Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar Talume

    Tatsuniyar Talume

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wata yarinya wai ita Talume sun je daji cin ɓaure ita da kawayenta da sauran ’yan matan garinsu, tare kuma da yayyensu mata. Bayan sun gama shan ɓaure, sai yayyen yaran nan suka ce da su: “Kowacce ta share hannunta, ta goge bakinta, kuma kada a ce za a ɓoye a kai gida.”

    Ashe Talume ta ɓoye wani ɓauren domin ta kai wa mahaifiyarta, ga kuma danƙonsa da ta bari a hannunta ba ta share ba domin ta riƙa lasa a hanya. Suna cikin tafiya sai ta riƙa tanɗar hannunta, tana jin zaƙin ɓaure, har suka isa gida. Da ta kawo ɓauren ta ba mahaifiyarta, sai ta tambaye ta da cewa:

    “Kai wannan ɓaure da zaƙi yake, a ina kika samo shi?” Sai ta ce da ita: “Ni da su yaya muka samo shi a daji.” Ana nan, ana nan, rannan Talume da ƙawayenta sun shirya za su je biki, sai ta roƙi mahaifiyarta ta ba ta aron zannuwanta ta ɗaura. Da uwar ta ji haka, sai ta ce mata: “Zan ba ki, to amma sai kin kawo mini irin ɓauren nan na kwanakin baya.”

    Sai Talume ta ce: “To bari in je daji ko zan samo shi.” Ta kama hanya tana tafiya har ta kai gindin ɓaure, ta rasa yadda za ta yi. Sai ta kama waƙa, tana yi ɓaure yana mayar mata suna cewa:

    Talume: “ɓaure, ɓaure ka ba ni ɓaure.”

    Baure: “Yarinya, in ba ki Baure? In ba ki Baure ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Baure: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Baure: “Ki je ina?”

    Talume: “In je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Baure ya ce mata ta iya waƙa, kuma ta je ta nemo kashin shanu ta kawo masa kafin ya ba ta ’ya’yansa. Ta kama hanya ta sami shanu suna kiwo. Kamar yadda suka yi da ɓaure, ga waƙar da ta fara suka amsa mata:

    Talume: “Shanu, shanu ku ba ni kashi.”

    Shanu: “Mu ba ki kashi, ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa ɓaure.”

    Shanu: “Ki kai wa Baure ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Shanu: “Ya ba ki ’ya’ya ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Shanu: “Ki kai wa inna ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Shanu: “Ta ba ni kaya, ki je ina?”

    Talume: “Ta ba ni kaya in je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai ɗaya daga cikin shanun ta ce: “Ki je ki kawo mana ciyawa mu ci, sai mu yi kashi ki kwasa.” Sai ta ce: “To.” Ta doshi inda ciyawa ta fito ta yi lif-lif, koriya shar gwanin ban sha’awa ta ce:

    “Ciyawa, Ciyawa ki ba ni ciyawa.”

    Ciyawa: “In ba ki ciyawa ki kai ina?”

    Talume: “In kai wa shanu.”

    Ciyawa: “Ki kai wa shanu su ba ki me?”

    Talume: “Su ba ni kashi.”

    Ciyawa: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa Baure.”

    Ciyawa: “Ki kai wa Baure ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Ciyawa: “Ya ba ki ’ya’ya ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Ciyawa: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya in je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Ciyawa ta ce: “Hanzarta ki ɗebo ruwa ki kawo. Ki zuba mini, in ya so ki yanke ni ki kai wa shanun.” Yarinya ta ce: “To, ciyawa, na gode.” Da ta isa bakin wani babban gulbi mai ruwa garai-garai, sai ta ce: “

    Gulbi, Gulbi, ka ba ni ruwa.”

    Gulbi: “In ba ki ruwa ki kai wa wa?”

    Talume: “Ka ba ni ruwa in kai wa ciyawa.”

    Gulbi: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni ciyawa.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa shanu.”

    Gulbi: “Su ba ki me?”

    Talume: “Su ba ni kashi.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa Baure.”

    Gulbi: “Ya ba ki me?”

    Talume: “Ya ba ni ’ya’ya.”

    Gulbi: “Ki kai wa wa?”

    Talume: “In kai wa babata.”

    Gulbi: “Ta ba ki me?”

    Talume: “Ta ba ni kaya.”

    Gulbi: “Ki je ina?”

    Talume: “In je biki, ’Yan mata duk sun tafi, Samari duk sun tafi.”

    Sai Gulbi ya ce: “Kai wannan yarinya da ƙoƙari kike, zo ki ɗebi ruwan da zai kashe wa Ciyawa ƙishirwarta domin ta yarda ki yanke ta.” Yarinyar ta ɗebi ruwa mai yawa salka-salka ta je ta zuba wa Ciyawa. Ciyawa ta ƙara kyau, abin sai wanda ya gani, sai ta ce da Talume:

    “Yanki yadda za ta ƙosar da shanun nan domin su yi kashi da yawa.” Sai ta yanka ta kai wa shanu, suka ci suka yi kashi mai yawa, kuma subul-subul mai kyau. Nan da nan Talume ta lafci kashin nan ta kai wa ɓaure ya yi murna da wannan kashin shanu da bai taɓa cin mai daɗi irinsa ba.

    Sai shi kuma ya zubo mata da ’ya’ya masu yawa, waɗanda suka nuna lugub ta ɗiba ta kai wa mahaifiyarta,ita kuma ta yi godiya, ta kawo kayan da ta nema ta ba ta. Talume ta sa kaya, ta je wurin biki ta tarar an gama biki, amma Kuraye suna yin nasu. Da Kurayen nan suka ga Talume, sai suka yi kanta za su cinye ta, sai ta gudu, suka bi ta, har gida.

    A gidansu kuma, sai ta tarar an rufe ƙofar kowane ɗaki. Sai ta doshi ƙofar ɗakin mahaifiyarta ta ce: “Iya buɗe mini ɗaki.” Sai mahaifiyarta ta ce: “Abin da ya biyo ki, ya cinye ki.” Haka ta yi ta bi ɗaki-ɗaki, ba wanda ya buɗe mata. Amma da ta je ɗakin kakarta ta buga, sai ta buɗe mata.

    Da Kuraye suka ga Talume ta shiga ɗaki, sai suka haƙura saboda tsoron ko tarko aka yi musu suka gudu, ita kuma ta tsira. Washe-gari bayan kowa ya tafi gona sai Talume ta tattara kayanta, ta bar garinsu; ta je wani gari ta sami miji ta yi aure, ta ƙi zuwa ko da ganin gida shekara da shekaru. Mahaifanta sun so ganin ta, amma ta ƙi zuwa gida.

    Ana nan sai mahaifan Talume suka ji labarin garin da ta yi aure, sai mahaifinta ya ce a je a gaya mata mahaifiyarta ta rasu. Aka kuwa same ta, aka gaya mata, amma ta ƙi zuwa. Bayan wasu watanni kuma ya ce a je a ce mata mahaifinta ya rasu. Aka je, aka gaya mata, amma ta ƙi zuwa.

    Daga ƙarshe dai sai aka tashi wani tsuntsu Goraje aka aike shi don ya gaya mata yayyenta da ƙannenta duk sun mutu. Goraje ya tashi fir, bai tsaya ba sai a ƙofar ɗakinta ya ce:

    Goraje: “Salamu alaikum Talume.”

    Talume: “Wa alekumus-salam Goraje.”

    Goraje: “Mahaifiyarki ta mutu Talume. Bariki ba gida ba.”

    Talume: “Bariki ba gida ba, Goraje, Uwata ƙi ni, Goraje, Baba ya ƙi ni, Goraje, Yaya ta ƙi ni, Goraje, Kaka ta so ni, Bariki ba gida ba, Goraje, Ku je ku binne, Goraje.”

    Sai tsuntsun ya koma ya shaida wa waɗanda suka aike shi, cewa Talume ta ƙi zuwa. Can sai wani maƙwabcin babanta da ya san tarihin abin da ya faru ranar da Kuraye suka bi ta za su kashe ta ya ce: “Idan kuna so ta zo, ku aika mata cewa kakarta ta rasu.” Jin haka ke da wuya sai aka sa tsuntsu Goraje ya je ya gaya mata kakarta ta rasu, ana can za a rufe ta.

    Sai ta ce da tsuntsu: “Ga ni nan, kada a rufe ta sai na gan ta.” Talume ta shirya kayanta ta je garinsu, ta isa har gida. Sai ta tarar duk mutanen gidan ba wanda ya mutu, amma duk sun tafi gonakinsu aiki, in ban da kakar nan tata. Ta gayar da ita, suka yi hira. Jim kaɗan ta ce za ta komagarin mijinta.

    Sai kakar ta ce da ita: “Kina da gaskiya, kama hanya, aure ba abin wasa ba ne.” Talume ta shirya ta ɗauki kayanta, ta kama hanya. Da iyayenta da yayyenta da ƙannenta suka dawo suka ji ta zo, amma ta ƙi jiran su, sai suka ce: “Kai wani hali sai su Talume.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Shan wahala a rayuwa ba ya hana a ƙarshe a sami kyautatawar hali.
    • Motsi ya fi zama
    • Mai nema yana tare da samu
    • Mahaƙurci, mawadaci.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Tatsuniyar Sarki, Gizo Da Kwarkwata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana a can kusa da garin da Gizo ke sarauta, wani tsoho yana cikin gonarsa yana kashe kwarkwata, sai ya ga wata ƙatuwar kwarkwata, har ya haɗa manyan yatsunsa zai murtsuke ta, sai ta ce da shi: “Kada ka kashe ni, zan yi maka tsaro a gonarka, kada ka kashe ni.”

    Sai ya tambaye ta: “Idan na bar ki, me za ki yi mini?” Sai Kwarkwata ta ce: “Kai dai ka sake ni a cikin gonarka ka gani.” Mamaki ya kamaTsoho, sai ya sake ta a cikin gonarsa. Ya yi kamar ya tafi gida, amma sai ya sami wuri ya ɓuya. Yana maƙe, sai ga wasu fadawan Sarki Gizo sun zo gonar sata.

    Da suka je za su yanki harawar wake sai Kwarkwata ta fara waƙa tana cewa:

    “Caca bille, caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawan Sarki Gizo,

    Sun zo satar harawar wake,

    Su kai wa dokin Sarki.”

    Waƙar Kwarkwata da ta ratsa fadawan Sarki sai suka fara rawa. Da Sarki Gizo ya ga shiru, sai ya tura dogarawansa, watau su Kiyashi da Kyankyaso da Fara su kamo fadawan da ya tura don su yanko harawar wake. Dogarawa na zuwa suka ce da fadawa: “Yaya Sarki ya tura ku ciyawa kuka yi zamanku?

    To, an ce mu kama ku.” Sai fadawan nan suka ce da dogaran Sarki: “Ku taɓa waken ku ma ku gani.” Da dogaran suka taɓa waken kamar za su yanki harawar, sai Kwarkwata ta shiga abin da ta saba:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Su ma dogarawa suka kama rawa. Ba damar komawa fada, balle Sarki Gizo ya san me ake ciki. Da daɗewar ta yi yawa, sai Sarki Gizo ya taso baradensa, wato manyan mayaƙansa, irin su Kudan zuma da Kunama da Sari-kutuf da Macizai da Rina da Kwarkwasa domin su kamo masa fadawa da dogarawa saboda sun yi wa Sarki ƙyuya.

    Suna isa suka fara daka wa fadawa da dogarawa tsawa, suna cewa: “Sarki ya aiko ku yankan harawar dawakinsa, ba ku koma ba. Kun raina Sarki ke nan ko?” Fadawa da dogarawa ba su tsaya wani wuni-wuni ba, suka ce da sojojin nan: “Ku taɓa waken nan kamar za ku yanki harawar ku ga abin da zai faru.”

    Sai suka taɓa; sai Kwarkwata ta rera waƙarta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Sojoji sun zo,

    Garin satar harawar wake,

    Su kai wa dawakin Sarki.”

    Sai su ma suka kama rawa. Da Sarki ya ji shiru, sai ya je gonar shi da kansa a fusace. Yana isa sai ya ga baradensa da dogarawansa da fadawansa suna ta dirkar rawa ba ƙaƙƙautawa a wannan gonar. Sai ya faɗa su da faɗa. Da suka ga ran Sarki Gizo ya ɓaci, sai wasu daga cikinsu suka ce: “Ranka ya daɗe, taɓa waken nan kamar za ka yanki harawar ka gani.”

    Gaya wa Sarki haka ke da wuya, sai ya ƙara harzuƙa, sai ya ce: “Zan sa a fille muku kawuna.” Baki ɗayansu sai suka ce: “Don girman ikon da ke hannunka ka taɓa waken ka ga abin damaki.” Sai Sarki ya taɓa wake, hannunsa na sauka a kan waken nan sai Kwarkwata ta shiga aikinta:

    “Caca bille, Caca bille,

    Burabusko bille,

    Fadawa sun zo,

    Dogarawa sun zo,

    Barade sun zo,

    Sarki ya zo satar wake,

    Ya kai wa dawakinsa.”

    To, Sarki Gizo bai yi rawar ba, saboda shirinsa ya fi na Kwarkwatar. Wato hatsabibancin Sarki ya fi na Kwarkwata ƙarfi. Sai ya ce da fadawansa: “Kai wannan gonar ta wace ce?” Tsoho da ke maƙe bai mabari fadawa sun yi wa Sarki jawabi ba sai furut ya fito ya faɗi a gaban Gizo ya ce: “Mai duniya ka daɗe, ni ne mai gonar nan.”

    Sai Sarki Gizo ya ce: “Wane aiki ka yi wa gonarka take yin haka?” Sai Tsohon nan ya ba Sarki labarin yadda suka yi da Kwarkwata. Sai Sarki Gizo ya ce: “Tana ina?” Nan da nan ya ɗauko ta ya je gaban Sarki ya miƙa masa ita. Sai Sarki ya ce da Tsoho yana son ya bar masa Kwarkwatar nan, kuma ya sa ta saki fadawansa da dogarawansa da baradensa da ta sa su rawa.

    Da ya roƙe ta sai ta sake su, suka daina rawar, kuma ya mallaka wa Sarki Kwarkwata. Sarki Gizo saboda jin daɗi ya kawo kuɗi masu yawa ya ba Tsoho, shi kuma ya tafi fada da wannan Kwarkwatar. Duk sanda yake cikin nishaɗi sai ya sa ta zo ta rera masa waƙoki iri daban-daban.

    Duk sanda yake cikin raha kuma sai ya tsokani dogarawansa da fadawansa da sojojinsa ya ce: “Na gaban Sarki waɗanda Kwarkwata ta ci ku da yaƙi.” Sai duk a fashe da dariya. Haka dai Sarki Gizo ya ci gaba da tafiyar da mulkinsa tare da fadawansa da dogarawansa cikin jin daɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Tausaya wa halittar Ubangiji yakan yi sanadin samun nasara.
    • Adalci shi ne sinadarin samun nasarar kowane shugabanci; azzalumin shugaba kuma ƙarshensa nadama.
    • Kula da kaya, ya fi ban cigiya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Tatsuniyar Kogi Mai Cinye Maƙaryata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ’ya’yansa su goma sha biyu. Wata rana sai ya samo ’ya’yan kaɗanya ya kai gidansa. Da ɗaya daga cikin ’ya’yansa ya ga kaɗanya nunanniya, sai ya ɗauka ya shanye. Mahaifinsu ya tambaye su wanda ya shanye masa kaɗanya, kowanne daga cikinsu ya ce ba shi ba ne.

    Ya sake tambayar su, kowa ya ce ba shi ba ne. Suka yi ta yin haka, shi kuma wanda ya shanye kaɗanya bai bayyana kansa ba. Can dai sai mahaifin nasu ya ce da su: “To, tun da kun kasa fitar da wanda ya shanye kaɗanyar nan, za mu je da ku kogin da ke cinye maƙaryata.

    Duk wanda ya shanye mini kaɗanya, to ko ruwa zai cinye shi.” Mahaifinsu ya shige gaba, suka bi shi duu, ba su tsaya ba sai a bakin kogin da kowa ya san yakan cinye marasa gaskiya. Zuwansu ke da wuya, sai babban cikinsu ya shiga kogi, ya fara wannan waƙa:

    “Kogi, kogi maganin maƙaryata,

    In ni ne na shanye kaɗanyar baba,

    Alkawari mai dare da rana,

    Cinye ni kogi,

    Tafi da ni kogi.”

    Da ya gama waƙar sai ya tsunduma cikin kogi, ya haye ɗaya gaɓar lafiya ya tsaya. Sai mai bi masa shi ma ya yi waƙa, ya faɗa kogin nan ruwan bai cinye shi ba. Haka dai suka yi ta shiga. Goma sha ɗaya suka haye ruwanlafiya. Da na ƙarshe ya zo ya shiga, sai shi ma ya sa waƙa:

    “Kogi, kogi maganin maƙaryata,

    In ni ne na shanye kaɗanyar baba,

    Alkawari mai dare da rana,

    Cinye ni, Cinye ni kogi, Janye ni kogi.”

    Tun bai gama waƙar ba ruwan kogin ya fara shan kansa. Kafin ’yan’uwan su farga, kogi ya fara janye shi. Sai ya fashe da kukan baƙin ciki da nadama; ’yan’uwan su ma suka fashe da kukan rashin ɗan’uwansu. Shi yana kuka, su ma suna yi, har ya nutse a ruwan nan, suka daina ganinsa.

    Da suka koma gida sai babansu ya ce da su: “To kun ga sakamakon taɓa kayan wani ba da yardarsa ba ko?” Suka ce: “Mun gani Baba, daga yau ba za mu sake taɓa kayanka ba sai ka ba mu.” Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yin cikakken bincike yayin da za a yi wani hukunci yana haifar da sakamako mai kyau.
    • Kwaɗayai mabuɗin wahala
    • Son zuciya ɓacin zuciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Tatsuniyar Kurege Da Biri

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Kurege da Biri suka ga wata yarinya, kowannensu ya nuna yana son ta da aure. Sai kowannensu ya aika a tambayo masa izinin nemanta da aure. Iyayen yarinya suka ce duk wanda yake son ‘yarsu da aure sai ya kawo musu fatun namun daji. Da Kurege ya ji haka, sai ya je wurin Kaza ya ce da ita: “Ina gayyatar ki aiki a gonata gobe.”

    Kaza na jin haka ta ce: “To, zan zo amma fa kada ka gaya wa Kyanwa.” Sai ya ce: “Haba me zai sa in gaya mata kuwa?” Daga gidan Kaza Kurege bai zame ko’ina ba sai gidan Mage, ya ce da ita: “Ina son za ki taya ni aiki a gona gobe.” Mage na ji sai ta yi farat ta ce: “To, amma fa kada ka gaya wa Kare, ka san idan ya gan ni a wurin zai cinye ni.”

    Kurege ya ce da ita: “Haba, ai na san haka, wa zai gayyaci wannan a gonarsa?” Yana fita sai ya nufi gidan Kare, ya same shi ya ce da shi: “Ina so ka taya ni aiki a gona gobe.” Da gari ya waye, tun da sassafe Kurege da Kaza suka isa gona, suna cikin aiki sai ga Mage. Sai Kurege ya ce da Kaza: “Maza ki ɓuya a cikin ciyawa.”

    Da Magenta isa kusa da Kurege sai ta ce: “Na ji kana magana kai da wane ne?” Sai Kurege ya ce: “Ni da Kaza ne, ga ta can a cikin ciyawa. Idan kin cinye namanta, ni ne da fata.” Nan da nan Kyanwa ta gano inda Kaza ta ɓuya. Tana ganin ta sai ta auka mata, ta murƙushe ta, ta kashe, ta cinye nama, ta ce da Kurege: “Ga fatar da ka ce kana so.”

    Kurege da Mage suka ci gaba da aiki a gona. Jim kaɗan sai ga Kare, ya zo yana haki bayan ya yi gudun ceton rai, saboda yara sun bi shi za su kashe a hanya. Bayan Kurege ya yi wa Kare barka da zuwa, sai Kare ya ce: “Kurege kai da wane ne a gonar nan?” Sai Kurege ya matsa kusa da shi ya kashe murya ya ce: “Ni da Mage ne, tana can tana aiki.

    Idan ka kashe ta, ka cinye naman, ka bar mini fatarta.” Kare ya yi godiya ya je ya shammaci Kyanwa ya turmushe ta, ya shaƙe wuyanta. Da ta mutu ya cinye naman, ya bar wa Kurege fatar. Sai Kare ya dubi Kurege ya ce da shi: “To amma fa ka san idan ka gaya wa Kura ba zan zo ba.” Kurege ya ce da shi, “Wa zai gaya wa Kura?

    Me za a yi da wannan sarauniyar kwaɗayi?” Da Kurege ya fita bai tsaya ba sai a ƙofar ramin Kura. Bayan sun gaisa sai ya ce da ita: “Na zo gayyatar ki aiki ne a gonata gobe da safe.” Yana rufe baki sai Kura ta ce: “Kai ni gobe ba zan sami dama ba, zan je cin wani mushe da na gani jiya.”

    Da Kurege ya ji haka sai ya ce da Kura: “Haba Kura, idan aka yi aikin gonata ba ki je ba, ai za a ce ni da ke mun ɓata. Kin san ke ce babbar ƙawata. Ki tuna fa mun sha yin abubuwa da yawa tare.” Wannan maganata Kurege ta yi wa Kura daɗi, sai ta dube shi ta ce: “To zan zo, amma fa kada ka gaya wa Damisa, ka san ta da nuna fin ƙarfi.”

    Sai Kurege ya ce da Kura: “Me ya gama ni da Damisa kuma? Ban san inda take ba ma yanzu.” Da Kurege ya fita sai ya nufi dutsen da Damisa take tare da ‘ya’yanta. Bayan ya gayar da ita, sai ya ce mata: “Ranƙi ya daɗe, ina roƙon ki zo aiki a gonata gobe da safe, idan da hali. Kin san ku manya sai kun sami hali.”

    Sai Damisa ta yi miƙa, ta buɗe bakinta, Kurege ya ga haƙoranta masu kaifi da tsini sai ta ce: “Kai Kurege wa ka gayyata bayan ni?” Sai Kurege ya yi durƙuson ban girma ya ce: “Kura dai tana ciki.” Da Damisa ta ji haka, sai ta ce: “Yawwa, ka kyauta yaron kirki, lallai zan zo.”

    Kare da Kurege suka kama aiki, amma saboda Kare ya ƙoshi da naman Kyanwa sai ya kwanta a gindin wani ƙargo ya fara barci. Can sai ga Kura ta iso ta dubi Kurege ta ce: “Abokina yanzu ba wanda ya zo aikin nan sai ni?” Sai Kurege ya ce: “Ai ke ƙawata ce, kuma kina da kirki, amma Kare ya riga ki zuwa, ga shi can ma yana barci.

    Idan kin cinye shi, ki bar mini fatar.” Da man Kura tana jin yunwa saboda Kurege ya sa ta haƙura da zuwa wurin mushen da ta gaya masa ta gani, sai ta ce: “Amma kuwa na gode.” Sai ta je ta kashe Kare a cikin ruwan sanyi saboda yana barci, ta cinye namansa ƙafaf saboda haɗama har ma ta fara cin fatar Kurege ya je ya fisge.

    Daga nan Kura da Kurege suka kama aiki a gonar. Can sai ga Damisa ta tunkaro gonar. Shi Kurege da ma ya san haka, amma Kura ba ta sani ba. Da ya fara hango Damisa tana zuwa, sai ya ce da Kura: “Babbar ƙawata, ai ya kamata ki ɓuya ina gani kamar za mu yi manyan baƙi.”

    A tsorace Kura ta sami gindin wata kuka ta raɓe. Da Damisa ta isa gonar sai Kurege ya ce: “Kai madalla, sannu da zuwa manyanmu.” Sai ta harare shi ta ce: “Ka ce Kura za ta zo, ko tana ina ne?” Sai Kurege ya nuna mata maɓoyar Kura sai ya ce da ita: “To, amma idan kin kashe ta, ina roƙo ki ba ni fatar.” Ta ce: “To na ji.”

    Damisa na faɗin haka sai ta nufi inda Kura ta ɓuya. Kafin Kura ta san abin da ake ciki, tuni Damisa ta sa haƙoranta masu kaifi da tsini ta tsinke jijiyoyin wuyan Kura ko shurawa ba ta yi ba. Kafin wani lokaci Damisa ta yi kaca-kaca da ita, ta cinye ta. Sai fatar kawai ta bari da ƙoƙon kanta. Da ta gama, sai ta je wurin Kurege ta ce: “Ga fatar can.

    Ka kuma gayyatar wata Kurar aiki a gonarka zan zo.” Kurege yana ƙyarma, ya ce da Damisa: “To, na gode, zan sanar da ke idan za a sake yin irin wannan aiki.” Cikin murna Kurege ya shiga tara fatun nan. A zuci ma ya riƙa cewa: “Yawwa, ni ne zan sami mata. Biri kam sai haƙuri.”

    Da Biri ya ji labarin abin da Kurege ya aikata, kuma ya ji yana cewa shi ne zai auri yarinyar nan sai a zuciyarsa ya ce: “Haba Kurege, za ka ga tsiyata kuwa.” Biri kuwa ya je ya samo gyaɗa mai yawa, ya bi hanyar gidan iyayen yarinyar yana zubarwa, wato inda Kurege zai bi don ya kai musu fatun da suka nema.

    Da Kurege ya kama hanya ya ga gyaɗa a warwatse sai ya fara tsinta yana cewa: “Yau daɗi goma, ga shi na samo fatu zan kai a ba ni mata, kuma ga ƙauyawa sun sayo gyaɗa daga kasuwa sun ajiye mini domin in ci in more.” Kurege na matsawa gaba, gyaɗar tana ƙara yawa, har dai ta kai shi bakin wani ƙasko wanda yake cike da gyaɗa.

    Sai kawai ya tsuguna a kusa da ƙaskon, ya zubar da fatu gefe, ya duƙufa a kan cin gyaɗa. Shi kuma Biri sarkin wayo sai ya bi ta bayan Kurege yana sanɗa, ya kwashe fatun nan Kurege bai sani ba. Biri ya tafi da fatu ya kai wa iyayen yarinyar nan, suka amsa, aka ɗaura masa aure da ita.

    Bayan Kurege ya ci gyaɗa ta yi masa karo, sai ya waiwaya zai ɗauki fatunsa, sai ya ga wayam, ba komai a wurin, sai ya ce: “Na tabbata Biri ne ya yi mini wannan aikin. Amma bari in kai musu ragowar gyaɗar wataƙila su yarda su ɗaura auren da ni.” Kurege na isa iyayen yarinya suka ce ai tuni Biri ya kawo fatu, har ma an ɗaura masa aure da yarinyar.

    Da Kurege ya ji haka, sai ya ba su gyaɗar da ya je da ita, tare da igiyar da ya tanada wai ta ɗaurin aurensa da yarinya, ya ce: “Ga wannan igiya za ta yi muku amfani, gyaɗar kuma ku soya ku ci.” Suka karɓa ya tafi. Kurege bai tsaya ba sai a gidan Biri, sai ya tarar da wani tsohon Biri, watau kawun ango, ya ce da shi: “Ni abokin ango ne.”

    Jin haka sai tsohon Birin ya ƙyale Kurege ya shiga inda ango ke barci. Da shigarsa sai ya sa wa Biri dafi a baki, wanda a ƙarshe ya kasa tashi daga wannan barcin, ya mutu. Sai nan da nan Kurege ya nemo garin dawa a gidan, ya cusa a bakin Biri, don a ce garin ne ya ci ya yi masa karo ya kashe shi.

    Can sai amaryar Biri ta shigo ɗakin ta ce: “Yaya na ga ango yana barci, amma kuma ga shi kamar yana cin wani abu?” Da ta ɗan taɓa shi, sai ta gane dai ya mutu, sai ta fara kuka, shi ma Kurege ya shiga kuka. Da ya yi shiru, sai ya ce da matar Biri: “Akwai wani Dodo a daji, ya kamata mu je ya gaya mana abin da ya kashe miki miji.”

    Da suka shiga dajin nan, sai Kurege ya ce ta jira shi yana zuwa. Nan da nan ya je ya zane jikinsa da gawayi, ya canza kamanninsa ya sha gabanta, ya tsaya kamar shi ne Dodon, sai ya ce: “Ke baƙuwata, ni ne Dodon baƙin daji, me ya kawo ki?” Ita kuma ba ta gane Kurege ba ne sai ta ce da shi: “Mijina ne ya mutu, ina son sanin wanda ya kashe shi.

    Kuma ina son sanin wanda zan aura.” Sai Dodo ya ce: “Ai Kurege abokin Biri ne, kuma ƙanensa ne saboda Biri ya girme shi ko?” Sai matar Biri ta ce: “Ba shakka haka ne, ko shi zan aura?” Sai Dodo ya kaɗa kai domin nuna amincewa. Ta ƙara tambayar sa, har dai ta tambaya sau uku, duk yana nuna cewa ta auri Kurege.

    Daga nan ya sallame ta, ta koma gidan Biri. Shi kuma Kurege ya je wani tafki ya yi wanka ya kama hanyar gidan Biri, ya tafi yana kuka. Da amaryar marigayi Biri ta ga Kurege yana kuka sai ta ce: “Mene ne kuma ya faru?” Sai Kurege ya ce: “Na tuna ɗan’uwana, kuma abokina ne.”

    Da ta ji haka, sai ta dubi Kurege a cikin tausayi ta ce da shi: “Ai Dodo ya ce kai zan aura saboda haka ka daina kuka, ka zo mu je a ɗaura mana aure.” Sai Kurege ya daina kuka, suka kama hanyar gidan iyayenta inda za a ɗaura musu aure. Aka ɗaura musu aure suka zauna cikin jin daɗi lokaci mai tsawo. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Zamba da cin amana mai yin sa ba ya kai wa ga nasara.
    • Komai za a yi ya kamata a yi shi cikin hikima da ƙwarewa, yin haka shi yake kawo samun biyan buƙata.
    • Ƙarya fure take, ba ta ‘ya’ya.
    • Matar mutum kabarinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Tatsuniyar ‘Yar ‘auta Da Kogin Rantsuwa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum mai mata ɗaya da ‘ya’yansu tara maza da mata, waɗanda yake ƙaunar su ƙwarai. Kullum idan ya je kasuwa, sai ya sayo kifaye tara saboda yaran nan. Suna nan haka cikin annashuwa, sai wata rana da ya kai kifayen nan tara, ‘yar autar gidan ta ɗauki ɗaya ta cinye ba tare da ta tambaya ba.

    Ta yi haka ne kuwa saboda wautar ƙuruciya. Da ya duba ya ga kifaye ba su cika ba, sai ya ce a tafi rafin Tantafane domin ‘yan ruwa su yi maganin wanda ya cinye kifin nan. Shi ke nan, da suka je sai babbar cikinsu ta fara waƙa tana cewa:

    “Kogi, kogin Tantafane,

    In ni na cinye kifin baba,

    Ruwa ka tafi da ni,

    Kar ka dawo da ni.”

    Da haka ɗaya bayan ɗaya har takwas daga cikin yaran suka yi waƙa, amma ruwan bai cinye su ba, ya rage ‘Yar auta. Ita kuma tana can gefe tana shirme irin na yarinta, sai suka ce: “Saura ke, ‘Yar’autar iya da baba.” A nan dai ‘yan’uwan suka matsa sai ta yi, har ma suka ce idan ba ta yi ba za su kashe ta.

    ‘Yar’auta ta sa ƙafafunta a cikin ruwa, ta yi waƙa ƙafin ma ta gama waƙar ‘yan ruwa sun janye ta, wato ruwa ya tafi da ita. To, akwai wata tsohuwa da ta saba da ‘yan ruwan da suka kama ‘Yar’auta. Sun saba da ita ne kuwa saboda ta fi shekara sha uku tana zuwa rafin nan kamun kifi.

    Saboda haka ba su cinye ‘Yar’auta ba domin sun ga kyakkyawa ce, sai suka ba tsohuwar nan ita riƙo. Yarinya ta bi tsohuwa kamar ita ce ta haife ta, ita kuma ta riƙe ta kamar ‘yarta. Ana nan, ‘Yar’auta ta girma, har masu neman aurenta suka fara fitowa, har mata fitar da ɗaya daga cikin manemanta, tsohuwa ta amince da zaɓen da ta yi.

    To, amma sai ta ce da manemin yarinyar: “Ka je ka kawo buhun kwarkwata, wannan ne abin da za a ba ‘yan ruwa.” Nan da nan yaron ya je ya gaya wa mahaifiyarsa ita da danginta suka haɗa ƙarfi; washe-gari suka kai wa tsohuwa buhun kwarkwata cikakke har da toliya.

    Ba tare da wani ɓata lokaci ba aka ɗaura musu aure, ‘Yar’auta ta tare a gidan miji. Ashe angon nan yayan ‘Yar’auta ne bai sani ba, amma ita ta gane, sai dai ta yi shiru ba ta faɗa ba. Duk sanda mazan gidan suka tafi gona, da ta fara dakan garin abincin da za ta yi musu, sai ta fara waƙa tana cewa:

    “In daki turmin gidanmu,

    In daki turmin gidanmu,

    Tim, ƙwal, ƙwal.

    A yau uwata,

    Ta zama surukata.

    Ubana ya zama surukina,

    Ƙannena ne abokan wasana.

    In daki turmin gidanmu,

    In daki turmin gidanmu,

    Tim, ƙwal, ƙwal.”

    To akwai wata tsohuwa da takan zauna a zaure duk sanda mutanen gidan suka bar amaryar nan a gida, takan ji abin da amaryar kan faɗa. Rannan sai tsohuwa ta ce da mutan gidan: “Idan kun shirya tafiya gona, ku laɓe ku ji abin da amaryar nan za ta faɗa.” Suka kuwa karɓi shawararta, suka kuma aikata abin da ta ce su yi.

    Ɗaya daga cikinsu ma ta koma cikin gidan, da amaryar ta gan ta sai ta ce da ita: “Me kike yi a gida?” Sai ta ce: “Na mance fartanyata ne na zo ɗauka, zan koma gona.” Da ta ɗauki fartanya, sai ta yi kamar ta kama hanyar gonar ne, jim kaɗan sai amaryar ta ɗauki turmi, ta hau daka tana yin waƙar da ta saba yi.

    Sai ko gaba ɗayansu suka fito daga maɓoyarsu suka ce: “Ashe ‘Yar’auta ce?” Ita kuwa sai dariya take yi tana cewa: “E, ni ce.” Nan take suka rungume juna, kowa sai kukan murna yake yi. Daga nan kuma sai aka manta da zancen aure ta ci gaba da zama a cikin danginta. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Shugabannin ƙwarai su suke ƙoƙarin hukunta marasa gaskiya ko da a cikin iyalinsu suka fito.
    • Hukunta marar gaskiya ba zai hana shi zama mutumin kirki ba.
    • Aukawa cikin wata hulɗa ba tare da yin bincike ba yakan haifar da matsala.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Kushewar baɗi sai baɗi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Gwaidayara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gwaidayara

    Tatsuniyar Gwaidayara

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can bakin Rafin Kada akwai wani mutum da yake zaune tare da matansa su huɗu; sai dukkaninsu suka sami ciki a lokaci ɗaya. Da watansu ya kama suka haifi ’ya’ya duka mata. Bayan mako guda na al’ada, ya raɗa wa uku daga cikin yaran nan sunaye. Ɗaya sunanta Halima, ɗaya Jummai, ta ukun kuma A’isha.

    Amma sai ya ƙi rada wa ’yar matarsa ɗaya suna. Sai mahaifiyar tata ta tambaye shi: “Me ya sa ni ba za ka sa wa ’yata suna ba?” Bai dai amsa ba, amma ya ce zai raɗa mata suna. Haka dai ta riƙa tuna masa, har wata rana a cikin gatse ya ce: “Ki je sunanta Gwaidayara.”

    Kwanci tashi, yaran nan huɗu suka data, suka isa aure, shi kuma ya tsaya ya tabbatar Halima da Jummai da A’isha kowacce ta sami mijin aure, watau ban da Gwaidayara. Kuma ya yi haka ne saboda bai cika son uwarta ba. Da uwar ta ga haka, sai ta durƙusa ta ce da shi: “Shin Mai gida, me ya sa ba za ka yi wa’yata aure kamar yadda ka yi wa ’yan’uwanta ba?”

    Sai ya dube ta ya ce: “Ki gaya mata ta riƙa bi na daji.” Uwar Gwaidayara kuwa ba ta jinkirta wajen sanar da ’yarta abin da mai gida ya ce ta gaya mata ba. Haka kuwa aka yi. Duk sanda uban zai je daji sai ta bi shi. Kullum haka, abu kamar da wasa ya ɗore. Wata rana da suka je tsakiyar daji sai wani baƙin maciji ya wuce sululu ta gabansu.

    Sai uban ya ce da Gwaidayara: “Ga mijinki nan, ki bi shi duk inda ya dosa.” To saboda biyayya irin wadda ta ga uwarta na yi wa mahaifinta, sai ta ce da shi: “To, Baba, na gode.” Daga nan ta dinga bin maciji, ba tare da jin tsoro ko shakka ba. To, ashe shi ba maciji ba ne, mutum ne kuma ɗan sarki.

    Da ya ga yarinyar na bin sa kamar yadda ubanta ya ce ta yi, kuma ya lura uban yarinyar ya kama gabansa, sai ya rikiɗa ya koma mutum; sai ya tambayi Gwaidayara: “Baiwar Allah me kika zo yi a nan?” Ganin abin da ya faru, sai tsoro da ɗimaucewa suka sa ta kasa yi masa wani bayani.

    Ya dai ji ubanta ya ce: “Bi macijin nan shi ne mijinki.” Da ƊanSarkin nan ya lura da ɗimautar da Gwaidayara ke ciki, sai ya ce da ita: “Kada ki dami kanki, ki ma daina jin tsoro; mu je garinmu a ɗaura mana aure, ai mahaifinki ya ba ni ke.” Sai shi da ita suka kama hanyar garin mahaifinsa; har suka isa, ta ga ana ta faɗuwa kasa ana gaishe shi.

    Da ya shiga gida, ya kai ta ta huta, sai ya ce su je wurin mahaifinsa. Suka je suka gai da Sarki, sai ya tambayi dansa: “Yarima Babba, lafiya na gan ka da wata yarinya; wace ce?” Sai ya ce da shi: “Ka daɗe, mai duniya, wannan yarinya da na zo da ita, ina neman izininka ne in aure ta.”

    A nan take kuwa Sarki ya amince. Bayan kwana biyu aka ɗaura musu aure, Sarki ya kawo dukiya mai yawa ya ba ɗansa da surukarsa. Ɗan Sarkin nan kuma ya ɗebi dukiyar ya je daji daidai inda surukinsa ya bar ’yarsa ya ƙanƙara gida suka tare shi da amaryarsa. Suna nan, wata rana sai uban Gwaidayara ya je gona, sai ya tarar da wasu mata na jan ruwa a rijiyar da ke kofar kataferen gidan nan.

    Waɗannan mata kuyangin Gwaidayara matar Yarima Babba ne. Ya roƙe su ruwan sha, amma suka hana shi, tare da bayanin cewa: “Ko za mu ba ka sai mun cika duk randunan Gwaidayara.” Da ma Gwaidayara ta saba takan leƙa ƙofar gidan ta taga. Da ta leƙa sai ta hango mahaifinta yana magana da ’yan aikinta.

    Sai ta kira ɗaya ta tambaye ta: “Me mutumin nan yake cewa ne?” Sai ’yar aikin ta ce: “Ya ce mu ba shi ruwan sha ne, muka ce sai mun gama cika randunanki.” Sai Gwaidayara ta ce: “Ku ba shi ruwan ya sha. Idan ya sha kuma ku ce ya shigo.” Bayan mahaifin Gwaidayara ya sha ruwa, sai ya ji a cikin ladabi ɗaya daga cikin kuyangin nan ta ce: “Gwaidayara matar Ɗan Sarki ta ce ka shiga gidan nan.”

    Sai ko ya shiga ya zauna a zaure, yana jira ya ga abin da zai faru. Kafin ta aika a gaya wa mai gidanta cewa mahaifinta ya zo, sai ta ji motsin shigowarsa gida. Bai tsaya a zaure ba, ko da yake ya ga baƙon mutum, amma bai san ko wanene ba.Sai Gwaidayara ta tunkari mijinta bayan fadawa sun tsaya a soro ta ce: “Yaya ka wuce mahaifina ba ka gai da shi ba?”

    Sai ya ce: “Yana ina? Ban gan shi ba.” A cikin karairaya irin ta matan da suka iya kissa ta ce da shi: “Ai shi ne a zaure, ai gara ku gaisa.” Sai mijin ya je suka gaisa, aka ba shi masauki irin na alfarma, ya yi wanka da ruwan ɗumi, ga tufafi sababbi an kawo masa; ya zaɓa, ya saka.

    Bayan mahaifin Gwaidayara ya ƙara hutawa, can da la’asar surukin da matarsa suka kawo kyankyandi gomiya ɗaya da biyar, cike da tufafi da kuɗi, suka ba shi. Wasu kayan nasa ne, wasu kuma tsarabar da zai kai wa matansa ce. Ya yi mamaki da godiya; bayi da fadawa suka ɗauki kayan, aka raka shi har gida.

    Da ya kai kayan tsarabar ya yi wa matan gidan bayani, sai suka ce: “Wannan tsarabar ’ya’yanmu ne suka aiko; wa zai ba Gwaidayara arziki haka?” Haka dai suka rabe kayan suka hana mahaifiyarta. Bayan ’yan kwanaki sai mahaifin su Gwaidayara ya shirya zai ziyarci sauran ’ya’yansa, wato Jummai da A’isha da Halima.

    A gidan Halima ya tarar ita da mijin ba su da abinci idan ban da birrai da ɓeraye saboda tsananin talauci; jikinta ya yi kirci, ba ta da ko sabulun wanka. Hatta tabarmar kwanciya ma ba ta da ita. Bayan ya gama ziyararsu zai tafi, sai ta ƙunshe masa kan biri da jelar ɓeraye biyar a tsumma ya kai wa mahaifiyarta tsaraba.

    Da uban ya je gidan Jummai, sai ya tarar ba su da wani abinci sai ganyen yaɗiya da gautan daji da tsamiyar ƙasa. Babu rumbu balle masussuka a gidansu. Bayan ya gama ziyararta, ita da mijin suka roƙo gaskami daga makwabta, ta sa a wani kata don ya kai wa mahaifiyarta tsaraba.

    A’isha ce mijinta yake da ɗan ƙarfi, domin ɗan abin da yake da shi, har dusa yakan samo ta tuƙa musu tuwo. Wani lokacin kuma sukan ci zogale da wake, kuma tana da zane sakakke da turmi da tabaryar yin aikatau. Da zai tafi gida ta ɗebo dusa mai yawa ta ba shi ya kai wa mahaifiyarta tsaraba.

    Da mijin ya koma gida, sai ya ce da matan nasa: “Ina so duk yaran nan kowacce ta zo da mai gidanta ranar Laraba mai zuwa.” Aka aika musu, kowacce ta ci ado, daidai arzilinta, ta taho tare da mijinta. Gwaidayara ce ta fara zuwa tun da sanyin safiya, ta shiga ɗakin mahaifiyarta da ke kusa da ƙofar gida, sauran matan gidan ba su san ma ta iso ba, tare da tarin kyankyandi cike da dukiya mai yawa.

    Sauran kowacce ta zo dukkaninsu suna fama da rama da gajiya, ga shi ba su da suturar kirki. Kowacce ta shiga ɗakin mahaifiyarta wai suna jiran ganin mugun halin da Gwaidayara da mijinta suke ciki. Can kuma sai ga mazansu su ma sun iso. Mijin Halima ya sha lagen wani luru da ya huje; mai gidan Jummai kuma ba komai a jikinsa sai bante.

    Mijin A’isha ne mai dama-dama, domin ya sa ’yar shara wadda ya aro a wurin abokinsa. Mijin Gwaidayara kuma ya tunkaro. Tun yana nesa ƙamshin turarensa ya cika gari, fadawa suna gaba, masu algaita na busa, makaɗa na ta kiɗa; sai kirari ake yi masa ana cewa: “Lafiya Yarima Babba Ɗan Sarki,angon Gwaidayara.”

    Bayan kowacce ta fito tare da mijinta, sai iyayensu mata suka kama kuka da nadamar halin da Jummai da Halima da A’isha da ake so suka shiga a gidajen aurensu. Nan take suka ba mahaifiyar Gwaidayara haƙuri bisa matsa mata lamba da wulaƙancin da suka dinga yi mata a baya. Ita kuma ta ce ta yafe musu.

    Gwaidayara ta kawo tufafi da kayan abinci da abin zaman gari mai yawa ta ba ’yan’uwanta kowacce da mijinta, ta ƙara wa kishiyoyin uwar kayan tsaraba waɗanda ba su taɓa jin labarin irinsu ba, suka yi godiya. Daga nan kuma uban ya ce ba sauran a wulaƙanta kowa a gidansa. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Illar nuna bambanci da tsana ga ɗaya daga cikin ’ya’yan da mutum ya haifa.
    • Haƙuri da biyayya ga iyaye da jure wa ƙuntatawarsu abu ne mai kawo arziki da nasara a rayuwa.
    • Nuna wa yaro gatanci da shagwaɓa shi wata hanya ce ta lalacewa da talauci da shiga halin da-na-sani.
    • Allah ne kaɗai yake arzutawa kuma yake talauta wanda ya so.
    • Allah gatan kowa.
    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Yan Mata Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Yan Mata Biyu

    Tatsuniyar ’Yan Mata Biyu

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wasu ’yan mata, ya da ƙanwa ne uwarsu ɗaya, ubansu ɗaya. Allah ya yi musu ƙira mai kyau, har ma wasu kan ce kyansu kamar na aljanu. Wata rana ƙaramar ta fita ƙofar gida tana rigar aya, sai wani mutum ya gifta ya gan ta ya yi mata sannu. Da ta amsa sai ya ce da ita: “Kin san kyan da kike da shi kuwa amma a ce wai ke ce kike rege aya?”

    Da ta ji haka sai mamaki ya kama ta, ta ce masa: “Ai da ka ga yayata da ba ka ce da ni kyakkyawa ba domin ta fi ni kyau nesa, ba kusa ba.” Kamar da wasa, sai wannan baƙo ya ce: “To kirawo ta mu gani.” Ta shiga ta gaya wa yayarta yadda suka yi da mutumin nan.

    Sai yayar ta ce: “Gaya masa ina aiki, ba zan sami damar fita wurinsa ba a yanzu.” Haka mutumin nan ya tafi. Jim kaɗan sai ya je ya rikiɗa, ya koma wani mutum daban, ya sake komowa, ya roƙi ƙanwar ta kirawo masa yayarta. Ta shiga ta gaya mata, suka fito tare.

    Baƙo ya ga tabbas; ya yarda da cewa yar ta fi ƙanwar kyau. Bayan sun gaisa, sai ya ce mata: “Na tura ƙanwarki ta kirawo ki ne domin in sanar da ke ina ƙaunarki.” Jin haka ya sa ta sunkuyar da kai saboda kunya tana murmushi ta ce: “To, na gode.” Shi kuma baƙon ya ce da ita: “Amma fa gidana a bayan gari yake, ina fata za ki yarda mu je ki gani.”

    Ba tare da musu ba kuma ta yarda. Amma kafin su tafi, sai ƙanwarta ta yi farat ta ce: “Ni ma zan bi ku, amma kafin mu tafi zan nemo izinin mahaifiyarmu tukuna.” Baƙon da yayarta suka ce: “To. Za mu je da ke, sai ki shiga ki gaya mata.” Bayan yarinyar ta gaya wa mahaifiyarsu kuma ta amince, sai suka kama hanya.

    Bayan sun ’yar tafiya ƙaramar ta yi tuntuɓe. Da ta gaya musu sai ta ji mutumin nan ya ce: “Idan jini ya fito zan shanye.” Sai ta ce: “A a, ai jini bai fito ba.” Haka dai suka ci gaba da tafiya, har suka isa gidan mutumin. Da isa sai suka lura ashe gidan an gina shi ne da gangar jikin mutum.

    Wannan fa ya sa su tsorata, amma dai suka danne tsoron. Ya buɗe ƙofa, suka shiga suka taɓa hira a gidan, sai ya rako su gida. Bai daɗe yana neman aure ba kuwa, aka ba shi ita, ta tare a gidansa, ƙanwarta kuma ta bi ta saboda ta riƙa taya ta aikin gida.

    Haka suka zauna kullum sai yayar ta kai wa mijin abinci, amma kuma ba ya cin abincin da suka kai masa da miyarsu, sai ya zubar da miyar, ya riƙa ci da jini. Ashe tsafi yake yi, yana tsotsar jinin ƙanwar matar ba a sani ba. Har wata rana yayar ta ce wa ƙanwar: “Kai amma kin rame.”

    Kanwar dai ba ta san abin da za ta ce ba. Ana nan kullum haka, har wata rana wata mata da ta ziyarce su ta ga mai gidan nan yana cin abincin da aka kai masa da jini. Sai ta je ta sami yayar yarinyar da ƙanwarta, ta gaya musu abin da ta ga mutumin nan yana yi, watau cin abinci da jini.

    Jin haka sai suka tambaye ta: “To, yaya za mu yi?” Sai ta ce: “Mu tona rami, mu sa ƙanwarki a ciki.” Da mutumin nan ya daina ganin ƙanwar matarsa ta kai abinci, sai ya tambayi matar: “Ni kuwa ina ƙanwarki ne? Na ga yanzu ba ta kawo mini abincina.” Sai ta ce: “Maigida, ai wannan yarinya ta tafi kallon wasa ne a ƙauyen kwaɗi.”

    Tun yana tambaya jefi-jefi, har ya zama a kullum sai ya tambaya. Kuma duk sanda ya tambaya sai ta ce: “Kanwata ta tafi kallon wasa.” Bayan ɗan wani lokaci sai ya ce da matar: “Ke ni fa zan je kauyen kwaɗin nan da kaina in dawo da ita.” Da ta ji haka sai ta ce: “To, ni ma ai na fi so ta dawo.

    Ka san ko banza tana taya ni aiki, kuma ita ke kawo maka abinci kullum.” Wata rana da mijin ya fita yawonsa, sai matar ta tura ƙanwarta gida, domin ta yi wa mahaifansu bayanin halin da suke ciki. Ta ƙara yi wa kanwar bayani da cewa: “Ki gaya musu za mu zo ganin gida tare da shi.

    Don haka ina son su haka rami mai zurfi, su haɗa wuta a ciki, ta ruru da kyau, sannan su rufe ramin da kirare; sai a yi shimfiɗa a kai, yadda idan ya zauna zai rifta cikin wutar, kowa ya huta da wannan aljanin mutum.” Iyayensu na jin wannan bayani, sai suka shirya duka yadda aka ce a yi.

    Mijin da matar suka shirya zuwa ganin gida, suka kama hanya. Suna isa gidan surukansa aka nuna masa shimfiɗarsa. Bai jima da zama ba ya fara jin ɗumi, sai ya tambaya: “Ina jin wani dumi-dumi, ko dai jikina ne?” Sai matar ta ce: “Lallai kam jikinka ne.” Kafin ta gama rufe baki, kiraren da aka rufe ramin da su, aka ɗora shimfiɗar da ya zauna a kai sun cinye.

    Nan take ya auka cikin ramin wutar nan ya ƙone ƙurmus, amma kuma sai ya tokarsa ta tsira ta zama bishiyar aduwa. Labarin yadda aduwar nan ta fito har ya kai kunnuwan Sarkin garin. Sai ya sa aka yi yekuwar, ya hana kowa shan ’ya’yan aduwar. Amma wata rana matan Sarki sun fita unguwa, sai suka riƙa cewa su sai sun sha ’ya’yanta, amma da wasa suke faɗi.

    To daman ɗaya daga cikin matan, tana da ciki, sai kwaɗayi irin na masu ciki ya sa ta tsinki ɗaya ta sha. Shanta ke da wuya sai bishiyar aduwar ta riƙa bin ta har ƙofar fadar Sarki. Sai aka gaya wa Sarki cewa ga fa aduwar nan ta biyo iyalinsa, har ma za ta shigar masa fada.

    Nan da nan Sarki ya shiga gida, ya tambayi matan yadda aka yi, suka yi masa bayani. Sai ya ce: “To, ba komai; za mu yi maganin wannan hatsabibin mutum, domin yana nema ya dami jama’ar ƙasata.” Sai Sarki ya umarci Sarkin baka ya magance wannan fitina.

    Nan da nan ya haɗa wani irin turare. Da hayaƙin turaren ya bugi bishiyar nan, sai ta narke kowa ya huta. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa 

    • Halin kirki shi ne abin duba ga mace ko namijin da za a aura ba kyau ba.
    • Hatsari ne a auri wanda ba a san asalinsa ba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Nasiru Da Nisiru

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Nasiru Da Nisiru

    Tatsuniyar Nasiru Da Nisiru

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can ƙasar Mazarƙwaila an yi wani yaro ɗan Sarkin Zaƙi, mai suna Nasiru. Yana da wani aboki wai shi Nisiru. Ana kiran baban Nasiru Sarkin Zaƙi ne, domin ya fi kowa yin kayan zaƙi a garinsu. Shi Nisiru yakan je ya sami Nasiru su tafi cin zuma, watau su ƙona itace hayaƙi ya kori ƙudan zuma, su kuma su kwaso saƙarta da ruwan.

    Haka suke yi kullum. Ana nan, ana nan, sai mahaifiyar Nasiru ta rasu. Rasuwarta ke da wuya sai kishiyarta ta shiga ba Nasiru wuya. To amma ɗan kishiyar uwar mai suna Aliyu yana son Nasiru sosai; ba ya nuna masa ƙiyayya ko kaɗan. Wata rana sai Aliyu ya ce wa Nasiru da abokinsa: “Yau zan raka ku cin zuma.”

    Da Nasiru ya ji haka sai ya ce da shi: “Ni fa ina tsoro kada mahaifiyarka ta yi faɗa.” Sai Aliyu ya ce: “Ba komai, ba za ta yi faɗa ba sam-sam.” Daga ƙarshe dai Nasiru ya haƙura, ya amince zai je da Aliyu. Lokacin da Nasiru da Aliyu suke wannan maganar, ashe wata mata magulmaciya ta ji su, sai ta je ta sami uwar Aliyu ta ce da ita: “Kin ga Nasiru da abokinsa Nisiru za su ja ɗanki daji su halaka shi.”

    Uwar na jin haka sai ta ce da matar nan: “Yanzu yaya za mu yi?” Da ’yar zugar ta sami gangara, kawai sai ta ce: “Akwai wani hatsabibin boka wanda za mu je ya ba mu maganin da zai kashe Nasiru kawai mu huta.” Wannan shawara ta tsorata uwar Aliyu, sai ta ce: “A a, ni fa ina tsoron kashe mutum.”

    Sai matar nan mai ingiza kantu ruwa ta ce: “Idan ba ki kashe yaron nan ba sai ya fi ɗanki arziki domin yana da ƙashin arziki.” Uwar Aliyu na jin wannan gurguwar shawara, sai ta ce: “To, shi ke nan mu je.” Uwar Aliyu da mai zuga ta suka je gidan boka suka yi masa bayani. Nan take kuwa ya kawo magani ya ba su, ya ce su zuba a nono.

    Ya tabbatar musu idan Nasiru ya sha maganin to zai mutu. Suka dawo gida, uwar Aliyu ta dama fura da nonon da aka zuba wa magani, ta ajiye wa Nasiru ita a gindin randa, ta danta Aliyu kuma ta ɗora a kan randar. Nasiru da Aliyu suka shiga gida, aka nuna wa kowa furarsa.

    Nasiru ya ɗauko tasa daga gindin randa zai fara sha, sai ya ga uwar Aliyu ta sa shi a gaba tana yi masa fara’a, har da wasa da dariya. Ganin haka ya sa shi shan jinin jikinsa. Sai ya ce da ita zai koma waje ya sha. Da ya fita waje, sai ya sami wani ɗan akuya ya ba shi furar ’yar kaɗan. Shan ta ke da wuya sai nan take ɗan akuyan ya faɗi matacce.

    Nasiru na ganin haka, sai ya yi rami ya binne ragowar furar, ya kwanta nashe-nashe, kamar ya mutu. Jim kaɗan sai ga mahaifiyar Aliyu ta leƙo sai ta ga Nasiru a kwance kamar ya mutu. Ba ta san sanda ta yi subur da baka ba cikin murna ta ce: “Yawwa, madalla. Tun da aka haifi yaron nan nake neman yadda zan gama da shi, ban sami nasara ba sai yanzu.

    Ba shakka wannan boka hatsabibi ne, na gode masa.” Tana cikin wannan murna, idanunta a rufe, ta ɗauki Nasiru ta kai shi bayan gari ta jefar; ko tunanin a rufe gawarsa ba ta yi ba saboda tsananin ƙiyayya. Shi kuma Aliyu ɗan’uwan Nasiru sai ya nemi uwar ta gaya masa inda yake.

    Da ƙyar dai ta yi masa bayanin da ya gane cewa yana bayan gari, sai ya fita nemansa, ya ci sa’a kuma ya rera wata waƙa a kusa da inda aka jefar da shi:

    Nasiru, Nasiru, Nasiru,

    Nasiru ɗan Sarkin Zaƙi,

    Nasiru tashi mu je shan zaƙi.

    Nasiru ya bar duniya,

    Nasiru ya tafi lahira.”

    Duk da cewa Nasiru yana kusa da Aliyu, bai mayar masa da wannan waƙa ba. Sai Aliyu ya koma gida a cikin matsanancin tashin hankali. Har ma dai ya ce da uwar shi fa ba zai ji daɗin zaman duniya ba, muddin ba ya ganin Nasiru. Can kuma, abokin Nasiru shi ma ya shiga tashin hankali rashin ganin abokinsa.

    Shi kuma sai ya sami uwar Aliyu ya ce:

    “Mamayo, mamayo, mamayo,

    Nasiru ya bar duniya,

    Nasiru ya tafi lahira.

    Nasiru ya bar duniya,

    Ni mazantafi lahira.”

    Da uwar Aliyu ta ji wannan waƙa, sai ta ce da Nisiru: “Ina ruwana ka tafi gaba da lahira ma, duk ɗaya ne.” Zuciyarsa cike da baƙin ciki ya kama hanyar daji. Yana cikin tafiya sai ya ga wani mutum a zaune ya gama kai da gwiwa; sai ya matsa kusa da shi ya ce: “Bawan Allah me ya same ka haka?” Yana ɗago kansa, sai abokin nan nasa ya gane ashe wanda ya fito nema ne sai ya tsorata.

    Amma abokin nasa sai ya ce da shi: “Haba mutumina, kada ka ji tsoron komai. Ni ne Nasiru.” Hankalin Nisiru ya kwanta, suka sami wuri suka zauna. Bayan sun yi ’yar hira, sai suka yanke shawarar barin garin don gudun mugun halin uwar Aliyu. Sai suka koma wani gari mai babbar kasuwa da karkara mai dausayi, ga filayen noma nan sai an zaɓa.

    Da yake su duka muzakkarai ne, sai halin zaƙaƙurancinsu ya sa suka shiga neman abin kansu. Kafin shekara ta dawo kowannensu ya mallaki dukiyar da an jima ba a ga masu kamarta ba. Wata rana bayan kamar shekara biyar Nasiru da abokinsa suna cikin halin baƙunta a wani gari, sai suka yanke shawarar cewa ya kamata su je ganin gida.

    Nan da nan ko suka yi laftun dukiya suka ɗora wa raƙuma, suka tafi da ita garinsu. Nasiru ya tarar da uwar Aliyu tana cikin mummunan talauci, ga tsufa ya kama ta, ƙanensa Aliyu kuwa ba ya komai, sai baranta a gidan wani tajiri. Nan take Nasiru ya ba ta dukiya mai tarin yawa.

    Ta shiga cin daɗi, ba da daɗewa ba ta murmure. Ya kawo jari mai kauri ya ba ƙanensa Aliyu. Shi da abokinsa kuma suka shirya suka koma wurin sana’arsu. Duk sanda uwar Aliyu ta zauna, sai ta shiga tunanin ƙetar da ta shirya wa Nasiru, da kuma irin alherin da ya saka mata da shi, ta yi da-na-sani. Ta roƙi gafararsa, ya yafe mata. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a rama alheri da mugunta.
    • Duk wanda ya daka ta magulmaci zai tsinci kansa a cikin nadama da dana-sani.
    • Mai hankali ba ya rama mugunta da sharri sai da alheri.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Marowata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Marowata

    Tatsuniyar Marowata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum a wata ruga da ke gefen Dajin Ganji. Yana zaune tare da matarsa da ’ya’yansu biyu. Suna da matashin sa ɗaya. Wata rana mai gidan da matar suka yanke shawarar cewa ya kamata su yanka san nan su ci nama. To amma su marowata ne na ƙin ƙarawa.

    Sai suka shirya cewa za su je dawa su yanka san inda ko ƙuda ba za su bari ya taɓa naman ba. Da zuwansu dajin sai suka tsuguna, suka yi kashi. Nan da nan ƙudaje suka rufe kashin; sai suka bar wurin wannan kashi, suka je wani wurin daban suka yi wani kashin. Nan ma ƙudaje suka yi cincirindo a kan kashin.

    Da haka da haka har suka yi kashin da ba wani ƙudan da ya bi. Sai mai gidan ya ce: “To, a nan za mu yanka san nan.” Bayan sun yanka san tun kafin su feɗe shi, sai ga wani ƙaton Zaki ya zo, sai ya ce da su: “Kai, me kuke yi a nan?” Mai gida na jin haka sai ya ce da shi: “Mun yanka sa ne, to amma ba wutar da za mu gasa shi.”

    Da Zaki ya ji haka sai ya ce: “To ku sam mini naman.” Duk da irin zafin rowarsu, sai suka yankar wa Zaki naman suka ba shi. Amma maimakon Zakin nan ya yi musu godiya sai ya ce: “Ku ƙara mini zan yi muku wata waƙa mai daɗin gaske.” Tun ma kafin su ƙara masa, sai ya fara rera waƙa yana cewa:

    “Ɗan ƙanƙanen abin nan, dungum,

    Waburga-burga ne, dungum,

    Naburga a ɗanɗane ni, dungum.

    Aboki yana kiran aboki, dungum,

    Aboki yana kiran aboki, dungum.”

    Da Zaki ya gama waƙar, sai suka sake yankar masa nama suka ba shi. Sai suka ce ya sake yin waƙar su ƙara masa. Da haka da haka, har naman ya ƙare. Sai suka ce da shi: “Ka ƙara yi mana waƙa mu ba ka ɗanmu.” Ba ko tare da Zaki ya yi gardama ba, sai ya rera musu waƙa, suka miƙa masa ɗansu.

    Daga nan kuma suka ce ya ƙara yin waƙar, za su ba shi ’yarsu. Zaki kuwa ya rera musu har ma ta fi waƙoƙin da ya yi a ba ya daɗi. Yana gamawa suka danƙa masa ’yar maƙwabtansu da ta biyo su dajin saboda taya su aikin nama. Can sai mutumin ya dubi Zaki ya ce: “Ƙara yin waƙar nan in ba ka matar nan tawa.”

    Abu kamar wasa, Zaki ya yi waƙa, mai gida ya ba shi matarsa. Abu kamar wanda aka jefa, sai ya ce da shi: “Ka ƙara yi zan ba ka kaina.” Zaki sa’a ta samu; sai ya yi waƙar, mai gida kuma ya miƙa kansa ga Zaki. A taƙaice dai Zaki ya sami uwa da uba da ’ya’ya biyu da naman saniya; sai ya kai su gidansa ya ajiye, ya tafi neman itacen da zai dafa naman san nan.

    Kafin ya dawo mai gida ya kwashi iyalinsa da naman sansa sun gudu. Bayan mai gida da iyalinsa sun yi ’yar tafiya, sai ya tsaya ya ce zai ƙirga su, don ya tabbatar ba a bar kowa a gidan Zaki ba. To, idan ya taɓa matarsa sai ya ce: “Ɗaya.” Ya taɓa ɗansa ya ce: “Biyu.” Da ya taɓa ’yarsa ya ce: “Uku.” Sai ya manta da kansa, saboda haka lissafi bai tashi daidai ba.

    Haka ya dinga yin wannan shirme, har wani mutum ya zo, ya ga abin da ke faruwa, sai ya ce da mai gida: “Idan na samo maka cikon mutum na huɗu lissafi ya cika, me za ka ba ni?” Sai mai gida da matar baki ɗaya suka ce: “Duk abin da ka zaɓa daga cikin abubuwan da muke da su za a ba ka.” Sai ya ƙirga su lissafi ya cika daidai.

    Daga nan sai ya dubi mai gida da matarsa ya ce: “To, ku cika alƙawari.” Sai mai gida da matarsa da ’ya’yansu suka tuɓe takalmansu suka rife; mai gida ya gyara hularsa, matar ta yi ɗamara, ’ya’yan kowa ya shirya. Baki ɗayansu sai suka zura da gudu, suka bar mutumin yana mamaki, amma cikin raha, saboda ya ga gwanayen wauta. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mai hankali ba ya rama mugunta da sharri sai da alheri.
    • Son kai yakan jefa mai yin sa cikin haɗari.
    • Marowaci yana iya zama tamkar dabba har ma ya cuci kansa.
    • Karshen azzalumi da-na-sani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Wani Mutum Da ‘Yarsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wani Mutum Da ‘Yarsa

    Tatsuniyar Wani Mutum Da ‘Yarsa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wani mutum da ke garin Yamutsawa ya je gidan Sarkin garin ya ce yana so zai ba Sarkin ‘yarsa ya aura. Shi kuwa Sarkin Yamutsawa ya daɗe da matansa biyu. Da Sarki ya ji haka sai ya sanar da shi cewa ba zai ƙara aure ba, idan ma ya auri mace ta uku, to kuwa zai gille mata kai.

    Sai mutumin ya ce: “Na ji, na yarda ka aure ta ko za ka gille mata kan.” Shi kuma mutumin daman malami ne ɗanbaiwa. Shi ke nan, Sarki ya aure ta. Kamar yadda Sarki ya faɗa, washe-garin ranar da amarya ta yi kwanan farko a gidansa, sai ya sa aka fille mata kai. Amma kuma kullum idan an fille kanta jim kaɗan sai ga wani kan ya fito.

    Ana nan, sai matan Sarki biyu suka sami ciki, amma ita ba ta samu ba. Ganin haka sai uban amarya ya sauya mata kama ya umarce ta da ta bi Sarki lokacin da zai fita farauta. Sai ko ta sami juna biyu a wannan lokaci. Bayan ‘yan watanni ciki ya fito, Sarki ya tambaye ta: “A ina kika sami ciki?”

    Ba ta tsaya wata inda-inda ba sai kawai ta ce: “Kai ne ka yi min.” Shi kuma ya musanta. Amma sai ta yi masa bayani dalla-dalla cewa ai ta sauya kama ne sanda suka haɗu, lokacin da ya je farauta. Da Sarki ya ji haka sai ya ce: “Ai mai waɗancan kamannin da kika faɗa ta fi ki kyau.” Da ta ƙara yi masa bayani, sai ya amince lallai shi ne mai cikin.

    Bayan wani ɗan lokaci kuma, sai Sarki ya tara matan nan su uku ya ce: “Kowacce ta je ta haihu a gidansu.” Sai kowaccensu ta kwashe kayanta, ta tafi gidansu. Ba da daɗewa ba kuwa sai ɗaya daga cikinsu ta haifi Ɓera, ɗayar kuma ta haifi yaro Ƙadangare, ita kuma amarya ‘yar mallam, ta haifi ɗa kuma ya yi kama da ubansa, watau Sarki.

    To daman ita wadda ta haifi Ɓera ta haihu ne a cikin toka. Wadda ta haifi Ƙadangare kuma ta haihu ne a daji. Ita kuma ‘yar malami, ta haihu ne a gidan ubanta, shi ya sa ta haifi mutum. Bayan sun gama wanka, jikin kowacce ya yi ƙwari, sai kowacce ta koma ɗakinta, watau gidan Sarki.

    Bayan ‘yan kwanaki da komawar matan Sarki, sai ya ƙ kulawa da amaryar domin shi har yanzu bai yarda da cewa ita ce ta haifi yaron nan ba. Sai ya yanke shawarar cewa a kai yaron reno gidan danginsa, kuma kada ɗaya daga cikin matan ta sake ganin sa har sai ya girma sai a kawo shi ya nuna uwarsa da kansa.

    A kwana a tashi, yaro ya girma, sai Sarki ya sa aka tara mutanen garin domin su ga abin da zai faru. Ya sa matansa su uku suka fito, ya tura a zo da ɗan. Yaro ya zo a kan Doki. Manufar taron dai ita ce yaron ya fidda wadda ta haife shi daga cikin matan Sarki. Sai kawai aka ji ya kama wannan waka: ”

    Wace ce uwata?

    Tambaya nake, Wace ce gyatuma ta?

    Wace ce iyata, wo-wo.

    Ina kara tambaya, Wace ce mahaifiya ta?”

    Sai matar Sarki wadda ta haihu a daji ta karɓi waƙa:

    “Ga ni, ga ni, ni ce, ɗana,

    Ga ni, ni ce mahaifiyarka,Ya kai ɗana.

    Ga ni, ni ce gyatumarka, wo-wo,

    Zo in rungume ka, Ya kai dana.”

    Da yaron ya ji bayanin da ta yi masa a cikin waƙar, kuma bai gamsu ba, sai ya rera wata waƙar yana cewa: “A a, a ina kika haife ni? Gaya mini, a ina kika haife ni? Aina kika haife ni, wo-wo?”

    Da mutanen gari da Sarki sai duk suka yi shiru, suna jira su ji abin da za ta ce, ko zai tabbatar ita ce uwarsa, ko kuma ba haka ba ne. Sai ta kashe murya wadda ta fi ta da zaƙi tana cewa: “Ai a daji na haife ka, A Dajin Ƙarangiya na haife ka. Kai Yarima, Ai a daji na haife ka, Ni a daji na haife ka, wo-wo.”

    Ba tare da wani ɓata lokaci ba, sai kawai ya ce: “Je ki gaba, Ki yi gaba, Ba ke ce mahaifiya ta ba. Je gaba,Ba ke ce mahaifiya ta ba Wo-wo, Ba ke ce mahaifiyata ba.” Haka ta kare, ta wuce tana jin haushi. Wadda ta haihu a toka ma ta zo, ita ma ya ce ba ita ce uwarsa ba.

    Da aka zo kan mahaifiyarsa, wadda ita ce ta ƙarshe da ta faɗi inda ta haife shi, sai ya yi wani gwauron tsalle don murna har sai da ya shallake rimin da ke kusa da fada. Jama’a ma suka ɓarke da sowa, sai ɗan Sarki ya je ya rungume uwarsa don murna. Shi kuma Sarki saboda jin haushin matansa sun yi masa ƙarya dangane da haihuwar magajinsa, sai ya sa aka fiffille musu kawuna.

    Ya sa aka raba ƙasarsa biyu. Shi ya ci gaba da mulkin rabi daga fadarsa, ɗaya rabin kuma ya mallaka wa ɗan. Malamin nan kuma uban matar Sarki ya riga ya tsufa. Jikansa ɗan Sarki kuma ya gina masa gida a ɓangaren ƙasar da uban ya mallaka masa. Labarin wannan abin mamaki ya wuce garin Yamutsawa domin ya gama ko’ina a garuruwan da suke kusa da shi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wajibi ne shugaba ya yi kyakkyawan bincike kafin ya zartar da kowane hukunci don ya kauce wa yin kuskure.
    • Son zuciya ɓacin zuciya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Biri Da Kare

    Edita@rumasau-kallamu