Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani gari wai shi Shadafi. Mutanen wannan garin koyaushe suna zaune cikin tsoro, saboda wata dodanniya da takan cinye duk wanda ya fita waje daga faɗuwar rana har gari ya waye. Ana nan, ana nan, sai dodanniyar nan ta lura takan zagaye garin baki ɗaya ba tare da ta sami wanda za ta cinye ba.

    Sai ta dinga yi wa kanta kirari tana cewa:

    “Wa zai iya da ni,

    Ni dodanniya,

    Wa zai ja da ni,

    Ni dodanniya.”

    Kowa ya yi shiru, ba wanda ya taɓa tanka mata, ko da sau ɗaya. Kwanci tashi, sai kawai wata rana wani baƙon saurayi ana kiran sa Auta ya je garin yawo. Da ya nemi masauki, sai kowa ya ki saukar da shi a duk faɗin garin, sai can dai wani tsoho ya ce masa zai ba shi masauki a wani gidansa da ba kowa a ciki, idan ba ya jin tsoro.

    Sai saurayi ya ce wa tsoho shi ba ya fita hira. Sai tsoho ya ce da shi to kada ya fita da daddare, domin idan ya fita, to tasa ta kare, saboda ƙila dodanniyar nan da ta addabi garin ta cinye shi. Saurayi ya yi murmushi, ya dubi tsoho ya ce: “Ba abin da zai sami mutum wanda Allah bai nufa ba.”

    Tsoho ya raka shi masaukinsa. Suka yi sallama tsoho ya koma gida, ya bar shi. Ko da suka rabu sai Auta ya zaro wata doguwar wuƙarsa ta farauta ya wasa, ta yi kaifi. Daga nan ya ɗauko wata ƙatuwar fitila, ya ajiye. Can cikin tsakiyar dare, sai ga dodanniya ta fito tana cewa wa zai iya ja da ita a garin nan, “Wa zai iya bugawa da ni, ni dodanniya?”

    Da Auta ya ji, sai ya kunna fitila, ya ajiye a daf da bakin ƙofa, ya ɗauko wuƙa ya riƙe a hannu. Sai ya kare inda zai tsaya da wani tsumma don kar fitila ta haska shi. Sai ya buɗe kofa, ya dubi inda dodanniya take, ya ce mata: “Ga ni, ni ne Auta, ni zan iya ja da ke; kuma in tsiya ce, har ma na fi ki.”

    Kafin ka ce kwabo ta zo da gudu, buguzum-buguzum, wai kar ya gudu ta rasa nama. To da man ido ɗaya ne da ita, kuma sai ta karkata kai ta leƙa ɗakin da idon da ke gani. Ba ta ga Auta ba saboda yana cikin duhu, haske kuma ya kashe mata idonta mai rai. Tana sa kai, sai ya sa wuƙarsa mai kaifin gaske ya cake idon mai kyau.

    Zafin dafi da kaifin sihirtacciyar wuƙar farautar nan ya kama ta; ta kiɗime, ta yi wani namijin ƙarajin da ya cika gari. Iskar bakinta ta karya dangar karan gidan da ɗan Auta ke ciki. A nan take muguwar ta faɗi, ta shiga birgima. Can sai ta yi wani irin gwauron numfashi, na fitar rai. Haka dai ta mimmiƙe a mace.

    Da gogan naka ya ga ta mutu, ba ta sauran motsi, sai ya tuɓe takalminsa ɗaya, ya ɗora a kan mushen muguwar. Ya shiga ɗaki, ya garƙe ƙofa, ya kwanta ramuwar barci.Da gari ya waye, rana ta daga kowa ya fito a garin sai ya ga dodanniya shirim, ba su san ta mutu ba. Duk wanda ya gan ta kwance sai ya gudu gidan Sarki ya ba shi labari.

    Daga bisani Sarki ya fito, ya je ya ga dodanniya a mace, ga wuƙa an caka a idonta, ga kuma takalmi ƙafa ɗaya a kan ruwan cikinta. Sai Sarki ya ce duk mutumin da ya zo da irin wannan takalmin, to shi ya kashe ta. Aka nemi gano ko wane ne, amma aka rasa saboda Auta yana ɗaki yana biyan bashin barci.

    Can hayaniyar jama’a ta sa ya farka, kuma da ya gane abin da ake yi, sai ya fito da ɗaya takalmin; ya je kan mushen dodanniyar, ya zare wuƙar da ya caka mata a ido; ya goge jinin jikinta, ya zaro kuben wukar, ya sa ta a ciki. Daga nan sai ya shiga masaukinsa, ya ɗauko jakarsa zai tafi.

    Duk abubuwan nan da ya yi, har ya gama bai ce wa kowa komai ba. A nan ne fa Sarki ya kira shi, ya tambaye shi daga inda ya fito ya zo garin nan, domin sun jima suna wahala saboda dodanniyar nan, ba tare da sun san da jarumi kamarsa a garin ba. Auta ya ce wa Sarki da mutanen garin su gode wa Allah da tsohon da ya ba shi wurin kwana, domin da bai ba shi ba, da ya bar garin ya wuce.

    Sai Sarki ya ce su tafi gida. Da suka isa, Sarki ya yi masa kyauta mai yawa; ya raba garin biyu ya ba shi rabi, kuma ya naɗa shi Sarkin yaƙin ƙasarsa. Auta ya zama babban jarumi wanda, a dalilinsa aka sami zaman lafiya da walwala a garin.

    Yanzu haka ma duk da ya tsufa, masana kan ce ya fi Iliya Ɗan Maiƙarfi iya yaƙi. Wasu kuma suka ce da kaɗan Sarkin Yaƙi Ganɗoki ya fi Auta gwaninta da jiƙuwa da magunguna. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri danƙo ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • Zaman duniya cuɗe ni in cuɗe ka ne.
    • Komai ya wuyato akwai maganinsa.
    • A karɓi baƙo da mutunci saboda gobe.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Tatsuniyar Samarin Ɓarayi Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani gari wai shi Komayya da ke kusa da Dajin Dila na yamma da ƙoramar Kada, akwai wasu samari su uku. Ɗaya ana kiran sa Ba-ka-son Asara; na biyunsu kuma Ɓarna; na uku Wayo.

    Kullum ba su da aiki sai su shiga gonakin mutane su tono rogo, ko su yi ta karya dawa ko gero ko masara, su je wani gari su sayar. Yau da gobe, abu ya ishi mutanen gari, har aka ɓullo da dabarar yadda za a kama ɓarayin nan.

    Da suka san an kafa doka a garin, sai Wayo ya ba su shawara a kan su je garin da ba a san su ba, su nemi abin yi. Suka yarda da wannan shawara, suka nufi wani gari. A wannan gari sai da suka yi shekara bakwai suna neman kuɗi, ba sa raba asusu.

    Sannu a hankali, suka tara kuɗin da suka cika asusunsu maƙil. Ganin sun sami kuɗi, sai suka yanke shawarar komawa gida. Da ranar tashinsu ta zo, sai suka kama hanya, har dai Allah ya kai su garinsu lafiya.

    Bayan sun isa gida, ba su ko shiga gari ba suka tarar da wata tsohuwa tana aikin sabulu. Sai suka ba ta ajiyar kuɗin a kan idan sun yi wanka, za su karɓa, tare da sharaɗin cewa kada ta ba kowa daga cikinsu kuɗin, sai su duka ukun sun haɗu.

    Tsohuwa ta ce: “To, ku da abin ku, ai yadda kuka ce za a yi.” Ta karɓi kuɗi, ta ajiye musu. Ko da suka shiga wurin wanka, har sun tuɓe kayansu, sai suka tuna ba su da sabulu. Sai suka sa Wayo ya je ya karɓo.

    Da Wayo yaje gun tsohuwa, sai ya ce mata: “Wai ki ba ni, ma’ana kuɗin.” Sai tsohuwa ta rantse, ta ce atafau, ba za ta ba shi ba. Sai Wayo ya koma ya sanar da ‘yan’uwansa, wai ta ce ba za ta bayar ba.

    Jin bayanin Wayo, sai suka je gaba ɗaya suka ce da ita: “Ai mu ne muka ce.” Da ta ji daga bakinsu, sai ta ɗauki kudi ta ba Wayo. Da kuɗi suka shiga hannunsa, sai ya kama hanya, ya gudu. Suka jira, kamar zai zo yanzu ne, ko sai an jima ne, shiru.

    Saboda sun gaji da jira, sai suka fito suka tambayi tsohuwa: “Ba ki ba shi sabulun ba ne?” Sai tsohuwa ta ce: “Wane irin zancen banza kuke yi, bayan kun ce in ba shi kuɗi, yanzu kuma ku ce sabulu?”

    Da jin kalaminta sai suka tubure a kan cewa ba ta isa ba, sai ta nemo shi su amshi kuɗinsu. Daga nan sai suka tafi wurin alƙali. Alƙali ya tambayi tsohuwa yadda aka yi. Ta kwashe labarin abin da ya faru ta gaya masa.

    Sai alƙali ya ce ta je ta nemo musu kuɗinsu a cikin kwana uku. Tsohuwa ta fita da kuka, tana tafiya. Sai ta haɗu da wani mutum, ya tambaye ta abin da ya faru. Sai tsohuwa ta ce: “Gara mutuwa da abin da ya faru da ni.”

    Daga nan ta yi masa bayani daki-daki, ta gaya masa abin da ya faru sarai. Da ta gama, sai ya ce da ita: “Ai wannan abu mai sauƙi ne.” Ta ce: “Kamar yaya fa?” Sai mutumin ya ce: “Ki koma wurin alƙali ki ce masa kin samo kuɗin.

    Idan ya ce ina suke, ki ce suna nan, amma sai samarin nan sun haɗu su uku kafin ki ba su.” Tsohuwa ta yi godiya. Washe-gari ta koma wurin alƙali, ta gaya masa cewa kuɗi sun samu, kamar yadda mutumin ya gaya mata, tare da bayanin cewa amma ba za ta bayar ba sai samarin nan sun hadɗ su uku.

    Alƙali ya ce: “Kina da gaskiya. Ku kuma samari sai ku yi ƙoƙari ku samo ɗan’uwanku, ku zo gaba ɗaya, don ku karɓi kuɗinku.” Daga nan kowa ya watse, samari suka tafi cikin ɓacin rai, ita kuma tsohuwa ta tafi da murna.

    Shi kuma Wayo yana tafiya har rana ta fadi. Sai ya yanke shawarar zai bi ta wata gajeriyar hanya, wadda ta ratsa ta cikin ɗaya daga gonakin da sukan je sata a da. Bai san cewa masu gona suna fakonta ba don yawan rogonsu.

    Saboda haka yana shiga gonar zai wuce sai suka auka masa. Yana zaton abokansa ne suka gan shi, sai ya zura da gudu. A garin gudun tsira sai ya jefar da jakar kuɗi; ko garin ma bai shiga ba, ya wuce. Masu fako a gonar rogo suka ɗauki kuɗi.

    Ba tare da wata fargaba ba suka rabe kuɗin tsakaninsu. Da wani daga cikinsu ya yi lissafi, sai ya gano kuɗin sun yi daidai da masararsu da rogonsu da dawarsu da wakensu da dai sauran amfanin gonakin da aka sace musu aka sayar.

    Daga ƙarshe dai suka ce kuɗin nan sakamako ne daga Allah. Biyu daga cikinsu sai suka sayi shanun turka, ɗaya kuma ya ƙara gona. Yanzu haka suna can suna cin duniyarsu. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a cin amana a kwana lafiya.
    • Ba da umarni a duƙunƙune ba da cikakken bayani ba yakan janyo asara.
    • Duk wayonka akwai wanda ya fi ka wayo.
    • Wayo a kan rashin gaskiya wauta ne.
    • Kowa ya ɗauko da zafi, bakinsa.
    • Dubu ta cika.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Muwa Muwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Muwa Muwa

    Tatsuniyar Muwa Muwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani daji an yi wata raƙumar dawa mai suna Muwa. Ba ta da ɗa ko ɗaya. Kullum in ta dawo daga kiwo, sai ta yi ta kuka saboda rashin haihuwar nan. Cikin ikon Allah rannan sai ta haifi ‘ya’ya huɗu. Saboda murna ta raɗa wa babban cikinsu suna Muwa Muwa, mai bi masa kuma Caccikarimba, na ukunsu kuma Malaladumba.

    Amma sai ta ƙi raɗa wa na huɗun suna, don ya fito a rame, ba ta son sa. Saboda yawan son ‘ya’yanta nata uku, sai ta gina musu ɗaki, ta saka su don kada ruwa da ƙura su taɓa su, amma sai ta bar ƙaramin a waje, ko ya mutu, ko ya yi rai, babu ruwanta.

    Kuma sai ta ce wa ‘ya’yanta ukun: “Idan kun ji muryata, ku buɗe ƙofa; idan ba muryata ba ce, to kada ku buɗe.” Kullum idan ta dawo daga kiwo sai ta ce: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai su fito su sha, su koma.

    Wata rana, Kura ta zo wucewa sai ta ji raƙumar nan tana cewa: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai suka fito suka sha, suka koma. Bayan uwarsu ta tafi, sai Kura ta zo bakin ƙofar da ƙatuwar murya mara daɗi ta ce:

    “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.” Sai yaran suka yi ihu, suka ce: “Ba muryar mahaifiyarmu ba ce.” Sai wannan abu ya sa Kura ta ji haushi ta bar wurin, tun kafin raƙumar ta koma wajen ‘ya’yanta.

    Kura na tafiya sai ta haɗu da wani Biri mai ba da magani. Sai ta ce idan dai gaskiya ne yana ba da magani, to ya mayar da muryarta kamar ta raƙumar dawar nan. Sai Biri ya nuna mata yin haka abu ne mai sauƙi a gare shi, amma da sharaɗin ba za ta ci komai a hanya ba, domin idan ta ci, muryarta za ta koma kamar da.

    Kura ta ce ta yarda. Sai Biri ya ba ta magani, da ta yi magana sai ta ji muryar kamar ta Muwa. Kura ba ta doshi ko’ina ba, sai wurin ‘ya’yan Muwa. Daga zuwanta sai ta ce: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.”

    Sai suka buɗe ƙofa, sai Kura ta yi wuf ta cinye su, ta tafi abinta. Ashe ƙaramin da uwar ba ta so, watau ramammen nan, yana ganin ta. Can da raƙumar ta dawo ɗakin ‘ya’yanta sai ta yi kamar yadda ta saba: “Muwa, Muwa zo ka sha, Caccikarimba zo ka sha, Malaladumba zo ka sha.”

    Sai da ƙaramin ya bari ta gama kiran su baki ɗaya, sai ya dube ta ya ce:”Muwa, Muwa ba ya nan, Caccikarimba ba ya nan, Malaladumba ba ya nan.” Sai uwar ta ce: “To, kai ɗin ma zo ka sha.” Sai ya je ya sha nononta, kuma daga wannan rana ta shiga son sa, har ya zamana in za ta fita kiwo sai su fita tare. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Bai kamata a nuna bambanci tsakanin ‘ya’ya ba, domin Allah kaɗai ya san mai amfani cikinsu.
    • Wuya maficiya ce.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.
    • Bora ya koma mowa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Tatsuniyar Abotar Biri Da Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Biri da kullum yakan je rafi wanka, bayan ya gama yawon cin ‘ya’yan itatuwa da tsalle-tsallensa ya gaji. Wata rana ya je wanka rafin da ya saba zuwa, sai ya haɗu da wani Kifi a cikin ruwa. Sai Kifin ya nemi su ƙulla abota da Birin. Biri ya amince, kuma suka yi wa juna alƙawari ba za su ci amanar junansu ba.

    Suna nan, abotarsu ta yi ƙarfi. Wata rana sai Biri ya ce zai je ganin gida, watau a can wani daji da danginsa suke. Da Kifi ya ji haka, sai ya shirya wa Biri kayan tsaraba, ya ba shi; suka yi ban kwana, Biri ya kama hanya, ya tafi. Bayan ya tafi, sai sauran kifayen da suke cikin ruwa suka fara gunaguni wai su ba su son abokinsa Biri.

    Har ma dai sauran kifayen suka shirya taro a ɓoye. A wurin taron waɗansu kifaye suka ce a kashe Biri, ko a kashe Kifin da ke abota da Biri. Sai babban kifayen ya ce: “A a, ba maganar kisa, domin kisan kai zai jawo gaba mara amfani tsakaninmu kifaye, ko kuma tsakaninmu da Birai.”

    Haka dai suka ci gaba da shawarwari, har wani ya kawo shawarar cewa a kira Kifi a gaya masa za a ba shi sarauta a fadar Sarkin Kifaye, amma sai ya zo da zuciyar abokinsa Biri kafin a naɗa shi. Duk suka amince da wannan shawara. Aka kira Kifi abokin Biri, aka yi masa bayani.

    Da ya ji bayanin da kifaye suka yi masa, sai ya ce da su: “Amma fa ni da Biri mun yi alƙawari ba za mu ci amanar juna ba. Kuma ni ba zan iya cin mutuncinsa ba idan aka ba ni sarautar.” Sai Kifi abokin Biri ya ce da danginsa kifaye su bari Biri ya dawo daga ganin gida, ya san zai yi duk yadda ya nemi ya yi.

    Suna nan, sai Biri ya dawo daga tafiya, sai ya je wajen Kifi kamar yadda ya saba, ya kai masa tsarabar da ya zo da ita daga gida. Suka gaisa sosai, kuma suka shiga hira. Can sai Kifi ya sanar da Biri cewa bayan ya yi tafiya ‘yan’uwansa kifaye sun ce za su ba shi sarauta, ya zama Sarkin Kifaye.

    Da Biri ya ji haka sai ya ce: “Kai, amma wannan labari da daɗi yake.” Sai Kifi ya ce: “To amma fa za ka raka ni cikin ruwa don ka gaishe su.” Biri ya ce: “To, ai sai mu je.” Suka yi nutso, har wajen taron kifaye. Sai abokin Biri ya ce: “Amma fa abokina, an ce sai na kawo wani abu kafin su ba ni sarautar.”

    Da Biri ya ji haka, sai ya dubi Kifi ya tambaye shi: “To mene ne suke so? Ka ba su mana.” Kifi kuma ya ce da Biri: “Ai abin da suke so a jikinka yake.” Biri ya ce: “Mene ne, fadi zan ba ka.” Sai Kifi ya ce: “Sun ce in kai musu zuciyarka ne.” Sai Biri ya ce: “Ai don wannan babu komai, zan ba ka.

    Amma ka san ba na yawo da zuciyata; tana can a kan bishiya na rataye ta. Bari in je in ɗauko maka.” A cikin murna Kifi ya ce: “To.” Ya raka Biri har bakin ruwa domin ya je kan bishiya ya ɗauko zuciyarsa ya kawo wa Kifi a nada shi sarauta.

    Da Biri ya samu ya fita daga cikin ruwan, sai ya hau bishiya ya ceda Kifi: “Daga yau ba zan sake abokantaka da kai ba. Kuma ba zan sake shiga ruwa ba.” Da wannan dabara Biri ya gudu. Shi ya sa har yau din nan Birai ke tsoron shiga ruwa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kowa ya ɗauki amana ya kamata ya riƙe ta da gaskiya.
    • Hassada ga mai rabo taki ce.
    • Kafin ka ga biri, biri ya ganka.
    • Dabara kashin kwance.
    • Iya ruwa, fidda kai.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Tatsuniyar Cin Amanar Ɗan’uwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ‘ya’yansa guda biyu. Suna nan, suna nan, sai wata rana babansu ya tura su neman furannin ƙawa. An ɗauka cewa duk wanda nasa ya fi kyau, to mahaifinsu zai fi nuna masa soyayya a gidan, kuma za a yi masa aure. Shi ke nan, sai suka je. Da suka je, sai ƙaramin ya tsinki fure mai kyau.

    Da yayansa ya gani, sai ya ƙwace, sannan kuma ya kashe shi. Sai ya kai furen nan gida. Sai babansa ya yi masa aure. Daga baya sai babansa ya tambaye shi inda ƙanensa yake, sai ya yi wa uban ƙarya, ya ce masa ya bar shi a baya, kuma zai ƙaraso gida ba da jimawa ba. Ana nan, ana nan, har wuni biyu, yaro bai dawo ba, Mahaifinsu ya jure ya kau da kai.

    Wata rana wani boka ya zo wucewa, sai ya ci karo da ƙashin yaron da aka kashe, ya ɗauka yana hurawa. Sai ƙashin ya fara rera wa bokan nan wannan waƙa: “

    Kai bokan nan kai bokan nan;

    Ƙashina ne kake hurawa.

    Baba ya aike mu daji, Mu samo furannin ƙawa,

    Nawa sun fi na ɗan’uwana kyau,

    Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Da boka ya ji haka, sai ya kai wa Sarki wannan ƙashi. Da Sarki ya hura sai ya ce:“Kai Sarkin nan, kai Sarkin nan, Ƙashina ne kake hurawa. Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, ni da yayana, Nawa sun fi na wana kyau, Sai ya ƙwace nawan, Ya kashe ni.”

    Sai Sarki ya sa a yi shela a sanar da mutanen garin cewa washegari gaba ɗayansu su zo ƙofar fadarsa, domin a tambaye su wanda ya yi wannan ɗanyen aiki. Da suka taru washe-garin, sai kowa ya ce ba shi ba ne. Sai Sarki ya ce, to za a sa duk wanda ke garin ya hura wuta, domin ƙashin zai faɗi wanda ya yi kisan kan.

    Sai aka fara ta kan mahaifin yaron da aka kashe. Da ya hura, sai ƙashi ya ce: “Kai babana, kai babana, Ƙashina ne kake hurawa, Kai ka aike mu daji, Ni da wana, mu samo furanni, Nawa sun fi nasa kyau, Sai ya ɗauke nawan, Ya kashe ni.” Sai Sarki ya ce to ya kira yaron, watau yayan wanda aka kashe.

    Ya zo, aka ba shi ƙashin ƙanensa, da ya fara hurawa, sai ƙashi ya ce: “Kai yayana, kai yayana, Ƙashina ne kake hurawa, Baba ya aike mu daji, Mu samo furanni, Nawa sun fi naka kyau, Sai ka ɗauke nawan, Ka kashe ni.” Sai Sarki ya ce to a kama yaron shi ma a kashe shi. Aka kama shi, aka kashe. Shi ke nan, an yi maganin wanda ya ci amana. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Cin amana kan jawo wulaƙanci.
    • Zafin nema ba shi ke kawo samu ba.
    • Idan Allah ya nufi mutum da arziki ba wanda ya isa ya hana.
    • Alhaki kare ne, mai shi yake bi.
    • Abin da ka shuka, shi za ka girba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Tatsuniyar Ya Tsinci Dami A Kala

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wasu yara su uku abokan juna. Wata rana sun je farauta sai suka kama maciji, suka aiki ƙaramin cikinsu ya nemo wuta domin su babbaka macijin, su ci; ya ce da su ba zai iya ba. Suka ba shi riƙon macijin, suka tafi neman wutar da kansu. Kafin su dawo ya saki macijin.

    Da suka dawo suka ce ina macijin, ya ce maciji ya fi ƙarfinsa, wai sun yi kokawa ya ka da shi a cikin toka, kuma ya gudu. Sai suka ce ba su yarda ba, sai ya biya su. Baki ɗaya suka shiga gari, ba su tsaya ko’ina ba sai a gidan su wannan yaron. Bayan sun yi wa iyayensa bayani, sai mahaifansa suka kori yaron daga gidansu domin a hore shi.

    Ya rasa inda zai zauna, sai ya shiga dajin da sukan je farauta da abokan nan nasa. Yaro ya gina gida a dajin nan, kuma ya faɗa a ransa cewa gara da bai kashe macijin nan ba. Can sai ga macijin nan ya fito, yaro ya gaya masa abin da ya faru. Sai ya ce da yaron ya bi shi gidansu domin su ci abinci.

    Yaro bai yi musu ba; suka kama hanya. To, ashe macijin nan ba maciji ba ne, wani ɗan sarki ne da yakan rikida ya zama maciji idan ya yi nishaɗi. Suna zuwa gidan aka kawo musu tuwo a kwanon tagulla, irin na gidajen manyan tajirai da sarakuna. Yaro bai saba ba, ya ce ba zai ci tuwo a kwanon tagulla ba, sai a cikin ƙwarya.

    Sai aka kawo masa abinci a ƙwaryar, ya kuma cinye shi duka; bai saba da rage abinci ba, kamar yadda akan yi a gidajen sarauta. Da zai kwanta sai aka yi masa shimfiɗa da buzun Sarki, sai ya yi fitsarin kwance a kai. Aka ce masa ya je ya wanke buzun. Yaro ya kama hanyar rafi domin wanke buzun Sarki.

    Amma sai ya faɗa wani gida haka kwatsam, ba tare da ya sani ba. Sai masu gidan suka ce masa in yana jin yunwa tun da sun ga shi baƙo ne, kuma ba su san irin nisan tafiyar da ya yi ba, ya ɗauki shinkafa ƙwaya ɗaya ya dafa; sai ya ɗauka, ya wanke, ya jefa a tukunya, ya ɗora sanwar shinkafa; sai ya ga ta cika tukunya; ya ci, har ya ƙoshi, kuma ya bar saura.

    Bayan ya yi wa masu gidan godiya, sai ya ce da su zai tafi gida. Sai suka ce ya ɗebi ƙwaiƙwaye guda uku, idan ya kama hanya ya fasa ɗaya. Da ya kama hanya ya ɗan yi nisa da gidan nan, sai ya fasa ƙwai ɗaya. Yana fasawa sai ya ga fatu masu yawa masu launi iri daban-daban.

    Sai ya kwasa, bai zame ko’ina ba sai gaban Sarki, da nufin Sarki ya zaɓi wadda yake so, Sarki ya zaɓa. Bayan yaron ya ƙara hutawa, sai ya ce da abokinsa ɗan Sarki, zai tafi. Sai abokin ya ce in babansa, watau Sarki, ya ba yaron kyauta, to kar ya karɓa, kuma ya ce masa ba ya son komai sai zoben da ke hannun Sarkin na hagu.

    Yaro ya matsa kusa da Sarki ya sanar da shi zai tafi. Da Sarki ya ji bayanin yaro, sai ya ce da shi ya faɗi duk abin da yake so zai ba shi. Sai yaro ya dubi Sarki ya ce ba ya son komai sai zoben da ke hannun Sarki na hagun. Sai ko Sarki ya ba shi; ya yi godiya, ya fita waje suka haɗu da abokinsa ɗan Sarki.

    Sai ɗan Sarki ya ce wa yaron nan abokinsa: “A duk sanda ka ji yunwa, sai ka ce zobe-zobe, mai shekara tamanin da takwas, zai ba ka duk abin da kake so.” Shi ke nan, yaro ya yi ban kwana da abokinsa, ya kama hanya.Yana cikin tafiya sai ya fara jin yunwa, kuma ba abin da zai ci. Sai ya zauna a gindin wata bishiya.

    Sai abokinsa ɗan Sarki ya zama maciji, ya same shi ya ce da shi: “Ka manta abin da na gaya maka ka faɗa wa zoben idan kana jin yunwa?” Sai ya tuna masa. Sai yaron ya ce: “Zobe, zoben shekara tamanin da takwas”. Zoben ya ce: “Me kake so?” Ya ce: “Ina son tuwo.” Sai ko ya ga tuwo; ya zauna ya ci har ya ƙoshi.

    Da ya tafi gidansa na ciyawa, sai ya ce: “Zobe, zobe mai shekara tamanin da takwas.” Sai zoben ya ce: “Me kake so?” Sai ya ce: “Ina so gidana ya zama mai kyau kamar na samarin da ke tashe a gari.” Sai ya ga gidansa da ɗakinsa sun yi kyau. Sai ya je gidan babansa ya ce ya zo ya kai su su ga gidansa.

    Sai suka bi shi, suka gano gidan. A gaban iyayensa ya kirawo sunan zobe mai shekara tamanin da takwas, ya sa zoben nan ya mayar da shi saurayi kyakkyawa. Daga bisani a wannan hali na kyau ya je neman aure gidan Sarki. Sarki ya sa masa sharuɗa, watau lallai sai ya kawo shanu masu yawan da ba a taɓa ganin yawansu ba a garin, tare da zannuwan da kamar ba za su ƙare ba saboda yawa.

    Nan da nan yaron nan ya sa zobe mai shekara tamanin da takwas ya kawo duk abin da aka nema. Sarki ya aura masa ‘yarsa. Suna nan, suna nan, sai wata rana yana wurin wanka, sai matar ta sace zoben, ta kai wa babanta. Sai aka kama yaron aka ɗaure. Sai yaron ya aiki kare da kyanwa da ɓera su je gidan Sarki su ɗauko masa zoben nan.

    Da suka je, kare ya ja Sarki da taɗi, kyanwa tana yi wa Sarki wasa, ɓera kuma ya shiga wajen da Sarki ya ajiye zoben, ya sato shi. Daga bisani suka yi sallama da Sarki, suka kama hanya domin su kai wa yaron nan zobe. Suna cikin tafiya, sai suka tarar da wani kogi, wanda dole sai sun haye shi kafin su kai gidan yaro.

    Sai kare ya goya ɓera da kyanwa domin su ƙetare ruwan. A garin tsallaka ruwan, sai zoben ya sulluɓe, ya faɗa cikin ruwa. Bayan sun isa gidan yaro sun gaya masa, sai ya ce su je bakin ruwa su ce da masu kamun kifi suna son hanjin kifayen da suka kama, suka feda. Aka yi ta kawo musu hanjin kifi, har aka ba su wanda zoben ke ciki.

    Sai suka kai wa yaron nan zoben. Da ya kira zobe mai shekara tamanin da takwas ya amsa masa, sai ya tambaye shi abin da yake so. Yaro ya ce ya na so zoben nan ya fitar da shi daga gidan maza, watau kurkukun da aka ɗaure shi a ciki. Nan take ko sai ya gan shi a gidansa. Can kuma sai ya lura da ɓera da kyanwa da kare ma suna nan.

    Sai ya tambayi ɓera abin da yake so. Ɓera ya ce daddawa yake so. Yaro ya tambayi kare abin da yake so ya ci. Kare ya ce yana so ya ci ɗanyen nama. Daga nan kuma yaro ya tambayi kyanwa abin da take son ci; ta ce ƙadangare take muradi. Sai yaron ya ce: “Zobe, zobe.” Kafin ma ya kai ga cewa mai shekara tamanin da takwas a duniya, tuni zoben ya tambaye shi abin da yake so.

    Sai ya ce yana son ɗanyen nama da daddawa da ƙadangare. Kafinya gama rufe baki har ya kawo masa su. Ba tare da jinkiri ba kowa ya ɗauki nasa, ya tafi. Sai yaron ya ce wa zoben yana son ya ga Sarki da matarsa ‘yar Sarki a gabansa suna rawa. Sai ko ya gan su suna rawa. Sai ya ce yana so ya ga sun mutu. Sai suka faɗa wuta, suka mutu. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri ɗanƙo ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • In za ka haƙa ramin mugunta, haƙa shi gajere.
    • Kowa ya yi da kyau, zai ga da kyau.
    • Kowa ya tausayawa wani, shi ma sai Allah ya tausaya masa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Tatsuniyar Ɗan Agwai Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Ɗan Agwai yana kiwon ɗan akuyarsa, har ya girma ya yi ƙiba. Sai wata rana ya kama shi ya kai shi kasuwa. Namun daji da yawa suka yi ta taya ɗan akuyar, to amma da zarar sun ji tarihinsa, sai su wuce, su ƙi saye. Ana nan, ana nan, har labari ya kai ga kunnuwan Kura, uwar son na banza.

    Sai ta shirya, ta je a yi cinikin ɗan akuya da ita. Kura ta ga ɗan akuya ya yi ƙiba, kuma tana so. Sai ta tambaya: “Nawa kuɗin ɗan akuyan nan?” Sai Ɗan Agwai ya ce wa Kura: “Ni fa kokawa ce za ki yi da ni ta kwana bakwai a jere. Idan kullum kina ka da ni har kwana bakwai ɗin a jere, to ɗan akuya zai zama naki.

    Idan kuma kin kasa, to mun dinga yin kokawar ke nan har sai ranar da kika sami nasara.” Sai Kura ta ce: “To na yarda.” Aka tara ’yan kallo, aka ce da su Kura za ta sayi ɗan akuyar Ɗan Agwai. Kowa ya share wuri ya zauna don kallon ciniki. Can sai Kura ta shirya, ta fito fage suka kama kokawa da Ɗan Agwai.

    Kura ta ka da Ɗan Agwai; ta rinƙa cin nasara har tsawon kwana shida. A kwana na bakwai sai Ɗan Agwai ya ka da Kura, ya yi mata shegen duka, har ta kasa tashi. Da ta murmure, da ƙyar ta kai gida. Sai ta ce: “Yau ban fita da sa’a ba.” Washe-gari ta fita, Ɗan Agwai ya sake tiƙa ta da ƙasa, har ta suma.

    Da ta samu aka kai ta gida, washe-gari sai ta ce da ’ya’yanta su ɓoye ta a cikin rumbu, kuma idan an zo neman ta, su ce ta yi tafiya. Da Ɗan Agwai ya yi jira a fagen kokawa, shiru bai ga Kurar ba kuma babu labarinta, sai ya je gidanta, ya yi sallama, amma sai ’ya’yanta suka ce mahaifiyarsu ta yi tafiya.

    Sai Ɗan Agwai ya ce: “To, amma bari in ɗan buɗe rumbun nan, don in ga hatsin da ke ciki.” Kafin yaran su hana, Ɗan Agwai har ya buɗe rumbun, ya leƙa; sai ga Kura a cikin rumbun. Sai ya ciro ta, ya kai ta fagen kokawa. Suka fafata; ya ɗauke ta sama, ya danƙara ta da ƙasa. Daga ƙarshe dai Kura ta koma gida, da rarrafe.

    Da ’ya’yanta suka ga haka, sai suka ce: “Baba, wannan sai fa mun nemi asirin da za ki sha ki sami nasara, in ba haka ba, wannan Ɗan Agwai zai kashe ki.” Washe-gari tun da sassafe suka shirya, suka tafi gidan wani boka neman asirin samun nasara a kan Ɗan Agwai. Da suka isa, suka yi wa boka bayani, sai ya ce: “Babu magani, amma akwai wata dabara ɗaya da zan taimaka muku da ita.”

    Suka yi shiru, suna ji. Sai ya ce: “Akwai wani mutum mai suna Mai-barci-bana ya tashi-baɗi; yana can a ɗakinsa yana barci. Yadda ake ta da shi shi ne, za a samo garwashin wuta a kai ɗakinsa, sai ku je ku ce da Ɗan Agwai: ‘Ga wani zai yi cinikin ɗan akuyarka da kokawa.

    A guje zai yarda zai bi ku; idan kun isa ɗakin mai barcin, sai ku zuba barkono a wuta, ku fita, ku bar su.’” To, da ma duk wanda ya ta da shi daga barci, sai ya kashe shi, muddin ya je kusa da shi. Sai suka je suka shirya yadda boka ya gaya musu. Kuma suka kawo Ɗan Agwai ɗakin Mai-barci-bana ya tashi-baɗi suka kulle su tare.

    Can sai hayaƙin barkono ya tashi. Da Mai-barci-bana ya-tashi baɗi ya ji zafin hayaƙin barkono, sai ya ce: “Wane ne yake damu na?” Yana tashi sai ya ga Ɗan Agwai a kansa. Sai kawai ya kashe shi, ya fito ƙofar ɗaki. Sai ya hango Kura gefe tana jiran ta ga abin da zai faru, ya ce mata ta raka shi farauta, yana jin yunwa.

    Kura ta yarda. Suka kama hanya. Da suka shiga daji, sai suka tarar da mutane masu yawa suna noma a gonar Sarki. Sai ya ce: “Ga nama, amma ba zai ishe ni ba. Amma bari mu ɗan taɓa.” Nan take ya kama mutanen nan ya murɗe wuyan kowannensu. Ya tara itace zai gasa, amma babu wuta. Daga nan ya hura bakinsa, wuta ta fito, suka gasa mutanen nan.

    Ya yi wa Kura tayi, ta ce tun da shi ne babba, ya fara ci. Yana cin naman mutanen nan, har ya ƙare, Kura ba ta ci ba. Bayan ya gama, sai ya sa Kura ta samo masa tsinken sakatar haƙora. Ta samo, ta ba shi. Duk sanda ya sakato nama daga bakinsa, sai Kura ta amsa, ta cinye.

    Da haka har ta ƙoshi. Daga nan Mai-barci-bana ya-tashi-baɗi ya ce, su je rafi shan ruwa. Da suka je, ya nemi Kura ta fara sha, ta ƙi, saboda shi ne babba, gara ya fara sha. Da ya kafa bakinsa, sai ya shanye duk ruwan rafin da ya taru a cikin shekara ashirin. Da ya fara cire haƙorinsa sai Kura ta razana, sai ta faɗi ta suma. Da Mai-barci-bana ya-tashi-baɗi ya ga haka, sai ya sa hannu ya ɗauki Kura, ya kama hanyar ɗakinsa. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Duk inda ka kai ga zalunci sai ka haɗu da wanda ya fi ka zalunci.
    • Wani lokaci dabara ta fi ƙarfi tasiri.
    • Kaddara ta riga fata.
    • Kura da shan bugu, gardi da amsar kuɗi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Tatsunyar Ɗan Buwaila Da Ɓangorinsa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani ƙauye wai shi Wake-Wake, kusa da Dajin Aljanu, inda aka yi wata mata mai ’ya’ya biyu, mace da namiji. Wata rana sai mahara suka kai wa ƙauyen Wake-Wake hari. Maharan kuma suna da yawan gaske kuma sun fi zaratan Wake-Wake yawa da tarin makamai.

    Faɗa ya ƙaure, aka yi musu kaca-kaca, ko’ina sai gawarwakin mutanen Wake-Wake ake gani a yashe. Mata da tsofaffi da ƙananan yara suka ruɗe, hankalinsu ya tashi, gigita ta yawaita. Da uwar yaran nan ta ga maharan sun hallaka jama’ar garin masu yawa, sai ta suri ’yarta domin ta kare ta daga ’yan harin.

    Da namijin ya ga haka sai ya ce: “Iya ni ba za ki kare ni ba? Ni ne fa idan na girma zan kula da gonarki, in gina miki gida kuma in tara miki shanu da sauran dukiya.” Sai uwar ta saki ’yar, ta ɗauki namijin. Da budurwar ta ga haka sai ta ce: “Haba Iya, ki kula da ni domin ni ce mai yi miki wanke-wanke da ɗaukar ruwa da shara, in taya ki girki da dai sauran ayyukan gida.

    Idan ba ki kula da ni ba, mahara suka kashe ni, wa zai taimake ki?” Da mahaifiyarta ta ji haka, sai ta ajiye namijin, ta ɗauki yarinyar suka ɓuya inda mahara ba za su gan su ba. Da namijin ya ga haka, sai ya shige cikin ganyen kabewar da ta yi yaɗo, ya ɓuya, ko motsi ba ya yi.

    Numfashinsa ma ba ya ɗaga cikinsa domin gudun kada a ga alamun mai rai a mafakarsa. Can sai ga maharan sun zo wucewa ta kusa da inda ya ɓuya, sai ɗaya daga cikinsu ya ce da sauran: “Kai baraden fama mu duba cikin ciyawar nan, na ji ƙanshin mutum.”Sai Jarmai, watau jagoransu ya ce: “Kai dai wawa ne, yaya mutum zai ɓuya a nan?

    Mu yi gaba mazajen fama.” Sai maganar Jarmai ta janye hankalinsu, ba su duba ba. Yaro dai ya haye hatsarin shan kaifin barandamin barade. Da yaron nan ya tabbatar maharan sun tafi, sai ya fita daga maɓoyarsa. Yana cikin tafiya sai ya ga bishiyar Buwaila. Sai ya faɗa ta da sara.

    Da sara ya fara ratsa bishiya sai ta ce: “Kai yaro, me za ka yi da ni ne idan ka sare ni?” Ko tsorata bai yi ba, sai ya ce: “Zan ci ne idan na sara, yunwa da ƙishirwa sun dameni.” Da bishiya ta ji haka, sai tausayi ya kama ta ta ce: “Zaga ta hannun dama za ka ga tukwane biyar, ɗaya ta abinci, ɗaya ta ruwan sha, ɗaya ta ruwan wanka, ɗaya ta wurin bayan gida, ɗayar kuma ta wurin barci.”

    Murna ta kama yaro ya ce da bishiya: “To, na gode.” Bayan ya ci ya ƙoshi, ya sha ruwa, ya yi wanka, sai ya zauna ya huta. Bishiya dai ta yaba da hankalinsa har dai suka saba. Yau da gobe dai har mutanen gari suka gane dangantakar yaro da bishiyar, sai suka yi masa laƙabi da Ɗan Buwaila.

    Ana nan, ana nan, sai wata rana bishiyar ta ce da Ɗan Buwaila: “Ya kamata ka mallaki dukiyar kanka saboda halin yau da gobe.” Sai ya ce: “Gaskiyarki, duk abin da kika yi mini na gode.” Can sai wata saniya da ke kiwo ta biyo ta kusa da bishiyar, sai bishiyar ta ce da Ɗan Buwaila, “Bugi cikin saniyar nan ka ga abin mamaki.”

    Da ya bugi cikin saniya sai ga shanu masu yawan da ba zai misaltu ba, garke-garke suna tuɗadowa, sai ta ce: “Duk waɗannan shanu fa naka ne.” Bayan wani lokaci, wasu mutanen garin su Ɗan Buwaila suka fara zunɗe suna cewa: “Ta yaya wannan yaro zai fi Sarki dukiya?” Wasu daga cikinsu suka ce: “A sare bishiyar kowa ma ya huta.”

    Kamar da wasa, sai aka yi gayya, aka sare bishiyar. Ɗan Buwaila ya zamanto maraya ba inda zai je neman shawara. A nan ne fa ya kama kuka. Can sai wata jijiyar bishiyar ta ce da shi: “Daina kuka Ɗan Buwaila, ɗauke ni ka ɗasa.” Da ya ɗasa jijiyar sai ko bishiyar Buwaila ta tsiro ta girma, wanda bai sani ba ma ba zai ce an taɓa sare wata bishiya a wurin ba.

    Da mutanen garin suka ga haka, sai suka sare wannan sabuwar bishiyar, suka shiga gari da ita. Sai wani ɓangore na jikin bishiyar ya ƙubuta ya je ya sami Ɗan Buwaila ya ce da shi: “Yanzu dai mutanen garin nan sun gama da ni, gara ka bar garin nan, in ba haka ba kuwa za su kashe ka.”

    Sai Ɗan Buwaila ya ce: “To.” Sai ɓangorin bishiyar ya ce da shi: “Ka ɗauki wannan ɓangori nawa ka tafi da shi duk inda za ka, kuma ka tafi da shanunka sun ishe ka zaman duniya. Kuma ka buga wannan ɓangorin a tsakiyar shanun, za su cure su zama ɗaya. Idan ka je garin da za ka zauna sai ka bugi saniyar da ɓangorin yawansu zai komo.”

    Shi ke nan, Ɗan Buwaila ya shiga tsakiyar shanu ya yi abin da ɓangorin bishiyar ya umarce shi sai shanun suka ɓata, sai saniya ɗaya tak, ya kama hanya. Yana cikin tafiya da saniyarsa ɗaya, har ya kai wani gari ya yi tambaya, aka nuna masa gidan Sarki, ya kuma isa ya yi gaisuwa a fada, sai ya sanar da Sarki buƙatarsa ta neman izinin zama a garinsa.

    Sarki ya yi murna, ya ce da shi: “Ai mu haka muke so jama’armu ta ƙaru.” Ya sa aka gina wa Dan Buwaila gida. Bayan ’yan kwanaki Ɗan Buwaila ya zama ɗan gari, sai ya bugi saniyar da ɓangoren bishiyar nan, sai yawan shanunsa ya komo. Nan da nan kuwa ’yan tsegumi suka ce da Sarki: “Bai dace a ce wani a garin nan ya fi ka dukiya ba.”

    Hassada da sara da suka da haɗa rigingimu dai suka yi yawa, har ta kai fadawa suka ba Sarki shawarar cewa: “Lallai Sarki ka yi wani abu don a ƙure ƙaryar yaron nan domin ya bar garin nan.” Sai Sarki ya yarda, amma fa ba domin ransa yana so ba. Sai ya ba da irin ƙwarya ya ce: “Ku ba shi a ce ya shuka yau kuma ta fito ta girma, ta yi ’ya’ya, ya fafai, a kawo mini duka a yau.”

    Da Ɗan Buwaila ya gaya wa ɓangorin bishiyar Buwaila sai ya ce da shi: “Ba komai, totse ni a ƙasa.” Da ya totse shi, sai ya ga idanu da baki sun fito masa, sai ya ce: “Idan ka je gaban Sarki ka tambaye shi wai ban da shi akwai wani Sarki a garin nan ne? Idan an ce babu, sai ka ce, to saboda me za a ce a kai wa Sarki mai daraja ruwa a cikin ƙwarya mai ɗaci?”

    Ɗan Buwaila ya je fada, a gaban Sarki ya yi yadda ɓangorin ya gaya masa. Sai Sarki ya ce: “Kana da gaskiya, yi tafiyarka.” Amma duk da haka masu suka ba su daina ba.Sai wasu kuma suka zuga Sarki wai a kai wa Ɗan Buwaila rago a ce ya sa shi ya haihu. Idan ya kasa, an ƙure shi ke nan, daga nan sai a kore shi daga garin.

    Sai Ɗan Buwaila ya gaya wa ɓangorin bishiyar; sai ya ce masa: “Ka je fada gaban Sarki kana kuka. Idan ya ce me ya sa kake kuka, ka ce masa an aiko maka cewa babanka yana naƙuda zai haihu. Idan suka ce ba su taɓa jin namiji da haihuwa ba, sai ka ce da su: ‘Ashe kun san ragon nan ma ba zai haihu ba ke nan.”

    Da safe ya ja rago har ƙofar fada ya ɗaure shi, ya shiga sai gaban Sarki, ya faɗi ya yi gaisuwa, yana kuka. Da Sarki ya ga hawaye a fuskarsa, sai ya ce: “Lafiya Ɗan Buwaila?” Sai ya ce da Sarki: “Ka daɗe mai duniya, adali, an aiko mini ne cewa mahaifina yana can yana naƙuda zai haihu.”

    Da fadawa suka ji haka, musamman ma masu yi masa hassada a gaban Sarki sai suka ce: “Ƙarya yake yi, yaya namiji zai yi naƙuda? Ai maza ba sa haihuwa.” Sarki dai bai ce komai ba, amma sai Ɗan Buwaila ya yi farat ya dubi Sarki yace: “To, Mai martaba sun ce maza ba sa haihuwa, amma an aiko mini rago an ce lallai in sa shi ya haihu.

    Ta yaya zan sa rago ya haihu?” Da Sarki ya ji haka sai ransa ya ɓaci, domin fadawansa sun sa ya yi kuskure. Sai Sarkin ya ce: “To, idan haka ne kuwa ina so wane da wane daga cikin fadawana su bar mini ƙasata. Suna nema su haɗa ni rigima da jama’a.” Nan take aka yi waje da su aka kai su can iyaka da ƙasar Wake-Wake.

    Kan tilas suka bi hanyar shiga Dajin Aljanu da ke kusa da Wake-Wake. Bayan kamar wata biyar da yin haka, sai Ɗan Buwaila ya nemi yardar Sarki domin ya je Wake-Wake ya zo da mahaifiyarsa da ’yar’uwarsa, su zauna tare. Sai Sarki ya ce da shi: “An ba ka izinin, idan ka dawo kuma zan aura maka ɗaya daga cikin ’ya’yana.”

    Sai ya yi godiya, ya koma gidansa, ya shirya, ya kama hanyar garinsu Wake-Wake. Ɗan Buwaila ya je ya kawo mahaifiyarsa da ’yar’uwarsa, Sarki kuma ya cika alƙawarin da ya yi masa na aurar masa da ’yarsa, suka zauna cikin farin ciki da jin daɗi, domin ya zama surukin Sarki, babu wani algungumi da zai sake sukar sa a gare shi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Haƙƙin iyaye ne su kula da ’ya’yansu maza ne ko mata.
    • Hassada ga mai rabo taki.
    • Mahaƙurci mawadaci.
    • Nuna jarunta da gwagwarmaya don neman kyakkyawar makoma.
    • Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.
    • Mai arziki ko a ƙwara ya sayar da ruwa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Tatsuniyar Darajar Neman Sani

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani mutum mai suna Duna wanda yake zaune da matarsa Delu a wani ɗan ƙauye da ke kusa da garin su Koƙi matar Gizo, sun jima da yin aure ba tare da Delu ta yi ko da ɓatan wata ba. Mijin dai bai damu ba, ita kuma ta dangana komai ga Mai sama.

    Ana nan sai wata rana Delu ta yi ɓatan wata. Ita da mai gidanta Duna suka yi murna. Bayan wata tara kuma ta sauka lafiya, ta haifi ɗa namiji. Bayan sati guda aka raɗa masa suna Maishuni. Da ya ɗan data, sai Duna ya ce da Delu: “Kin ga dai ga shi mu mun rayu cikin duhun jahilci, ya kamata mu tura Maishuni makaranta.”

    Ta ce: “Haka ne, amma fa ina tsoron kada ya galabaita a can.” Mai gidanta ya rarrashe ta, ta fahimci darajar sani, ta yarda a kai yaro wurin neman sani. Bayan mahaifin ya shirya sai ya ɗauki Maishuni suka tafi ya kai shi wani gari a wata tsangaya, ya haɗa shi da wani babban masani; ya kuma shiga cikin ƙolaye.

    Da Duna zai tafi sai ya ce da ɗan: “Ko da bayan na rasu, idan ka dawo gida kana so ka gane mahaifiyarka, sai ka yi cigiya. Duk wadda ta ce ita ce sai ta gaya maka a inda ta haife ka.” Yaro ya yi shiru yana saurare. Da uban ya gama sai ya ce: “To, me za ta faɗa in gane ita ce?” Sai mahaifinsa ya ce: “Idan ta ce a tsakar ɗaki ta haife ka, to ita ce mahaifiyarka.”

    Ya yi ban kwana da Maishuni ya koma garinsu. Uban bai fi wata tara da komawa ba sai ya rasu. Delu ta yi baƙin ciki matuƙa, domin ba ta san garin da mai gidanta ya kai ɗansu karatu ba. Ta cigaba da zama cikin haƙuri. Ana nan bayan kamar shekara ashirin da bakwai, sai Maishuni wanda tuni ya zama babban malami, kuma mai dukiya, ya ji yana son zuwa ganin mahaifarsa.

    Amma fa bai san sunan garinsu ba. Ya yi ta bincike, har a ƙarshe ya sami waɗanda suka yi masa kwatancen garin. Bayan ya shirya sosai, sai ya kama hanyar garinsu. Da ya shiga garin sai ya kama wannan waƙa ta cigiyar mahaifiyarsa: “Wace ce mahaifiyata? Wace cemahaifiyata?”

    Sai wata mata wadda ba ta wuce sa’arsa ba ta ce: “Ni ce mahaifiyarka, Samari ai ni ce mahaifiyarka.” Da ya dube ta sai shakka ta kama shi. Da gani ya san ba ta yi shekarun da za a ce ta haifi kamarsa ba, amma dai saboda halaye irin na masu sani da kuma bin umarnin mahaifinsa sai ya ce: “A ina kika haife ni? Faɗi inda kika haife ni.”

    To da yake ta ga alamun sukuni tare da Maishuni, sai ta ƙirƙiro zancen da take ganin ya dace da matsayinsa ta ce: “A kan gadon ƙarfe, A kan gadon ƙarfe.” Sai da ya bari ta gama hauragiyarta, sai kawai ya mayar mata da wannan jawabi inda ya ce:“Ba ke ce mahaifiyata ba, Ba ke ce mahaifiyata ba.”

    Sai ya kama hanya tare da masu raka shi, suna ta tafiya dai a cikin gari. Da suka kai tsakiyar gari sai ya fara rera waƙarsa. Mata suka fito, wata ta ce a kan gado, wata kuma ta ce kan tabarma, wata ma cewa ta yi a kan gadon zinariya. Haka dai, ba wadda ta faɗi gaskiyar magana.

    Har sai da shi da abokan tafiyarsa suka fara gajiya, sai can ya ga wata mata a zaune ta kasa rogo. Da gani ka san ta jigata, ko da yake ba ta karaya da rayuwa ba sai ya dube ta ya ce: “Wace ce mahaifiyata?, Wace cemahaifiyata?” Wannan waƙar ta sa Delu yin murmushi da tunanin baya.

    Ta so ta gane muryar Maishuni, to amma sai ta yi shakka irin ta natsuwa, sai kawai ta mayar masa da waƙa: “Ni ce mahaifiyarka, Ni ce mahaifiyarka.” Sai Maishuni ya ji kamar ya gamsu da maganarta, saboda muryarta ta yi kama da wata murya da ke tsakiyar birnin zuciyarsa, sai ya ce: “Ina kika haife ni?, Ina kika haife ni?”

    Wannan tambayar da ya yi ta sa ta tunanin cewa lallai ga alama Maishuni ne Allah ya dawo mata da shi gida. Ga bayanin da ta yi: “Na haife ka a tsakar ɗaki, Nahaife ka a tsakar ɗaki.” Da jin jawabin da ta mayar masa, sai farin ciki ya cika masa zuciya. Nan take idanunsa suka cika da ƙwalla, amma ya yi ta maza ya kanne.

    Ya je gabanta ya durƙusa, ya gaishe ta yana mai cewa: “Lallai ke ce mahaifiyata, Lallai ke ce mahaifiyata.” Ta tashi suka shiga cikin gida. Bayan shi da abokan tafiyarsa sun huta, sai ta shiga ba shi labarin rayuwarta da rasuwar mahaifinsa da yadda jikinta yake gaya mata cewa za su gana.

    Shi kuma ya ba ta labarin baiwar da ya samu daga Allah, ta ilimi da dukiya mai amfani, kuma ga shi tana da rai za ta more shi. Suka yi koke-koke na jin daɗi. Bayan Maishuni ya huta, sai ya nemi izinin mahaifiyarsa a kan ya gina mata kataferen gida. Aka gina ya kawo kuɗi ya cika mata tukwane da wani ɗan ƙaramin rumbu.

    Kafin ya koma kwaso iyalinsa kuma, ya yi magana da dattijan gari da sauran shugabanni don a nuna inda za a gina makaranta. Ya kawo kuɗin aikin kuma ya bayar. Bayan ’yan kwanaki ya koma garin da ya yi karatu da nufin ya kawo iyalinsa mahaifarsa. Aka gama ginin makaranta, shi kuma ya kwaso iyalinsa da dukiyarsa ya dawo garinsu ya zauna shi ne babban malami a garin inda ake zuwa ɗaukan karatu daga ko’ina a wannan yanki nasu. Kurunkus.

    Abubuwan DaLabarin Yake Koyarwa 

    • Ilimi shi ne gishirin rayuwar duniya. Ilimi shi ne tushen duk wani alheri da ake samu.
    • Maƙurci, mawadaci.
    • Ƙaddara ta riga fata.
    • Arziki a ƙasa yake, tako shi ake.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Tatsuniyar Ladi Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata yarinya kyakkyawa tana tare da iyayenta waɗanda suke maƙwabtaka da surukan Gizo a wani ƙauye wai shi Yana. Sunan yarinyar Ladi. Wata rana sai ƙawayenta suka biya mata domin su tafi bayan gari cin kaɗanya. Da yayyenta suka ji inda za su, sai suka ce kada ta je saboda akwai wani mugun Dodo da yake kashe mazauna Yana in sun fita bayan gari.

    Ladi ta ƙeƙasa ƙasa, ta kafe ita sai ta je. Sai ta sha ɗamara, ta ɗauki sanhon zuba kaɗanya, ta bi ƙawayenta, suka fita bayan gari. Ba su tsaya ba sai gindin wata babbar kaɗanya da ta yi ’ya’ya birjik, abin ban sha’awa da sa marmari. Sai ɗaya daga cikin ’yan matan nan ta ce: “Kowacce ta hau kaɗanya ta ɗebi rabonta.”

    Kowacce ta hau, suna cikin kaɗar kaɗanya, sai Dodon nan ya zo gindin bishiyar ya tsuguna, ya ce: “Ku ’yan mata, ku sauko in cinye ku.” Sai ko suka fashe da kuka saboda tsoro, idanu suka raina fata, ciki ya ɗuri ruwa, kowacce sai kyarma take yi, duk sun ɗimauta. Can sai wata mai wayo daga cikinsu ta kama waƙa tana cewa:

    “Dodo, Dodo,

    ba ni ce Ladi ba,

    Ladi fara ce, kyakkyawa,

    In ta yi dariya, nono ne ke zuba,

    In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.”

    Da Dodon ya ji wannan waƙa, sai ya yi wani irin gunji, ya yi miƙa da gyatsa ya ce: “Sauko ’yata ba da ke nake ba, Da Ladi nake, Zan kakkarya ta, In sha madararta da ke zuba.” Da ƙawayen Ladi suka ga yadda ɗayarsu ta ceci kanta daga sharrin Dodo da wannan waƙa, sai wata daban kuma ta ɗauka:

    “Dodo, Dodo, ba ni ce Ladi ba,

    Ladi fara ce, kyakkyawa.

    In ta yi dariya, nono ne ke zuba,

    In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.”

    Da ya ji wannan waƙar ma, sai ya mayar mata da cewa:“Sauko ’yata ba da ke nake ba, Da Ladi nake, Zan kakkarya ta, In sha madararta da ke zuba.” Sai ta sauko, ita ma ta kama hanya, ta gudu gida. Da haka da haka duk ’yan matan nan suka sauko, saura Ladi ita kaɗai ta rage a kan kaɗanya, ƙasa kuma ga Dodo yana jira ta sauko ya halaka ta.

    Kamar dai dabara za ta ɓace mata, amma dai ita ma ta kama waƙa irin wadda sauran suka rera: “Dodo, Dodo, ba ni ce Ladi ba, Ladi fara ce, kyakkyawa, In ta yi dariya, nono ne yake zuba. In ta yi murmushi, madara ce ke zuba.” Sai Dodo ya ce: “Na ji ba ke ce Ladi ba, amma sauko in cinye ki, yunwa nake ji.”

    Da Ladi ta ji lafazin Dodon, sai ta fashe da kuka. Tana cikin kuka sai wani tsuntsu ya sauka a kan kaɗanyar kusa da ita ya ce: “Me ya sa kike kuka?” Sai ta ba shi labarin yadda ƙawayenta suka yi suka gudu, amma Dodo ya ce sai ya cinye ta. Da tsuntsu ya ji halin da Ladi take ciki sai ya ce: “To, ina dabara?”

    Sai Ladi ta yi masa kwatancen gidansu domin ya je ya gaya wa mahaifanta. Tsuntsu ko ya je ya gaya musu. Iyayen ko ba su ɓata lokaci ba, suka yi gayyar jama’a don a je a ceto ta. Da yake suna da farin jini a garin, nan da nan majiya ƙarfi suka ɗebo makamansu, aka zo inda Dodo yake aka yi sukuwar salla a kansa aka yi kaca-kaca da shi.

    Ladi ta sauko, sai gida tare da jama’ar gari. Daga wannan rana Ladi ta daina zuwa ko da ƙofar gida, sai da yardar iyayenta ko yayyenta. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Rashin bin maganar magabata yana sa a faɗa cikin hatsari.
    • Zaman lafiya da jama’a yana kawo samun taimakon gaggawa a lokacin da buƙatar hakan ta taso.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Talume

    Edita@rumasau-kallamu