai ya laɓe, har sai da ta yi nisa.

    Sai ya je ya shiga gidan, ya zarce har ɗakin da ta ajiye abincin, ya zauna ya cinye shi kakaf. Daga nan sai ya ɗauki akushin tuwon, ya yi kashi a ciki ya kuma ɗauki akushin miya ya yi fitsari a ciki, shi ma ya rufe, ya sai kai ya yi tafiyarsa.Shi kuwa Ndoffiwa ashe wurin hirarsa ya je.

    Da suka gama hira, sai ya gayyaci abokansa su je cin abinci a gidansa. Duk da cewa ba shi da mace, ya tabbatar kwartuwarsa za ta kai abinci. Suka shiga gida, ya ɗauko akusa. Yana buɗe akushin tuwo, sai ya ga tsibin kashi. Da ya buɗe akushin miya kuma, sai ya ga fitsari; zarnin fitsarin da ɗoyin kashin suka buge shi tare da abokansa.

    Kamar sun haɗa baki, sai suka ce: “Ka gayyato mu gidanka domin ka wulaƙanta mu shi ya sa ka ba mu kashi ko? Lallai ka cika mara kunya.” Haka a fusace suka fice, suka bar shi. Shi kuma kwarto sai ya shirya a zuciyarsa zai kawo wata kwartuwar, domin ya ɓata wa Hodanego rai saboda ta kai masa kashi da fitsari a madadin abinci.

    Sai ya tafi wajen wata kwartuwar. Bai jima da fita ba, Hodanego ta koma gidansa ɗibar akusa. Da ta ɗaga, sai ta ji da ɗan nauyi sai ta ɗaga faifan da ke kai domin ta ga ko bai ci abincin ba ne. Tana buɗewa sai ga wani gandareren kashi, wanda ya kume ɗakin da ɗoyi. Wannan abu ya baƙanta mata rai.

    Sai ta fusata, baƙin ciki ya kama ta. A cikin zuciyarta ta ce: “Amma Ndoffiwa ba shi da mutunci. Na kawo masa abinci a mutunce, amma kuma ya saka mini da kashi da fitsari a akusa? Bari zan yi maganinsa.” Nan take ta juye kashin nan da fitsari a kan gadonsa. Ta sa kai ta yi tafiyarta.

    Ba da daɗewa ba, Ndoffiwa ya koma gidansa tare da sabuwar kwartuwarsa. Da suka shiga ɗaki ta zauna a kan gado, sai ta ji alamar laima, sai ta taɓa da hannunta, ta ji. Nan da nan ta gane ashe kashi ne. Nan take ta miƙe a fusace, ta shiga ƙwala wa Ndoffiwa ashariya, ta ce ashe shi ƙazami ne.

    Ta zazzage shi ta more, sai ta kaɗe zanenta, ta fita daga ɗakin, ta bar gidan. Da fitarta, sai ya kwashe kayan ɗakinsa ya wanke. A cikin daren nan kuma Arɗo ya zagaya inda ya yi shanya, ya kwashe kayan. Sai ya kai su rafi ya zuba, suka bi ruwa. Da gari ya waye Ndoffiwa ya je kwaso shanya, amma bai ga ko bante ba.

    Baƙin ciki ya cika shi, sai ya yanke shawarar ya bunƙa wa ɗakinsa wuta; gobara ta tashi ya yi kururuwa, mutane suka taru aka kashe gobara. Wani ya kawo wani tsumman riga ya ba shi. Da ya sa rigar, kuma ya lura hankalin mutane na wajen kashe gobara sai kawai ya sulale, ya bar garin. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Aure ba wasa ba ne; dole a kiyaye ƙa’idojinsa ko kuma a yi da-na-sani.
    • Abin kunya kan sa mutum garinsu ya gagare shi zama.
    • Rama cuta ga macuci ibada ne.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Marainiya Mai Turmi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Marainiya Mai Turmi

    Tatsuniyar Marainiya Mai Turmi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata Marainiya a wani gari. Sanda iyayenta suka rasu ba su bar mata komai ba, sai wani turmi. Turmin kuwa wani shu’umi ne mai ƙwanƙwamai, to amma sauran mutanen gari ba su san haka ba. Sai turmin ya ce da ita: “To, tun da ba ki da uwa, ba ki da uba, ni ne zan tsaya miki a madadinsu.”

    Wannan magana ta faranta wa Marainiyar nan rai. Sai ta dafa wa turmi ta ce: “To, na gode. Yanzu watau duk abin da nake so za ka ba ni?” Turmi ya ce da ita: “Ba shakka, zan ba ki duk abin da kika nema.” Yarinya ta ci gaba da zama da turmi.

    Suna nan, suna nan, sai wata yarinya ta ji labarin yadda Marainiyar da turmi suka yi, sai ta ce za ta gwada ta ga gaskiyar batun. Sai ta dafa shinkafa, ta je gidan Marainiya da ita ta ce mata: “Kin ce turmin gidanki zai iya ba ki komai ko? To, ya dafa miki shinkafa mu gani in ba ƙarya ba.”

    Marainiya na jin wannan, sai ta gaya wa turmi a cikin waƙa:

    “Turmi, turmi, tangariya,

    Gori ake yi min, Turmi tangariya.”

    Turmi ta ce: “Gorin me ne?”

    Marainiya ta ce: “Gorin shinkafa, Turmi tangariya,

    In da shinkafa, Sai ka ba ni, Ka ba ni shinkafa, Turmi tangariya.”

    Kamar abin dabo sai ga shinkafa har ta fi ta baƙuwar yarinyar yawa da kyau. Da baƙuwar yarinya magulmaciya ta ga haka, sai ta ce: “Na ga wannan, amma zan sake gwada turmin nan.” Can daf da lokacin faɗuwar rana, sai ta je gidan Marainiya da zinariya mai yawa a ƙulle a haɓar zanenta, sai ta ce da Marainiya: “Na zo da zinariya, idan Turmin nan ya isa ke ma ya ba ki.”

    A nan ma Marainiya ba ta yi shakkar komai ba, ta je ta dafa Turmi, ta rera wannan waƙar neman biyan buƙata: “Turmi, turmi, tangariya, Gori ake yi min, Turmi tangariya.” Turmi ya ce: “Gorin mene ne?” Marainiya ta ce: “Turmi gorin zinariya, Turmi tangariya. Idan da zinariya, Turmi ka ba ni.”

    Kafin ta gama rufe baki sai ga zinariya tsibi-tsibi, har da wani tarin zinariya kamar girman ƙwan kaza. A wani tarin kuma kamar girman dutsen murhu. Wuri duk ya haske, algungumar yarinya kuma nan take ta suma saboda mamaki.

    Amma da ta farfaɗo maimakon ta saduda, sai ta ce: “Na ga wannan ma bari in kawo saurayina, ke kuma ma Turmi ya ba ki naki mu gani.”Sai ta kawo saurayi har ƙofar gidan. Ita kuma Marainiya ta shiga ta gaya wa Turmi. Sai Turmi ya ce da ita ta rufe idanunta, sannan ta buɗe bayan ta yi ƙirga ɗaya zuwa bakwai.

    Da ta yi haka; tana buɗe ido sai ta ga wani tsulelen saurayi kyakkyawan gaske, wanda har magulmaciyar yarinyar da kanta ta ce: “Ban taɓa ganin kyakkyawan saurayi kamar shi ba.” Sai baƙin ciki da kishin abin da Turmi ke yi wa Marainiya suka sa magulmaciyar yarinyar ta kashe kanta.

    Da labari ya bazu a gari, sai aka taru ana kallon gawarta, ana mamakin abin da ya kai ta ga faɗawa wannan asara. Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa

    • Ɗa nagari ba ya rama mugunta da sharri sai da alheri.
    • Nuna ƙyashi da baƙin ciki a kan baiwar da Allah ya yi wa wani mutum halaka ce da ta sa a yi mummunan ƙarshe.
    • In Allah ya rufa wa bawa asiri, ba mai tona masa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Janniya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Janniya

    Tatsuniyar Janniya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata mata mai ɗa wai shi Janniya. Suna zaune ita da kishiyarta tare da mijinsu cikin lumana. Wannan mata kuma tana da garken shanu. Bijimin da ke cikin shanun kuma yakan yi magana kamar mutum. Ana nan, ana nan, wata rana uwar Janniya da kishiyarta suna zaune suna taɗi, sai ta ce da kishiyar: “Ina jin fa na kusa mutuwa. Idan na mutu ki kula da Janniya.”

    Da kishiyar ta ji haka sai ta ce: “Haba! Ai ko ba ki faɗa ba ma zan kula da shi, ai ɗana ne.” Sai uwar Janniya ta ce: “To, na gode da kika yi wannan alwashi.” Bayan kamar kwana huɗu da yin wannan zance, sai uwar Janniya ta ce ga garinku nan! Ita kuwa kishiyar sai ta mallaki shanun da uwar Janniya ta bari.

    Suna nan, kullum sai ta zuba wa Janniya magunguna na asiri iri-iri a cikin abincinsa. To amma duk sanda Janniya ya zo cin abincin, sai wannan bijimin sa ya gaya masa, kuma ya hana shi ci. Sai ya rinƙa rera waka yana cewa:

    “Janniya Jannati,

    Janniya Jannati.

    Kishiyar uwa Janniya, Jannati, Janniya,

    Ba uwabace Janniya Jannati.

    In za ta ba ka tuwo,

    Tuwo damagani, Janniya Jannati.

    In ta ba ka, Janniya Jannati,

    Ka tona rami, Janniya Jannati,

    Agindin turkena, Janniya Jannati.

    Ka binne tuwon, Janniya Jannati.

    Kar ka ci, Janniya.”

    Kullum haka, amma duk da rashin cin abinci kamar yadda ya kamata, wannan bai sa Janniya ya rame ba. Yau da gobe sai kishiyar uwar ta gane wannan san ne ke tona mata asiri, sai ta matsa wa mijinta ya amince a yanka san nan mai magana. Shi kuma san duk ya ji abin da aka shirya, sai ya ce da Janniya: “Idan an yanka ni, ka ce a ba ka kai da ƙafafuwana da kayan ciki.

    Sai ka binne su. Yin haka zai karya duk wani makaru da za ta yi maka.” Shi ke nan da aka yanka sa, sai Janniya ya roƙi a ba shi duk waɗannan abubuwan. Aka ba shi, shi ko ya je ya binne. Sai kishiyar uwar ta ci gaba da ba shi sammu iri-iri, to amma saboda ya yi abin da san nan ya faɗa, sai duk makarun da take yi ba wanda ya kama shi.

    Kullum sai haske yake ƙarawa, ita kuma baƙin ciki na damunta. Wani Falke ya ce, baƙin ciki kan kashe irin waɗannan mutane. Haka ko aka yi. Ta ci gaba da lalacewa, har dai a ƙarshe bakin ciki ya kashe ta. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Duk wanda yace zai canza hukuncin Allah ƙarshensa nadama da halaka.
    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Maharbi Da Zaki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Maharbi Da Zaki

    Tatsuniyar Maharbi Da Zaki

    Ga ta nan, ga ta nan ku.

    An yi wani maharbi da ke gefen Dajin Shiddar, a can yamma da ƙasar Sarkin aljanu. Wata rana ya fita farauta a daji, sai ya ga wani rami, bai yi wata-wata ba sai ya kutsa kai ya shiga. Ashe ramin nan na Zaki ne. Zaki ko na ganin sa sai ya yo kansa. Mutumin nan ya fito ya kama gudu, har ya fita daga dajin ya shiga karkara.

    Zaki dai na bin sa, har ya tarar da wani manomi, ya ce da shi: “Mai gida ka taimake ni.” Manomin ya ce: “Me ya koro ka haka?” A cikin tsoro da ɗimuwa maharbin nan ya ce: “Zaki ne, Manyan Dawa. Sai manomin ya ce: “A gaskiya tun da Zaki ne ya fafaro ka, abin ya fi karfina; ba zan iya taimaka ma ba.”

    Da ya ji haka, sai ya ci gaba da gudu. Har dai ya tarar da wani manomin a wata gonar yana tiƙar aiki. Shi ma sai ya ce da shi: “Don girman Allah ka taimake ni mana, Zaki ne ya biyo ni zai kashe ni.” Shi ma dai wannan manomi ya gaya wa maharbi ba zai iya taimakon sa ba, domin Zaki ya fi ƙarfinsa.

    Sai maharbin nan ya ci gaba da gudu, har ya tarar da Gizo. Shi ma ya yi masa bayani cewa Zaki ne yake bin sa zai kashe, kuma yana son taimakonsa. Sai Gizo ya yarda zai taimake shi. Nan da nan ya kama shi, ya jefa shi cikin yanar da ya saka. Can sai ga Zakin nan ya tunkaro a guje.

    Sai ya tsaya ya tambayi Gizo ko ya ga wani maharbi? Gizo ya ce bai gani ba. Sai Zaki ya fusata, ya ce da Gizo: “To, idan ba ka gan shi ba, kai zan cinye ka.” Kamar da wasa, sai ya kai wa Gizo wawura. To, da man ɓangaren yanar Gizon da Zakin ya auka wa yana da dafi, yanar kuma tana da ƙwarin da ko Zaki ba zai iya tsinka ta ba.

    Yanar ta dabaibaye Zaki, dafin jikinta kuma yana daɗa raunana shi. Tausayin Zaki ya kama maharbin nan da Gizo, har suka fara yin ƙoƙarin kuɓutar da shi; to amma saboda dafin yanar nan da kuma shaƙe wuyan Zaki da yanar ta yi, kafin su gama warware yanar har rai ya yi halinsa.

    Su kuma manoman da maharbi ya roƙa su taimake shi suka ki, tsegumi ya sa sun biyo bayan Zaki domin su ga yadda zai kashe maharbin nan. Amma da suka isa inda Gizo yake, suka tarar da yanarsa da dafin da ke jikinta, sun halaka Zaki, kuma ga maharbi garau, sai mamaki ya kama su.

    Saboda borin kunya, sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “Da man ina da niyyar taimakon ka, amma ba ka tsaya ba. Na san kuwa shi Gizo da ya taimake ka, bai fi ni kirki ba.” Sai baki daya suka fashe da dariya, suka fara haƙa ramin da za su binne Zaki don gudun kada ya yi wa Gizo ɗoyi a mazauninsa. Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa

    • Rashin kyakkyawan tunani kafin aikata abu yakan jefa mutum cikin halin ƙaƙa-naka-yi.
    • Taimakon Allah yana iya zuwa ta inda ba a zata ba.
    • Kowa ya ɗebo da zafi,

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura

    Tatsuniyar Kurege Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege da ƙawarsa Kura suka fita farauta. Suna cikin tafiya, sai suka tarar da inda hanya ta rabu biyu. Hanyar da ta yi dama, doguwa ce, wadda ta yi hagu kuma gajeriya. Sai Kurege ya ce da Kura: “Tun da ke ce babba, sai ki bi doguwar hanyar, watau ta dama, ni kuma ƙarami in bi gajeriyar, wadda ta yi hagun.”

    Kura ta ce: “A a, kai ƙarami ka bi babbar hanya, ni zan bi ƙaramar.” Sai ya ce: “To, shi ke nan mu tafi.” Kowa ya kama hanyarsa. Kura da ta bi gajeriyar hanya ba ta sami komai ba, sai wani ɗan ƙanzo. Da lokacin da za su haɗu ya matso, sai ta je inda suka shirya za su haɗu da Kurege, ta tsuguna tana jira.

    Shi kuwa Kurege mai doguwar hanya, sai ya yi ta tafiya har ya gaji. Sai ya sami inuwar wata bishiya ya zauna yana hutawa. Da sanyin inuwa ya ratsa shi, sai ya ce: “Kai, amma wannan inuwada daɗi take.” Sai kawai ya ji bishiya ta ce: “Ai ma sai ka ɗanɗana ganyena ka ji irin daɗinsa!” Sai Kurege ya tsinki ganyen bishiyar nan ya sa a baki ya tauna.

    Sai ya ce: “Kai, amma wannan ganye da daɗi yake!” Sai bishiya ta ƙara da cewa: “Ai don ma ba ka ɗanɗana cikina ka ji ba?” Sai Kurege ya tambaye ta ya ce: “Yaya zan yi in ɗanɗana cikinki?” Sai ta ce: “Idan kana so ka shiga cikina sai ka ce: ‘Buɗe bus’ sai ka shiga.

    Idan ka ce: ‘Rufe kif’ bayan ka sha zumar, za ta rufe.” Kurege ya yi godiya, ya matsa kusa da bishiya ya ce: “Buɗe bus.”Tana jin haka sai ta tsage, Kurege ya shiga ya tarar da zuma ya zauna ya sha, har ta yi masa karo. Ya ɗebi wata kuma ya cika jakarsa. Da ya fito daga cikin kogon bishiya, sai ya ce: “Rufe kif.”

    Sai bishiya ta rufe, ya yi godiya, ya kama hanyar zuwa inda suka shirya za su haɗu da Kura. Da ya isa inda suka yi alƙawarin haɗuwa da Kura sai ya tarar da ita tana barci. Ya shure ta, ta farka. Sai ta gan shi yana tanɗar baki, alamun ya ci daɗi, ta tambaye shi, “Kai, me ka samo ne mai daɗi haka?”

    A cikin yanga da burga, Kurege ya ce da Kura: “Na samo wani abu ne mai daɗi, ke kuma fa?” Cikin nadama da mairairaita ta ce: “Ni kam ban samo komai ba sai wani ɗan kanzo. Yunwa ma nake ji. Ɗan ba ni abin da ka samo in ɗanɗana mana.” Sai ya ce: “Idan na ba ki a cikin jaka, za ki cinye har da jakar, amma bari in dangwalo miki.”

    Kurege ya sa tsinke ya dangwalo zuma, ya miƙa wa Kura; ta karɓa ta sa a baki sai ta lumshe idanu da zaƙin zuma ya ratsa ta; sai ta cinye har da tsinken. Nan take fa sai kwaɗayinta ya motsa, ta ce da Kurege: “Gaya mini inda ka samo wannan zuma mai daɗi domin ni ma in je in samo.” Sai ya yi mata kwatancen bishiyar da ta ba shi zuma; Kura ta kama hanya.

    Da ta isa ko hutawa ba ta yi ba, sai kawai ta tsunki ganyen bishiya ta sa a bakinta. Sai daɗi ya sa ta ce: “Amma wannan ganye da daɗi yake.” Da bishiya ta ji haka sai ta ce: “Ai wannan ma kaɗan ne, ba ki ɗanɗana abin da ke cikina ba.” Kura ba tare da ta tambayi yadda ake shiga cikin bishiyar ba, sai kawai ta ce: “Buɗe cikin in shiga in ci daɗin da kika faɗa.”

    Nan take bishiya ta buɗe wa Kura cikinta, ta shiga ta fara warwason zuma, tana sha. Da daɗin zuma ya kwashe Kura sai ta fara wannan waƙar: “Buɗe bus, Rufe kif, Mu sha zaƙi, Kurege ba wayo, Nafi shi shan zuma, Zuma mai daɗi, Ke bishiya rufe kif.” Sai ko bishiya ta rufe.

    Bayan wani ɗan lokaci sai ta ce da Kura: “Ki yi maza ki gama, masu ɗakin nan fa sun kusa dawowa.” Amma saboda wauta irin ta Kura, sai ta ce da bishiya: “Ba komai ko sun zo, ai ina da ƙarfin da zan kore su. Idan sun gan ni ma za su gudu.” Sai ta ci gaba da shan zuma. Ta sha ta ƙoshi, amma kuma ta mance abin da za ta faɗa ƙofa ta buɗe.

    Tana cikin wannan hali ne fa kudan zuma suka dawo daga cin furanni. Suna shiga saƙarsu da ke cikin kogon bishiya suka tarar da Kura; nan take suka far mata da harbi, tana kuka da kugi irin wanda aka san ta da shi. Ta ruɗe, ta rinƙa cewa: “Kif, bishiya kif” maimakon ta ce: “Bus.” Can dai ta yi sa’a ta ce: “Buɗe bus.”

    Bishiya ta buɗe, Kura ta fito da ƙyar, duk jikinta ya kumbura saboda harbin zumar da ta sha; sai ta kama gudu, tana haɗawa da waiwaye, ta doshi inda Kurege ke jiranta. Da Kura ta matsa kusa Kurege ya ga yadda jikinta ya zama, sai ya nemi sanin abin da ya faru.

    Sai ta kwashe labari ta gaya masa; shi kuma ya ce da ita: “Kin cika mantuwa.”Haka dai Kura ta koma gida tana jinya.Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Rashin yin abu da kyakkyawar niyya shi yake sa yin nadama.
    • Yin abu da zuciya ɗaya zai kawo taimakon Allah.
    • Haɗama da rashin godiya ga Allah sukan sa a yi da-na-sani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ɗan Kutungayya

    Ɗan Kutungayya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ke zaune awani gari mai suna Raƙumawa tare da matarsa da ’ya’yansu su goma sha ɗaya. Rannan sai matar ta haifi ɗa namiji, ya zama na goma sha biyu. Da haihuwar yaro kuwa sai ya yi magana ya ce wa uwarsa: “Kada ma a yi wahalar raɗa mini suna, domin sunana Ɗankutungayya.”

    Ya ƙara da cewa, ragon sunansa ma kada a yanka, a bar masa ya rinƙa hawa. Iyayen suka yi haka, jama’ar gari suna ta mamakin wannan yaro da abubuwan da ya yi. Ana nan, ana nan, sai wata rana yayyen Ɗankutungayya suka shirya za su gidan wata mata da suka saba zuwa gidanta hira da ’ya’yanta su goma sha biyu.

    Sai Ɗankutungayya ya ce zai bi su amma babban wansu ya hana shi bin su. Amma ya bari sai da yayyen suka tafi, sai ya bi su a baya. Da isarsu gidan, sai matar ta yi musu maraba; ta yi musu shimfiɗa, suka zauna; ta kawo musu abinci mai daɗi suka ci, suka fara hira. Amma fa duk zuwan da suke yi gidan ba su san cewa matar nan dodanniya ce ba.

    Suka zauna suna ta hira kamar yadda suka saba kullum. Kuma duk sanda suka yi barci a gidan, Dodanniyar kan tashe su, su tafi gida. Ashe duk wannan dabara ce take yi don su saki jiki da ita, wata rana ta cinye su. Kuma tuni ta yi tanadin manyan tukwanen dafa su, ta sha romo.

    To a daren da suka je tare da Ɗankutungayya ma, duk sauran sun yi barci in ban da shi. Can cikin dare sai ya ji ana wasa wuƙa sai ya ce a ransa: “A a, lafiya kuwa?” Sai ya kwanta ya yi kamar yana barci. Da aka ɗan jima sai ga Dodanniya tana sanɗa, har ta shiga wajen yara.

    Ɗankutungayya yana kallon ta, tana riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙa sai ƙyalli take yi. Da ya ga lallai ta nufi yayyensa, sai ya yi tari da ƙarfi. Da ta ji tarinsa, sai ta koma da sauri. Da aka jima, sai ta sake dawowa; shi kuwa Ɗankutungayya ya ƙara yin tari, ta koma. A zuwanta na uku ne fa da ta ji tarin Ɗankutungayya, sai ta ɓoye wuƙa ta leƙo ta ce: “Kai ɗan samari ba ka barci ne?

    ”Sai ya ce: “Ai ni ba na barci in ba a kan rairayin ƙorama mai sanyi ba.” Da ta ji haka, sai ta ɗauki masaki ta tafi neman rairayin ƙorama. Kafin ta dawo sai Ɗankutungayya ya fito da wata ’yar batta, ya buɗe bakinta, ya zazzago wani magani, ya matsa kusa da wutar da ta hura, ya barbaɗa maganin nan a cikin wutar, sai wani hayaƙi ya tashi.

    Da ’ya’yan Dodanniya da yayyensa suka shaƙi wannan hayaƙi, sai barcin da suke yi ya ƙara nauyi. Nan da nan Ɗankutungayya a cikin sauri irin na hatsabiban mutane ya bi ya tuɓe wa ’ya’yan Dodanniya kayan jikinsu, ya sanya wa yayyensa. Kuma ya tuɓe wa yayyensa nasu kayan, ya sanya wa ’ya’yan Dodanniya.

    Da ya gama wannan aiki sarai, sai ya kwanta, ya shiga jira. Can sai Dodanniya ta dawo, ta kawo rairayi ta ba Ɗankutungayya. Sai ya ce: “Yawwa, iya; na gode. Yanzu zan yi barci.” Da aka jima sai Dodanniya ta dawo da wata sharɓeɓiyar wuƙarta a hannu, ta iske Ɗankutungayya ya yi barci.

    Nan da nan cikin gaggawa da ƙeta ta bi duk ’ya’yanta ta yanke, tana zaton samarin da sukan je hira gidanta ne. Amma ba ta yanka Ɗankutungayya ba, saboda ta ga shi ƙarami ne. Ta ƙyale shi, da nufin ta kiwata shi ya yi ƙiba. Da Dodanniya ta fita za ta fara shirin kwashe naman da take zato ta samu, sai Ɗankutungayya ya zaro battar nan tasa ya sake barbaɗa garin maganin nasa a kan wuta.

    Kafin kifta ido, hayaƙi ya murtuke ɗaki. Cikin gaggawa ya tashi yayyensa, ya gaya musu abin da ya faru, kuma ya ce su yi maza-maza su gudu gida. Ya ce shi zai bi su da gari ya waye, kada su jira shi. Take suka sulale, suka gudu. Da gari ya waye, sai Dodanniya ta zo za ta fara tattara waɗanda ta yanka, a zatonta ’yan’uwan Ɗankutungayya ne.

    Yana ganin ta sai ya kaɗa battarsa, sai ga ragonsa ya zo ya harari Dodanniya, yana yi mata kallon raini ya ce: “To, waɗannan fa ’ya’yanki ne kika yanka. Ba ’yan’uwana ba.” Da ta lura da haka, sai ranta ya ɓaci ta yi wani ƙaraji, ta yi wuf ta kai masa bara za ta cafke shi, sai ya bauɗe.

    Ta sake rarumo shi, amma sai ya ɗare bayan ragonsa. Rago kuwa kamar ya san zancen, sai ya kama sukuwa kamar walƙiya, ya tsere mata fintinkau ya bar ta sororo a cikin baƙin ciki. Dodanniya ta ɗauko ɗan magurjinta na tsafi ta bi ’ya’yanta tana buga wa kowannensu a kai.

    Nan da nan namansu ya zama na tumakai, ta soye suka cinye ita da autarta. Daga nan ta yi alƙawari sai ta rama ƙetar da Dankutungayya ya yi mata. Bayan ’yan kwanaki, sai Dodanniya ta je bakin garin su Ɗankutungayya ta rikiɗe ta zama kanya kuma ta kwanta ’ya’ya da yawa, har sun kusa nuna.

    Da yaran gari suka ga kanyar sai suka yi murna. Da ta nuna, sai wasu daga cikinsu suka dinga kaɗo ’ya’yan suna sha. Har dai wata rana yara da yawa suka hau kanta suna ɗiba. Da Dodanniya ta ga haka sai ta tashi sama da su, ba ta tsaya ba sai a gidanta. Nan da nan ta gaya wa autarta cewa nama ya samu.

    Sai ta umarce ta da ta wanke tukwane. Tana kuwa cikin wanke tukwane sai Ɗankutungayya ya ji labarin abin da ya faru, sai ya rikiɗa, ya zama ɗanmaraki, ya je gidan Dodanniya. Da zuwansa sai ya fara cin shuke-shuken da ke gidan, watau dai yana yi mata ɓarna. Yana cikin wannan ɓarna sai Dodanniya ta ce wa yaran da ta sato, su je su kori ɗan marakin mai yi mata ɓarna.

    Da ya ga sun doshe shi, sai ya ƙi gudu; amma da suka zo dab da shi, sai ya ɗan gudu ya ɗan matsa gaba kaɗan kuma ya ci gaba daɓarna. Yara kuma suka ɗan matsa kusa da shi, ya ɗan ƙara gaba kaɗan. Haka dai ya dinga jan su, har sai da suka yi wa Dodanniya nisa. Sai ya rikiɗa ya zama mutum, ya ce da yaran nan su hanzarta su gudu.

    Ya jaddada musu cewa idan ba su gudu ba, Dodanniya za ta cinye su. Da suka ji haka, sai suka sheka da gudu, suka koma garinsu, suka gaya wa iyayensu abin da ya faru. Shi kuwa Ɗankutungayya sai ya hau ragonsa, ya koma gidan Dodanniya. Da ya tabbatar ta gan shi, sai ya yi mata gwalo ya ce mata: “Na kuɓutar da yara daga sharrinki, sun koma wurin iyayensu.

    Ni ne Ɗankutungayya na yi miki gayyar tawa, wadda ba za ki iya ramawa ba har abada.” Wannan abu da Ɗankutungayya ya yi wa Dodanniya da maganar da ya gaya mata, suka sa ta shiga tunani da ƙulla yadda za ta ɗauki fansa a kansa. Ana nan, sai Dodanniya ta rikiɗa, ta zama mace kyakkyawar gaske, ta ɗauki wani adudu ta je cin kasuwa.

    Masoya suka yi ta kanta, kowa yana so ya aure ta amma ta ce ba wanda za ta aura, sai wanda ya buɗe wannan adudun. Samari da yawa suka gwada, amma duka suka kasa. Bayan ’yan kwanaki, har samari sun fidda rai, sai ɗaya daga cikin yayyen Ɗankutungayya ya ji labari, ya bincika inda take a kasuwa ya je kuma ya gan ta, sai ya ji yana son ta.

    Ita kuma Dodanniya ta gane shi, saboda haka sai ta yi tsafi ta yadda idan ya gwada buɗe adudun zai buɗe. Da zuwansa kuma ya gwada sai adudun ya buɗe, mutane suka yi ta mamaki, shi kuma ya yi murnar samun kyakkyawar mata. Aka ɗaura aure, ba ta jima ba ta tare a gidansa.

    Amma bayan ’yan kwanaki sai ta ƙwakwale wa mijin ido ɗaya, ta tafi da shi ta bar shi da jinya. Ɗankutungayya da jin wannan aika-aikar ya tabbatar da cewa Dodanniya ce. Don haka ya ƙudiri aniyar sai ya ɗauko fansar abin da ta yi wa yayansa. Sai ya rikiɗa ya zama Bafulatana, ya ɗauki nono, ya je gidanta talla.

    Da isarsa sai autar Dodanniya ta fito ta saya. Shi kuma ya yi mata araha. Kullum sai ya kai tallar nono, Dodanniya ba ta gane gogan ne ba. Da haka har Dodanniya ta saba da Bafulatana ƙwarai da gaske. Wata rana sai Bafulatana, watau Ɗankutungayya ya zo gidan Dodanniya a fusace.

    Dodanniya ta tambayi Bafulatana dalilin fushinta, sai ta ce: “Wani mutumwai shi Ɗankumale yake zuwa yana kashe musu shanu. Ga shi yanzu duk sun kusa ƙarewa.” Dodanniya ta ce: “Ke ba sunansa Ɗankumale ba, sunansa Ɗankutungayya. Mugun mutum ne.

    Ba shanunku kaɗai ba, ku kanku ma ku yi hankali da shi. Ni ’ya’yana goma sha ɗaya ya sa na kashe. Kwanan nan ma na kusa makantar da ɗan’uwansa. Kin ga idon yayansa da na ƙwakule.” Sai Bafulatana ta ce: “Tir, da ganin idon lalatacce.” Sai Dodanniya ta ce: “Yau saura kwana uku ma in ba kyanwata idon mugun ta cinye.”

    Bafulatana ta ce: “Kash, da idon nan zai yi wa ƙanena daidai da kin ba ni shi. Shekaran jiya saniya ta harbi idonsa ɗaya ya fashe ya tsiyaye.” Cikin ɗoki da ƙeta Dodanniya ta ce: “Af, don wannan ai sai in ba ki.” Da jin haka sai Bafulatana ta yi farat ta ce: “Ai ko na gode.” Dodanniya ta ƙara yi wa Bafulatana gwaninta, sai ta gaya mata yadda za ta sa masaidon ta ce:

    “A nemo ƙwaiƙwayen kifi guda bakwai da hantar baƙin kare, da ƙiyashi guda bakwai da ƙaucin maƙe, a shanya su bushe, sai a niƙa, a rinƙa sa masa a gurbin idon har kwana uku. A rana ta huɗu, sai a sa idon, zai zauna daram.” Bafulatana, watau Ɗankutungayya, ta amshi ido, ta yi godiya.

    Da ta gusa kaɗan, sai ta tuɓe kayan Fulani, sai ga Ɗankutungayya ya bayyana. Sai ya yi wa Dodanniya gwalo, ya ce: “Kin ga, ni ne Ɗankutungayya.” Sai ya yi wani hatsabibanci ya ɓata, Dodanniya ta daina ganinsa. Bai tsaya a ko’ina ba sai gida. Da ya isa ya yi yadda Dodanniya ta kwatanta masa, idon yayansa kuma yazauna daram, kamar ba a taɓa ƙwakule shi ba.

    Rannan kuma sai Dodanniya ta rikiɗa ta zama kyanwa. Ta kama hanya ba ta tsaya ko’ina ba sai a gidan su Ɗankutungayya. Da shigarta sai ta iske shi yana barci; sai ta lafaba, har ta kai kusa da shimfiɗarsa. Sai ta yi wani ƙaratu irin na tsafinta, ta tofa masa a fuska, sai ya zama ɓera sai ta ɗauke shi ta kai gidanta, ta sa shi a ƙuryar ɗaki.

    Daga nan ta yi masa wani tofin, ya koma mutum.Ita kuma ta rikiɗa ta zama mutum. Sai ta harare shi, fuskarta murtuk, tana cike da fushi, ta ce: “Ɗankutungayya, yau fa ga ni ga ka, ƙaryarka ta ƙare.” Ɗankutungayya bai tsorata ba, kuma bai ce mata komai ba. Can da Dodanniya ta ɗan huta, sai ta sa autarta tsaron Dankutungayya, ita kuma ta kama hanyar kasuwa sayen kayan yaji wanda za ta dafa shi da shi.

    Tafiyarta ke da wuya sai Ɗankutungayya ya yi wa ’yar auta dabara, ya karɓi kayan jikinta ya sa, ita kuma ya sanya mata nasa. Can sai ya ji motsin Dodanniya ta dawo, ya zabura, ya tarye ta yana ƙwaikwayon maganar ’yar auta, yana yi mata maraba. Bayan wani ɗan lokaci kuma sai ga ’yar a cikin kayan Ɗankutungayya, tana yi mata maraba.

    Sai Ɗankutungayya ya dubi Dodanniya ya ce mata: “Ga munafukin nan Ɗankutungayya yana nuna wa wai shi ne ni ’yar autarki har da cewa, ‘Sannu da zuwa inna’. Yau dai ƙaryarsa ta ƙare.” Sai Dodanniya ta ce: “Lallai kam; bar ni da lalatacce!” Nan take ta yi wuf, ta shaƙo ’yarta, ta sa wuƙa ta yanka.

    Tana gamayanke autarta, sai Ɗankutungayya ya buga tsalle gefe, ya kwance zannuwan da ya ɗaura, ya dubi Dodanniyar nan ya ce: “’Yar auta kika yanka, ni ko ni ne Ɗankutungayya, gwanin gayya. Na yi miki gayyar tawa!” Yana gama faɗa mata haka sai ya yi wal, ya ɓace. Dodanniya ta kama ’yarta ta tuɓe kayan jikinta, sai ta ga lallai kuwa autarta ce ta yanka. Nan take sai ta haɗiyi zuciya ta mutu.

    Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa 

    • Kaunar juna da son ’yan’uwa kan ƙara danƙon zumunci. *
    • Mugunta fitsarin faƙo ce kan wanda ya yi take komawa.
    • Dan’uwa rabin jiki.
    • Kaiƙayi koma kan masheƙiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Tatsuniyar Musare Da Hodanego

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani mutum mai mata biyu, da ’ya’ya biyu. Uwargidan tana da ɗanta mai suna Musare; amaryar kuma tana da ’ya wai ita Hodanego. Ana nan har yara suka girma. To da ma shi mahaifinsu yana da dabbobi masu yawa, sai ya ba Musare Akuya guda, ita kuma Hodanego da take ƙarama, ya ba ta Kaza.

    Suna nan, duk sanda Musare ya nemo wa akuyarsa abinci ya zuba mata, sai Hodanego ta saki kazarta ta je ta watsar da abincin. Kullum haka, har dai rannan yunwa ta kashe akuyar Musare. Ya yi haƙuri bai ce komai ba, amma kuma sai kullum ƙanwar ta riƙa yi masa dariya, tana tsokanar sa.

    Daga ƙarshe dai sai ya ɗan yi magana, sai uwar Hodanego ta kama shi da duka. Amma saboda kara irin ta matan kirki, mahaifiyarsa ba ta ce komai ba. Wata rana sai uwar Musare ta kwanta ba lafiya, har jikinta ya fara ruɓewa ta fara wari, sai kishiyarta ta fara yi mata tsiya da ’yan maganganu, har da zagi tana cewa ita fa wari ya fara damun ta a gidan.

    Haka dai, kullum sai Musare da mahaifiyarsa su shiga ɗaki su yi ta kukan baƙin ciki. Da ciwo ya tsananta, sai ta ce da shi: “Ka tashi ka shiga dajin nan ka nemo mini magani.” Sai ya ce da uwar: “To.” Washe-gari da sanyin safiya ya fita, ya kama hanyar dajin don nemo magani.

    Yana cikin dokar daji sai ya haɗu da wata tsohuwa ita kaɗai tana dogara ’yar sanda. Da ta ji motsinsa sai ta ce: “Don Allah ɗan nan ka taimake ni ka ɗora ni kan hanya wadda zan bi
    in shiga gari.” Sai ya dube ta cikin murya lallausa ya ce: “Ayya, ai kin baro hanyar da nisa, amma bari in kai ki.”

    Tsohuwa ta ce: “Yawwa, na gode.” Ya shiga gaba, tana biye da shi har suka isa hanya. Sai tsohuwa ta ce da shi: “Ɗana da ma ina so in gwada kirkinka ne, kuma zan taimake ka a kan abin da ka fito nema.” Mamaki ya kama Musare, sai ya ce: “To.” Sai tsohuwa ta ci gaba da yi masa bayani tace:

    “Ka bi wannan hanyar, kada ka tsaya har sai ka tarar da wata babbar tsamiya, sai ka tsuguna a gindinta ka roƙi duk abinda kake so.” Musare ya yi mata godiya, ya bi inda ta nuna masa har ya isa gindin tsamiyar da ta kwatanta masa. Musare na isa ya tsuguna, ya roƙi maganin ciwon da ke damun mahaifiyarsa.

    Sai kawai ya ga ƙullin magani ya faɗo daga wata sheƙa da ke kan tsamiyar. Ya ɗauka ya yi
    kamar zai miƙe tsaye, sai ya ji an ce: “Idan kana da wani abu da kake buƙata, ka tambaya a ba ka.” Ya waiga bai ga kowa ba, amma sai ya ce: “Ciwon da ke damun uwata ne kan gaba da komai; maganin nan ma ya isa. Na gode.”

    Kafin ya gama rufe baki sai ya ga an fito masa da wani Doki ya sha ado da gwalagwalai da kayan sa wa iri-iri da dukiya mai yawa, sai ya ji an ce: “Dokin da kayan nan duka naka ne.” Ya sake dubawa bai ga kowa ba, sai ya sake yin godiya. Da ya lura dai an sallame shi, sai ya ɗare kan Doki, ya kama hanya bai zame ba sai gida, ya shiga ya ɗaure Doki, ya doshi ɗakin mahaifiyarsa.

    Da ya shiga ɗakin sai ya tarar saboda ƙarfin maganin da aka ba shi, har mahaifiyarsa ta warke. Sai ya ba ta labarin yadda suka yi da tsohuwa. Ita kuma ta gaya masa cewa kishiyarta ma bayan tafiyarsa ta kamu da irin ciwon. Mahaifiyarsa ta yi masa godiya, kuma ta umarce shi da ya kai wa kishiyarta maganin ita ma ta sha.

    Nan take ya ɗauki maganin ya fita tsakar gida, ya kira Hodanego ya ba ta maganin ta kai wa mahaifiyarta. Da kishiyar uwar ta karɓi maganin ta sha, kuma nan take ta warke. Wannan lamari ya sa ta shiga cikin wani hali na jin kunya, sai kawai ta fashe da kuka, ta tashi ta shiga ɗakin uwar Musare tana ba ta haƙuri.

    Ita kuma ta ce da ita ta yafe mata. Da haka suka ci gaba da zama gidan mijinsu, kamar ya da ƙanwa, ba sauran kishi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kyakkyawar tarbiya jari ce ga mai ita; sai mai tarbiyar ƙwarai ne yake yin afuwa.
    • Idan ka ga mutum mugu kuma maƙetaci to dama ba shi da tarbiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Marayu Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Marayu Biyu

    Tatsuniyar Marayu Biyu

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani mutum shi da matarsa suna zaune cikin farin ciki a wata ’yar unguwa ta mafarauta da ke bakin wani daji. Suna nan sai matar ta sami juna biyu. Bayan’yan watanni ta haifi ɗa namiji. Uwar da mai gidanta suka yi murna ƙwarai, zaman daɗi ya karu a tsakaninsu.

    Bayan matar ta yaye wannan ɗa na fari, sai kuma ta sake samun ciki, amma kuma sai mai gidanta ya rasu kafin ta haihu. Haka dai ta ci gaba da renon yaron da abinda ke cikinta, har Allah ya sa ta haihu lafiya. A haihuwa ta biyukuma ta sami mace.

    Tana zamanta da ’ya’yanta, kullum suna wasansu da’yar ƙiriniyar ƙuruciya irin wadda ba a rasa ba, sai ita ma ciwon ajali ya kama ta. Ta kwanta jinya, sai ta kira ɗanta tace da shi: “Jikina yana gaya mini ciwon nan ba na tashi ba ne.

    Don haka ga ƙanwarka nan, ba ta da kowa a duniyar nan sai kai, ka kula da ita.” Sai ya ce da uwar: “Zan yi bakin ƙoƙarina.” Bayan ’yan kwanaki kaɗan sai ta ce ga garinku nan. Yaran nan ƙanana su biyu suka zama marayu, da ma kuma duk dangin iyayensu sun mutu. Suka zama dai ba su da kowa.

    Duk da cewa yaron nan bai gama ƙwari ba, amma a kullum da safe sai ya shiga daji ya farauto ƙananan dabbobi, ya tsinko ’ya’yan itatuwa su ci, su ƙoshi shi da ƙanwarsa. Haka dai ya ci gaba da renon ƙanwarsa; duk sanda ta fara kuka irin na yarinta, sai ya shiga yi mata waƙar lallashi, yana cewa:

    “Yi shiru ’Yar’auta,

    Ba ni da kowa sai ke,

    Ba ki da kowa sai ni.

    Baba ya tafi tun bara,

    Iya ma ta tafi tun bara,

    Kuma ba su dawo ba.

    Ba dangin uwa, balle na uba,

    Yi shiru ’Yar’auta,

    Yi shiru ƙanwata.”

    Duk sanda ta ji ya yi mata wannan waƙa sai tayi shiru, komai zafin kukan da take yi. A duk lokacin da zai fita daji farauta kuma sai ya ɓoye ƙanwar har ya je ya dawo, kullum haka wata da watanni, har dai ya saba da namun daji, kuma sun lura yakan zuba wani abincin da ya samu a daji a cikin jakarsa ya tafi da shi ƙauyensu.

    Wata rana da ya je farauta ya gama, sai namun daji suka tsare shi da hira. Suna cikin hira sai Zaki yace da shi: “Amma kullum na ga idan ka sami abinci, kakan tafi da shi a jakarka. Ina kake kai wa ne? Ko kana da iyaye ne da kake kai musu?” Sai yaro ya ce ai ba shi da kowa illa ƙanwarsa ɗaya da iyayensu suka rasu suka bar su tare, ya kare da cewa: “Ita nake kai wa abincin nan.”

    Jin wannan bayani ya sa duk suka tausaya masa. Sai ya yi ban kwana da su, ya tafi gida. To ashe Kura ta laɓe ta ji abin da ya faɗa. Wata rana yaro ya tafi farauta kamar yadda ya saba, sai Kura ta laɓaɓa ta je gidansu, ta gano inda ya ɓoye ƙanwarsa ta kama ta ta cinye.

    Da ya dawo gida ya nemi ƙanwarsa inda ya ɓoye ta domin ya ba ta abinci, sai bai gan ta ba, ya kama kuka, ya dai ƙara bincikawa ko ya ganta, amma abin ya ci tura. Amma da ya ɗan duba bayan daki, sai ya ga jini-jini a inda Kura ta cinye ta. Ganin haka ya sa ya koma daji, ya tara namun daji yana tambayar su wanda ya cinye masa ƙanwa daga cikinsu.

    Duk namun dajin da ke wurin kowanne ya ce ba shi ya cinye masa ƙanwa ba. Sai Kurege ya ba Zaki shawara yace: “Ya shugabanmu, ni ina ganin abin da ya kamata ka yi shi ne duk naman dajin da ya je shan ruwa bakin rafi ka tsaya a wurin ka sa ya amayar da abin da ya ci mu gani.”

    Zaki ya amince da wannan shawara, sauran namun daji ma suka yi murna da ita. Da kowa ya yi amai a bakin rafi ba a ga wanda ya yi aman yarinya ba. Har za a baje kowa ya kama hanyarsa, can sai aka ga Kura ta taho tana ɗingishin ƙarya, wai ba ta da lafiya.

    Sai aka gaya mata abinda ake yi, sai ta ce: “Ni da ba ni da lafiya, tun safe ban ci komai ba, balle in yi amai.” Da namun daji suka ji haka sai suka yi shiru. Can sai Kurege ya dubi Zaki ya ce: “Manyan Dawa, da gaskiya ne ba ta ci komai ba, me ya sa za ta zo shan ruwa?Karya take yi; ai dole ta kakaro aman ko da cikinta ba komai.”

    Duk sauran namun dajin nan sai suka ce da Zaki maganar Kurege gaskiya ce. Sai Zaki ya harari Kura, ya daka mata tsawa yace: “Dole sai kin yi amai mun gani; idan ba haka ba kuwa yanzu in kashe ki, mu cinye namanki.”

    Nan da nan Kura ta yi amai, sai ga yarinyar ta fado. Da yaro ya ga Kura ta yi aman ƙanwarsa sai ya ce: “Shi kenan, gaskiya ta tabbatar cewar da aka yi Kura ma-ci amana ce.” Kafin ka ƙifta ido sauran namun dajin nan sun far mata, suka yagalgala ta. Shi kuma yaro ya ɗauki ƙanwarsa, ya wanke ta, sai ga ta ta tashi sumul kamar ba a taɓa ta ba, sai ya sa ta a gaba suka kama hanyar gida.

    Haka ya yi ta renon ta har ta girma, aka aurar da ita. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Gaskiya dokin ƙarfe ce.
    • Karya fure take ba ta ’ya’ya.
    • Macuci ƙarshensa kunyata da halaka.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Tatsuniyar Wata Mata Da Aljani

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata mata a wani ɗan ƙauye, wadda ta jima tare da mijinta, amma ba su sami haihuwa ba. Sun nemi maganin samun haihuwa, amma ba su sami biyan buƙata ba, sai suka dangana.

    Ana nan, ana nan, wata rana matar ta je gona tana noma, sai ta ji kukan yaro a gindin wata bishiya. Da ta matsa kusa, sai ta ga wani jariri a cikin tsumma, sai ta ɗauke shi ta goya, ta kuma ɗauki fartanyarta, ta koma gida.

    Da mijinta ya dawo sai ta ɗauko jariri ta kawo masa, tace da shi: “Da man ina da kwantaccen ciki, shi ne yanzu ka ga na haihu a gona.” Mijin ya yi shiru, yana tunani, sai ya ce: “Anya kuwa ke ce kika haifi jaririn nan?” Ta dage cewa ita ce ta haife shi.

    Sai ya ce: “To mun gode wa Allah.” Suka ci gaba da renon yaro, amma duk sanda suka je gona da shi sai ya riƙa kuka ya hana su aiki. Da matar ta ga haka na faruwa kullum, sai ta je cikin danginta ta ɗauko ƙanwarta domin ta riƙa renonsa a gida idan sun tafi gona ita da mijinta.

    Rannan mai gida da matar suka tafi gona suka bar yaro a hannun mai reno. Can sai mai reno ta ga yaron ya rikiɗa, ya zama babban mutum, sai ya yi aman ’yan mata goma sha biyu. Ya buɗe rumbu, kuma ya fito da hatsi suka sussuka suka niƙa, sai ya kwashe garin ya barbaza shi a tsakar gidan; sai kuma ya haɗiye ’yan matan, ya rikiɗa ya koma ƙaramin yaro.

    Can da mai gida da matar suka dawo, suka ga ɓarnar da aka yi musu, sai matar ta kama ƙanwarta da duka wai ta yi mata ɓarna. Yarinya tace ba ita ba ce, yaron ne. Sai yayarta ta ce: “Ta yaya wannan ƙaramin yaro zai buɗe rumbu, ya ɗebo hatsi, ya sussuƙa shi ya niƙe ya zubar?” Ba su dai yarda da bayanin yarinyar ba.

    Haka dai, kullum idan sun fita sai ya yi wata ɓarna, kuma sai matar nan ta doki ƙanwarta. Wata rana matar ta kama ƙanwar tana duka akan ɓarnar da yaron ya yi, sai wata tsohuwa ta kira ta tacemata: “Wannan duka da kike yi wa ƙanwarki fa ba ta da laifi.

    Wannan yaron da yake gidanku ba ki sani ba tsohon aljani ne kika kawo gidan.” Mamaki da tsoro suka kama matar, amma sai tsohuwar ta ci gaba da bayaninta tana cewa: “Idan kina son ki tabbatar, gobe kada ku je gona; bayan gari ya waye ku fita ku ce za ku gona; sai ku zo ku ɓuya a gidana, za ku ga komai da idanunku.”

    Sai ta ce: “To. Allah ya nuna mana goben.” Da gari ya waye mijin da matar suka shirya, kamar za su gona. Da suka fita sai suka ɓuya a gidan tsohuwa. Bayan wani ɗan lokaci sai suka ga yaron ya rikiɗa, ya zama babba; suna gani ya buɗe bakinsa ya yi aman ’yanmata goma, nan da nan ya hau rumbu ya buɗe ya ɗebo hatsi, nan take ’yan matan nan kuma suka sussuƙe hatsin, suka niƙe shi, suka shiga watsar da garin a cikin gida, suna yi suna waƙa.

    Da matar ta ga abin da yaron ya yi sai ta gaya wa mijinta gaskiya da cewa, ai da ma ba ɗanta ba ne, kuma a gona ta tsince shi. Sai mijin ya ce: “Tun farko daman na yi shakka, ga shi ta tabbata ƙarya kika yi mini.” Sai ta faɗi tana kuka, ta shiga hurwa tana ba shi haƙuri, tace: “Ai da wannan ɗa, gara mu zauna babu.”

    Da tsohuwa ta ga abin da ke gudana tsakanin mijin da matar, sai ta ce: “Yanzu abin da za ku yi domin ku rabu da wannan masifa shi ne, ku samo akuya da ƙwaikwaye guda
    bakwai, sai ku ce za ku je ganin gida. Bayan kun kama hanya kun shiga daji, sai ku sami gindin tsamiya ku ce za ku huta.

    Idan kun shimfiɗe yaron sai ku ajiye ƙwaikwayen nan bakwai a gefensa ku ɗaure akuyar a jikin tsamiyar. Can sai ku ce kun yi mantuwa.” Ta ce da su: “Kuna jin abinda nake faɗa?” Suka ce: “Muna ji sarai.” Ta ci gaba da ce wa matar: “Ki ce za ki koma gida ki ɗauko abin da kika manta.

    Daga nan kada ki dawo. Jim kaɗan shi ma mijinki sai ya ce zai bi sawunki saboda kin daɗe. To idan kun tafi kada ku koma; da zarar ya ga kun daɗe zai tashi ya tafi abinsa”. Sai suka yi wa tsohuwa godiya suka koma gida. Da gari ya waye sai matar nan da mijinta suka ce za su ganin gida, sai suka samo duk abubuwan da tsohuwa tace su nemo.

    Da lokacin tafiya ya yi sai suka kama hanya har suka isa gindin wata tsamiya, sai mijin yace ya kamata su huta a nan; suka ɗaure akuya a gindin bishiya suka zauna, can sai mijin ya ce: “Kash!, mun yi mantuwa.”Sai matar ta ce: “To bari in je in ɗauko.”

    Mijin ya ce: “To gara ki yi sauri.” Bayan matar ta tafi, sai ya ce ta daɗe, bari ya bi sawunta. Shi ma ya tashi ya bar wurin. Da ya yi nisa sai ya ɓuya. Yana nan yana kallon gindin tsamiya, can sai ya ga yaro ya rikiɗa ya zama tsoho tukuf da sanda; sai ya kunce akuyar, ya riƙe a hannunsa; kuma ya ga ya ɗebi ƙwaiƙwayen nan bakwai ya kama hanya ya shiga ƙungurmin daji.

    Da mijin nan ya ga haka, sai shi ma ya juya, ya kama hanyar gida. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa
    • Ƙarya da ha’inci masifu ne da ke iya ɓata zamandaakadaɗe cikin amana.
    • Neman afuwa da lafiya su ne kaɗai ke iya magance matsala a zaman amana.
    • Tsintacciyar mage ba ta yin kyanwa.
    • Ƙarya fure take, ba ta ’ya’ya.
    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.
    Danna nan don karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta
    Edita@rumasau-kallamu