Tag: yadda ake

  • Tatsuniyar ‘Yar Mowa Da ‘Yar Bora

    Tatsuniyar ‘Yar Mowa Da ‘Yar Bora

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A wani gari an yi wani mutum mai mata biyu da ’ya’ya biyu, ’yan mata; ɗaya sunanta ’Yar Mowa, ɗayar kuma ’Yar Bora. Suna nan, ran nan sai mijinsu ya rasu. Bayan ɗan wani lokaci kuma sai uwar ’Yar Mowa ta rasu, ta bar uwar ’Yar Bora kaɗai. To da ma kafin ta rasu, ta kira kishiyarta tace mata: “Don Allah ga amanar ’yata nan; ki kula da ita.”

    Sai tace: “To.” Amma da ta rasu sai uwar ’Yar Bora ta fara ganawa ’Yar Mowa azaba. Kullum ita ke yin hidimar gida, ba ta da lokacin hutawa. Wata rana da gari ya waye sai aka ga ’Yar Bora ta yi fitsarin kwance, amma sai uwar ’Yar Bora ta ce ai ’Yar Mowa ce ta yi. Saboda haka ta matsa mata sai ta je Rafin Bagaja ta wanke shimfiɗar da aka yi wa fitsari.

    To Ruwan Bagajar nan kuwa yana cin mutane. Amma tunda ba yadda ta iya, sai ta ɗauki shimfiɗa ta kama hanyar rafi. Tana cikin tafiya a daji da ta ga rafi sai ta kama waƙa tana cewa:

    “Kogi, kogi,

    Ko kai ne Ruwan Bagaja,

    Bagajar kauye da ’Yar Sarki,

    Da ’Yar Bora ta yi fitsari,

    Aka ce ni ce,

    Sai na wanke

    A Ruwan Bagaja.”

    Tafiyar ‘Yar Mowa Sai kogi ya ce: “Ni ba ni ne Ruwan Bagaja ba. Ni Ruwan Madara ne. Idan za ki zauna ki sha to.” Sai ta ce ta gode; taci gaba da tafiya. Can sai ta tarar da wani ruwan, sai ta sake maimaita waƙar da ta yi. Sai kogi ya ce mata shi Ruwan Zuma ne. Idan tana so ta zauna ta sha. A nan mata ce ta gode, ta ci gaba da tafiya.

    Sai ta tarar da Kogin Shinkafa da Kaji, sai ta rera waƙar nan, kogi yace mata: “Ni Kogin Shinkafa da Kaji ne. Idan kina so ki zauna ki ci.”A nan ma ta yi godiya, ba ta ci ba; ta yi gaba. Jim kaɗan kuma sai ta tarar da Ruwan Jini. Bayan ya ji bayaninta a cikin waƙa, sai ya ce: “Ni ba Ruwan Bagaja ba ne. Ni Ruwan Jini ne. In za ki sha to.”

    Sai ta ce ta gode ta yi gaba. ’Yar Mowa dai ba ta gaji ba, ta ci gaba da tafiya har ta tarar da wani ruwan. Da ta yi irin waƙar da ta saba sai yace: “Ni ne Ruwan Bagaja; amma ke kuwa wannan yarinya me ya kawo ki wurina inda ba a zuwa?” Sai ta feɗe masa biri har wutsiya a kan abin da ya faru da irin halin da take ciki bayan rasuwar mahaifiyarta.

    Da Ruwan Bagaja ya ji sai ya ce: “To ai sai ki wanke a nan.” Nan take ta yi godiya, ta tsuguna ta wanke shimfiɗa, amma kafin ta gama har dare ya yi. Da ta gama, ta tashi za ta tafi sai kuma ga hadari ya taso, amma kuma ga babu wurin fakewa. Can sai ta hango wata ’yar bukka, ta ko nufi wurinta ta fake.

    Tana zaune a ciki, sai ta ga wata fitila ta kunna kanta da kanta, mamakin wannan ya kama ta, sai kuma ta ga cinya a gefeɗaya. Kafin ta gama mamaki sai kuma ta ga kai shi kaɗai a gefen cinya yana motsi. Sai cinya ta ce da ita: “Kai yanayi miki maraba.”
    Can kuma sai cinya ta yi nata motsin, sai kai yace da ita: “Cinya ma tana yi miki maraba da zuwa.”

    Duka dai yarinya tana amsawa da cewa: “Na gode da wannan maraba.” Suna nan zaune, sai kai ya yi wani motsi, sai cinya ta ce da yarinyar: “Wai yunwa yake ji; ki ɗauki
    wancan kwanon ki ba shi abinci.” Ba tare da wani musu ba, ’Yar Mowa ta tashi ta zuba masa abinci, ta zauna kusa da shi da abincin a kan cinyarta har ya ci ya ƙoshi.

    Sai ya sake yin wani motsin, sai cinya tace da yarinyar: “Wai ki ba shi ruwa.” Nan da nan ta ba shi ruwa. Suna zaune a haka, can sai ga wani wafcecen kumurci ya shigo, amma kuma ba ta ji tsoro ba. Jim kaɗan sai ta ga macijin ya fara aman ƙwaiƙwaye. Ya amayar da uku ƙanana, daga baya ya yi aman wasu manya uku.

    Da ya gama, sai cinya ta yi wani motsi, sai kai ya ce: “Wai idan gari ya waye za ki tafi, ki zaɓi ƙwaiƙwaye uku ki tafi da su, kuma kada ki fasa sai kin isa kusa da garinku.” Ta ce: “To. Na gode, Allah ya kai mu goben.” Da gari yawaye, sai ’Yar Mowa ta tsuguna ta zaɓi ƙwaiƙwaye uku, amma kuma ƙanana ta zaɓa. Ta kama hanya tiryan-tiryan, ta doshi garinsu.

    Sakamakon ‘Yar Mowa 

    Da ta isa bayan gari, sai ta fasa ƙwai ɗaya, sai ta ga ingarman doki da adon kayan ƙawa da sauran kayan alatu iri-iri. Da ta fasa ƙwai na biyu kuma, sai ta ga ’yan mata gomiya goma suna ɗauke da kayan ado da kayan sa wa iri-iri. Da ta fasa ɗayan, sai ga dukiya har da gida ƙerarre, da duk abin da za a nema don jin daɗin duniya a ciki.

    Sai ta yi godiya ga Allah, ta taka ta hau dokin nan, ba ta zame ko’ina ba sai a ƙofar gidansu. Da kishiyar uwar da ’Yar Bora suka gan ta da dukiya da kwalliya kamar sarauniya, sai kishiyar uwar ta nemi sanin yadda ta sami wannan abu haka. A nan ta ba ta labarin zuwanta Ruwan Bagaja, har zuwa inda ta fasa ƙwaiƙwayen nan guda uku. Sai uwar ’Yar Bora ta ce ita ma sai ’yarta ta je washegari, ita ma ta samo nata.

    Tafiyar ‘Yar Bora

    Washe-gari tun da duku-dukun safiya, uwar ’Yar Bora ta tura ta wai don ta je ta wanke shimfiɗa a Ruwan Bagaja. Ita kuwa ta kama hanya. Da ta je Ruwan Madara sai ta yi
    waƙa kamar yadda ’Yar Mowa ta yi. Sai ruwan yace, “Ni Ruwan Madara ne, ba Ruwan Bagaja ba. Amma in kina so, ki zauna ki sha.”Sai ta ce: “To.”

    A nan ta zauna, ta sha madara har sai da ta ƙoshi. Ta tashi ta yi gaba, ko godiya ma ba ta yi ba. Da ta tarar da Rafin Shinkafa da Kaji, sai ta yi masa waƙa. Sai ya ce shi ba Ruwan Bagaja ba ne, Ruwan Shinkafa da Kaji ne; idan za ta ci, ta zauna ta ci. Sai ’Yar Bora ta ce: “Ai ko ba ka faɗa ba zan ci”. Sai tazauna ta ci har ta ƙoshi.

    Ta sami ruwa ta kwankwaɗa, ta yi gaba. Da ta isa Ruwan Jini sai ya ce shi ba Ruwan Bagaja ba ne, shi Ruwan Jini ne. In za ta sha to. Sai ta yi masa gatsine, ta bugi cinya irin yadda masu tsiwa kan yi, tace: “Me zan yi da wani ruwan jini?” Sai ta tofa masa yawu, ta wuce. Da haka dai ’Yar Bora ta ci gaba har ta kai ga Ruwan Bagaja.

    Da ta tambaya ya ce shi ne Ruwan Bagaja, sai shi kuma ya tambaye ta abin da ya kai ta neman Ruwan Bagaja. Sai ta ce ta zo ne ta sami irin dukiyar da ’yar’uwarta ta samu a nan. Sai Ruwan Bagaja yace: “To ga shi kuwa yanzu dare ya fara yi.” Kafin ma ya gama yi mata bayani sai hadari ya taso. Da ta hango wata bukka sai ta je ta shiga ta fake ruwa.

    Can sai fitila ta kunna kanta, sai ta ga cinya a gefe. Sai ta yi kururuwa, a gefe kuma sai
    ta ga kai ya ce da ita: “Kada ki ji tsoro.” Daga nan sai cinya ta yi motsi, sai kai ya ce: “Wai sannunki da zuwa.” Da ta ji haka sai ta yi tsaki, irin wanda ta saba yi wa mutane, ta ce: “Mene ne kuma na wata cinya tace tana gaishe ni?” Da cinya ta ji haka sai ta yi motsi.

    Sai ta dubi yarinyar tace: “Kai ya ce wai ki ba shi abinci yana jin yunwa, ga abincin can ki ɗauko ki ba shi.” A nan ma sai ta sake yin tsaki ta ce: “Kamar ni in ba shi abinci?” Sai ta tashi ta ɗauko abincin. Da ta ga ƙafafun kaji ne da kifi da naman rago da alkaki da nakiya, sai ta zauna ta cinye. Tana cin wannan abinci, sai cinya ta sake yin motsi.

    Shi kuma kai sai ya ce: “Wai ki ba shi ruwa.” Sai ta ce: “Amma fa cinyar nan da raini kike.” Da ta ɗauko ruwan sai kawai ta shanye, ta bar kai bai ci ba, kuma bai sha ba. Suna nan zaune, sai ga ƙaton kumurci ya shigo, sai ’Yar Bora ta ƙwalla ihu. Maciji bai kula ba, ya fara aman ƙwaiƙwaye shiɗa. Uku manya, sauran ukun kuma ƙanana.

    Sai cinya ta yi motsi, sai kai ya ce: “Wai idan za ki tafi gobe ki ɗebi ƙwai uku ƙanana, in kin je bayan garinku sai ki fasa.” Da ta ji haka, sai ta karkace kai irin na marasa kunya tace: “Yau na ji wani abu, ku za ku gaya mini in ɗiba? Ai koba ku faɗa ba zan ɗiba.”

    Sakamakon ‘Yar Bora

    Da gari ya waye, sai ta ɗebi ƙwaiƙwaye uku amma manya, ta tafi. Da ta fara ’yar tafiya sai ta ce: “Yanzu wai har ma sai na je gida zan fasa kayana?” Sai kawai ta fasa ƙwai
    biyu tare. Tana fasawa sai ga jakai da kutare da ƙudaje suna bin ta. Sai ta fasa na uku, sai ga tarkacen shara da tsummokara tili-tili. Sai kutaren nan suka ɗora ta a kan jaki, suna raka ta.

    Kudaje na bin su har gida. Da uwar ta ga ’yarta, sai ta gudu. Da ’yar ta ga uwar tana gudun ta, sai ta ce da ita: “Tsaya mana, ni ce ’yarki fa.” Sai uwar ta ce: “A’a, yau na rabu da ke, ba ni ba ce.” Sai ta gudu ta bar ta da kutarenta da jakan nan da ƙudaje suna ta zaga gari. Mutanen ƙauyukan kusa da su da suka ji labari suka yi ta tururuwa suna zuwa kallo. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yi wa yara kyakkyawar tarbiya shi ne babban jarin da za su juya don samun kyakkyawar rayuwa.
    • Rashin tarbiya mai kyau shi ne jigon kaiwa ga rashin nasara.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ba ya aikin komai sai ya fita farauta, yana haƙar ramukan Ɓera. Idan ya kamo ɓeraye yakan yanka ya yi bandar naman ya kai kasuwa ya sayar. Wani lokaci yakan fita wannan farauta tare da wani maƙwabcinsa, har ma sun yi suna ƙwarai wajen wannan sana’a tasu.

    Wata rana shi da maƙwabcinsa sun fita farauta, sai suka ga wani babban rami. Da suka tsaya za su haƙa sai maƙwabcin ya ce: “Wannan fa ramin Kura ne bana Ɓera ba. Kada mu tono abin da zai cuce mu.” Sai ya ce da shi: “Kai dai ka cika tsoro, idan dai kai ba za ka haƙa ba, ka tafi ka ba ni wuri.” Da maƙwabcin nasa ya ji haka sai ya tafi abinsa, ya bar shi yana tona ramin.

    Da ramin ya yi zurfi sosai, sai yasa ƙwaryarsa domin ya kama ɓerayen da yake zato suna cikin ramin. Sai ya ji an buge ƙwaryar. Da ya duba sai ya ga ashe Kura ce, har ma ta miƙo ƙafarta waje. Nan da nan ya jefar da kayan haƙan ya kama gudu. Yana cikin gudu ne ya tarar da wasu manoma a gona, sai ya ce da su: “Ku taimake ni ku ɓoye ni mana, ga Kura nan ta biyo ni za ta cinye.”

    Da suka ji haka sai suka ce: “A a, ka yi gaba, ba za mu iyaba.” Haka ya ci gaba da gudu, har ya tarar da wasu mutane masu noma da hanci, ya roƙe su da su ɓoye shi; su ma suka ce ya yi gaba. Ya sake yin gaba da gudu, har ya tarar da masu noma da duwawu, sai ya tsaya ya ce su taimake shi, amma su ma suka ƙi.

    Sai ya ci gaba da gudu, har ya hango wata ’yar bukka sai ya matsa kusa ya leƙa; amma
    ba komai a ciki sai Kunkuru yana zaune. Sai ya dubi Kunkuru ya tambaye shi: “Ina mai bukkar nan? Ina so ya taimake ni ya ɓoye ni.” Sai Kunkuru ya ce: “Ai ni ne mai bukkar, shigo zan ɓoye ka.”Sai mutumin ya ce da Kunkuru: “Manya ma ba su ɓoye ni ba sai kai da karambani za ka ce ka ɓoye ni?”

    Kunkuru ya ce da shi: “Kai dai shigo mana ka gani.” Mai neman Ɓera dai ya tsaya da gardama, har ma ya juya zai tafi, amma kafin ya fara tafiya sai ya hango Kura ta doso bukkar, kuma ya san idan ya fita za ta kama shi. Ai bai san sanda ya kutsa bukkar Kunkuru ba, kuma ya ɓoye shi. Da Kura ta ƙaraso sai ta ce da Kunkuru:

    “Da namana a ɗakin nan.” Kunkuru ya ce: “Babu namanki a ɗakin nan.” A nan Kunkuru da Kura suka kama faɗa, kafin wani ɗan lokaci Kunkuru ya kashe Kura. Da mutumin nan ya ga haka, abin ka da halin ɗan Adam sai kawai ya ce da Kunkuru: “Ni kuma ai nama ya samu a araha; bari ma in feɗe shi, kuma ina son ƙwaryar.”

    Da Kunkuru ya ji haka sai ya ce da shi: “Ka haƙura da fatar Kurar nan mana, ta fi maka amfani. Ka ma kwashe naman nata ga baki ɗaya.” Mutumin nan dai ya ƙi, ya dage shi dai ƙwaryar Kunkuru yake so. Kunkuru dai ya yarda, ya kuma ce da shi: “To, zan haɗa ka da karnuka su raka ka garinku, domin duk sanda fatar Kurar nan za ta cinye ka sai su kama ta da ci.”

    Da ƙyar dai mutumin ya yarda ya tafi da karnukan. Mutumin nan shi da karnuka sun kama hanya sun yi nisa, sai ya ji ya gaji, ya ajiye fata a gindin wata bishiya zai huta. Ajiye ta ke da wuya sai ta fara motsi tana kukan Kura. Da karnuka suka ga haka sai suka rufar mata, suka murƙushe ta, ta daina kukan, kuma ta daina motsi, ya tashi ya ɗauka suka ci gaba da tafiya.

    Bayan wani lokaci kuma, sai ya tsaya zai yi fitsari, fata kuma ta fara motsi. Karnuka kuma suka fara haushi fiye da irin wanda suka yi a baya. Sai mutumin wai ya ji haushi, ya daka musu tsawa, har suka tsorata suka gudu. Kafin ka ƙifta ido, ai fatar nan ta rufe mutumin nan ta cinye shi, kowa ya huta da taurin kansa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Taurin kai da rashin ɗaukar nasiha babu abinda yake jawo wa mai shi sai cutarwa da faɗawa halaka.
    • Wanda bai ji bari ba, ya ji hoho.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A wani ɗan ƙauye da ke yamma da Dajin Kurege, akwai wani manomi da matarsa makauniya. Suna cikin zama irin na rufin asiri, sai Allah ya yi masa cikawa. A lokacin kuwa tana goyon jariri mai suna Zama. Uwar tasa kuwa ta sha wuya wajen renonsa. Kullum sai ta je ta yo bara kafin ta ciyar da kanta da ɗanta.

    Mijinta kuma bai bar dukiya ba sai shanu biyu kawai da Zama ya gada. Ita kuma mace ce mai tsinkaye da riƙon amana, sai ta kai shanun nan wani garke, a rugar wasu makiyaya da ke kusa da ƙauyensu. Ta yi haka ne da nufin a kiwata su, idan yaron ya girma, kuma shanun sun yaɗu, ta nuna masa abin da ubansa ya bar masa.

    Kuma duk abin da ɗanta yake so takan je ta barato masa. Sannu a hankali, yaro ya girma ya isa aure. Wata rana bayan sun ci abincin dare, sai uwar ta kira shi tace: “To, Zama, da ma ina jira ne idan ka yi hankali sosai in danƙa maka abin da ka gada daga mahaifinka. Amma na kai su garke ne, a rugar wasu makiyaya.”

    Da ya ji lafazin mahaifiyarsa, sai ya tambaye ta: “Menene? Wane irin abu ne?” Ta ce: “Shanu biyu ne ya bar maka, amma ban sani ba ko yanzu sun ƙaru?” Sai ta kama hannunsa ta ce: “Mu je inda aka kai shanun, mu jiyo labari.” Ta yi masa kwatancen hanyar da za su bi; suka kama hanya, har ya kai su.

    Mai garke ya yi musu maraba suka gaisa kamar yadda ya kamata, sai makauniya ta tuna masa shanun da ta kawo masa kiwo tun shekarun baya da suka wuce. Sai mai garke ya ce: “Haka aka yi kuwa. Ai yanzu shanu sun hayayyafa, har ma sun kai ashirin.” Da ta ji haka sai ta yi masa godiya, ta ce da shi: “To, ga magajinsu ya kawo ƙarfi, buƙatu sun taso, shi yasa muka zo mu kora su.”

    Sai mai garke ya ware musu shanunsu; suka kama hanyar gida, Zama yana kora su har suka je gida. Bayan sun ɗan huta da kwana biyu, sai uwar tace da Zama: “Ya kamata yanzu kam ka yi aure domin ina so in sami jikan da zan rinƙa wasa da shi.” Sai ya ce da ita: “To, amma fa ni ba zan yi aure a ƙauyen nan ba sai dai daga birni.”

    A kwana a tashi, wata rana sai Zama ya shiga birni, ya je kasuwa; sai ya tarar an sa wata kyakkyawar yarinya a gaba, makaɗa na cashewa, ana yi mata kirari, da waƙe- waƙe. Sai ya tambayi wani ɗan kallo da cewa: “Me yasa aka kewaye wannan yarinya mai kyau kamar aljana, ana yi mata kiɗa da waƙa?” Sai ya ce da shi: “Saboda kyauta ne uwarta tace duk mai son ta, sai ya ba ta duk dukiyar da ya mallaka, kafin ya aure ta.

    Duk masu dukiyar da ke garin nan kuma sun kasa.” Da ya ji haka sai ya yi tsaki, ya ce: “Ni zan aure ta.” Sai ya matsa kusa, ya sa aka yi he!, ya ce: “A gayawa uwar yarinyar cewa ni zan aure ta, kuma zan ba da duk dukiyar da na mallaka.” Wani daga cikin danginta ya ce: “To me ka mallaka?” Zama ya ce: “Ina da riƙaƙƙun shanu ashirin.”

    Sai dangin ya ce: “To, ka je ka kawo su za a ba ka ita.” Da Zama ya ji haka, sai kurum a cikin ɗoki ya koma gida ya gaya wa mahaifiyarsa cewa ya sami wadda zai aura. Uwar ta ce: “Wane sharaɗi iyayenta suka sa maka?” Sai ya ce: “Sun ce sai na ba su duk dukiyata kafin su ba ni ita.”

    Uwar daga farko ta yi murna, amma da ta yi tunani kaɗan sai ta ce: “Kai ɗan nan, wannan fa shi ne iyakar abinda ka mallaka, babu hikima a ce ka ba su ita gaba ɗaya.” Wannan magana dai ba ta shigi yaron ba. Sai kawai yace shi fa sai ya auri wannan yarinyar. Sai uwar ta ce: “Shi kenan, yi abin da kake so.”

    Yaro ya tashi ya kwance shanu ya kora su gidan iyayen yarinyar da zai aura. Suka karɓa suka kuma ba shi yarinyar, aka ɗaura aure ya ɗauki matarsa ya kai ta gidansu, ya je kuma ya sanar da mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: “Ai ya kamata ka kai ni in yi mata barka da zuwa.” Bai yi wata-wata ba ko sai ya kama sandarta ya kai ta har ɗakin amaryar.

    Amma da ta ga mahaifiyar Zama makauniya ce, sai ta ƙi yi mata magana, ta nuna cewa ai ba ta yi wa makafi magana. Uwar kuma ba ta nuna damuwa a kan halayyar surukarta ba, saboda haƙurin da Allah ya ba ta. Ana nan, bayan ’yan kwanaki sai amarya ta ce da Zama: “Ni fa na gaji, ba zan iya ci gaba da girki a gidan nan ba.”Sai ya ce: “To, yaya kike so a yi?”

    Ta ce da shi: “Mai dafa abinci za ka nemo mini.” Da ya ga matarsa ta kafe a kan haka sai ya gayawa mahaifiyarsa. Ita kuma ta ce da shi: “Ba komai, ni zan ci gaba da dafawa; ai da ma tun kafin ta zo, ni nake dafawa.”Haka ta ci gaba da yi musu girki, surukarta kuwa ta ci gaba da zaman ƙwambo.

    Ana nan, sai wata rana matar Zama ta tambayi mijin inda ya samo shanun da ya kai gidansu ya aure ta. Sai ya kwashe labarin yadda ya ci gadon mahaifinsa, ya gaya
    mata. Da ta ji haka sai ta ce: “Ai ba ka da wayo, mahaifiyarka ta cuce ka domin ta ɓoye sauran shanun. Ka je ka bincike ta da kyau, za ta gaya maka inda sauran suke.”

    Nan da nan ya tashi ya je ya sami mahaifiyarsa, ya fara yi mata rashin ladabi da faɗa, wai sai ta fito masa da sauran shanunsa. Ita kuma ta ce da shi: “Haba ɗana, ban ɓoye maka komai ba.” Haka dai Zama ya yi ta yi wa mahaifiyarsa rashin ladabi har tsawon wasu ’yan kwanaki.

    Da matar Zama ta ga bai yi wa mahaifiyarsa wulaƙanci kamar yadda take so ba, sai ta ce da shi: “Ni fa zan koma gidanmu; domin na gaji da zama da makauniya a gidan nan. Yanzu lallai sai ka san inda za ka kai ta, ko kuma ni in tafi gidanmu.” Sai ya ce: “Kada ki damu. Yanzu faɗi yadda kike so a yi da ita.”

    Jin haka fa ya sa ta yi murmushi ta ce: “Ina son ka kai ta cikin jeji inda kuraye suke shan ruwa, sai ka ce ta jira ka, kai kuma ka gudo gida. Washegari sai ka je ka kwaso ƙasusuwanta bayan kuraye sun cinye ta. Daga nan sai ka gaya wa mutane cewa ta yi ɓatan kai ne a jeji, kuraye suka cinye ta.” Ya ce: “Idan na yi haka za ki haƙura da komawa gidanku; za ki zauna da ni?”

    Sai matar ta kashe murya, ta dube shi, ta ce: “Ƙwarai kuwa. Idan ka yi haka, ba inda za ni.” Zama ya je ya ce da mahaifiyarsa: “Yanzu na yi wani tunani ina son ki zo mu je in kai ki inda za ki sami maganin makantarki.” Sai ta ce: “To.” Nan da nan ta shirya a cikin murna, suka kama hanyar daji, har suka kai tsakiya inda kuraye kan taru, ya ajiye ta a gindin wata bishiya, ya ce da ita:

    “Zauna nan, ni kuma zan je neman wani itace da za a haɗa maganin. Idan ban dawo ba, kada ki motsa daga nan.” Ta ce da shi: “To. Na gode Zama, ka kyauta da ka kawo ni
    gidan masu magani.” Shi ko bai ma damu da godiyar da take yi masa ba, sai kawai ya kama hanya ya koma gida ya baro ta a wannan dajin.

    Ita kuwa ta zauna tana jiransa har dare ya yi. Idan ta ji motsi sai ta ce: “Zama ne? Ka dawo?” Sai ta ji kukan kura a bayanta, amma ba ta razana ba. Wannan dajin kuma bayan kuraye da sauran namun da ke dajin, akwai aljanu a wurin da yawa. Aljanun ne ma suka zagaye ta, suna mamakin abin da ya sa ta zo wuri mai hatsari haka.

    Can sai ɗaya daga cikinsu ya rikiɗa ya je ya ce: “Ke matar nan me ya kawo ki nan?” Sai ta ce: “Ɗana ne Zama ya kawo ni, don neman maganin makantar nan tawa.” Sai aljanin nan ya ce: “A a, nan fa mutane ba sa zuwa, domin tsakar daji ne, amma zan taimake ki yadda za ki tafi gida.” Sai ta ce: “A a ɗana ya ce in jira shi a nan; idan na tafi zai yi mini faɗa.

    Gara in jira shi ai zai zo ya same ni.” Da tausayi ya kama aljanin nan, sai ya gaya mata cewa za su warkar mata da makantar. Kamar da wasa, da suka yi wani siddabaru irin nasu, sai kawai ta ga ta fara gani. Buɗe idonta bai sa ta yi niyyar tafiya ba, har gari ya waye ta farka daga barcin da ta yi, ta shiga jiran ɗanta.

    Kafin ya zo sai ta ga shanu masu yawa, garke-garke, ta tambayi aljanin nan da ya rikiɗa ya zama mutum, ko shanun nan na wanene? Sai ya ce da ita, ai nata ne duka, sun ba ta kyauta. Makauniyar nan tana zaune can sai ga Zama ya iso. Ya kuma zo ne don ya kwashe ƙasusuwan mahaifiyarsa saboda ya tabbatar da kuraye sun cinye ta a cikin dare.

    Maimakon haka, sai kawai ya ji ta kira shi daga nesa, saboda jikinta ya ba ta cewa ɗanta ne, ko da yake dai ba ta taɓa ganin sa ba sai wannan rana. Har ya juya zai gudu sai
    ta ce: “A a, kada ka gudu mana. Ni ce mahaifiyarka.” Da ya isa kusa da ita, sai ta kwashe duk labarin abinda ya faru tsakaninta da mutumin da ya taimake ta, ga idanu sun samu, kuma ga shanu.

    Zama ya kora shanu, shi da mahaifiyarsa suka koma gida. Da matarsa ta gan shi da garken shanu, kuma ga mahaifiyarsa tana gani raɗau, sai haushi da mamaki suka kama ta. Shi kuma Zama ya kwashe labari ya gaya mata. Jin haka ya sa ta ce ita ma dole ne ya kai uwarta dajin nan idan yana son zama da ita.

    Sai ya ce: “To, zan yi duka binda kike so, saboda ina son ki.” Bayan kwana uku da dawowar uwar Zama daga dajin mutuwa, matarsa ta tafi garinsu, ta ɗauko uwarta, domin ita ma a kai ta can ta samo shanu. Haka kuwa aka yi ya ɗauke ta ya kai ta daji ya baro. Da ta ji kukan kura na farko, sai ta kiɗime ta kama ihu, ta tsure.

    Nan take kuwa kuraye suka far mata suka cinye ta. Da gari ya waye Zama da matarsa suka kama hanyar daji domin su koro shanun uwar matarsa, amma da suka je inda suka kai ta, sai suka tarar sai ƙasusuwanta; kuraye sun cinye ta, kuma ba shanu. Tun daga dajin matar Zama ta kama kukan baƙin ciki, ta kasa komawa gida ta tare a gindin wata kurna tana ta sharar kuka. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Gaskiya da riƙon amana su ne maganin makirci da makirai.
    • Hassada da ganin ƙyashi su suke sa a faɗa kogin da-na- sani.
    • In za ka gina ramin mugunta, gina gajere.
    • Tun ran gini, tun ran zane.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Tatsuniyar Sandar Arziƙi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani gari da ya yi iyaka da ƙasar Aljanu, akwai wani mutum mara sukuni da matarsa, da ɗansu ɗaya. Suna zaune a cikin wannan hali, sai ɗan ya isa aure. Iyayen nasa sai suka ce da shi: “Yanzu ga shi ka isa aure, amma ba mu da abin da za mu aura maka mata da shi.”

    Amma mahaifinsa yana da wata sanda; sai ya ba shi ita yace: “Ka kama hanyar duk garin da ka zaɓa a zuciyarka; sandar za ta zama sanadin yin aurenka.” To, da yake yaron mai biyayya ne, sai ya karɓi sandar ya cewa mahaifansa: “Na gode, kuma na tafi. Allah ya ba ni sa’a.”

    Baki ɗaya suka ce: “Amin.” Yaro yana cikin tafiya a daji, sai ya tarar da wasu mutane suna jifan tsuntsaye. Sai ɗaya daga cikinsu yace: “Kai yaro, ka taimake mu da aron sandar nan taka mu jeho tsuntsu mana.” Ba tare da wani musu ba, sai kawai ya ce: “Ga ta.” Suka karɓa, suka jeho tsuntsaye da yawa da ita.

    Amma kuma sai sandar ta maƙale a jikin rassan bishiyar. Da ya ga sandarsa ta maƙale, sai ya fara waƙa yana cewa: “Tam, tam, Sai kun biya ni sanda ta. Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni. Takan cishe ni, Tai min aure.” Sai suka ce: “Kash, ga shi kuwa ba mu da komai sai dai mu ba ka tsuntsu ɗaya.”

    Sai ya ce: “To, ku ba ni.” Suka ba shi tsuntsu, ya karɓa ya kama hanya. Yana cikin tafiya sai ya tarar da wata mace ta girka abinci. Sai ta ce da shi: “Kai yaro, ba ni tsuntsun nan naka in gani.” Da ta karɓa, sai kawai ta gyara shi, ta yi miya da shi. Yana ganin haka sai ya ce: “

    Tam, tam, Sai kin biya ni tsuntsuna, Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai ta ce: “Wayyo samari, ai ban san haka abin yake ba, sai dai ba ni da komai sai tuwon nan da ka gani.”

    Da ya ji haka sai ya karɓi tuwon mara biyar, ya kama hanya riƙe da abinsa. Yana cikin tafiya, sai ya tarar da wasu manoma, sun yi aiki sun gaji; yunwa ta sa sun galabaita. Da suka ga tuwo a wurin yaro, sai suka ce: “Ɗanyaro mu ga tuwon nan mana.” Da suka karɓa sai suka cinye. Da ya ga sun cinye masa tuwo, sai ya fara waƙar da ya saba

    “Tam, tam, Sai kun biya ni tuwona, Tuwona da mai girki ta ba ni, Da ta karɓi tsuntsuna,
    Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai suka ce: “To ga shi ba mu da komai. Amma in kana son fartanya ko magirbi, sai mu ba ka ɗaya.”

    Da ya ji hakasai ya ce: “Ba komai, ku ba ni magirbi, ya wadatar.” Nan take suka ba shi magirbi ɗaya, ya kama hanya. Yana cikin tafiya, ya kusa isa wani babban birni, sai ya tarar da wasu mutane sun fara haƙa ƙabari za su yi jana’izar wata gawa. Da suka ga magirbi a hannunsa, sai babbansu ya ce: “Yaro ba mu aron magirbin nan mana mu haƙa ƙabari.

    ”Ba wani musu, sai ya ba su. Suna cikin tonon rami, sai magirbin ya kare da ganin haka sai ya fara wakarsa: “Tam, tam, > Sai ka biya ni gawata, > Gawata da masu haƙar ƙabari suka ba ni, > Masu tonon ƙabari da suka karya magirbina, > Magirbina da manoma suka ba ni, > Manoma da suka cinye tuwona, > Tuwona da mai abinci ta ba ni, > Mai abinci da ta karɓi tsuntsuna, > Tsuntsuna da maharba suka ba ni, > Maharba da suka ɓatar da sandata, Sandata dauwatataba ni, > Ubana ya ba ni, > Yakan cishe ni,
    > Ya yi min aure.” >

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Yin biyayya ga magabata tare da jure wahalhalun rayuwa sukan kawo nasara a rayuwa.
    • Mai arziki ko a ƙwara ya sayar da ruwa.
    • Arziki a ƙasa ake tako shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku. A wani ɗan ƙauye, an yi wata mata mai ’ya’ya biyu, mace da namiji. Sunan namijin Fugo shi ne wa; ita kuma macen sunanta Awa, ita ce ƙanwa. Shi Fugo maƙeri ne. Ana nan, sai wata rana wani mutum daga wani gari mai nisa ya zo ya ce yana son ya auri Awa, sai aka yarda, aka ba shi ita.

    Bayan an gama biki, sai ya ɗauki matarsa suka tafi garinsu, wanda ba a bin hanyar zuwansa da rani saboda akwai wani dodo da kan tsare hanyar, ya cinye matafiya duk lokacin rani. Amma kuma da damina ba ya taɓa kowa. Ana nan, ana nan sai a wata damina Fugo ya je garin mijin ƙanwarsa Awa don ya gaishe su.

    Bayan ya dawo da rani sai mahaifiyarsu ta rasu, kuma ana so a aikawa Awa garin da take aure, to amma ba hali saboda a cikin rani ne; kowa yana tsoro kada ya bi hanyar dodon nan ya cinye shi. Ana cikin neman mai zuwa, sai kurciya ta ce za ta je ta gaya wa Awa saƙon. Sai ko aka ba ta saƙo, ta tashi sama, ba ta sauka ba sai a kan ɗakin Awa.

    Awa na kwance a ɗaki, sai ta ji kurciya tana waƙa, tana cewa:

    “Awa, Awa kina barci,

    Ga uwarki can,

    Tana barci tun shekaran jiya,

    Tun shekaran jiya ba ta tashi ba,

    Ki shirya, za ki dakan gero.”

    Sai ta fito ta saurara da kyau, ta fahimci lafazin waƙar kurciya, sai ta fashe da kuka, har da kururuwa. Da mijinta ya ji, sai ya shigo ya tambaye ta abin da ya faru. Sai tace an aiko mata da rasuwar uwarta ne. Da ya ji haka sai yace: “To, ga shi hanya ba za ta biyu ba. Yanzu yaya za a yi?”

    Duk da cewa Awa ta san dodo yana hanya kuma tabbas idan ta bi hanyar zai cinye ta, sai ta ce ita kam lallai sai ta je ta gano kushewar mahaifiyarta tun ba ta daɗe da rasuwa ba. Da mijin Awa ya lura lallai ta tsaya kai da fata sai taje, sai ya ce: “To, shi ke nan, sai mu yi wata dabara, mu yanka miki shanu, mu raba su gida bakwai, idan dodo ya taso zai
    cinye ki, sai ki jefa masa kashi ɗaya.

    Da haka har ya ƙoshi, ke kuma ki isa gida.” Sai Awa ta ce: “To na gode, mai gida.” Aka kama shanu, ya yanka, ya sa aka kasa nama gida bakwai, aka zuba wa Awa a cikin masaki. Da ranar da aka sa ta zo, sai ta kama hanya, ɗauke da masakin nama. Tana cikin tafiya a daji, sai dodon nan kwatsam ya ɓullo, yana tafiya yana waƙa, yana cewa:

    “Maraba, lale, lale,

    Wannan mata, lale,

    Ina za ki je?

    Gaya mini, ina za ki je?”

    Dodon nan baƙi ne ƙirin, ga gashi duguzunzun; abin gwanin ban tsoro. Idan ya buɗe baki sai turiri ke fita. Amma Awa ba ta tsorata ba, sai kawai ma ta mayar masa da waƙa:

    “Ni Awa, ni Awa,

    Zan je makokin mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan je kai kayan mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan kai kayan miya,

    Kayan miyar mutuwar uwata.”

    Sai dodo ya matso kusa da ita ya ce: “Buɗe in gani; menene a ciki?” Da ta buɗe masaki ya ga naman sa ne, sai ya ce: “Ko dai ki ba ni ko in haɗiye ki.” Sai ta ce: “Idan ka haɗiye ni zan yi maka kuka.” Sai dodon ya ce: “Yi kukan mu ji.” Sai ta ce:

    “Wai, wai, wai, Gari ya yi zafi,

    Uwata ba ta nan,

    Uwata ta tafi lahira.”

    Tana gama waƙar, sai ta ɗauki yankan nama ɗaya ta jefa masa. Da ya tsaya yana ci, sai ta kama hanya tana sauri. Kafin ya cinye ta yi nisa. Da ya cinye, sai ya sake bin ta, ya sha gabanta ya kama waƙa, ita kuma sai ta mayar masa. Duk sanda ta jefa masa naman, sai ta fara gudu, shi kuma ya ɗauki naman ya tsaya ya cinye.

    Da ya cinye sai ya sake bin ta. Haka suka rinƙa yi, har naman ya ƙare. Ba ta yi
    nisa ba sai ta yar da masakin, ta kama gudu. Shi kuma da ya cinye nama, sai ya bi ta. Da ta ga dai ya kusa kamo ta, sai ta hau bishiya, shi kuma ba zai iya hawa ba; sai ya tsaya a gindin bishiyar.

    Can sai ya ɗaga kai ya ce da Awa: “Ki sauko in cinye ki”. Ita kuma ta rasa yadda za ta yi, sai kwatsam ga kurciya ta sauka a kan bishiyar. Sai Awa tace da ita: “Idan na aike ki wurin yayana me za ki ce da shi?” Sai kurciya ta ce: “Zan ce da shi Fugo kana maƙera kana ƙira, amma ƙanwarka tana can a kan bishiya dodo zai cinye ta a dokar daji.”

    Sai Awa ta ce da kurciya: “Yawwa, haka za ki je ki faɗa masa.” Nan take kurciya ta tashi sama, ba ta tsaya a ko’ina ba sai kan bishiyar da ke kusa da maƙerar Fugo. Da saukarta ta fara waƙa tana maimaita saƙon da aka aiko ta sanar wa Fugo. Da ya ji waƙa, sai ya ɗaga kansa sama, ya ga kurciya, ya kuma fahimci abin da ta faɗa.

    Sai ya shiga shiri, domin bai ga ta zama ba, saboda dodo zai kashe masa ƙanwa. Ya ɗebi makamai irin waɗanda yake ƙerawa, kamar masu da kwari da baka da takubba da sauransu, ya kwance karnukan farautarsa guda goma, sai ya ce da kurciya ta tashi sama, zai bi inuwarta har gindin bishiyar da dodo ya tsare masa ƙanwa.

    Haka Fugo ya kama hanya, kurciya na yi masa jagora. Idan ya saki hanya, sai ta yi waƙa, shi kuma ya bi inda ya ji muryarta, har dai suka isa. Suna zuwa, sai suka tarar da dodon a inuwar bishiyar yana barci. Ba tare da jinkiri ba, sai Fugo ya zaro kibiya ya ɗirka wa dodon nan. Kafin ya farka, sai da Fugo ya yi masa ruwan kibau kamar ashirin.

    Da ya farka, kafin ya wartsake Fugo ya jefa masa masu kamar guda tara. Amma duk da haka da ya wartsake sai aka ji yana cewa: “Kai wane cinnaka ne yake damuna?” Shi kuma Fugo sai ya zaro wasu kibau masu dafi, ya dinga ɗana su yana sakar wa dodo ɗaya bayan ɗaya a idonsa na dama, nan take idonsa ya tsiyaye.

    Kafin ya san abinda ake ciki, Fugo ya sake auna ɗaya idon, kuma ba kuskure ya same shi. Shi ma nan take ya tsiyaye, dodo ya zama ba ya iya gani. Tuni dafin kibiyar ya bi jikin dodo, har ya zamanto ba zai iya tashi ba. Sai Fugo ya ce da Awa ta sauko. Sai dodo ya ce: “Ki sauko in cinye ki.” Da Fugo ya ji haka, sai ya zare takobi ya sassare dodo, ya yi masa gunduwa-gunduwa.

    Awa tana gani, amma da ta yunkura za ta sauko, sai guntayen naman dodo suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Da Fugo ya ga haka sai yasa karnukansa suka cinye naman dodon gaba ɗaya, sannan ya ce ƙanwarsa ta sauko. Da ta miƙo ƙafarta za ta sauko, sai ƙasusuwan suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Sai ya sake sa karnukansa suka cinye ƙasusuwan.

    Daga nan kuma ta sake miƙo ƙafarta za ta sauko, sai busasshen jinin dodon da ke ƙasa ya ce, ta sauko ya cinye ta. Daga nan dai sai Fugo ya sa karnukansa suka gwaguye jinin da ya yi kasko a ƙasa, har dai suka tabbatar babu kome a wurin, sai ya ce to ta sauko. A nan ne fa ta sauko lafiya, yasa ta a gaba, suka kama hanyar gida.

    Nan da nan labari ya bazu cewa Fugo Sarkin Maƙera ya kashe dodo, kuma hanya ta yi lafiya, rani da damina, babu sauran fargaba. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Haƙuri da juriya da nuna jarumta sukan sa a shawo kan matsala komai tsaurinta.
    • Farar aniya laya.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha-maza-ha-mata sai ya gani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani ƙaramin ƙauye da yake kusa da wani daji ai cike da dodanni. Ɗaya daga cikin dodannin ya matsawa mutanen wannan ƙauyen, yana kama su ya bautar da su. Yakan fita ɗibar kayan miya duk ranar Asabar. Saboda haka mutanen ƙauyen suka daina fita ɗibar kayan miya a ranar da Dodon yake fita domin kada ya kama su ya mayar da su bayi.

    Mutanen da ya kama ne sukan dafa masa abinci da sauran wahalhalun gida na yau da kullum. Ana nan cikin haka shekara da shekaru, sai wata rana wata yarinya wai
    ita Umbagila ta ƙudurce a zuciyarta cewa za ta je ɗebo kayan miya ranar da Dodo yakan je, watau ranar Asabar.

    Sai ta gaya wa uwarta. Da uwar ta ji abin da tace sai ta dube ta ta ce: “Kada ki je domin ranar Asabar Dodo yakan je ɗibar kayan miya, idan kin je zai kama ki.” Umbagila ta ce da uwarta: “Ni dai ki yi min addu’a lallai kam zan je.” Haka dai ta haƙura ta ƙyale ta ta ɗauki ƙwarya ta shiga dajin da mutanen ƙauyen kan je neman kayan miya.

    Tana cikin cirar ganyen lalo da ayayo da karkashi da barkono da sauran kayan miya, kwatsam sai ta ji motsi a bayanta, kafin ta juya sai ta ji Dodo ya cafke ta. Tana ganinta a hannun Dodo sai ta fashe da kuka. Da ya ga ta fara kuka, sai ya ce mata ta daina kuka, idan ta yarda za ta aure shi ba zai cinye ta ba.

    Ba tare da gardama ba Umbagila ta ce da Dodo: “Na yarda in aure ka.” Shi ke nan Dodo ya kai ta gidansa ya ajiye ta, kuma ya ce daga wannan rana ba zai ci abincin da bayi suka dafa ba sai wanda ta dafa. Duk sanda Dodo ya je farauta, ko yawace-yawacensa ya dawo, da ya iso kusa da gida sai ya fara waƙa yana cewa:

    “Umbagila matata,

    Umbagila amaryata,

    Umbagila ina tuwona?”

    Ita kuma da ta ji sai ta amsa masa da cewa:
    “Dodo mijina,

    Ga tuwonka can a bakin randa,

    Ga furarka can a bakin randa,

    Ga ruwan sha nan a bakin randa.”

    Haka dai suka ci gaba da zama da Dodo. To dama Dodo yana da wata hatsabibiyar kaza a gidansa. Wata rana ya tafi yawo, sai Umbagila ta haɗa kayanta za ta gudu. Da kaza ta ga alamar za ta gudu, sai ta kira Dodo tace: “Dodo, Dodo za ta gudu.” Nan da nan ya dawo gida yace: “Na ji labari za ki gudu.”

    Sai ta yi masa murmushi tace: “A a, na shanya kayana ne, kuma yaya zan gudu in bar mijina?” Da ya ji haka sai ya ce: “Yawwa matata, na san ba za ki gudu ba.” Sai ya fita harkokinsa. Kullum idan Umbagilatayi ƙoƙarin gudu, sai kazar nan ta fallasa ta. Rannan dai sai ta zauna ta kama kuka a daidai lokacin da ta san Dodo ya kusa dawowa.

    Da ya shigo gida ya tarar tana kuka sai yace: “Me ya sa ki kuka, matata?” Sai ta ce: “Ina so in ci kaza ne, kuma na san ba ni da wanda zai ba ni ita.” Sai ya ce da ita: “Yanzu  saboda wannan ne kawai kike kuka?” Ta ce: “E, saboda haka ne.”Ya ce: “To, daina kukan haka, zan yanka miki kaza.” Sai ko ya kama kazar nan mai fallasa ya yanka suka cinye.

    Bayan sun cinye, sai Dodo ya fita farauta. Ita kuma ta shiga haɗa kayanta za ta gudu. Sai gashin kazar nan ya kira Dodo yace: “Dodo, Dodo, dawo gida matarka za ta gudu.” Tana jin haka sai ta shiga ɗaki ta ɓarke da kuka. Can Dodo ya iso gida ya tarar da matarsa tana sharar kuka, sai ya nemi jin abin da ke damun ta.

    Ta ce masa: “Bana son ganin gashin kazar nan a gidan nan.” Da jin haka sai ya tattara gashin kazar ya ƙone, ya sa bayinsa suka kwashe tokar suka kuma ƙanƙare jininta daga wurin da aka yanka ta. Washegari da Dodo ya tafi yawonsa, sai Umbagila ta kwashe ’yan komatsenta, ta gudu gidansu, ta kuɓuta daga sharrin wannan Dodo. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ƙin bin umarnin iyaye yakan janyo wa ɗan ya fuskanci matsaloli masu yawa a rayuwarsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kusa da dajin Ƙanzon Kurege, akwai wani mutum da ke zaune da matarsa. Mace ce mai haƙuri da son taimakon mijinta a hidimar da yake yi ta kula da gida. Suna nan, sai Allah ya ba matar ciki. Sannu a hankali, ciki ya girma, sai mijinta ya ce tunda cikinta ya girma, ta daina zuwa rafi ɗaukar ruwa, amma sai tace ai babu mai taimaka mata.

    Ta ci gaba da zuwa ɗaukar ruwan. Ana nan, wata rana matar nan ta je ɗaukar ruwa sai ta fara naƙuda a bakin rafi. Da sauran matan da suka je ɗaukar ruwa tare suka ga halin da ta shiga, sai suka kai ta gida. Da haihuwa ta zo, sai ta haifi jarirai goma sha ɗaya. Goma daga ciki ba su da jiki; guda ɗaya ne kaɗai cikakken mutum.

    Bayan kwana bakwai aka raɗa wa kowannensu suna. Karamin cikinsu, watau mai jiki, sai aka sa masa suna Kurma. Yaran nan suna nan yau da gobe har suka girma. To amma sai
    aka lura sauran goman duk miyagu ne, har ma sun fara ƙoƙarin cinye ƙanen nan nasu. Da iyayensu suka ga haka, sai suka kira Kurma suka ce: “Tun da ‘yan’uwanka ba za su bar ka ba, gara ka sulale cikin dare ka yi tafiyarka wani gari.”

    Can cikin dare sai babansu ya ta da Kurma daga barci ya ba shi wata sanda ya ce ya kama hanya ya tafi kawai. Kurma ya karɓi sandar da ubansa ya ba shi, ya kama hanya a cikin daren ya fice daga garin. Da gari ya waye, ‘yan’uwan suka leƙa ɗakinsa, ba su ganshi ba, sai suka tambayi uwarsu inda yake; ta ce ba ta sani ba.

    Da suka tambayi ubansu, sai ya ce da su: “Kurma ya ce in ba shi sanda zai
    je wani gari, kuma na ba shi ya tafi.” Da suka ji jawabin ubansu sai suka rasa yadda za su yi. Bayan Kurma ya koma wani gari da zama, sai ya haɗu da matar da yake so ya aura. Saboda ba shi da dukiyar da zai yi auren, sai ya sayar da sandar nan da ubansa ya ba shi lokacin da zai baro garinsu, ya biya sadaki aka ɗaura musu aure.

    Kurma yana nan zaune da matarsa cikin jin daɗi. Bayan wani lokaci sai matar ta ce: “Mai gida ya kamata mu je garinku ganin gida domin in san garinku da danginka da mahaifanka.” Da ya ji abin da ta faɗa sai ya ce: “Mhm, watau ba ki sani ba ne, ai ‘yan uwana duk ba su da gangar jiki, kuma mayu ne, idan mun je za su cinye mu.” Sai ta ce a a, ita dai sai sun je tun da mahaifansa suna nan ba wani mugun abu da zai faru.

    Da ya ga ta matsa sai sun je, sai ya ce: “To kada ki ce na hana ki zuwa, ki shirya mu tafi.” Bayan sun kammala shirye-shirye, sai suka kama hanyar garinsu Kurma. Da suka isa ƙauyen, suna shiga gidan sai suka ci karo da ɗaya yana mirginawa a ƙasa. Da matar Kurma ta ga kai ne yake mirginawa babu gangar jiki, sai tsoro ya kama ta, ta fashe da kuka.

    Su kuwa ‘yan’uwan Kurma da suka ji shi ne ya zo har da matarsa, sai suka kama waƙa suna cewa: “Lale, lale, Maraba da Kurma, Kurma lale, Kurma sannu da zuwa, Kurma lale, Kurma ina sandarka ne?” Da Kurma ya ji sun nemi sanin inda sandar da mahaifinsa ya ba shi, sai ya ce: “Na sayar da sandar.” Sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “Me ka yi da kuɗin?” Sai ya ce: “Na yi aure da su.” Suka ce: “Ina matar?”

    Sai Kurma ya amsa wa mai tambayar: “Ga ta nan a bayana, tana kuka.” Wani kuma ya tambaye shi: “Me ya sa take yin kuka?” Haka dai suka rinƙa yi masa tambayoyi, har suka shiga cikin gidan. Da uwarsu ta ga ɗanta, sai ta zo ta tarye su shi da matarsa a cikin murna a tsakar gida, ta ce su shiga ɗaki, suka shiga. Suka ƙara hutawa, har zuwa faduwar rana.

    Da dare ya yi sai uwar ta kira Kurma ta ce: “Ka san ‘yan uwanka mayu ne, me ya sa ka kawo ‘yar mutane a cinye ta?” Sai ya amsa da cewa: “Tana so ta gaishe ku ne da baba.” Sai uwar ta ce: “To shi ke nan, idan an ɗauke ƙafa zan ɓoye ku a rumbu, in sun tambaye ni in ce kun tafi; idan sun kwantasai kugudu.” Da dare ya tsala, sai ta ɓoye su a rumbu.

    Can cikin dare sai ɗaya daga cikin ‘yan’uwan Kurma ya tambayi uwarsu inda Kurma da matarsa suke. Sai ta ce: “Ai sun tafi.” Sai ya ce: “To amma yaya nake jin ƙanshin mutum a gidan nan?” Sai ta ce: “Ai ni ma mutum ce, in kuma za ku cinye ni to.” Sai baki ɗayansu suka ce: “A a, ba za mu cinye wadda ta haife mu ba.”

    Don uwar ta kwantar musu da maitar da ta motsa, sai ta ce musu: “Ai ba su tafi ba; sun je gai da ƙawayena ne; da zarar sun dawo zan dafa su.” Can cikin dare sai uwar ta taso Kurma da matarsa da ke barci a rumbu ta ce musu: “Ba ku ga babanka ba saboda ya yi bulagiro. Ga shi kuma lokacin gudu ya yi, sai ku kama hanya kafin su gane.”

    Ashe da ma ‘yan’uwan tuni suka zaci za a yi musu dabara ne, suka fice daga gidan suka tafi jiran Kurma da matarsa a bayan gari. Kurma da matarsa sun kama hanya za su gudu, sai wani da ya sanshi ya gaya masa cewa ‘yan’uwansa suna can a kan hanya suna jiran sa shi da matar su cinye su. Yana cikin wannan tsoro da damuwa, sai ga wata tsuntsuwa ta zo.

    Sai Kurma ya roƙe ta, ta ɗauki matarsa ta tsallakar da ita can gaba da inda ‘yan’uwansa suke fakonsu shi da matarsa. Nan take tsuntsuwa ta yarda, matarsa ta hau suka tashi sama. Shi kuma Kurma sai ya ɗauki ganga yana kiɗa har ya isa inda ‘yan’uwansa suke. Da ya isa sai ya fara waƙa.

    Su kuma sai suka tambaye shi matarsa; sai ya ce ya bar ta a gida. Da jin haka sai suka kama hanyar gida da gudu. Shi kuma da ya ga sun yi nisa, sai ya kama hanya ya yi ta gudu, har ya je ya sami matarsa suka yi tafiyarsu. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Bin iyaye bin Allah.
    • Tarbiya ce garkuwar kowane yaro.
    • Ceto daga Ubangiji yakan zo ne ta kowane hali.
    • Makusancinka na iya zama makashinka.
    • Zumunci maganin bala’i.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kudu da garin su Gizo da Koƙi akwai wata mace mai ’ya’ya mata su huɗu, waɗanda ubansu ɗaya. Suna nan zaune cikin jin daɗi, sai ciwo ya kama mijinta, watau uban yaran nan. Da ya ga kamar ba zai tashi ba, sai ya sa aka yi wa ’yan matan nan huɗu aure. Bayan kamar wata uku da aurar da su, sai ya cika.

    Ɗaya daga cikin ’ya’yan nan ta yi aure a garin da ba a barci; ta biyu ta yi aure a garin da ake tsinkar gauta da hanci da tsinkar kuɓewa da ƙirji; ta uku kuma ta yi aure a garin da ba a cin abinci, ba a kashi sai dai a sha romon nama; ta huɗun ta yi aure a garin da ba a kwana a gida sai a can sararin sama. Wata rana sai matar ta shirya za ta ziyarci ’ya’yanta.

    Sai ta ɗauki ƙwarya ta kama hanya sai garin ’yarta ta fari, watau garin da ba a barci. Da ta je gidan ’yarta, sai ’yar ta razana ta ce: “Inna me ya kawo ki garin nan da ba a yin barci?” Tun da tana son ganin ɗiyarta, sai ta ce mata: “Ai tun da babanku ya rasu ban sake barci ba.” Sai ’yar ta ce: “To shi ke nan.” Suka zauna ta yi mata abinci ta ci.

    Da dare ya yi sai suka kama hira a cikin ɗaki. Can sai uwar ta fara gyangyaɗi. Da ’yar ta ga haka, sai ta ce da gyatumarta: “Kada ki yi barci fa.” Sai ta juya suka cigaba da hirarsu da mijinta. Jiki da jini, can sai uwar ta kwanta ta kama barci. Da mijin ’yar ya lura surukarsa ta kwanta tana barci, sai ya fita ya tara mutane ya ce surukarsa ta rasu.

    Da gari ya waye, sai masu haƙa ƙabari suka tafi maƙabarta suka kama aiki. Aka shiga shirye-shiryen binne wannan matar. Data ji hayaniyar mutane, sai ta fito tana yi musu magana, tana cewa ita fa ba ta mutu ba, barci kurum ta yi. To su ba su san barci ba. Sai
    wani daga cikin mutanen da suka taru ya ce wa sauran da ke saurarenta: “Yaya kuke magana da fatalwa bayan kun san ta mutu?

    Mutum zai mutu ya dawo ne?” Wannan abu ya tsorata matar, saboda haka sai ta koma cikin ɗakin ’yarta; sai ’yarta ta ce: “To kin san na gaya miki ba a barci a nan garin; su ba su san barci ba.” Baƙuwar nan ta rasa yadda za ta yi. Idanu suka raina fata. Can dai wata dabara ta faɗo wa ’yar. Ta dubi uwar ta ce: “Zo in fitar da ke ta danga ki gudu, in ba haka ba za su binne ki da rai.”

    Sai ta ja ta suka bi ta bayan gida, ta buɗe mata hanya ta gudu ta nufi garinsu. Bayan kwana ɗaya da komawar matar nan gida, sai ta ce bari ta je garin ’yarta ta biyu, watau garin da ake tsinkar gauta da hanci kuma a tsinki kuɓewa da ƙirji. Sai ta kama hanya har ta isa garin. Da ta isa gidan ’yar, sai ’yar ta ce: “Inna me ya kawo ki nan?

    Kin sani fa a nan garin ba a cin abinci. Kowa sai dai ya tsinki kuɓewa da ƙirji, kuma ya tsinki gauta da hanci. Shi ne iyakar abinda mukan ci. Idan kuma ba ki tsinka ba, to kuwa ba za ki ci komai ba.” Da jin haka sai uwar ta ce: “Haba, ai mu ma a garinmu da ƙirji muke tsinkar kuɓewa, sai da na auri babanku na daina.” Sai ’yar ta ce: “To shi ke nan.”

    Da yamma ta yi duk sauran matan gida suka ɗunguma gona tsinkar kuɓewa tare da baƙuwar. Kowa ya kama yana tsinka, har suka ƙoshi. Amma baƙuwar nan ba ta tsinka ba, ƙirjinta ko ya dame ta da ƙaiƙayi. Haka ta kwana da yunwa. Washe-gari ma kowa ya tsinki kuɓewa da gauta da ƙirjinsa, amma ban da ita.

    Ta sake kwana da yunwa. Da ta ga ta kwana biyu ba ta ci komai ba, sai ta gaya wa ’yar za ta koma gida. Da ’yar ta ji haka, sai ta dubi uwar tace: “To, bari in raka ki.” Sai ta riƙe wa uwarta ƙwaryarta ta raka ta bayan gari, suka yi bankwana, kowa ya koma garin da yake. Da matar nan ta isa gida ta huta kwana ɗaya sai ta shirya ziyartar ’yarta ta uku, watau dai ba ta daddara ba.

    ’Yar kuwatanacan garin da ba a cin nama ne sai dai romo, domin su zubar danama suke yi idan sun dafa. Sai ta haɗa kayanta, ta kamahanyasai garin ’yarta ta uku. Da ta isa sai ’yar ta yi mamakin ganinta, kuma ta ce da ita, “Inna ba za ki iya zama a garin nan ba fa sabodaa nan ba a cin abinci, ba a yin kashi, kuma ba a cin nama sai dai romon naman.”

    To abin ka da wanda ya saba da gardama, sai uwar ta ce: “Haba, ai ni rabona da cin abinci tun sanda babanku ya mutu.” Da ta ji bayanin uwar sai ta ce: “To shi ke nan.” Sai suka zauna. Da lokacin cin abinci ya yi, sai ta ga ’yarta ta dafa nama mai yawa, ta tsiyaye romon, za ta zubar da naman, sai tace: “Haba ’yar nan ai kin gaji, bari in je in zubar miki da shi.” Da ta karɓi nama ta fita bayan gida sai ta zauna ta cinye shi duka.

    Bayan ta dawo sai ’yar ta tambaye ta: “Yaya na ga kin daɗe baki dawo ba?” Da uwar ta ji wannan tambaya sai ta ce: “Ai bayan gari na kai.” Sai ’yar ta ce: “To madalla, hakan ya yi.” Can cikin dare sai uwar ta tashi daga barci ta ce wa ’yar tana jin kashi. Sai ’yar ta ce mata: “Ki tuna fa na gaya miki ba a yin kashi a nan garin, shi ya sa ma ba mu da shadda a nan garin.”

    Da kashin ya matsanta wa uwar, sai ’yar ta ba ta tukunya ta cika ta da kashi; ’yar kuma ta ɓoye tukunyar kashin. Da gari ya waye sai kajin garin suka kama cara da kuka suna cewa: “Kukuruku, an yi kashi a garin nan.” Idan akuya ma za ta yi kuka sai ta ce: “Be, be, be, an yi kashi a garin nan.” Haka dai duk dabbobi suka dinga yin wannan fallasa a cikin kukansu.

    Da abin ya yi yawa sai Sarkin garin ya tara mutanen garinya ce: “Wane ne ya yi kashi a garin nan?” Kowa ya ce bai sani ba. Aka yi ta bincike, kowa yana cewa bai yi kashi ba, kuma ba su san wanda ya yi ba. Da Sarki ya ga magana tana nema ta yi tsawo, sai ya ce: “To za a yi al’adar da aka saba yadda duburar duk wanda ya yi kashin nan za ta riƙa waƙa, kowa ya ji a gari.”

    Sarki ya sa aka yi magani; nan take duburar matar nan ta fara waƙa. Da ’yar ta ji sai ta ce: “Inna zo in raka ki domin kada a sani mu ji kunya.” Nan dai a cikin gaggawa ta tattara kayanta, ta raka ta bakin gari suka yi ban kwana ta tafi bayanta na waƙa. Matar nan tana cikin tafiya a dajin da ke tsakanin garin da ta je da wanda za ta, sai ta haɗu da wani Bafulani yana kiwo; sai yace yana son abin nan da ke yin wannan waƙa mai daɗi haka.

    Sai tace: “Zan ba ka idan za ka ba ni shanu biyu.” Kamar da wasa sai ya amince da hakan. Ta ce masa ya yi kashi ya shafa mata, abin zai koma jikinsa. Sai ya ba ta shanu biyu, kuma ya yi kashi ya dangwala ya shafa mata. A nan take abin ya koma jikinsa, yana waƙa. Sai ya shiga daji da shanunsa yana murna.

    Ita kuwa ta kora shanunta biyu ta shiga gari, ta je gida ta ɗaure kayanta. Bayan kwana biyu sai matar nan ta shiga shirin zuwa wurin ɗaya ’yarta wadda a garin da take aure ake kwana a sama. Shi kenan ta ɗau hanya, tana isa garin ta zarce gidan auren ’yarta. Da ta ga uwarta ta yi murna, amma sai ta ce mata: “Sai dai fa mu a nan garin idan dare ya yi muna tashi sama mu kwana a can ne saboda mayu suna yawan zuwa nan.”

    Sai uwar ta ce: “Ai babu komai, zan yi tsalle in hau sama kamar yadda kowa zai yi.” A nan ne fa ’yar ta ce: “To yi tsallen mu gani.” Kamar da gaske, uwar ta fara gwadawa. Da ta ɗaga ƙafa sai ta faɗi, ta yi ta yi, har ta gaji, kuma ga shi dare ya yi. Tun da an riga an makaro, sai ’yar ta ce wa uwar: “Zan ɓoye ki a cikin ɗaki, amma kada ki yi magana ko da za ki ji ana ta buɗe-buɗe da bincike a ɗakin.

    Domin mayun ne ke neman mutanen da ke kwana a ƙasa su cinye.” Uwar ta amsa mata cewa ba za ta yi magana ba. Can matar tana kwance a ɗaki sai ta ji motsi da ɓuruntu. Sai ta manta da dokar da ’yar ta sa mata ta rashin magana, ta ce: “Wane nenan?” Kafin ta gama rufe baki mayun nan sun afka kanta, sun cinye ta. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Idan ka baƙunci gari ka tarar da mutan garin kowa da wutsiya to kai ma ka sami zangarniya ka saka, sai ka zauna lafiya.
    • Wanda bai ji bari ba, ya ji hoho.
    • Da muguwar rawa, gwamma ƙin tashi

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kusa da dajin aljannu wanda aka ce ya yi iyaka da bangon duniya, akwai wata mata mai ’ya’ya maza su bakwai. Ana nan, ana nan sai yaran suka girma, har dai suka isa aure. Da gyatumarsu ta ga sun isa aure, sai ta tara su ta ce: “Ya kamata a ce yanzu kun yi aure, tunda ga shi Allah ya sa duk kun girma, kowa ya mallaki hankalinsa.”

    Da suka ji haka, sai babban cikinsu ya ce wa uwar: “Za mu yi aure, amma muna so a sama mana ’yan mata bakwai waɗanda suke uwarsu ɗaya.” Sai babarsu ta ce: “Kash, amma ai duk garin nan babu irin ’yanmatan da kuke so, sai dai ku tlafi nema wani garin.”

    Sai suka bi maganar mahaifiyarsu, suka shirya suka kama hanya za su neman matan aure. Bayan ’yan bakwai sun bar gari sun kama hanya, sun yi tafiya mai nisa, sai suka haɗu da wata mata da ’yarta ɗaya suna noma. Da ta ga samari bakwai rigis, sai ta ɗaga kai ta dube su tace: “Sannunku samari.” Su kuwa suka amsa gaisuwarta a cikin ladabi.

    Sai ta tambaye su inda za su. Sai babbansu ya ce mata: “Za mu je neman matan aure ne.” Da ta ji haka sai ta ce: “To ga ’yata idan za ku aura.” Tare da ban girma sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “A a, muna neman ’yan mata bakwai ne waɗanda suke uwarsu ɗaya kamar mu.” Wannan bayani ya rufe mata baki, sai ta ce: “To, shi ke nan; ni dai
    ’yata ɗaya ce idan za ku karɓe ta.”

    Sai suka ce: “A a, mun gode.” To ashe wannan mata aljana ce ba su sani ba. Da suka yi nisa daga inda take, sai ta yi irin saurin aljannu ta je can gabansu a wata gonar da ’ya’ya mata biyu. Saboda suna da ladabi da girmama manya, a nan ma suka gaishe ta, ba tare da sun san ita ce ba, saboda ta sauya kama. Matar nan ta tambaye su labarinsu, suka faɗa mata tare da bayani a kan abin da suka fito nema.

    Sai ta nuna za ta ba su ’yanmatan nan biyu idan sun amince. A nan ma dai a cikin hikima suka yi mata bayanin cewa ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya suke nema. Suka wuce suka bar ta a wannan gonar. Da matar nan ta ga sun wuce, sai ta ɓata, ta je gaba ta ƙara sake kamanni. Ta shiga wata gonar tare da ’yan mata uku.

    Haka dai ta dinga yi musu har sai da suka kai biyar. Sai suka ce su fasai sun sami ’yan matan da su ma bakwai ne kamar su. Sai aljana ta sake ɓata, ta rikiɗa ta zama wata mata kyakkyawa mai ’ya’ya mata bakwai suna taya ta noma. Da samari bakwai suka zo za su wuce sai matar ta yi musu sallama. Da suka gaisa sai ta tambaye su inda za su.

    Kamar yadda suka saba yin bayani a baya, sai suka ce za su neman aure ne, to amma sai ’yan matan da zasu aura ɗin sun kai bakwai, kuma ’yan ciki ɗaya kamar su. Da jin haka sai ta ce wa babban cikinsu: “To tun da mun haɗu ni ma ina da ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya kamar ku, in kun yarda sai in haɗa ku.” Sai baki ɗaya suka amsa mata: “Yawwa; yanzu muka sami matan da za mu aura.”

    Daga nan sai matar nan ta kai su gidanta, ta sa ’yan matan suka yi wa samarin nan ruwa. Da suka ɗebo ruwa suka kawo, sai kowacce ta ba wanda za ta aura; amma fa ruwan ba ruwa ne na gaske ba, duk jini ne, in ban da na ɗan’auta; shi yarinyarsa ba ta kawo masa ruwan jini ba.

    Da ’yan matan suka tafi sai ɗan’autansu ya ce kada su sha ruwan da aka ba su saboda jini ne, ba ruwa ba. Da sauran suka ji haka, sai suka zubar, ya ba su nasa suka sha suka ƙoshi. Can kuma sai ’yan matan suka shiga dafa wa baƙinsu abinci. ’Yan mata shiɗa suka ɗebo naman mutane da uwar ta yi tanadi, suka shiga dafa wa samarinsu; amma ƙaramar cikinsu ta ɗan’auta, sai ta ɗebo naman shanu ta girka wa masoyinta ɗan’auta.

    Da suka dafa abinci suka kawo wa mazajensu, sai da aka zo cin abinci, ɗan’autansu ya ce su zubar da abincin domin da naman mutane a ciki. Da suka zubar sai ya kawo musu nasa suka ci, har suka ƙoshi. Da dare ya yi, sai aka nuna wa kowannensu ɗakinsa shi kaɗai. Amma ɗan’auta da amaryarsa sai suka shiga wata bukka.

    Can bayan duk sauran sun yi barci, sai surukarsu, watau aljana ta fara wasa wuƙarta domin ta riga ta yanke shawara idan dare ya yi za ta yanka su duka. Saboda ɗan’auta ya san abin da matar take son yi, sai ya zagaya ya shiga kowane ɗaki, yana cire wa mazan kayansu yana sa musu na mata, su kuma matan yana sanya musu kayan mazan.

    Da ya gama, ya koma ɗakinsa ya shirya ya kama tona rami har zuwa garinsu. Da ya gama sai ya kwanta yana sauraron matar nan ta dinga shiga ɗaki-ɗaki tana yanka ’ya’yanta ba tare da ta sani ba. Da ɗan’auta ya tabbatar matar ta gama yanke-yanken ta koma, sai ya fita ya tashi duk ’yan’uwansa don su gudu.

    Sai suka shiga ramin da ya tona suka tafi gida. Ita kuwa aljana da gari ya waye sai ta fara buga ƙofofin ’ya’yanta don su tashi, amma shiru. Da ta karairaya ƙofofin ta shiga ɗakunan, sai ta tarar ashe ’ya’yanta ne ta yanka gaba ɗaya. A nan take ta fara kuka. Da ta ɗan huce, sai ta ce sai ta yi maganin yaran nan.

    Sai ta rikiɗa ta zama goɗiya ta shiga garin ’yan bakwai. Da ta je daidai gidansu sai suka gan ta. Sai ɗan’auta ya ce a bar shi ya kama ta, sai babbansu ya ce: “Ai kai ne ƙarami don haka bai kamata ka kama goɗiyar nan ba.” Sai ya bari babbansu ya kama ta ya ɗaure ta cikin gidansu yana kiwonta, har ta yi ƙiba, ta yi kyau.

    Bayan wasu kwanaki sai ɗan’auta ya ce da yayansa: “Yau zan kai maka goɗiyarka rafi.” Sai ya ce: “To, na gode.” Sai ya kwance goɗiya ya kai rafi ya ɗaure a jikin bishiya; sai ya samo wata babbar sanda ya fara jibgar goɗiyar nan yana waƙa yana cewa: “Ba goɗiya ba ce, aljana ce.”

    Ya doke ta sosai har ta rame. Da ya koma gida da goɗiyar sai yayansa ya ga duk jikinta jina-jina, kuma ta rame. Ganin haka sai yayan nasa ya kama shi da faɗa. Sai ɗan’auta ya ce: “To shi ke nan, muna nan da kai za ka zo ka yi da-na-sani.” Washe-gari sai babban wan su ɗan’auta ya hau goɗiyar domin ya kai ta rafi shan ruwa.

    Amma da goɗiyar ta ga sun fita daga cikin gari, sai ta kama sukuwa kamar za ta tashi, ba ta tsaya ba sai a gidan aljanar da ta so yanka su. Tana isa ta zame, ya faɗo ƙasa, kuma ta rikiɗa ta koma siffarta ta aljana. Sai ta dube shi tace: “’Yan banza; ni kuka kashe wa ’ya’ya, to duk sai na cinye ku. Tashi ka jiƙa waccan tokar miyar don zan dafa ka da ita in an jima da daddare.”

    Sai ya tashi ya jiƙa tokar miya; sai aljana ta ce: “Zauna kusa da tokar don da ita zan dafa ka.” A can gida ba a ga yayan ɗan’auta ya dawo ba, sai ɗan’auta ya rikiɗa ya koma ɗan maraƙi ya je gidan aljana. Daga shiga sai ya nufi inda ɗan’uwansa yake zaune, ya ture tokar da ke gabansa.

    Da babban ya ga haka sai ya ce wa aljana: “Kin ga ɗan maraƙi ya zo ya zubar da ruwan tokar.” Sai aljana ta ce: “Maza ka kwashe ka kai can waje, ka dawo ka sake jiƙa wata.” Shi kuwa sai ya bi umarninta. Ya kori ɗan maraƙi waje, sai ya sake jiƙa toka ya zauna a gefe. Yana zaune sai ɗan maraƙi ya sake zuwaya zubar da ruwan tokar.

    Sai ya tashi ya kirawo aljana ya gaya mata cewa ɗan maraƙin nan ya sake zubar da ruwan tokar. Sai aljana ta ce: “To ka kora shi ka kai shi bakin gangaren can mai
    nisa.” Da ya kora ɗan maraƙi har suka yi nisa da gidan aljana, sai ga ɗan maraƙi ya koma ɗan’auta. Sai ya dubi yayansa ya ce: “Ai dama na gaya maka ka yi hankali da goɗiyar nan.”

    Ba dai tare da ɓata lokaci ba sai ya ce da yayansa su tafi gida. Nan da nan suka kama hanya. Can da aljana ta ga shiru, sai ta bi sawu, sai ta ga alama lallai sun gudu. Sai ta ce: “Zan yi maganin ɗan’auta.”A nan take aljana ta rikiɗa, ta zama kyakkyawar budurwa ta shiga garin su ’yan bakwai, tana tafiya har ta kai ƙofar gidansu. Da suka gan ta sai suka ce dukkansu kowa yana son ta, amma daga ƙarshe suka amince a bar wa yayansu ita.

    Suka bar masa, aka ɗaura musu aure. Da dare ya yi suna ɗaki da matarsa sai ya ga ta rikiɗa ta zama aljana; sai ta ce: “Kun ɗauka za ku tsira daga sharri na ne?” Kafin ya ma gane abin da yake ciki, sai ta yi farat ta ƙwaƙwale masa ido, ta tafi da shi. Da gari ya waye aka buga ƙofa, sai aka ji shiru. Ɗan’auta ne ya kira yayansu ya amsa, sai ya gayawa ƙannensa amarya ta ƙwaƙwale masa idanu.

    Ɗan’auta ya ce shi kenan, ya san abin da zai yi; ya kama hanya ya je bakin rafi ya cika cikinsa da ruwa, ya rikiɗa ya zama tsohuwa, ya yafa mayafi ya tafi gidan aljana. Da ya isa ya yi sallama, sai ta amsa. ’Yar tsohuwa ta shiga ta ce wa aljana ta ji an yi mata rasuwa shi ya sa ta zo yi mata gaisuwa, kuma ta ƙara ba ta haƙuri da rashin da ta yi.

    Da aljana ta ji jawabin tsohuwa, sai ta yi mata godiya, kuma tace: “To me zan ba ki ne tsaraba tun da kin zo yi mini ta’aziyya daga nesa?” Sai tsohuwa ta ce: “Haba babu komai, sai dai ina da wata matsala da ta dame ni.” Da aljana ta ji haka sai ta ce: “Wace irin matsala ce?” Sai tsohuwa ta shiga marairaita ta ce wai yau mijinta ya yi shekara da shekaru ba shi da ido, da yana gani ma da tare za su zo gaishe ta.

    Da ta ji wannan sai ta ce wa tsohuwa: “Haba ai babu komai; ina da wasu idanu da na ƙwaƙwalo na zo da su jiya. Sai ki ɗauka, idan kin je gida ki jiƙa su a rama ki sa masa su.”
    ’Yar tsohuwa ta yi godiya, ta ɗebi idanu ta kama hanya. Da ta fita waje sai ta rikiɗa, Ɗan’auta ya koma kamanninsa na farko ya ƙyalkyace da dariya.

    Ashe aljana ta gane shi ne ya zo; sai ta ji haushi ta ce: “Na san yadda zan yi da shi da ’yan’uwansa.” Da ɗan’auta ya je gida, sai ya samo rama ya jiƙa idanun, ya sanyawa yayansa, nan da nan ya fara gani. Ana nan sai wata rana ’yan bakwai suka tafi daji su yanko ciyawa. Da suka yanka, sai kowa ya ɗaure tasa, amma sai ɗan’auta ya ga wani babban maciji ya shiga ta yayansu.

    Sai kawai yace: “Yaya ka bar mini taka zan ɗauka, kai ka ɗauki tawa.” Sai yayan ya amince da maganar ɗan’auta. Sai ɗan’auta ya sami igiya ya ɗaure ciyawar yayan nan tamau, yadda macijin nan ba zai iya motsi ba. Ya yi haka ne domin ya san aljana ce ta zama maciji.

    Da kowa ya ɗauki ciyawarsa suka kama hanyar gida, can sun kusa da gari sai suka tarar an hura wuta tana ci ganga-ganga, abin ban tsoro. Sai ɗan’auta ya jefa ciyawarsa a cikin wutar. Da suka ga haka, sai ’yan’uwansa suka ce: “Me ya sa ka jefa ciyawar ka a cikin wuta?” Sai ya ce: “Ku tsaya za ku gani.” Can da wutar ta lafa, sai ya ɗauki kara ya tona ciyawarsa, sai suka ga macijin nan ya ƙone ƙurmus.

    Mamakin baiwar ɗan’auta ya kama ’yan’uwansa. Shi kuwa ba abin da ya dame shi; sai yace musu: “Mu tafi gida, daga yanzu ƙaryar aljanar nan ta ƙare.” Wannan ne ya sa a ko ina ake tsoron ’yan bakwai. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba kullum akan kwana a kan gado ba.
    • Yawan shekaru ba shi ne wayo ba, Allah na yin baiwarsa ga wanda ya so yaro ne shi ko babba.
    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata mayya a wani gari, tana zaune da mijinta, har ta sami rabo. Daga ƙarshe ta haifi ɗanta namiji aka sa masa suna Malgwi. To da man tun tana da cikinsa ubansa ya rasu, ya bar dokinsa, wanda yaron ya gada. Uwar ta kula da dokin har Malgwi ya girma, ya zama saurayi kyakkyawa.

    Wata rana sai wata ƙawar uwar Malgwi ta ziyarci gidansu. Sai ita da baƙuwa suka zauna a tsakar gida suna hira. Sai ƙawar tace da ita: “Ya kamata ki san yadda kika yi da ɗanki tun da ya girma ya kai a cinye shi.” Sai uwar ta ce: “E, ai ina shiri, kuma a daren yau zan gama da shi, na ga ya fara shige-shige.”

    Ashe Malgwi yana bakin ƙofar ɗaki yana jin duk abin da suke faɗa; sai ya fita waje ya sami wuri ya zauna, ya kama kukan zuci yana cewa ashe uwarsa mayya ce bai sani ba? Kuma ƙila ma ita ce ta cinye babansa, yanzu kuma za ta cinye shi. Nan dai ya yanke shawarar barin garin; sai ya je ya kwance dokin da ubansa ya mutu ya bari, ya ɗaura masa sirdi ya hau ya kama hanya, ya bar garin.

    Da uwar Malgwi ta fito daga ɗaki ta ga an kwance doki, sai ta fita tana tambaya ko an ga wanda ya kwance doki. Sai waɗanda suka gani suka gaya mata cewa ɗanta ne ya wuce a kan dokin, ya bar garin. Sai ta koma gida ta sa rigar maitarta, ta fito bin sawun Malgwi. Duk sanda ta yi taku ɗaya sai ta je kusa da shi, shi kuma sai ya ƙara zaburar doki, yana sulalewa yana waƙa yana cewa: “Dokin baba kai ni gari ba kusa ba.”

    Ita kuma uwar tana ba shi amsa tana cewa: “Ga ni nan Malgwi, ga ni nan ɗana.” Haka dai tana gudu ɗuwawunta biyu suna motsi suna waƙa suna cewa: “Ka tumbuɗe ka durje, Da ka faɗi bakin maza.” Ita kuma tana cewa: “Ga ni nan Malgwi, Ga ni nan dana.” Haka ya ci gaba da sukuwa a kan dokin nan.

    In sun haɗu da mutane sun tambaye shi abin da ya sa shi gudu haka sai yace:
    “Abin da ke bayana fi ƙarfin kowa, ku ba ni hanya.” Yana cikin wannan gudun ceton rai, sai wasu mutane suka sake tsai da shi, amma sai ya ƙi tsayawa har dai ya kai gaɓar wani babban gulbi; sai dokin ya tsaya.

    Da Malgwi ya ga dokin ya tsaya, sai ya fara waƙa yana cewa: “Dokin baba kai ni gari, ba kusa ba.” Da doki ya ji waƙa sai ya faɗa cikin ruwa yana ninƙaya har suka haye, kuma suka shiga cikin wani ƙungurmin daji wanda ke cike da aljannu da manyan namun daji. A nan ne fa shi da dokin suka yi cirko-cirko, suka kasa yin gaba, balle kuma baya.

    Da ƙurar hanya ta lafa, sai ga wasu manyan namun daji a tsugune suna kallon Malgwi da dokinsa. Sai suka tambaye shi labarin halin da yake ciki, sai ya yi musu bayani. Da suka ji bayaninsa, sai suka ba shi izini ya sami wuri a gindin wata bishiya da ke kusa ya zauna ya huta. Da ya ɗan zauna yana hutawa, sai namun dajin nan suka ce masa za su taimake shi.

    Ya ɗaure dokinsa, ya yanki ciyawa ya sa a gabansa, doki kuma ya fara ci. Can Malgwi ya fara hutawa, har da ɗan gyangyaɗin gajiya, sai ga uwarsa ta iso inda yake a guje, tana haki da waƙa. Sai ɗaya daga cikin namun dajin nan ya buɗe bakinsa, wanda ya fiƙofar gari girma. Ita kuwa idanunta sun rufe, ga shi ta doshi Malgwi gadan- gadan za ta yi masa rungumar mutuwa irin ta mayu, sai ta faɗa bakin babban naman dajin nan, ya haɗiye ta.

    Bayan ya haɗiye ta, sai ya sami ruwa ya sha, ya yi gyatsa kuma cikinsa ya ɗan ɗaga kaɗan, amma fa bai ƙoshi ba, saboda ya daɗe bai ci komai ba. Sai namun dajin suka dubi Malgwi suka ce masa: “Mun yi maka maganin mayyar nan. Idan ka ga dama sai ka kama hanya ka koma garinku.”

    Da Malgwi ya ji haka, sai ya yi musu godiya; ya kwance dokinsa, ya ɗaura masa sirdi, ya hau, ya haye ruwa, ya kama hanyar garinsu, bai tsaya ba har gida. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Makusancinka na iya zama makashinka:
    • Ana zaton wuta a maƙera, ashe tana masaƙa:
    • Mai rabon ganin baɗi, sai ya gani:
    • Ceto daga Ubangiji yakan zo ta kowane hali:
    • Zarmewa wajen kula da yaro takan janyo masa bala’i ta fuskar da ba a zata ba.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Awa Da Dawi

    Edita@rumasau-kallamu