Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Gizo ne yana yawonsa sai ya tarar da tarin kashi a wani wuri. Bai tsaya ba, ya tsallake ya yi tafiyarsa. Jim kaɗan sai Kura ta bi ta wurin, ita ma ta ga kashin, sai ta kama da ci, kuma ta ji kashin yana da daɗi, sai ta ce: “Lallai duk wanda ya yi kashin nan, namansa zai zama mai daɗin gaske.”

    Nan fa ta yanke shawara a kan sai ta gano wanda ya yi kashin. Saboda haka ta hau wani kututture ta shiga jira. Ta daɗe amma ba ta ga kowa ba. Haka ta haƙura; a cikin fushi ta kama hanyar barin wurin. Tana cikin tafiya sai ta ga wani tarin kashin a ƙarƙashin wata bishiya.

    Wannan kashi ya tayar mata da kwaɗayi; nan take dai ta cinye shi sarai. Ta yi gaba, sai kuma ga wani kashin. Shi ma ta cinye shi duka. Haka dai ta dinga tarar da kashi tsibi-tsibi tana cinyewa, ba ta rage ko kaɗan ba. Amma har yanzu tana mamakin wanda yake yin sa, saboda haka sai ta sake hawa wani kututture mai tudu tana jira.

    Nan ma ba ta ga kowa ba. Ganin haka, sai ta sake dabara, ta tona rami ta shiga fako. Nan ma ba ta ga komai ba. Daga nan sai ta buɗe bakinta, wai komai kashin ya zo ya shiga ciki ta cinye shi. Ba ta jima da bakinta a buɗe ba, sai Gizo ya je ya yi kashi, kashin kuma ya faɗa bakinta.

    Ta ji kashin Gizo da daɗi ta ce: “Ashe da man Gizo ne ke yin wannan kashi. Ko ina yakan sami naman da yakan ci ya sa kashinsa ya yi daɗi haka?” Kura dai ta ga gara ta ci gaba da fakon Gizo, sai ta sake hawa sama, ta shiga jiran komawarsa. Shiru, shiru. Gizo bai je ba sai washegari.

    Ya sake zuba kashi; yana gama yi sai Kura ta sauka ta yi kansa. Ta kama shi ta riƙe gam-gam; sai ta tambaye shi inda yake samun naman da yake ci. Da fari Gizo ya ce ba zai gaya wa Kura ba don yana tsoron kada a kashe shi idan ya faɗa. Kura ta ce: “Ko ka gaya mini ko kuma in kashe ka.”

    Saboda tsoro, sai Gizo ya ce: “To, za mu yi alƙawari a yau kawai. Wato zan gaya miki.” Kura ta amince; suka kama hanya Gizo ya kai ta inda yake samun naman. Da zuwansu wurin sai ya ce: “Buɗe, buɗe, buɗe.” Sai wata ƙofa ta buɗe, suka shiga. A ciki sai ga gwafanni da sanduna a kafe an rataye nama ba iyaka a jikinsu.

    Da shigarsu sai Gizo ya ce: “Rufe, rufe, rufe.” Nan take ƙofa ta rufe. Da yake masu tsaron ƙofar sun saba ganin Gizo, ba su hana su ba, kuma ba su nemi sanin abin da ya kawo su ba. Gizo ya kwaso nama da yawa ya ba Kura, ta ci, ta yi guzurin wani mai yawa. Daga nan suka fita, suka kama hanyar gida.

    Da dawowarsu gida Kura ta shiga tunanin komawa wurin naman nan ita kaɗai. Bayan kamar mako guda sai ta sami labarin Sarki ya tafi rangadi. Sai ta sami ’yar rakiya daga cikin danginta bisa cewa za su je ziyara ne. Suka kama hanya har suka isa inda suka je cin nama tare da Gizo.

    Ta yi irin maganar da ta ji Gizo ya yi a wancan lokaci: “Buɗe, buɗe, buɗe.” Sai ƙofa ta buɗe. Suka shiga, suka ci nama har suka ƙoshi, suka lafci wanda za su tafi da shi
    gida, sun ga banza ta faɗi. Ba da dadewa ba Sarki ya dawo daga rangadi. Ya tarar
    naman da ya yi tanadi ya ragu ƙwarai.

    Ya tambayi masu tsaro, amma suka kasa yin bayani mai gamsarwa. Sarki ya sa aka tara mutanen garin duka. Ya gaya musu ya yi alƙawari duk wanda ya gaya masa wanda ya sace masa nama zai aura masa ’yarsa. Gizo ya san masu gadi kan iya tona masa asiri, sai yace ya san wanda ya yi ɓarnar.

    Fadawa suka ce ya faɗa. Nan da nan ya nemi izini, aka ba shi domin ya je ya zo da wanda ya yi wannan ta’adi. Bai zame ko’ina ba sai a ƙofar ramin Kura. Da ya tambaya aka ce ta yi tafiya, sai ya ce: “Kash, ashe ba za ta sami irin naman da Sarki yake ba jama’ar da ya tara a fada ba kenan.

    Idan ta dawo a gaya mata ta je fada Sarki zai yi rabon nama mai yawa.” Da jin haka sai Kura ta fito daga inda ta ɓuya ta ce: “Gani. Ba inda na je. Mu tafi in sami rabona.” Suka fita. Ba su tsaya ba sai a fada. Da isarsu ’yan tsaron nama suka ce: “Ba shakka, Kura ce ta cinye naman Sarki.”

    Kafin ta farga, tuni an hau ta da bugu. Da aka kai ta ƙarshe, sai aka farke cikinta. Hanji da tumbi da uwar kashi da tubura da huhu da zuciya da kashi, duk suka zuba. Kura dai a taƙaice nan ta mutu. Sarki kuwa dama mai jan girmansa ne. Nan take ya cika alƙawari, watau Gizo ya zama surukinsa. Suka yi zamansu lafiya. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Iya gani iya ƙyalewa.
    • Alƙawari kaya ne.
    • Mai rabon shan bugu, ba ya jin kwaɓa.
    • Kowa ya daka rawar wani, ya rasa turmin daka tasa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Tasalla mace ce wadda ke zaune a wani kauye mai suna Saladuna. Tana kiwon wani kifi babba. Ta daɗe da wannan kifin, har sun saba da juna. Tasalla tana ciyar da kifin a kullum gwargwadon ƙarfinta. Saboda sabon da suka yi da juna, har yakan riƙa yin tsalle cikin wasanni da ita.

    Wata rana Tasalla ta yi tafiya, sai mutanen ƙauyen suka kama kifinnan suka cinye. Kowa ya ji daɗin naman kifin. Da Tasalla ta dawo sai ta nemi kifinta ko sama ko ƙasa, ya ɓace. Ta yi ta tambaya da cigiya ko ta ji wani abu game da kifin, amma ba ta sami bayani daga bakin kowa ba.

    Nan take ta shiga kukan takaici. Wannan ya sa ta yi wani siddabaru da ya ƙarar da ruwan garin, kowa ya rasa ko da ruwan wanke ido, balle na wanka da girki. To amma akwai wani mutum ɗaya da Tasalla ke jin nauyi, kuma tana matuƙar ƙaunarsa.

    Sai aka turo mata shi domin ya roƙe ta, ko za ta warware siddabarun da ta yi suka rasa ruwan sha. Ga irin abin da yake cewa da ya tunkari inda take:

    “Tasalla, Tasalla, Ki ji tausayina,

    Ki sam min ruwa in sha.

    Ki ji tausayi na, Ki sam min ruwa in sha.”

    Sai ta mayar da jawabi tana tambaya:

    “Wane ne yake neman ruwa?
    Wane ne yake neman ruwan sha?”

    Sai mutumin ya ce: “Ni ne masoyinki, Ni ne nake roƙon ruwa in sha.” Tasalla ba ta amince ba. Tana fushi a kan cinye mata kifi, saboda haka ta hana mutumin ruwa. Sarkin garin da fadawansa suka ɗunguma suka je roƙon ta, amma ta ƙi sauraronsu. Ba yanda ba su yi ba, amma ta ƙi.

    Sai can uwarta ta zo ita kaɗai ta roƙe ta ruwan sha. Saboda ƙaunar da take yi wa uwar, sai ta daina fushin da take yi. Nan take ta warware siddabarun da ta yi, ruwa ya samu kowa ya wadata da shi. Daga bisani mutanen garin suka zo suna ba Tasalla haƙuri, kuma suka amince lallai sun yi mata laifi da suka cinye mata kifi.

    Duk mutanen garin suka ɗauki alƙawari za su nemo mata wani kifin. Bayan ‘yan watanni suka samo mata wani kifin. Sabon kifin yana da ruwan zinari, kamar dai wanda aka cinye; wannan yasa zaman lafiya tsakaninta da su ya tabbata. Kifin ya girma, kuma ya dinga hayayyafa. Daga ƙarshe dai har kifin ya zama ya wadaci mutanen garin.
    Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Soyayya da tausayi a rayuwar duniya ya haɗa da zaman mutum da halittar Allah ga baki ɗaya.
    • Soyayya tsakanin ɗa da iyaye tana da ƙarfi ƙwarai fiye da yadda mutum ke zato.
    • Ɗaukar abin wani ba da izininsa ba zalunci ne.
    • Tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan doka.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna na don karanta Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana mutuwa ta je wani ƙauye da saniya da ta turke, tana neman wanda zai sayi wannan saniya a ƙauyen. Mutane suka tsorata baki ɗaya suka ƙi. Can Gizo ya dubi mutuwa ya ce shi yana so. Suka yi yarjejeniya a kan baɗi Mutuwa za ta dawo ta yanke kunnuwan Gizo.

    Wato kunnuwan sun zama kamar da su zai biya saniyar. Nan da nan sai Gizo ya yanka saniyar shi da matarsa Koƙi suka dafa, suka ci, suka ƙoshi. Da shekara ta kewayo sai ga Mutuwa ta zo fansar bashi. Ta fara cigiyar wanda ya sayi saniyarta. Ta shiga gari tana cigiya, har ta kai gidan Gizo.

    Gizo na nan amma kuma ya gaya wa matarsa Koƙi ta gayawa Mutuwa cewa ya yi tafiya. Amma kuma ya ɓuya ne a cikin ramar da aka shuka a tsakar gidan. Saboda haka da Mutuwa ta tambaya sai Koƙi ta gaya mata cewa ai mijinta ya yi wata doguwar tafiya bai
    dawo ba. Mutuwa ta yi mamakin jin haka, ta ce: “Yaya Gizo zai yi tafiya bayan kuwa mun yi alkawari a kan yau ne lokacin haɗuwarmu?”

    Saboda haka sai Mutuwa ta tuna da wata dabara wadda za ta yi ta kama Gizo. Sai ta tafi kasuwa ta sayo ganga ta zo gidan Gizo ta yi ta kaɗawa tana waka, tana cewa:

    “Ina Gizo, Koki ina Gizo?”

    Koƙi ta fito ta nanata cewa: “Ai maigidana ya yi tafiya yau da wata uku bai dawo ba.” Mutuwa ta san Gizo yana da wayo. Saboda haka ta cewa Koƙi: “Kin ga kuwa Gizo ya tafka asara. In da yana nan zan ba shi wata saniyar ne. Da mun yi haka din sai in tafi in dawo baɗi in karbi kunnuwa biyu.”

    Koƙi dai ta zauna a kan cewa maigidanta ya yi tafiya. Amma da Gizo ya ji zancen Mutuwa za ta ba shi wata saniyar, sai kwatsam ya fito yana cewa: “Ai ga ni nan; rabu da Koƙi, ƙarya take; ina nan.” Da fitowar Gizo sai Mutuwa ta kama shi ta yanke kunnuwansa. Ta kuwa yanke su a gurguje ta yanda Gizo bai san kowane ne ya yi masa wannan shigar sauri ba.

    Ya ma zaci ko Mutuwa ce ta turo ɗanta ya yi wannan aiki. Har yau an ce Gizo na can ƙauyen yana jinyar yanke masa kunnuwa da Mutuwa ta yi. Duk mutanen gari suka yi ta yi wa Gizo dariya da ba’a suna cewa: “Ai ga irinta nan. Kwaɗayi mabudin wahala.” A taƙaice dai, ba wanda ke tausaya wa Gizo a kan abinda ya same shi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Alƙawari kaya ne.
    • A halin zaman duniya ya kamata mutum ya tsaya ga magana guda don yawan canza magana yakan zubar da mutunci.
    • Kowa ya ci ladan kuturu, ya yi masa aiki.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata yarinya mai suna Yelwa. Tana da ƙawaye da yawa. Wata rana Sarkin garinsu ya umurci ‘yan matan garin su je rafi, su kamo kifi bisa sharaɗin cewa duk wadda ta kamo ta yi masa miya mafi daɗi, ita zai aura. Da man sauran ‘yan matan sun tsani Yelwa.

    Saboda haka bayan sun kamo kifi sai suka haɗa baki suka jefa ta a cikin kogin ta nutse. Da farko har ruwan zai tafi da ita, to amma ta yi sa’a, wata tsohuwa ta zo ta tsamo ta. Wannan tsohuwa kuwa tana da baiwa. Yelwa kuma ta kwashe labarin duk abin da ya faru ta gaya mata. NantTsohuwar nan ta ji tausayinta.

    Nan da nan ta kama wani ƙaramin kifi ta ba ta, kuma ta ba ta wata ‘yar tukunya, ta ce mata ta sa wannan kifi a cikin tukunyar ta rufe, ta kiwata shi. Washe-gari da Yelwa ta buɗe tukunyar sai ta ga wani babban kifi a ciki. Ta yi mamakin yadda kifin ya girma haka. Ta kama kifin ta dafa, ta ɗauka ta nufi fada.

    Kafin ta je an soma biki har an rufe ƙofa. Ta roƙi dogarai suka buɗe mata, ta shiga. Kafin zuwanta Sarki ya riga ya ɗanɗana dukkan miyar da ‘yan matan suka kai, amma babu wadda ya gamsu da ita. Saboda haka da Yelwa ta kai tata miyar, Sarki bai so ya ɗanɗana ta ba, sai da tsohuwar nan ta matsa kusa da shi ta raɗa masa cewa ya taɓa.

    Sarki ya taɓa ya ji miyar Yelwa zaƙi cakwai, abin ba dama. Ba da ɓata lokaci ba washe-gari Sarki ya bayyana mata buƙatarsa ta aurenta. Yace in ta yarda ta je ta shaida wa iyayenta a ɗaura musu aure nan da kwana biyu Yelwa ta tafi tana kuka saboda baƙin cikin maraici, domin tuni mahaifanta suka mutu.

    Ta fara batun zuci tana cewa: “Kaito, yaya zan yi da raina yanzu, ga ni ba ni da iyaye.” Can sai ta kama waƙa tana cewa:

    “Ke tsohuwa mai ceto,

    Ke tsohuwa mai baiwa,

    Sarki na so ya aure ni.

    Ke tsohuwa mai ceto,

    Sarki yana so ya aure ni,

    Amma ga shi ba ni da iyaye,

    Yaya zan yi a halin yanzu?”

    Can sai ga tsohuwar ta bayyana, ta ce mata ta daina kuka, kar ta damu, komai zai yi kyau. Ta umurce ta da ta je ta samo ƙwari biyu ta kawo mata. Da ta kawo sai tsohuwar ta mai da su mutane, mace da namiji, wato sun zama iyayen Yelwa ke nan. Daga nan suka tasam ma fada, aka ɗaura aure.

    Nan fa sai ƙawayen Yelwa suka ji kunya, suka nemi gafararta. Yelwa kuma ta yafe musu saboda halinta na haƙuri. Ita da ƙawayen suka zauna lafiya, har kowaccensu ta yi nata auren. Sai dai akwai ɗaya daga cikin ƙawayen mai mugun hali. Ba ta daina jin haushin rasa auren Sarki ba.

    Saboda ƙyashi da hassada, sai ta shiga ƙulle-ƙulle da haɗa husuma domin ta kashe wa Yelwa aure. Ba abin da take so a duniya kamar ta ga auren Yelwa da Sarki ya mutu. Wata rana ta kama hanya ta je fada da nufin kashe Yelwa, amma ba ta yi nasara ba. Dogarai suka kama ta.

    Duk da cewa ta so kashe Yelwa, amma ita ba ta so a hukunta muguwar ƙawar nan tata ba. Ta roƙi mijin a ƙyale ta domin ƙila ta gyara halinta. Sarki ya yarda, ya kuma tara mutanensa kaf ya shaida musu matuƙar ƙaunar da ke tsakaninsa da Yelwa. Ya tabbatar musu har ita kanta cewa a ko da yaushe iya ransa zai yi duk abin da ya dace don ya kyautata zama da soyayyar da ke tsakaninsu. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Taimakon Allah yana samun bawansa ta hanyoyi daban-dabaninda bai zata ba.
    • Yafe wa wanda ya musguna maka wani alheri ne da zai sa mai laifin ya canza halinsa nan gaba.
    • Rabo dangi ajali.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata tsohuwa mai ‘ya’ya uku mata. Sannu a hankali suka girma, har suka kai munzalin aure. Saboda haka ta ce da kowaccensu ta fid da mijin aure. Nan da nan Allah ya ba kowacce wanda za ta aura. Suka yi aurensu, kowacce ta tare a gidan mijinta a garuruwa daban-daban.

    Bayan ‘yan kwanaki kaɗan, sai tsohuwa ta ce ya kamata ta ziyarci kowacce a gidanta a garuruwan da suke. Ta fara da zuwa garin ‘yarta ta fari ta tarar kusan dukkan mutanen garin kowa maye ne. Ga shi kuma suna da jela da kunnuwa dogaye, kamar dodanni. Ta tambayi inda gidan ‘yarta yake. Mutane suka kwatanta mata.

    Da ta je gidan ‘yarta ta karɓe ta a cikin murna matuƙa. Ita ma ‘yar ta zama mayya, tana kuma da wutsiya da dogayen kunnuwa. Sai uwar ta tsorata. Ko da yake an karɓe ta da fara’a, ta yi tunanin cewa ya kamata ta koma garinsu da wuri. Ba da sanin uwar ba ashe ‘yar da mijinta sun shirya a kan za su cinye ta cikin daren.

    Da dare ya yi sai suka saɗaɗa cikin ɗakin da suka saukar da ita a ɓoye, amma suka tarar ba ta yi barci ba. Sai suka koma a kan cewa washe-gari za su ƙara yin ƙoƙari ko za
    su same ta ta yi barci. Ita kuma ganin haka sai ta shirya da sassafe za ta gudu ta bar garin. Gari yana wayewa, ko ban kwana ma ba ta yi da su ba, ta kama hanya.

    Ta shiga dajin Allah tana ta hanzari ba ta tsaya ba sai gidan ‘yarta ta biyu. Ita ma wannan ‘yar ta karɓe ta da murna ƙwarai, sai dai ta gaya wa uwar cewa a ƙauyen idan dare ya yi sukan rikiɗa su zama fari, su je su kwana a kan wata bishiya. Uwar ta ce ba ta damu ba, za ta bi su.

    Da dare ya yi dukkan mutane suka koma bayan gari suka rikiɗa, suka zama fari. Suka ɗunguma gaba ɗaya sai kan itacen da suka saba kwana. Tsohuwa dai ba ta bi su ba, ta zauna ita kaɗai a gida. Ba a daɗe ba hadari ya taso, aka yi ruwan sama mai yawa, ta jiƙe sarai. Da gari ya waye sai ta bar wannan garin ta nufi ‘yarta ta uku.

    Da ta je garin sai ta tarar mutanen suna soya naman shanu. ‘Yarta ta karɓe ta da hannu bibbiyu. Sun ɗan sammata naman amma da gargaɗin cewa kar ta cika cikinta domin a garin ba a ƙashi da fitsari. ‘Yar ta ce in fa ta karya dokar to Sarkinsu zai sa a kashe ta. Uwar ta yi banza da gargaɗin; ta ci naman sai da ta ƙoshi.

    Can cikin dare ta ta-da ‘yarta a kan cewa tana so ta je bayan gari. ‘Yar ta ce: “To, ba ga abin da na gaya miki ba. Daman na gaya miki abin da ke faruwa a garin.” Ba da ɓata lokaci ba ta ɗauki uwar ta kai ta bayan gari. Da gari ya waye sai mutanen garin suka dinga jin wari ta ko’ina, suka je suka shaida wa Sarki.

    Sarki ya ce lalle akwai wani baƙo da ya shigo garin. Da ‘yar ta ji haka sai ta yi maza ta ɗauke mahaifiyarta, ta raka ta har sai da ta bar garin. Sarki ya aika a nemo ta, amma ba su gan ta ba. Ta riga ta gudu. Tsohuwa tana kan hanyar komawa gida ne ta gamu da wani mutum. Bayan sun gaisa sai ta tambaye shi ko zai ci naman da ta yo guzurinsa.

    Ta ce da mutumin idan ya ci naman ya je garin ya yi kashi, zai sami wata kyauta. Mutumin kuwa ya karɓi naman ya ci. Da ya je garin ya yi kashi sai aka kama shi. A maimakon a ba shi wani abin arziki sai suka kashe shi a zaton shi ne ya yi kashin nan na kwanan baya. Ita kuma tsohuwa ta koma ƙauyenta lami lafiya. Ta ɗauki
    alƙawari cewa ba za ta ƙara karambanin zuwa ziyarar ‘ya’yanta ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Wajibi ne ga baƙo ya saurari gargaɗin masu masaukinsa.
    • Kowane tsuntsu, kukan gidansu yake yi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Kunya Take

    Yadda Kunya Take

    “Kunya tana kawo dukkan alheri” (Manzon Allah SAW)

    Kunya wata ɗabi’a ce da take hana mutum aikata rashin ɗa’a ga Allah ko ga mutane. Kunya ɗabi’a ce da Allah ya yi umarni da shi tun tale-tale ba a addinin musulunci kaɗai ba, duk addinai kunya abu ne da aka yi umarni da shi, kuma abu ne mai kyau.

    Wannan ya sa Manzon Allah SAW yace: “Yana daga cikin abinda mutane suka gada daga kalaman hikima na Annabawa magabata – shi ne – Idan ba ka jin kunya, toh ka aikata abinda ka ga dama” Allah Ta`ala ya ba mu labarin wasu `yanmata da Annabi Musa ya shayar da dabbobinsu lokacin da ya bar Masar ya nufi Madyana a cikin suratul ƙasas.

    Wannan ƙissar an kawo ta a littafin Linjila ta Annabi Isa (AS) a wannan ƙissar an nuna yadda waɗannan ‘yanmata ko ɗaya daga cikinsu take ta jin kunya lokacin da za ta ta kai Annabi Musa AS wurin mahaifinsu ta yadda tana tafiya amma tana jin kunya.

    A addinin musulunci wanda yake addinin ne da bai bar komai ba mai kyau sai da ya yi umarni da shi, sannan duk wani abu mummuna ya yi hani da shi, ya yi umarni da jin kunya. Manzon Allah SAW ya ce “ Kunya tana daga cikin imani”.

    Kunya a addini ta kasu kashi biyu:

    Kunyar Allah; wanda shi ne mutum ya rinƙa ganin girman Allah ta yadda ba zai aikata wani abinda ya saɓa wa umarnin Allah ko ya ƙi aikata abinda Allah ya umarce shi ba. Idan mutum yana jin kunyar Allah to, ba zai aikata abinda Allah ya hana shi ba ko ya ƙi aikata abinda Allah ya umarce shi ba, saboda ya san Allah yana ganinsa. Wannan zai sa ya rinƙa ganin girman Allah.

    Kunyar mutane; wannan tana ƙasa da wancan na farkon. Kunyar mutane tana hana mutum aikata abinda ya ga dama a cikin rayuwar yau da gobe a cikin mutane. Zai hana shi aikata abinda Allah ba ya so. Ba wai don mutum ya ƙi aikata wani abu dan tsoron Allah ba, sai dan kunyar mutane. A’a, Bahaushe ya ce: ana barin halal don kunya. Abinda ake nufi shi ne, wani abin ba saɓa wa Allah ba ne, amma a al’adance ba daidai ba ne, idan dai addini bai wajabta shi ba, toh mutum zai iya bari don kunyar mutane. Wannan shi ma abu ne mai kyau.

    Manzon Allah SAW da kansa an rawaito cewa yana da tsananin kunya kamar yadda budurwa take da kunya. An san yadda budurwa- a da- su ke da kunya. Shi yasa Manzon Allah SAW ya ce idan aka tambayi budurwa kan maganar aure, toh shirunta shi ne amsa. Wannan ya nuna irin kunyar da budurwa take da shi ba zai ba ta dama ta amsa kai tsaye ba.

    Haka aka rawaito ce wa Sayyidina Uthman RA yana da tsananin kunya. Manzon Allah SAW ya ce: har Mala’iku suna jin kunyar Sayyidina Uthman. Manzon Allah ya ce shin ba zan ji kunyar wanda mala’iku suke jin kunyar sa ba.

    Nana Aisha RA an rawaito tana cewa: Da aka binne Manzon Allah SAW a ɗakinta da Sayidina Abubakar, tana iya cire kayanta ko mayafinta idan ta shiga ɗakinta, saboda mijinta ne da mahaifinta, amma da ka binne Sayyidina Umar a ɗakin sai ta ce sai na daina cire kayana ko mayafina a ɗakin saboda ina jin kunyar Sayyidina Umar. Duk da ba a raye yake ba, yana kabarinsa, amma tana jin kunya cire mayafinta a inda aka binne shi.

    Ba a musulmi ba kaɗai, har cikin waɗanda ba musulmi ba ana samun masu kunya saboda ɗabia’a ce mai kyau. A tarihin babban malamin nan Sir Issac Newton, ana faɗin cewa mutum ne mai kunya sosai da kamun kai, har ta kai ba ya son magana sosai a gaban jama’a.

    A mata kuma akwai irin su Isabella Clara Eugenia (1566 – 1633) duk da cewa mai mulki ce sosai, amma mace ce mai kunya da kamewa sosai. Akwai Maria Sibylla Merian (1647 – 1717) wadda tana daga cikin mata kaɗan da suka shahara a ɓangaren kimiyya a wacan lokacin, amma ta zaɓi gudumawarta ya fito fili ba ita ba, saboda ta fifta kunya, kamun kai da mutunci.

    Ga su ire iren Sarauniya Alexandra(1844 – 1925), matar Sarki Edward VII, `yar sarakai ce daga ƙasar Denmak, kuma matar basarake amma ba ta jefar da kunya, mutunci da kamun kai ba. Da waɗannan ɗabi`u ake gane ta duk inda ta shiga a Ingila alokacin duk da ba ta yawan fita jama`a.

    An kawo waɗannan ne don a nuna kunya ba addinin musulunci ne kaɗai ya yi umarni da ita ba, har ma sauran addinai da al`ummu daban daban. Kuma abu ne da mutane suke ƙaunar mai wannan sifar, da kuma yaba masa.

    Kunya ba ƙauyanci ba ne, ba kuma rashin wayewa ko gaɓanci ba ne, a a, ɗabi`a ce mai kyau. Manzon Allah SAW ya ga wani mutum yana yi wa ɗan`uwansa faɗa kan cewa ya faye jin kunya. Sai Manzon Allah SAW ya ce masa: ƙyale shi, kunya ba abinda take kawowa sai alkhairi” wannan ya nuna mana kunya alheri ce, ba kauyanci ba ne ko rashin wayewa. Kuma rashin kunya ba wayewa ba ne kuma ba wayo ba ne ko birnanci.

    A wannan zamanin musamman na Social Media, matasa da yawa sun tsame kansu daga jin kunya, musamman mata, waɗanda su ya kamata su kasance kan gaba wurin nuna wannan ɗabi`a kyakkyawa. Abubuwa na baɗala, lalacewa da rashin albarka duk sun yawaita a tsakanin matasa, ba don komai ba sai rashin wannan ɗabi`a ta kunya.

    Manzon Allah SAW ya yi gaskiya da ya ce “Wanda ba ya jin kunya ya aikata abinda ya ga dama” saboda rashin kunya da matasa ba ji yanzu, ya sa suke ta tsula tsiyar su a Social Media. Mata suna nuna tsaraici a fili, ana maganganun batsa, da baɗala, kai har ta kai ka ga ana nuna fasiƙanci a fili.

    Waɗanda suke waɗannan ayyukan na ashsha ba sa jin kunyar kowa, shi yasa suke abin da suka ga dama. Ka ga budurwa da ake sa ran za a same ta mai tsananin kunya amma ta fito duniya tana nuna tsaraicinta a fili ko tana magaganun batsa. Ba abinda ya jawo haka sai rashin kunya.

    Ci gaban zamani da ilimin zamani ba su ne suke ba da gudunmawa wurin ƙaruwar rashin kunya ba kaɗai, ga misalai nan da yawa na mata da maza wanda sun kai wani matsayi na karatun zamani amma sun kame kansu, suna da kunya da mutunci. Sannan a hannu guda kuma wasu ko bihim ba su sani ba, amma fitsara da sheɗanci ya zama musu abin tutiya.

    Manzon Allah SAW ya ce kunya ba ta kawo komai sai alkhairi, duk mai kunya toh zai ga sakamakon kunyarsa, ita ɗabi`a mai kyau ba ta faɗuwa ƙasa banza kuma tana da amafani. Akwai tagomashi mai yawa a nan duniya da kuma lahira. Kunya ba za ta bar mutum ya saɓa wa Allah ba, kunya ba za ta bar mutum ya wulaƙanta ba, kunya tana jawo wa mutum ɗaukaka da daraja.

    Rashin kunya takan sa mutum ya saɓa wa Allah, rashin kunya takan sa mutum ya wulakanta, takan jawo ƙasƙanci, taɓewa, da na sani da nadama. Manzon Allah SAW ya ce: “kunya tana da ga cikin Imani” duk mai kunya yana da imani, mara kunya shi kuma akasin haka. Imani kuwa ba inda yake kai mutum sai ɗa’a, ɗa’a kuma aljanna take kai mutum kai tsaye. Allah ka sa mu dace. Amin.

    Danna nan don karanta Shaiɗanin Wannan Ƙarni: JEFFERY EPSTEIN

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wasu dogarawa ne dai su uku masu suna Gi da Ɗa da kuma Ɗo. Aikinsu shi ne gadin gidan Sarki. To, akwai wani mutum kuma a garin sunansa Giɗaɗo. Shi ke nan, Sarki kuma yana da kaji da yawa a gidansa. Wadannan dogarai kuma su Gi da Ɗa da Ɗo kullum suna zuwa kamun fari.

    Idan sun zo da su sai su zuba wa kajin Sarki. In kajin sun ga farin, sai su zo suna ci. Su kuma dogaran sai su kama guda uku, kowa da tasa. Sai su je su gasa, su ci. To, kullum a ƙofar gidan Giɗaɗo suke gasawa. Shi ke nan, yau da gobe, sai Sarki ya ga kaji suna ƙarewa. Sai aka soma bincike; in aka tambayi wannan, sai ya kalli wancan.

    In aka tambayi wancan, sai ya kalli wannan. Sai Sarki ya ce in ba su faɗa ba, za a kashe su. To, akwai wani Bafulani da kan kai wa Sarki nono kullum. To, in ya tashi zuwa sai su haɗu da Gi, da Ɗa da Ɗo. To, ba ya iya bambanta sunayensu. In ya tashi kiran su, sai ya ce: “Giɗaɗo.” Kullum in sun haɗu, sai ya ce: “Giɗaɗo, ina za ka je?”

    Sai su ce ai Sarki ne ya aike su, su kai kaji wani gida. Kullum haka. Shi ke nan, ana cikin yi musu tambayoyi game da ɓacewar kajin Sarki, sai ga Bafulanin nan ya zo. Da ya ji zancen da ake yi, sai ya ce ai ya san waɗanda suka ci kajin. Sai aka ce to, ya faɗa. Sai ya ce: “Ai Giɗaɗo ne.” Sai Sarki ya ce: “Kai ɗan Fulani, ka faɗi gaskiya.

    Giɗaɗo ba zai zo ya kama kaji a gidana ya ci ba.”Jin haka ya sa Bafulani ya ce: “Wallahi Giɗaɗo ne yakan ci kaza kullum. Idan ina zuwa kawo nono mukan haɗu yana riƙe da kaza. Kuma idan na ce ina za shi da kaza, sai ya ce Sarki ya aike shi.” Sai Sarki ya ce a je gidan Giɗaɗo.

    Da aka isa ƙofar gidansa, sai aka tarar da gashin kaji ya cika ƙofar gidan, saboda kusa da gidansa dogarawan Sarki kan je su fige kajin da suka sato daga gidan Sarki. Sai aka ce to a shiga a kamo shi. Sai aka shiga gidansa, aka kamo shi. To, da aka tambaye shi bayani a kan kaji, sai ya ce shi bai sani ba, don shi bai isa cin kaza ba, balle ya je gidan Sarki da masu gadi, har ya kama kaza, ya gasa, ya ci.

    Sai Sarki ya ce: “To, in ba kai ba ne, sai ka gaya min wanda zai zo ƙofar gidanka da kaza, ya yanka, ya fige, kuma ya gasa, ba ka sani ba.” Giɗaɗo ya ce sam-sam, shi bai sani ba, kuma bai san wanda ya ci kaza ba. Sai Sarki ya kasa gane gaskiyar al’amari. Sai dogarawa suka ce tun da a ƙofar gidansa aka ga gashin kajin, ai sai a kashe shi.

    Sai Sarki ya ce to a kama shi a kashe. Sai Gi da Ɗa da Ɗo suka ingiza ƙeyarsa waje, suka je suka kashe shi. Da yake da man ba su da gidajen kawunansu, sai suka mamaye gidansa, watau sun ci nasara, har da gadonsa. Sarki bai san maciya kajinsa ba. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kuskure ne a zartar da hukunci ba tare da yin kyakkyawan bincike ba.
    • Maciyin amana komai daɗewa sai ya ga mummunan sakamako.
    • Ba a yin azzalimin sarki, sai bafade.
    • Wata shari’ar sai a lahira.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Tatsuniyar Ɗantsintuwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata mata da mijinta, suna zaune a wani ɗan kauye. Sun daɗe tare, to amma Allah bai ba su haihuwa ba. Wata rana matar nan ta je gona, sai ta tarar da jinjiri a kan dutse, sai ta ɗauko. Ashe wannan yaro ba mutum ba ne, ɗan aljani ne, ba ta sani ba.

    Sai ta kawo yaron gida. Da mijin ya ga yaro, sai ya tambaye ta inda ta samo shi. Sai ta ce, ai ɗan tsintuwa ne, sai mijin ya ce, anya wannan mutum ne kuwa? Sai matar ta ce ai da ma ta san zai ƙi amincewa da yaron. Don gudun zuciyar matarsa, sai ya ce: “To, shi ke nan na yarda mutum ne, kuma ki riƙe shi.” Suka ci gaba da renon yaron.

    To, matar kullum tana zuwa gona da yaron. Daga ƙarshe dai ta samo yarinyar da za ta riƙa yi mata reno a gidan idan ta tafi gona. Kullum idan za ta tafi sai ta dafa musu abinci. To, da zarar ta tafi gona ta bar su da mai renon, sai ya rikiɗa ya zama babba ya kama yarinyar nan ya ɗaure, ya cinye abincin duka ya hana ta, ya yi ta wasanni iri-iri da rawa.

    Sai ya lura matar nan ta kusa dawowa daga gona, sai ya kunce mai renonsa ya koma yaro, ya yi ta birgima a ƙasa yana kuka. Idan iyayen sun dawo sai su hau kan mai reno da duka. Idan za ta yi magana ko bayani, sai su ce ta yi shiru, domin su a ganinsu yaron yana kuka ne saboda ta hana shi abinci, kuma tana dukan sa, har yana birgima.

    Kullum haka, sai wata rana wata tsohuwa maƙwabciyarsu ba ta je gona ba. Tana ɗaure dangarta, sai ta hango ɗan jariri ya miƙe, ya ɗauko igiya ya ɗaure mai renonsa, ya fara waƙa, yana rawa. Ya kuma cinye abinci duka, ya hana ta, tana ɗaure. Haka tsohuwa ta yi ta leƙen su, har yamma ta yi.

    Sai ta ga ya koma yaro, ya kama birgima, yana kuka, har iyayen suka dawo. Washe-gari sai tsohuwa ta yi kiran masu gidan, ta zana musu duk abin da ta gani. Ta ce idan sun shirya za su gona, su je gidanta su ɓuya, za su ga duk abin da yake yi. Sai suka amince. Washe-gari, suka shirya tafiya gona, amma sai suka shiga gidan tsohuwa suka ɓuya.

    Can sai yaron ya fara yin abin da ya saba, suna gani, abin ya fara ba su mamaki, har ya gama. Da suka dawo gida, sai suka ƙi dukan mai reno, shi kuma sai ya ƙi barin kuka. Sai matar ta shirya, ta tafi gidan boka, ta yi masa bayani.

    Sai boka ya ce, idan ta je gida washe-gari da safe ta sayo ɗan akuya ƙosasshe, ita da mijin su ja shi su yi ta tafiya, sai sun ga wata babbar bishiyar kuka. Ya ƙarasa da cewa: “Sai ku ajiye yaron, ku ce za ku huta. Sai ku ɗaure ɗan akuyan. Sai mijinki ya ce zai je ya yi fitsari, sai ya gudu. Ke kuma, sai ki ce za ki dubo shi, sai ki bi shi, kada ku juya”.

    Sai suka amince. Da gari ya waye, sai suka je suka samo ɗan akuya ƙosasshe, suka ɗaura igiya a wuyansa. Sai suka ce za su je wani ƙauye gaisuwa, sai matar ta ɗauki yaro ta goya, suka kama hanyar daji. Suna cikin tafiya, sai suka hango wannan babbar kuka, sai mijin ya ce su je su huta a gindinta.

    Da suka je, sai suka yi duk yadda bokan nan ya ce su yi, watau suka yi dabara, suka gudu. Da suka isa gida, sai tsohuwar ta sami matar ta ce to daga yau ta daina ƙwadayin sai ta sami ɗa ta kowace hanya, kuma ta rungumi ƙaddara sai abin da Allah ya yi da ita a rayuwarta.

    Da ɗan aljani ya gaji da jira, ya ga shiru, sai ya miƙe ya kunce ɗan akuya, ya riƙe, ya kama hanyarsa, ya shiga ƙungurmin daji, bai sake komawa gidan mutanen nan ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Zafin nema ba ya kawo samu.
    • Yi haƙuri da godiya ga abin da Allah ya ƙaddara a rayuwarka ta duniya.
    • Tsintacciyar mage ba ta yin kyanwa
    • Son zuciya, ɓacin zuciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Tatsuniyar Ɓarayin Albagadadi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani attajiri a wani gari ana kiran sa Albagadadi. Ba abin da yake so kamar ya ji wani yana neman taimako, domin ya taimaka masa. Duk ranar Jumma’a mutane kan taru maƙil a ƙofar gidansa, suna karɓar sadaka.

    Ana nan, ana nan, wata rana sai wani saurayi ya je wajensa ya ce masa yana son masauki, ko ya sami aikin yi a garin. Sai Albagadadi ya sauke shi a gidansa. Sannu a hankali, sai yaron nan ya zama hadiminsa, watau ya riƙa yi masa aikace-aikacensa na gida. Yaron kuma makarancin Alkur’ani ne sosai.

    Kullum idan Albagadadi zai je unguwa, ko dai wani wuri, to tare za su. Sai mutane suka sa wa yaron suna Sheikh Ali Albagadadi. Tun da yaron nan ya shiga gidan Albagadadi, sai komai nasa ya sauya; arziƙin uban gidansa ya yi ta bunƙasa. Duk abin da ya saya, ko gonar da ya noma, sai riba ta riɓanya ta da.

    Wata rana Albagadadi ya zauna tare da abokansa, sai ya kira Sheikh Ali ya ce yana son duk wanda yake wurin ya ba shi wani labari da zai faranta masa rai, zuciyarsa ta kwanta. Sai Sheikh Ali ya ce: “Wanda duk ya yalwata wa wanda ke cikin matsi, to shi ma Allah zai yalwata masa duniya da lahira.

    Wanda ya rufa asirin wani a yayin da yake buƙatar rufin asiri, to shi ma Allah zai rufa masa asiri duniya da lahira. Kuma duk wanda ya ba da sadaka tamkar wanda ya yi shuka ne, domin idan aka shuka masara kwaya uku, za katarar ta tsiro fiye da dubu uku. Kamar haka ne Allah yake saka wa masukyauta.”

    Duk wurin aka yi tsit ana jin bayaninsa. Sai ya ci gaba da cewa: “Ita sadaka takan gusar da bala’i da masifa, ta karya maƙiyi da Shaiɗan, kamar yadda ruwa yake kashe wuta, kuma ta goge zunubin mutum.” Kafin Sheikh Ali ya gama zancensa mai amfani, sai ya ga hawaye na kwarara daga idanun Albagadadi.

    Ganin haka sai ya dakatar da maganarsa. Rannan suna gida da daddare, sai suka ji muryar mutane a cikin gida. Ashe ɓarayi ne riƙe da makamai suka dira gidan da nufin yin sata, to amma ba sa iya ganin komai a cikin gidan. Can dai Ali Albagadadi ya yi tari, kuma tarinsa sai ya fasa ɓarayin, suka runtuma da gudu.

    A garin gudu, ɗaya ɓarawon ya faɗa rijiya, wuyansa ya karye. Na biyun kuma ya faɗa wani gida a kan wani dutse mai kaifi, shi ma ya mutu. Na ukunsu da ya samu ya fita bayan gari yana gudun ’yan bin sawu, sai ya yi ƙundunbala ya faɗa a kan wani kwazazzabo da yake zato tafki ne.

    A nan take shi ma ya sheƙa lahira. Da gari ya ƙarasa wayewa, jama’a suka daɗa taruwa, sai aka ɗebi ɓarayin nan aka binne su a rami. Mutanen garin suka yi ta mamakin yadda ɓarayin nan ba su saci komai a gidan Albagadadi ba, kuma sai suka riƙa cewa Allah ne ya kare shi saboda taimakon da yake yi wa mutane.

    Wannan kariya da Allah ya ba Albagadadi daga muguwar aniyar ɓarayi ce sanadiyyar da mutanen garin idan za su nemi tsari daga maƙiyansu sukan ce: “Kamar mutuwar ɓarayin Albagadadi.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ladabi da biyayya kan jawo arziƙi.
    • Mai arziƙin da ke tallafa wa mabuƙata Allah ne zai kare shi ya daɗa bunƙasa arziƙinsa.
    • Kyauta sadaka ba sa tauye arziƙin kowa.
    • Aikata alheri ga kowa, sakayya na wurin Allah.
    • Sadaka maganin asara.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Tatsuniyar Ƙuda Mai Kwaɗayi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wata ƙuda da ’ya’yanta. Kullum sukan je mahauta a kasuwa neman abin da za su ci, idan sun ƙoshi su koma gida. Wata rana sai ƙudar ta ja ƙawarta suka je mahautar neman abinci tare.

    Bayan sun samo, sai suka kama hanyar gida domin ita mai ’ya’yan ta kai musu gida, ta yi wa ƙananan cikinsu ƙoto. A kan hanyar komawa sai suka gamu da wani mai zuma. Sai ƙudar ta ba ƙawarta ƙunshin abincin da ta samo wa ’ya’yan ta kai musu, saboda za ta bi mai zuma ko ta kalato musu zumar.

    Kawarta ta karɓi jaka ta nufo gida, ta ba yara; sai babbar cikin ’ya’yan ta tambayi inda mahaifiyarsu ta tafi. Kawar ta ce mata ta bar gyatumarsu a kasuwa, wurin mai zuma. Ko da ta ji haka, sai ta kama kuka ta ce ai kwanan uwarsu ya ƙare, tun da ta bi mai zuma.

    Sai yarinyar da ƙawar uwarta suka yanke shawarar gara su je kasuwar su gani ko za su taho da ita. Sai suka hangi mai zuma, suka leƙa jikin ƙwaryarsa, sai suka gan ta a manne cikin sakar zuma, ta mutu.

    A nan duk suka fashe da kuka, suka tashi fir, ba su tsaya ba sai gidansu. Da suka ba da labarin rasuwarta, sai aka shiga zaman juyayi. Duk inda kuka ga ƙudaje sun taru cunkus, to zaman juyayin suke yi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabudin wahala.
    • Garin neman gira, an ya da ido.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Auta Da Dodanniya

    Edita@rumasau-kallamu