Tag: yadda ake

  • Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Makaɗan Hausa sukan sadar da waƙoƙin da suka yi bisa maƙasudai ne daban-daban gwargwadon waɗanda aka yi domin su. Waɗannan wurare da ake yin sadawar sababbin waƙoƙin baka sun haɗa da:

    i) Gidajen al’umma na ɗaiɗaikun mutane kamar gidajen sarakuna da gidajen malamai da gidajen attajirai; da gidajen masu jarumta da sauran gidajen masu sana’a da kuma sauran gidaje na ɗaiɗaikun al’umma.

    ii) Wurare na bukukuwa; kamar bikin aure da bikin suna da bikin kalankuwa da bukukuwan sarauta na al’adar Hausawa da bukukuwan masu sana’o’i da bukukuwan nunin amfanin gona da bukukuwan murna da bukukuwan da akan shirya na musamman da sauransu;

    iii) Dandali na shirya wasannin yara; tun a musamman lokacin kiɗan kalangu na ‘yan mata da na asauwara da kuma kiɗan duma da makamantansu.

    iv) Wuraren farauta; a fagagen da ake farauta a cikin dazuzzuka akan yi wa mafarauta sababbin waƙoƙi; kuma ana sadar da su da waƙoƙin ne a lokacin farautar a cikin dajin farauta, musamman a yayin da alalmisali, farauta ta rincime; ana buga in buga.

    Waƙoƙin da Kassu Zurmi ya yi sababbi; na farauta ya rera su ne kuma ya sadar da su kai tsaye a fagen farauta.

    v) Wurin noma, haka abin yake wurin manoma, musamman a yayi na gayyar noma a wata gona; kamar a Gandun Sarki, ko a gonar wasu Sarakai, ko a gonakin taimakon sauran talakawa. Nan ake sadar da sababbin waƙoƙi ga manoma, musamman waɗanda suke da sarautun noma kamar; Sarkin Noma da Madakin Noma da Gojen Noma da Kayayen Noma da sauran jaruman noma da makamantansu;

    vi) Wurin wasanni; Wurin wasannin al’ada a ƙasar Hausa wuri ne da ake rera sababbin waƙoƙi, a kuma sadar da su ga waɗanda aka yi wa su da sauran jama’a masu sauraro.

    Wurin wasannin al’ada sun haɗa da:

    – Wasan Asauwara wadda ake yi a kowace ranar kasuwa ta gari. Ana yin wasan Asauwara a ranar cin kasuwa ta wani gari da yammaci ne, gab da kamar la’asar sakaliya wato kasuwa za ta watse. A wasan Asauwara ana yin waƙoƙi ne tsakanin matasa-‘yan maza da ‘yan mata ko zabiyi da kuma zabiya. Kuma ana yin wasan Baura da kiɗan Baura, a wannan lokaci ma ana rera waƙoƙi sababbi da zimmar sadar da su.

    – Wasan kokawa

    – Wasan dambe

    – Wasan Sharu: wanda ake yi a lokacin da Hausawa suka shaƙu da Fulani

    – Da sauran wasanni.

    Wurin wasannin al’adun Hausawa, wuri ne ma wanda ake sadar da waƙoƙin baka na Hausa.

    vii) Wuraren Tarukan Makarantu:

    A lokacin da Hausawa suka sadu da Turawa, musamman a zamanin mulkin mallaka; Turawa suka ƙagi makarantu ga Hausawa tun daga zamanin karatun manya har zuwa karatun yara; an kakkafa wa Hausawa makarantu na boko daban-daban.

    To a yanzu a waɗannan makarantu tun daga na boko da kuma na islamiyoyi da a masallatan addinin Musulunci; duka ana yin taruka mabambanta kamar:

    – Tarukan fitar ɗalibai.
    – Taruka na aikin makarantu, kamar tarukan gama makaranta wato Convocation a Jami’a.
    – Taruka na maulidi, kamar Maulidin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da na Shaihunai da na Mujahidai da na sauransu.
    – Tarukan ga-Fili-ga-mai-doki.
    – Taruka na Musamman.
    – Da sauransu.

    viii) Wurare na Musamman

    Akwai kuma wasu wurare da ake shirya taruka na musamman domin kawai a rera waƙoƙi sababbi; a sadar da su ga mutanen da aka yi wa su da sauran jama’a na musamman. A ire-iren wurare da muhallai na musamman waɗanda ake nema domin a sadar da waƙoƙi sababbi sukan ƙunshi;

    – Wuri wanda aka zagaye shi, kuma aka yi masa shuke-skuke na ciyayi da wasu hakukuwa masu ƙayatarwa; musamman masu ƙara ganin ido ko warware kwarkwatar ido;

    – Wuri da aka tanada a matsayi na Gadina;

    – Wurin da aka tanada a matsayi na utel-utel ko ɗakin taro na musamman a manyan garuruwa da birane;

    – Wurin da aka keɓe domin shaƙatawa, ko na masaukan baƙi;

    – da sauransu da yawa.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    Tatsuniyar Barewa Ta Auri Mutum

    Ga ta nan ga ta nan ku.

    Wata barewa ce, sai ta rikiɗa, ta zama mace kyakkyawa. Sai ta ɗauki ɗan kwatashinta ta ɗora a ka ta tafi tsakiyar karofi ta ajiye.

    Da ta ajiye, sai ta ce duk wanda ya jefa ‘yar tsakuwa ta buɗe kwatashin nan, shi ne mijinta. Sai wannan ya ɗauki tsakuwa ya jefa bai buɗe ba, wancan ya jefa tsakuwa bai buɗe ba.
    Sai aka sami wani ya jefa ‘yar tsakuwa, Ya buɗe, sai ta ce ta sami miji, shi za ta aura.

    Suka tafi garin ita yarinyar, wurin iyayenta za a ɗaura mata aure da wannan mutumin.
    Sannan aka ɗaura musu aure ta zo ta tare gidan mijin. Kullum ranar girkinta sai a ce ta je ta ciro kuɓewa a gonar mijin ta yi miya.

    Da ta je gonar sai ta yar da zanenta ta yi birgima a ƙasa ta zama barewa ta yi kiran ‘yan uwanta, ta yi waƙa ta ce:
    Cinkalkal, cinkalkal kalaya,
    Turmin ‘yan kale ya yi fure, ceɗiya.
    Tudu na korar tudu, Marina.
    Tudu na korar tudu da ƙaho.

    Ban da ƙanƙan.

    Sai ‘yan uwanta su zo su taru su ciccinye kuɓewa. Sa’annan in sun gama sai sun tafi gida.
    Ita kuma sai ta yi birgima ta komo mutum ta ɗauki zanenta ta ɗaura. Sai ta koma gida ta dinga cewa; ‘Ni da gangan aka tura ni. Ga shi nan ban samo komai ba.’

    To, ran nan sai mijinta ya bi ta gonar. Sai ya gan ta tana birgimar, sai ya ga ta rikiɗe ta zama barewa. Sai ya ga ta yi kiran ‘yan uwanta bareyi da waƙa. Bareyi suka taru a gonar jingim. Duk suka cinye kuɓewa. Suna cikin ci sai ya fasa su. Sai ya ga matarsa, ta gan shi.
    Ya komo gida.

    Sai ta ɗauko kuɓewar ta biyo shi. Ta tarar da shi a gida.

    Ya ce, ‘Wace ce?’
    Ta ce, ‘Ni ce’.
    Ya ce, ‘Ina za ki?.
    Ta ce, ‘Ɗaki za ni’.
    Ya ce, ‘A a, koma daji’.
    Sai ta ce ta ƙi. Sai ya biyo ta a guje ya kora ta daji.

    Daga nan ba ta sake dawowa ba.

    Shi ke nan. Ƙurunƙus.

    Domin karanta Tatsuniyar Gizo da Giwa  danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tarihin Malam Mahmud Manzo Arzai

    Tarihin Malam Mahmud Manzo Arzai

    An haifi Malam Mahmud ɗan Muhammad ɗan Mahmud dan Muhammad a Damagaran cikin Jamhuriyar Nijar. Malam Mahmud ya zo Kano a lokacin girma ya fara kama shi. Malam Mahmud ya taso a hannun mahaifinsa a inda ya karanci Alƙurani.

    Ya shahara da sada zumunci da yawan kyautatawa ga baƙo da ɗan gari. Malam Mahmud ya yi tafiye-tafiye na neman Alƙur’ani izuwa alƙaryu masu nisa irinsu Inkibalwa da tsangayar Kolorum. Don haka ma ya sadu da manyan malamai irinsu Gwani Ahmad da Malam Yahaya da Alaramma Malam Yusuf wanda ake yi wa laƙabi da Malamin Mali da gwani Mahmud halifan Gwani Dipchan (shugaban makaratan Ƙasar Hausa) inda ya naƙalci ilmin Alƙur’ani da Rasmu da Tajwidi.

    Malam bai gushe ba yana kutsawa cikin neman Alƙur’ani da fannoninsa, har sai da ya sauka birnin Kano. A lokacin da ya iso kuwa almajirai suka riƙa dandazo don su sha daga tafkin ilminsa. Abu ne mai wahala ƙwarai da gaske ƙididdige yawan almajiran Malam Mahmud Manzo Arzai.

    Kaɗan daga cikinsu sun haɗa da Malam Muhamud Danja Zuwo, da Malam Lawan Saleh da Malam Gali Adhama.

    Wannan makaranta ta Malam Manzo ba ta gushe ba tana wanzuwa a hannun zuriyarsa cikc da ɗaruruwan almajirai, lokacin da Malam Manzo ya rasu babban ɗansa Malam Muhummad Mahmud wanda aka fi sani Malam Usman shi ya jagorance ta tare da taimakon ‘yan uwansa Malam Muktari Manzo mai koyar da ilimin Tajwidi da Malam Laminu shi ne mai darasu sai Malam Mustafa da Malam Abba da Malam Sunusi da Malam Ibrahim.

    Tsokaci

    Makarantar Malam Manzo Arzai ta shahara da ladabtar da kangarrarun yara ta hanyar addu’o’i da yi musu tarbiyya da karatun Alƙur’ani da lazimta musu addinin. A inda ake sanya su a mari. Mutane kan taso gari da gari don kawo ‘ya’yansu. Da yawa wannan tsari na tarbiyyantarwa ya kan taimaka wajen gyara tarbiyyar kangagararru har sai ka ga sun wayi garisun kintsu.

    Wasu ma sun zama malamai, albarkacin addu’o’i da lazimta musu Sallah akan lokaci da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma

    Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma

    An haifi Malam Muhammad Barnoma ɗan Gwani Muktari a garin Misau. An ce bayan mahaifinsa Gwani Muktari ya yi hijira daga Barno shi ne ya kafa Masarautar Misau bisa tsantsar Shari’ar Musulunci a wancan lokacin.

    Malam Muhammad Barnoma ya taso a garin Misau cikin kulawar mahaifinsa, kuma ya yi karatun Alƙur’ani da sauran fannoni wurinsa. Mahaifinsa Gwani Muktari ya fita da shi daga ƙasa Misau har suka sauka a garin Kila cikin ƙasar Bauchi. Daga nan ne ya dawo Kano ya sauka wurin Mashahurin malamin ilmi Malam Mahmud Salga.

    A lokacin kuwa da Sarkin Gumel Nakuta ya nemi Malam Salga ya tura masa wani daga almajiransa don ya karantar da su AIƙur’ani da ilmi, sai ya umarci Malam Muhammad Barnoma da ya wakilce shi. Malam Barnoma ya kafa makaranta a Gumel ya kuma yaɗa ilmi har tsawon shekaru 60. Malam Barnoma ya haifi manyan ‘ya’yansa a Gumel. Da ga bisani ya dawo Kano ya cigaba da ba da karatu har ya rasu.

    Bayan rasuwar Sheikh Barnoma, ɗansa Malam Usman Barnoma ya cigaba da jagorantar wannan gida da makaranta.

    An haifi Malam Usman a garin Aikawa da ke Gumel a shekarar 1943. Ya haddace Alƙur’ani yana ɗan shekara goma sha huɗu, Malam Usman Barnoma ya yi karatu wurin Malam Sani Lukoro a Unguwar Gyaranya da ke Kanon Dabo.

    Malam Usman ya shahara da kyawawan halaye da yawan karamci, ga shi kuma ma’abocin bincike da nazari cikin littafan Musulunci. Saboda irin himmarsa an ce yana karanta izu arba’in a kowace rana. Manyan malamansa sun haɗa da Shehu Atiku da Malam AbdulMajid Salga da Malam Sani Mahmud. Manyan almajiransa kuwa sun haɗa da.

    – Dr. Muhammad Nuruddeen Musa
    – Dr. Abdullahi Saleh Pakistan
    – Malam Mahmud Barnoma
    – Malam Hamza Abdullahi

    Makarantarsa ta shahara da shigar da tsarin zamani cikin karantarwarta musamman ma sanya kayan makaranta da azuzuwa da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Alaramma Malam Aliyu Ɗan Kadawa (1868- 1998) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Fati Nijar danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Hanyoyin Farfaɗo Da Tsangayun Alƙur’ani

    Hanyoyin Farfaɗo Da Tsangayun Alƙur’ani

    Kamar yadda muka gani a sashe na ɗaya babi na ɗaya cewa, a da tsangayun alƙur’ani suna da gata da wasu haƙƙoƙi cikin baitul malin hukuma. A lokaci guda kuma malaman alƙur’ani suna samun ayyuka a hukuma.

    A lokaci guda kuma al’amarin da yaba su ƙima da yalwar rayuwar har suka bunƙasa suka yaɗu. Sai daga baya suka rasa gata a lokacin da bature ya zo ya dagula lissafin waɗannan tsare-tsare, ya kawo nasa ya dasa a matsayin kishiya bora da mowa. Ana nan har sai da tsangayu da malamansu da almajiransu suka zama abin tausayi marasa gata cikin al’umma.

    Malamai da wasu masu kishin addini, kai a waɗansu lokuta ma har ƙungiyoyin turawa kan nuna damuwarsu game da irin halin da tsangayun alƙur’ani da almajirai ke ciki. An gabatar da tataunawa da tarukan ƙarawa juna ilimi a wurare daban-daban cikin mabambantan lokuta, da niyyar tsamo wasu tsangayun ko almajirai daga irin matsin rayuwar da suka samu kansu aciki.

    Irin wannan yunƙuri ya haɗa da yunƙurin shirin bayar da ilimin firamare na duniya (UBE) da ƙungiyar haɓaka musulunci da ke Kano (IDN) da hukumar ilmantar da malamai (NTI) da asusun agazawa ilimi (ETF) da hukumar ilimin manya ta ƙasa (NMEC) da cibiyar binciken ilimi ta arewa da ke arewa house (NEPR) da jami’ar Ahmadu Bello zariya da wasu daga hukumomin majalisar ɗinkin duniya kamar su Hukumar kula da yara da ilmi da abinci ta Duniya (UNICEF da UNESCO).

    A matakin gwmnatoci kuwa an samu wani makamancin wannan hoɓɓasa daga wasu gwamnatocin jihohi na Arewa misali jigawa, Sokoto, Kebbi, Zamfara, Katsina da Bauchi.

    An kafa hukomomi a waɗannan jihohi don kyautata waɗannan makarantu, galibi da sunan Hukumar Ilimin Larabci da Addinin Muslunci (Arabic and Islamic Education Board). A Kano kuwa abin sai alasan barka.

    Duba ga irin yadda gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau ta rungumi makarantun Alƙur’ani da niyyar dawo musu da haƙƙoƙinsu a hukumance kamar yadda abin yake a tarihinmu. Don ƙarin haske sai a nemi ƙudirin gwamnatin Shekarau kan cibiyar ilimin addinin Musulunci “Action Plan” wadda aka ƙaddamar a ranar 23 ga watan Oktoba, 2003. Mai karatu zai iya fahimtar hanyoyin farfaɗo da tsangayu da raya su ta fuskoki biyu bisa matakai biyu cikin abin da ya gabata kamar haka:-

    1. Yunƙurin ƙungiyoyi da cibiyoyi masu zaman kansu.
    2. Yunƙurin wasu daga ciki gwamnatocin jihohin Arewa.

    Babbar matsalar mataki ko yunƙurin farko wanda ƙungiyoyin da na ambata a baya suka yi shi ne, mafi yawa sun tafi akan lallai sai an haɗe tsarin karantu tsangaya da ilimin zamani (integration).

    Wannan tunani yana da wuyar ɗabbaƙawa kuma yana da haɗari ga makomar karatun Alƙur’ani mai inganci irin na tsangaya.

    Kada mai karatu ya manta da cewa mafi yawan ƙungiyoyin gwamnatin tarayya da Turai suna kallon tsangaya a matsayin tushen bautar da yara ƙanana da wulaƙanta su (Child Abuse/Child Labour) wanda ya kamata a magance ta hanyar haɗe su da makarantun firamare na hukuma. Malaman Alƙur’ani kuwa a nasu ɓangaren su ba sa son sallama makarantarsu ɗungurungum ga wata hukuma.

    Irin wannan ra’ayi ne ya hana da yawansu haɗa fannonin ilmi Musulunci irin su Fiƙhu, Hadisi, da Tafsiri da karatun Alƙur’ani. Tunanin makaranta Alƙur’ani a tsarin tsangaya ya ginu bisa inkarin gwamnati da tsare-tsarenta. Saboda a ganinsu ta hanyar ta ne aka kawo karatun boko wanda turawa ‘yan mishan suka juyar da musulmi da yawa zuwan addini kirista, musammam ‘yan ƙabilar yarabawa.

    Wannan yasa da yawan makaranta yin ƙaura da almajiransu zamanin turawa don kada a tilasta musu shiga tsarin karatun boko. Baya ga wannan kuma, mu ɗauka an haɗe tsangayunmu na Alƙur’ani a tsarin koyon karatu da lissafi cikin ilimin firamare.

    Shin mene ne makomar irin fa’idojin da tsangaya kaɗai muke samu irin su baiwar rubutun alƙur’ani da ka da ingantacciyar tilawa? Yaya za mu yi da jama’armu musamman a karkara inda babu wadatattun makarantun boko kuma ba masu son sanya ‘ya’yansu a makarantun bokon?

    A ganina in har kundin tsarin mulki zai ba wa ‘yan ƙasa damar zaɓen tsarin rayuwarsu da abin bautarsu, to mai son karatun tsangaya ya fi cancantar a ba shi dukkan tallafi ya yi karatunsa cikin yanayi mai inganci ba tare da an tursasa shi kan abin da ba ya so ba.
    Su kuma gwamnatocin jihohin Arewa da suka nuna kishinsu ga wannan ɓangare na tsangaya sai mu ce sambarka.

    Amma akwai sauran aiki domin kuwa in har ana son farfaɗo da tsangayun Alƙur’ani da raya su dole ne a dawo musu da martabarsu ta hanyar:-

    1. Juyin-juya Hali a Ɓangaren Ilmi Jihohin Arewacin Najeriya:-

    Ma’anar wannan shi ne samar da wani ƙudirin siyasar ilmi a jihohin Musulmi da ke Arewacin Najeriya Wanda zai ayyana ilmin tsangaya a matsayi ɗaya da karatun boko, tare kuma da yin doka a majalisa ko kuma ta kowace hanya da ta dace don ɗorewar ƙudirin.

    2. Samar da daidaito ga Tsangayun Al-ƙur’ani Cikin Dukkan Haƙuƙuwan da Gwamnati ke ba wa Ilmin Zamani:-

    Babu shakka kowace irin damuwa muka nuna game da ingantuwar tsangayun Alƙur’ani da kyautatuwar rayuwar almajirai, hakan ba zai yi tasiri ba har sai tattallin arzikinsu ya bunƙasa. Ma’ana rayuwarsu ta samu gata tabbatacce maimakon gutsura musu ɗan wani abu da bai taka kara ya karya ba.

    Idan har za a daidaita tsangayu da sauran sassan ilmin zamani to dole gwamnati ta dubi dukkan fuskokin da take tallafar ilmin boko, tun daga albashin malamai da gina sababbin makarantu, da gyara waɗanda suka lallace da kuma irin ciyarwar da ta ke yi wa ‘yan makarantar kwana da irin kayan aikin da take ba su.

    Jimillar waɗannan kuɗaɗe su ya kamata a duba wajen ba wa tsangayu buƙatunsu na rayuwa. Wani abu mai ban sha’awa shi ne ma’abota tsangayu mutane ne da abin duniya bai shamakance idanuwansu ba. Matuƙar hukuma ta kula da matsuguninsu da abincinsu da ‘yar buƙatarsu ta yau da kullum, to kuwa za ka ga an magance wani kaso mafi girma daga matsalolinsu.

    Don haka, irin matakan da gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau ta ɗauka a Kano wani abin koyi ne ga dukkan gwamnatocin Arewa.

    Domin karanta cikakken bayani akan Matakan Farfaɗo Da Tsangayun Alƙur’ani Da Raya Su danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Zubin Tsangaya Yake danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai Alfarma 7th February 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai Alfarma 7th February 2025

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr. Abdullah Awwad

    Mai Fassara: Dr Usman Muhammad Ahmad

    Shugaban Shashi: Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

    Huɗubar Masallaci Mai Alfarma: Sheikh Dr. Abdullah Awwad 12/06/1446H

    HUƊUBA TA FARKO

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Masa, muna neman taimakonSa da gafararSa, kuma muna neman tsarinSa daga sharrin kawunammu da munanan ayyukammu, duk wanda Allah Ya shiryar, to, babu mai ɓatar da shi, kuma duk wanda Ya batar, to babu mai shiryar da shi.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa.

    (Ya ku waɗanda kuka ka yi Imani, ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kusa Musulmi)

    (Ya ku mutane, ku ji tsoron Ubangijinku, Wanda Ya halicce ku daga rai guda ɗaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma ya yaɗa maza da mata masu yawa daga gare su, kuma ku ji tsoron Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye yanke zumunci, lallai Allah Mai kula da ku ne)

    (Ya ku waɗanda kuka yi Imani, ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacce take daidai, Zai kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gafarta muku zunubbanku, kuma duk wanda ya yi ɗa’a ga Allah da ManzonSa, to haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)

    Bayan haka:

    Lallai mafi gaskiyar zance shi ne Littafin Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi sharrin lamura su ne ƙirƙirarru, kuma kowane ƙirƙirarren abu bidi’a ne, kuma kowace bidi’a ɓata ce.

    Bayan haka:

    Ya ku mutane! Lallai Allah Wanda hikimarSa ta ɗaukaka, Ya halicce ku ne domin ku bauta Masa, kuma Ya kallafa muku ayyukan da za ku iya, don haka, ku aikata su. Ku ji tsoron Allah ta hanyar bin umarninsa, da nisantar abin da ya hana da manyan zunubai, kuma ku yi la’akari da abin da ke cikin Alƙur’ani mai girma na ababen lura.

    Haƙiƙa Allah ya saukar da shi a gare ku don ku bi shi, domin lallai yana daga cikin mafi girman tanadi na samun tsira, saboda abin da yake ƙunshe da shi na farillai da mustahabbai da halacci da haramci da wa’azozi da jan kunne, to me ya sa zukata ba sa bin umarninsa, kuma ba sa barin abin da ya hana kuma ya tsawatar, kuma ba sa jin tsoron wanda ya san bayyane da boyayye cikin ayyukan bawa, da sirrikansa da kuma zahirinsa!

    Haƙiƙa gafala ta yi musu katutu, kuma sha’awace-sha’awacen zukata sun kautar da su daga lura da ababen suka saɓa musu, sai su ka ji daɗin ɗanɗanon ɓarnarsu, kuma suka jahilci ɗacin sakamako da za a musu a lokacin mutuwarsu, don haka, sai suka doge a kan saɓonsu, ba su ji tsoron yini da za a damƙe su ta ƙafafunsu da makwarkwarɗarsu ba.

    Ranar da za a ninka azaba ga wanda ya bar salla kuma ya tozarta ta, wanda ya yi sakaci game da lamarin zakka kuma ya ƙi ba da ita, wanda ya keta alfarmar watan Ramadana ya sha azumi a cikinsa, wanda ya jinkirta faralin Hajji alhalin yana da ikon yi kuma ba tare da wani uzuri ba.

    Ranar da za a shayar da mashayin giya da ruwan ɗiwa, a kwankwaɗa masa abin da zai ɗanɗani kaito da kuɗarsa da shi daga ruwan mugunyar ‘yan wuta. Ranar da za a sako harasan wuta ga mazinata da fajirai, kuma a dake su da bulalunta ta gabansu da bayansu.

    Maciyin riba kuma ya ci daga bishiyar zaƙƙum, lallai zina da cin riba ba su taɓa bayyana a cikin wasu mutane ba face sai sun sauko wa kansu da azabar Allah, muna neman tsarin Allah daga fushinsa da azabarsa, kuma azzalumai za su wanzu a cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa, da kuma inuwa ta turnuƙun hayaƙi.

    Ku saurara! Lallai duk wanda ya shagala da kansa, to, ba zai samu lokacin aibata waninsa ba, kuma duk wanda gazawarsa ta dame shi, to, idanuwansa za su makance daga ganin gazawar waninsa da abin da yake aikatawa, don haka, ku kame harsunanku daga keta mutuncin mutane- Allah ya muku rahama- saboda lallai Allah Yana kusa da harshen duk wani mai magana, kuma duk wanda ya keta mutuncin ɗan’uwansa kuma ya cutar da shi da magana ko da aiki, to, Allah Shi ne Abokin husumarsa.

    Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: ((Waɗanda suke cutar da muminai maza da muminai mata ba tare da sun yi laifi ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage da kuma zunubi bayyananne)).

    Babban malami Ibnu Usaimin Allah Ya masa rahama ya ce: “Wato suna jifansu da abin da ba su aikata ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage, wato ƙarya. Ƙage kuma, shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da bai tare da shi; don haka ne ma lokacin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi tambaya game da yi da wani, sai ya ce: “Shi ne ka ambaci ɗan’uwanka da abin da yake ƙi”. Ya ce: Ya Manzon Allah! Idan ɗan’uwana yana tare da abin da nake faɗi fa? Ya ce: “Idan yana tare da abin da kake faɗi, to haƙiƙa ka ci namansa, idan kuma ba ya ɗauke da shi, to, haƙiƙa ka masa ƙage”. Muslim ne ya rawaito.

    Sannan Allah Ya masa rahama ya cigaba da cewa: Kuma cutar da Mumini yana kasancewa da magana da kuma aiki, kuma hanyoyinsa na da yawa, lallai waɗanda suke cutar da muminai ba tare da sun yi laifin komai ba, to, haƙiƙa sun ɗauki nauyin ƙage wa kawunansu, kuma shi ne ƙarya, da kuma laifi bayyananne, shi ne uƙuba mai girma, Allah Ya amintar da mu”. A nan maganarsa ta ƙare, Allah Maɗaukakin Sarki Ya masa rahama kuma Ya saka masa da alheri bisa hidimarsa ga Musulunci da Musulmi.

    Ya Ubangijinmu, Ka sanya harsunanmu su kasance masu tsarki, zukatanmu su kasance masu ƙaunar muminai. Ya Ubangijinmu, Kada Ka sanya ƙiyayyar waɗanda suka yi imani a cikin zukatanmu. Ya Ubangijinmu, lallai Kai Mai tausayawa ne, Mai jinƙai.

    Ya Allah Ka tsare mu daga son zuciya, da kuma bin zuciya mai yawan umarni da mummuna, sannan Ka tsare mu daga shaiɗan la’ananne. Ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah! Kuma ku yi gaggawar yin amfani da damar da aka ba ku matuƙar tana nan. Ku ci gaba da ingantattun ayyukanku muddin ana karɓar su, kuma ku kakkaɓe kawunanku daga aikata laifi matuƙar igiyar rayuwa bata katse ba.

    Kuma ka rage buri, ya kai wanda ya ruɗu, domin rayuwa gajeriya ce. Ka tsarkake aikinka ga Allah domin Mai duba aikin Mai gani ne, kuma ka bar kusakuranka, domin lissafin mai tsauri ne. Kuma ka gyara laifukanka ta hanyar tuba, domin makoma ta yi maka daɗi.

    Imam Ahmad -Allah Ya yi masa rahama, da Imamul Bukhari Allah Ya yi masa rahama a cikin “Al-Adabul-Mufrad”, da kuma Albaihaƙi da isnadi mai kyau, sun rawaito daga Abdullahi bin Amr Allah ya yarda da su: cewa Annabi tsira da amincina Allah su tabbata a gare shi ya ce:

    (Ku yi jinƙai, za a jiƙanku, ku yi gafara, za a gafarta muku. Kaicon waɗanda suke zama kamar masakin magana. Bone ya tabbata ga masu dogewa da yin abin da suka sani cewa mummuna ne). Ma’anar “Masakin magana”: su ne waɗanda suke sauraron magana amma ba sa fahimtar ta, kuma ba sa aiki da ita.

    A’uzubillahi minash shaiɗanir rajim, bismillahir Rahmanir Rahim: (Sai ka yi bushara ga bayina () Su ne waɗanda suke sauraron magana kuma su bi mafi kyawun ta, Waɗannan ne waɗanda Allah ya shiryar, kuma waɗannan su ne ma’abota hankula).

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da kuma dukkan Musulmi, don haka, ku nemi gafaranSa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jinƙai.

    HUƊUBA TA BIYU

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo mai ɗorewa tare da wanzuwarSa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo da ba ya ƙarewa sai idan Ya nufa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo na dindindin, ba abin da zai samu wanda ya faɗe shi sai yardarSa. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, yabo dauwamame a kowane ƙiftawar ido da numfashin abu mai rai.

    Tsira da aminci su tabbata ga Annabinmu Muhammad da Alayensa da Sahabbansa da waɗanda suka bi shiriyarsa kuma suka yi kira irin kiransa.

    Bayan haka:

    Ku ji tsoron Allah ya ku Musulmi don ku rabauta, ku fargar da kawunanku daga gafala, kuma ku bi hanyar tsira, idan ba ku aikata haka ba kuka tasaya, to fa ku sani cewa shi ajali tafiya yake da ku, kyawawan ranaku na wucewa, ita mutuwa kuma tana farke a farfajiyarku, kuna nufin samun duniya Shi kuma Allah Yana nufin Lahira.

    Ya ku bayin Allah!

    Ku yawaita salati da sallama ga mafakar mutane a babbar matsaya ranar Alƙiyama, Annabinmu kuma mai cetonmu Muhammadu tsira da amincin Allah mai yawa su tabbata a gare shi da Alayensa.

    Ya Allah ka ƙara yarda da Halifofi shiryayyu da sauran Sahabbai gaba ɗaya, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako. Ya Allah Ka amfanar da mu da son su, kuma Ka tashe mu cikin tawagarsu, kuma kada Ka karkatar da mu daga bin tafarkinsu da hanyarsu ya Mafi karamcin masu karamci. Ya Allah! Ka ƙarfafa Musulunci da Musulmi, Ka ɗaukaka Kalmar gaskiya da Addini da falalarka.

    Ya Allah! Ka ƙarfafa Shugabanmu kuma Majiɓincin lamuranmu da gaskiya da yin daidai da dace, Ka yi riƙo da hannunshi ga ayyukan nagarta da taƙawa, Ka azurta shi da mashawarta nagari, Ka ɗaukaka AddininKa da kalmarKa da shi, Ka sanya shi ya zama mai taimako ne ga Musulunci da Musulmi, kuma Ka haɗa kan Musulmi da shi a kan gaskiya da shiriya ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah! Ka datar da shi da Yarimansa da ‘yanuwansa da mataimakansa zuwa gaskiya da shiriya da kuma duk abin da yake akwai gyara ga al’umma da ƙasa a cikinsa, Ka saka musu da alheri saboda kulawarsu da Masallatai biyu masu alfarma da daraja, da kuma duk abin da suke gabatarwa saboda cigaban Musulunci da Musulmi.

    Ya Allah! Ka datar da masu jagorancin Musulmi ga yin aiki da Littafinka da Sunnar Annabainka Muhammadu – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- Ka sanya su su zama rahama ga bayinKa Muminai, Ka haɗa kansu akan gaskiya ya Ubangijin talikai, Ka kuma datar da duk jagororin Musulmi ga duk abin da yake gyara ne ga Ƙasa da mutanen.

    Ya Allah! Ka saki labulan suturtawarka akan ƙasarmu da kuma dukkan ƙasashen Musulmi. Ya Allah! Muna kamun ƙafa da yardarKa kada Ka yi fushi da mu, kuma muna kamun ƙafa da amincinKa kada Ka yi mana uƙuba, kuma muna nema tsarinka daga azabarKa, ba mu iya kaiwa matuƙa wurin yaɓonKa kamar yadda Ka yabi kanKa.

    Ya Allah! kada ka yi mana azaba da munanan ayyukanmu, kuma kada Ka kama mu da abin da wawayen cikinmu suka aikata, Ka isar mana duk wani abin da ya dame mu, kuma Ka kasance Mai ƙarfafawa da ba da nasara a gare mu.

    Ya Allah! Lallai mu muna roƙon Ka farin ciki da zai lulluɓe zukatanmu da ‘yantuwar Masallacin Ƙudus daga hannu Yahudawa ‘yanƙwace, Ya Allah Ka jefe su da kibiyarKa da ba ta kure, Ka saukar musu da uƙubarKa mai tsanani, ya Majiɓincin masu rauni, ya Ma’boci ƙarfi mai tsanani! Ya Mai gudanar da giragizai! Ya Mai rusa rundunonin maƙiya! Ka saukar wa ‘yanta’adda azaba mafi tsanani, Ka sanya su abin ɗaukar izina ga masu hankali.

    Ya Allah! Muna roƙon Ka farin ciki saboda samun nasarar Musulmi a kan abokan gabansu azzalumai. Ya Allah! Lallai mu muna roƙon gafararKa, saboda lallai Kai Ka kasance Mai yawan gafara ne, don haka Ka saukar mana da ruwan sama mamako, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Ka saukar mana da ruwan sama, ya Allah! Lallai mu wata halitta ce cikin halittunKa, don haka kada Ka hana mu falalarKa saboda zunubanmu.

    Ya Allah! Ka karɓa daga gare mu lallai Kai Mai ji ne kuma Masani, kuma Ka karɓi tubarmu lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne Mai tsausayi. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Mazanni, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Danna nan don karanta Addu’ar Shiga Masallaci

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Kamannin Jariri

    Kamannin Jariri

    Sakamakon binciken kimiyya na asibiti bai tabbatar da cewa idan namiji ya riga mace yin inzali, ko kuma idan mace ta riga namiji fitar da ruwan saduwa, to, jaririn da suka haifa zai yi kamannin jiki irin na wanda ya riga kawowa ba.

    Abin da ilimin kimiyya na likitanci ya tabbatar shi ne gadon kamanni yana da alaƙa ne da ƙwayoyin halittar gado waɗanda ake kira “genes”. Duk lokacin da ma’aurata suka sadu kuma har juna biyu ya shiga, to kowanne daga cikin ma’auratan zai bai wa jaririn ƙwayoyin halittar gado guda biyu.

    Waɗannan ƙwayoyin halittar gadon ne suke ɗauke da umarnin yadda nau’in halittar jikin jaririn za ta kasance ta ɓangaren fuskarsa, launin idonsa, gashin jikinsa, launin jikinsa, muryarsa, tsawon jikinsa, da sauransu. To, amma akan samu wasu ƙwayoyin halittar gadon su zamo sun fi wasu karfi.

    Don haka, idan ƙwayoyin halittar gadon da namiji ya bai wa jaririn sun fi na macen ƙarfi, to, jaririn zai yi kama da mahaifinsa. Idan kuwa ƙwayoyin halittar gadon da mace ta bai wa jaririn sun fi na namijin karfi, to, jaririn zai yi kama da mahaifiyarsa.

    In kuma ƙarfinsu daidai da juna ne, to, zai ɗebo kamannin jikin mahaifinsa, ta wani ɓangaren, sa’annan ya ɗebo kamannin jikin mahaifiyarsa, ta ɗaya ɓangaren. Kuma ba saurin kawowa ne yake sanya ƙwayoyin halittar gadon miji su fi na mace ƙarfi ko na mace su fi na namiji ƙarfi ba. A a, wannan tsarin Allah SWT ne.

    Game da cewa ko akwai wani yanayin kwanciyar jima’i wacce take zaburar da samun juna biyu? Amsa ita ce babu wata kwanciyar da sakamakon binciken kimiyya na asibiti ya tabbatar da cewa lallai idan aka yi ta a lokacin jima’i, to, za a iya samun ciki.

    Sai dai, ana tsammanin cewa kwanciyar jima’i wacce namiji zai hau kan mace, alhalin ita kuma tana kwance a kan gadon bayanta (missionary style), ko kuma akasin shi wanda namiji zai kwanta akan gadon bayansa ita kuma mace tana samansa (cowgirl style), sun fi bayar da damar shiga can ciki (deeper penetration) afwan .

    Ita kuwa shigar can ciki za ta iya sanya ruwan maniyyin namiji ya shiga kusa da bakin mahaifa (cervix), kuma hakan zai taimaka wajen haɗuwar ‘ya’yan maniyyin namiji da ƙwan haihuwar mace, domin samun sauƙin ƙyanƙyashe ƙwan haihuwar.

    Amma ƙa’idar da ya kamata mu fahimta, ita ce cewa samun juna biyu ya danganta ne da saka ƙwan haihuwa (ovulation), lafiyar halittun haihuwar mace (female’s reproductive organs health), ingancin ‘ya’yan maniyyin namiji (sperm cells health), isasshen ruwan maniyyi (adequate sperm count), da kuma uwa-uba yin jima’i a daidai lokacin da mace take yin ovulation (timed intercourse).

    Members kuyi hakuri fa, karatun ne wani lokacin yana da ‘yar wahala.

    Danna nan don karanta Zinariyar Awa Ga Jariran Mu

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Wasu Daga Malaman Alƙur’ani A Jihar Zamfara

    Wasu Daga Malaman Alƙur’ani A Jihar Zamfara

    Irin malaman da suka ba da gudunmawa wajen yaɗa ilmin Alƙur’ani a Zamfara sun haɗa da:

    1. Malam Maharaz Yanfuɗo

    2. Malam Yusuf Godar

    3. Malam Lawwali na Zariya Bakin Kasuwa

    4. Malam Muhammad Bello

    5. Malam Bawa Sagai

    6. Liman Zaid Bakin Marina

    7. Malam Salih Niyas

    8. Malam Umar Maitela

    9. Malam Murtala Malamawa

    10. Abdullahi Mai Saƙa

    11. Malam Yahaya Yalwa

    • 12. Malam Abdullahi Shira Masa

    Domin karanta cikakken bayani akan Wasu Daga Malaman AIƙur’ani A Kebbi (Lardin Zuru) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Asalin Sunan Ƙabilar Ƙuraish danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Hadisai Na Ƙarya Da Raunana A Kan Ashura

    Hadisai Na Ƙarya Da Raunana A Kan Ashura

    Ƙirƙirar hadisai da yaɗa su yana ɗaya daga cikin manyan  hanyoyi da ‘yan bidi’a suke bi domin yaɗa bidi’o’insu, musamnan hadisai na falalar mutane lokuta da wurare.

    Ranar ashura da azuminta da yin kuka a ranar da shafa kan maraya da cika-ciki da sauransu, sun samu rabo mai tsoka a cikin hadisan ƙarya da raunana.

    Shaihin malami Abul Faraj Abdurrahman Ibnul Jauzi Rahimahullahi (A.H.S. 510 Y.M.S 597) yace: Waɗansu jahilai masu da’awar su ahlussunna ne, sun ƙirƙiro hadisai kan falalar ashura wai don su muzgunawa ‘yan shi’a, duka su biyun ba ruwan mu da su.

    Duk da cewa hadisin ya inganta cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi umarni da yin azumin ashura yace yana kankare zunubin shekara, amma ba su gamsu da wannan ba sai da suka ƙirƙiri hadisai masu ɗimbin yawa akan hakan.

    Ga wasu daga cikin waɗannan hadisan ƙarya:

    1-An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu); yace Haƙiƙa Allah ta’ala Ya wajabtawa banu Isra’ila azumin ranar ashura; shi ne ranar 10 ga watan Muharram, kuma wanda ya yi azumin wannan yini a cikin sa Allah zai yalwata masa wannan shekarar. Ku yi azumi a wannan ranar saboda a ranar Allah Ya karɓi tuban Annabi Adam (Alaihis Salam).

    A ranar Allah Ya ɗaukaka Annabi Idris (Alaihis Salam), a ranar; Allah ya kuɓutar da Annabi Ibrahim (Alaihis Salam) daga wuta; a ranar Annabi Nuhu (Alaihis Salam) ya fito daga jirgin ruwa; a ranar aka saukar da Attaura ga Annabi Musa (Alaihis Salam); a ranar aka fanshi Annabi Isma’il (Alaihis Salam) daga yanka.

    A ranar Allah Ya fitar da Annabi Yusuf (Alaihis Salam) daga kurkuku; a ranar Allah Ya dawowa da Annabi Yaaƙub (Alaihis Salam) ganinsa, a ranar Allah Ya yaye wa Annabi Ayuba (Alaihis Salam) bala’in da ya same shi. A ranar Allah Ya fitar da Annabi Yunusa (Alaihis Salam) daga cikin kifi; ita ce ranar da ruwa ya yi hanya a bani Isra’ila.

    A ranar Allah Ya gafartawa Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) zunubansa waɗanda suka gabata da waɗanda suka jinkirta. A ranar Annabi Musa (Alaihis Salam) ya ƙetare ruwa, a ranar Allah ya karɓi tuban mutanen Annabi Yunusa wanda ya yi azumi a wannan rana, za a kankare masa zunuban shekara arba ‘in.

    Ranar farko da Allah Ya halitta ita ce ashura ranar ashura aka fara yin ruwan sama. Rahamar da taf ara sauka a duniya ranar ashura ta sauka. Wanda ya yi azumi a wannan rana, kamar wanda ya yi azumin gaba ɗayan zamani ne. Shi ne azumin annabawa.

    Wanda ya raya daren ashura za a ba shi ladan ibadun halittun sammai bakwai. Wanda ya yi salla raka’a huɗu ya karanta Fatiha da ƙulhuwa ƙafa hamsin, Allah zai gafarta masa zunuban shekaru hamsin da suka wuce, da shekaru hamsin masu zuwa, za a gina masa minbari dubu na haske a cikin mala’iku.

    Wanda ya shayar da wani kurɓi ɗaya na ruwa, zai kasance kamar wanda bai taɓa yin saɓo ba. Wanda ya ciyar da miskinai a ranar har suka ƙoshi, zai ƙetare siraɗi kamar walƙiya. Wanda ya yi sadaka ranar ashura zai kasance kamar wanda bai taɓa hana mai bara ba.

    Wanda ya yi wanka ranar ashura ba zai ƙara yin rashin lafiya ha sai dai cutar ajali. Wanda ya sa kwalli ranar ashura, ba zai yi ciwon ido ba a wannan shekarar. Wanda ya shafa kan maraya a ranar ashura, za a ba shi ladan wanda ya kyautatawa gaba ɗayan marayun duniya. Wanda ya yi azumin ashura za a ba shi ladan mala’iku dubu goma, wanda ya yi azumi ranar ashura za a ba shi ladan aikin hajji da umra dubu. Wanda ya yi azumin ashura za a ba shi Ladan shahidai dubu. Wanda ya yi azumin ranar ashura za a rubuta masa ladan sammai bakwai.

    A ranar aka halicci sammai da ƙassai da duwatsu da koguna, da al’arshi; da alƙalami da lauhul Mahfuz da mala’ika Jibrilu. A ranar ashura aka ɗaga Annabi Isa (Alaihis Salam) zuwa sama, a ranar aka ba wa Annabi Sulaimam (Alaihis Salam) mulki.

    A ranar ashura za a yi tashin alƙiyama. Wanda ya gaishe da mara lafiya ranar ashura za a ba shi ladan wanda ya gaishe da marasa lafiyar duniya.

    Shaihin malami Ibnul Jauzi ya ce: “babu wani mai hankali da zai yi kokwanto kan cewa wannan hadisi ƙarya ne. Kuma wanda ya ƙirƙiro shi ya tonawa kansa asiri inda ya ce; ranar ashura ita ce ranar farko da Allah ya halitta, alhali kwanaki tara ne suke gabatar ranar ashura, to su kuma yaushe aka halicce su? Kuma wai a ranar aka halicci sama da ƙasa da duwatsu ranar Juma’a Alhali wannan ya saɓawa sahihin hadisi.

    Sannan ga lada mai yawa wanda ya saɓawa ƙa’i’dojin shari’a, ya ya za a yi daga azumin rana ɗaya kawai a ba wa mutum ladan hajji da umra da shahidai dubu.

    2- A wani hadisin na ƙarya an ce wai a ranar ashura aka halicci Annabi Adam (Alaihis Salam); aka haifi Annabi lbrahim (Alaihis Salam); aka haifi Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wa Sallam)! Kuma wai a ranar Allah Ya dai-daita a bisa al-arshi; kuma wai wanda ya bai wa mai azumin ashura abin buɗa baki; za a ba shi ladan wanda ya ciyar da gaba ɗayan al’ummar Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Kuka Ranar Ashura danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Watan Muharram danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Nasiha A Kan Mata

    Nasiha A Kan Mata

    MATA 10 WAƊANDA  ALLAH YA TSINE MUSU: –

    ﺍﻟﻮﺍﺷﻤﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺷﻤﺎﺕ
    1. Mata masu tsaga fuskokinsu. –

    ﺍﻟﻨﺎﻣﺼﺎﺕ ﻭﺍﻟﻤﺘﻨﺼﻤﺎﺕ

    2. Mata masu aske gashin gira. –

    ﺍﻟﻤﺘﻔﻠﺠﺎﺕ
    3. Mata masu kankare hakori (wushirya). –

    ﺍﻟﻮﺍﺻﻠﺔ ﻭﺍﻟﻤﺴﺘﻮﺻﻠﺔ
    4. Mai ‘karin gashi da wadda ake ƙara mata gashi. –

    ﺍﻟﺘﻲ ﺳﺨﻂ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺯﻭﺟﻬﺎ
    5.Matar da mijinta ya yi fushi da ita. –

    ﺍﻟﻤﺘﺸﺒﻬﺎﺕ ﺑﺎﻟﺮﺟﺎﻝ
    6. Mata masu shigar maza.

    ﺯﻭﺍﺭﺍﺕ ﺍﻟﻘﺒﻮﺭ
    7. Mata masu yawan ziyartar kabur-bura (maƙabarta).

    – ﺍﻟﻨﺎﺋﺤﺎﺕ
    8. Mata masu kururuwa akan mamaci. –

    ﺍﻟﻤﺤﻠﻞ ﻟﻪ
    9. Mata masu auren kashe wuta. –

    ﻛﺎﺳﻴﺎﺕ ﻋﺎﺭﻳﺎﺕ ﻣﺘﺒﺮﺟﺎﺕ
    10. Mata masu bayyana tsiraicinsu.

    Ka da ku manta TSINUWA ita ce nisanta daga rahamar Allah!
    ﻗﺎﻝ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ” ﻳﺎﻣﻌﺸﺮ ﺍﻟﻨﺴﺎﺀ ﺗﺼﺪﻗﻦﻭﺃﻛﺜﺮﻥ ﻣﻦ ﺍﻹﺳﺘﻐﻔﺎﺭﻓﺈﻧﻲﺭﺃﻳﺘﻜﻦ ﺃﻛﺜﺮ ﺃﻫﻞ ﺍﻟﻨﺎﺭ ” ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ
    Manzon Allah (SAW) ya ce: ‘Yaku taron mata! ku yi sadaƙa, kuma ku yawaita neman gafara (Istigifari) Allah ya gafarta Mana.

    Danna nan don karanta Abin Da Ya Kamata Mu Sani

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu