Tag: yadda ake

  • Makaɗi a Sarrafa Harshen Waƙa

    Makaɗi a Sarrafa Harshen Waƙa

    Kamar yadda aka yi bayani a baya, makaɗi yana amfani da gurbin furuci na gaɓoɓi a cikin kalmomi da jimloli ya samar da zubin waƙa.

    Ta haka makaɗi yake sarrafa harshe, ya harhaɗa ƙwayoyin sauti da amon kiɗa, ya saƙa saɗaru cikin ɗiya, ya rera wa masu ji da sauraro saƙonni masu ɗaga hankali, masu cika fuska, masu daɗi, masu garɗi masu shaguɓe da baƙar magana, masu fallasa muruwa da soke daraja, masu barkwanci, masu tumasanci, masu nuna kasawa, masu ƙasƙantawa da sauransu waɗanda kuma suke yi domin manufofi mabambanta.

    A wajen ɗorawa da tafiyar da harshen waƙa, makaɗan baka na Hausa suna bin hanyoyi iri-iri waɗanda muhimmai daga cikinsu suka haɗa da:

    4.1 Harshe na Nuna Hikima

    Hikima a harshe ta shafi iya magana bisa dacewa da manufa ba tare da tsawaitawa ba. Hikima kuma takan danganci ƙarfin ƙwaƙwalwa ko ƙarfin basira wajen gina zance mai ma’ana tare da ayyana manufa daga mutum ɗaya-ɗaya ko al’umma. A wani bi ma manufar hikima ba takan bayyana a sarari ba, takan zama a sakaye ta yadda a kullum za a dinga ƙoƙarin fahimta ko ganowa.

    Hikima kuma takan zama yin wani abu wanda zai birge mutane (CNHN, 2006: 200). Yahya (2012: 238) shi kuma yana ganin hikima wadda ta jiɓinta da harshe takan shafi hanya ko matsalolin rayuwa ta bayyana su cikin zaɓen kalmomi da za su ɗora a kan zance mai armashi.

    Makaɗan Hausa sukan yi amfani da harshe mai hikima domin sakaya zance ko su kaifafa tunani ko su zurfafa tunani ko su taƙaita ma’ana ko su saka galmi a zance ko su kawar da gwangwani ko su saka gwangwani ko su yi barkwanci ko su dagule tunani ko su ƙawata rai ko su saka jin daɗi ka su burkuta zuciya ko su tayar da hankali da sauransu.

    Sau da yawa kuma makaɗan sukan saka wasu maganganu na hikima ko azancin harshen Hausa kamar karin magana da baƙar magana da ba’a da shaguɓe da zambo da habaici da kirari da makamantansu waɗanda makaɗan suke ƙawatawa tare da taƙaita tunaninsu a waƙoƙinsu.

    Haka kuma makaɗa sukan yi amfani da dabaru na jan hankali waɗanda suke raɗe da hikima cikin kwatantawa da ƙarfafawa da jaddadawa da shirɓacen kalmomi ko na ma’anoni duka a mabambantan zubi na ɗiyan waƙoƙinsu. A wannan ɓangare, makaɗan sukan yi kamantawa da siffantawa da jinsintarwa da alamtarwa da kinaya da gamin bautar kalmomi da jaddadar ƙarfafawa da zubi mai jan rai da baubawan burmi da sauransu (Ɗangambo, 2007: 43-54).

    Misali, idan aka dubi waƙar Shata ta ‘Sani Audi’ da ta ‘Habu na Habu’ da ta ‘Ummaru ɗan Ɗanduna na Gwandu’, za a ga Shata ya sarrafa hikimomin harshe iri-iri cikin mabambantan manufofi.

    Tabbas harshe na nuna hikima a wajen ciro kalmomi na gwaninta da kwatance na ayyana wani yanayi ko siffa ko hali za a iya ganin misalin haka a wannan ɗa na waƙar ‘Gwabron giwa uban Galadima ɗan Sambo, ginshimi, Ginshiƙan Amadu na Maigandi kai a uban Zagi’:

    Jagora: Ɗiyan Alibawa ku hanƙure,
    ‘Y/Amshi: Don Allah ya yo uban zagi, x2
    : Domin kura ta wuce,
    : Ana ɓacin laka kamar ita,
    Jagora: Domin,
    ‘Y/Amshi: Kura ta wuce, ana ɓacin laka kama ita.
    Jagora: Ko jiya na iske gamdayaƙi da tuji,
    : Sun iske jinjimi,
    : To sun ko mirɗa gardama,
    : Sun iske su bubuƙuwa ruwa,

    ‘Y/Amshi: Dannan ni kau ina gaton gaɓa,
    : Sai niƙ ƙwala gaisuwa,
    : Su ko sun daƙile ni duk,
    : Ni ko niƙ ƙara gaisuwa,
    : Dannan gurbin da a cikin gurbi,
    : ya amsa gaisuwa.
    Jagora: Dannan sai jinjimi da yas sullata,
    : Yas suntule su dut,
    ‘Y/Amshi: Shi ko tuji da ad da girman baki,
    : Yak kwashe jinjimi,
    : Dannan bubuƙuwa da tur rura,
    : Tag gangame su dut,
    : Rannan nis san duniyag ga,
    : Komina ne wani mayin wani,
    Jagora: Rannan,
    ‘Y/Amshi: Nis san duniyag ga
    : Komina ne wani mayin wani.
    (Gusau, 2009:145)

    4.2 Harshe na Nuna Fasaha da Nagarta

    A Ƙamusun Hausa an bayyana fasaha ita ce gwaninta ko ƙwarewa (CNHN, 2006:136). Ita kuma kalmar nagarta tana nufin kyawun abu ko ingancinsa (CNHN, 2006: 355).

    Makaɗan baka na Hausa sukan yi amfani da harshe mai nuna fasaha ta fito da gwanintar abu ko ƙwarewar wani abu kan wani ko kuma harshe mai fitar da nagarta a kan kyawo ko inganci na wani abu. Yanayin harshe na nuna nagartar abubuwa a rayuwa ya mamaye zubi na waƙoƙin baka na Hausa har ma wasu daga cikin makaɗan sukan bayyana nagarta da zubi na fasaha na waƙoƙinsu.

    Bawa Namiji Jega a wani ɗan waƙa ya tabbatar da fasahae harshe ita ce ke gaba, mai yin jagoranci a wajen shiryawa da rera waƙa mai ma’ana, mai garɗi.

    Dubin abin da yake faɗa:

    Jagira: Kalangu na da daɗi,
    : In ga fasaha ta yi.
    ‘Y/Amshi: Shalla Barayar Kada,
    : Fadama da sanyi take.
    (Bawa Namiji Jega: Waƙar ‘Shalla Barayar Kada’)

    Ibrahim Narambaɗa ya nuna fasaha tana daga cikin hanyoyin sarrafa harshe da ke nuna darajar makaɗi a fagen waƙa. Yana cewa:

    Jagora: Ai ba a gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi mƙamina ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi zalaƙata ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi fusahata ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Ƙaryab banza,
    : Yaro bai kai inda Narambaɗa,
    : Mai tabarukun Sarki,
    : Gogarman Tudu jikan Sanda,
    : Maza su ji tsoron ɗan mai Hausa.
    (Gusau, 2003: 74).

    Fasaha da nagartar harshe sun bayyana a zubin wannan ɗa na waƙar ‘Abin duniya tahowa na’:

    Jagora: Na ji an ce a daina ma al’ada,
    : Al’ada tana nan tana aiki,
    : Karatun mutum bai wuce salla,
    : Dole sai an yi Alhamdu Lillahi,
    : To, ashe ko kana nan ga al’ada,
    : Kowaɗ ɗauki kayan da bai ima,
    : Bawa tilas ya dawo ya yasshe su,
    : Abin duniya mai tahowa na,
    : Ran da duk ya wuce sai ga labari,
    : Sai ga labarin nan a tashe shi,
    : Wane ai yayi irin tashi.

    Jagora: Rigimar mutum dut ta rai nai ta,
    : Ran da dut babu rai tashi ta ƙare,
    : Kur’ani babu gamtsi ciki,
    : To Hadisi da ko ba a ruwaito ba,
    : Abin ga ko ko zari na mu tanye ku,
    : Abin duniya mai tahowa na,
    : Ran da duk ya wuce sai ga labari,
    : Sai ga labarin nan a tashe shi,
    : Wane ai yayi irin tashi.
    (Bawa Namiji Jega: Waƙar ‘Abin Duniya’)

    Daga cikin waƙoƙin da makaɗan Hausa suka aiwatar masu ɗauke da harshe na fasaha da nuna nagarta akwai waƙar ‘Ɗan’adam’ da waƙar ‘Aiki duka aiki ne’ da waƙar ‘Tica uban karatu’ na Ɗanmaraya Jos da waƙar ‘Mai Martaba ɗan Bayero’ da waƙar ‘Kano garin saye da sayarwa’ da waƙar ‘Na ɗauki angara na saƙala’ na Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa da makamantansu.

    4.3 Harshe na Nuna Yanayi

    A luggance kalmar yanayi tana iya zama hali irin wanda ake ciki, kamar damina ko sanyi ko zafi ko bazara da sauransu (CNHN, 2006:478). A ma’ana ta fannu, yanayi yakan nufi bayyana halayyar abu ko halin aukuwar abubuwa ko nuna kamanni na abubuwa (Gusau, 2008:463).

    Sau da yawa, makaɗan Hausa sukan zaɓo kalmomi su sarrafa su a waƙa su kuma dace da halayyar aukuwar abubuwa da wuri da lokaci da fasalin abu. A waƙar ‘Haji Garban Bichi ɗan Shehu’, Shata yana gaya wa Alhaji Garban Bichi game da harkokinsa na ciniki cewa:

    Jagora: kaka ta matso uban Nura,
    : Gyaɗa ta fara jar fata,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.

    Jagora: Auduga ta fara kitse Garba,
    : Gyaɗa ta fara jar fata,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.

    Jagora: Gabas riƙa yamma ta kama,
    : Gusun riƙa arewa ta samu,
    : Baba gabas riƙa na yamma sun samu,
    : Gusun riqa arewa ta kama,
    :Kaka ta yi uban nura,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.
    (Gusau, 2009:340-341)

    4.4 Harshe na Gwagwarmaya

    A wata ma’ana an nuna gwagwarmaya tana nufin yin fama ko karawa da wani (CNHN, 2006: 180). Wata ma’ana ta gwagwarmaya takan ƙunshi bijirereniya ko fanɗarewa ko kangara. A gwagwarmaya akan ƙarfafa hanyoyin ƙwatar rayuwa kamar neman abinci ko kiyaye haƙƙi ko neman waraka daga wata cuta ta bayyane ko ta ɓoye ko kishin ƙasa da al’adu ko kishin addini ko makamantan waɗannan hanyoyi.

    Wasu makaɗan Hausa sukan shirya waƙoƙi bisa harshe na gwagwarmaya da ke neman daidaito a rayuwar al’umma. Wasu daga cikin waƙoƙin baka waɗanda aka shirya su ta harshen gwagwarmaya sun haɗa da waƙar ‘Buɗaɗɗiyar Wasiƙa’ da ta ‘Raba Gardama Ɗansani’ da ta ‘Alƙalami ya zarce takobi’ da waƙar ‘Jami’a Gidan ban Kashi’ 1-3 na Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa.

    Akwai waƙar ‘Shegiyar uwa mai kashe ‘ya’yanta PDP’ ta Haruna Aliyu Ningi da Waƙar ‘Haɗa kan Nijeriya’ ta Musa Ɗanba’u da waƙar ‘Babbar Ƙasar Shehu Ɗanfodiyo’ ta Alhaji Mamman Sarkin Taushin Katsina da waƙar ‘Haɗa kan Nijeriya’ ta Ɗanmaraya Jos da waƙar ‘Allah rayan jihar Katsina’ da ta ‘Muriki Abincinmu’ na Gargajiya na Alhaji Mamman Shata Katsina da makamantansu.

    4.5 Harshe na Faɗakarwa

    Kalmar faɗakarwa tana nufin faɗakarwa ko luraswa ko yin nuni ko ishara domin a lura. Kalma ce wadda take daga faɗaka wato farka ko lura ko kula (CNHN, 2006:129). Maganar Hikima wadda Hausawa suke cewa, ‘nuni cikin nishaɗi’ tana nufin yin faɗakarwa cikin wata siga ta raha ta amfani da harshe mai karsashi, mai daɗin ji, mai motsa rai.

    A faɗakarwa ana tunatar da mutum ne a kan waɗansu al’amuran rayuwa waɗanda suke yi masa tambihi ya aiwatar da su ko kuma ya guje musu. Yawanci a faɗakarwa akan ƙara tunasarwa ne, ko a lura da wasu abubuwa, ko a janyo hankali zuwa gare su (Auta, 2008:75-76).

    A harshen waƙa makaɗan Hausa sukan yi faɗakarwa a kan wasu abubuwa na al’umma domin su tunashe su, su lurar da su ta amfani da kalmomi na nasiha da wayar da kai da jawo hankali, musamman akan yin aure da neman aure da zaman aure da zawarci da haƙƙoƙin iyaye da na ‘ya’ya da yaran gida da faɗakar da matakan zamantakewa a gida da unguwa da gari da ƙasa da tuni kan matsayi da halayen sababbin abubuwa masu faruwa a rayuwar al’umma da sauran abubuwa na zamantakayya.

    Akwai waƙoƙin baka da yawa matuƙa a kan harshen faɗakarwa, kuma har wa yau makaɗa na ta aiwatar da su. Misalan waƙoƙin harshen faxakarwa sun haxa da waqar ‘Jawabin Aure’ da waqar Kwalara’ da waƙar ‘Gulmawuya’ na Ɗanmaraya Jos da waƙar ”Don salla da Salatil-Fati’ da waƙar ‘Noma aikin ‘Yan’arewa’ na Alhaji Mamman Shata da waƙar ‘Cutar Taɓin Hankali’ da waƙar;’Irin Ginin Sakarkari’ na Alan Waƙa da waƙar ‘Naira da Kwabo Sabon Kuɗi Haruna Uji da sauransu.

    4.6 Harshe na Nuna Alhini

    Kalmar alhini tana nuni a kan juyayi ko tausayawa a kan wani rashi na mutuwa (CNHN, 2006:12). Harshen alhini, harshe ne wanda ake ɗura wa kalmomi na yin ta’aziyya tare da sanyaya wa mutum da aka yi wa rashi tare da ba shi haƙuri da yin addu’a.

    Makaɗan Hausa sukan yi alhinin mutuwa a zubin waƙoƙinsu, musamman ma waƙoƙin turken ta’aziyya. Tubalan ginin harshen alhini ya ƙunshi kalmomi na tausayawa da juyayi da nuna jimami da addu’a da ba da haƙuri da kalmomin sambarka a kan halayen mai mutuwa ko kalmomi masu tuna ayyukan da ya yi kyawawa, ayyuka na taimako, ayyuka na inganta rayuwa da sauransu. Misalan waƙoƙi na harshen alhini sun hada da waƙar ‘Allah jiƙan Ciroman Gwambe’ ta Mamman Shata da waƙar ‘Mutuwa ba ki da sabo’ ta Abdussalam, Shatan Nijar da waƙar ‘Ɗamarar ko ta Kwana’ ta Alan Waƙa da sauransu.

    Dubi abin da Shata ya faɗa a harshen ta’aziyya cikin alhini:

    Jagora: Kowa yam mutu bai sauri ba,
    : Mu da muke nan ba mu daɗe ba,
    : Sai mun zo Ciroman Gwambe.
    ‘Y/Amshi: Allah jiƙan Ciroman Gwambe.

    A wani ɗa Shata yana cewa:
    Jagora: Ni me zance ma Sarkin Gwambe,
    : Sarkin Gwambe ya yi rashi,
    : Haka ni ma Mammalo mai ganga,
    ‘Y/Amshi: Allah jiƙan Ciroman Gwambe.
    (HBTKA, 2003:32&38).

    4.7 Harshe na Sanya Sambarka

    Sambarka, kalma ce wadda ake amfani da ita don nuna godiya ko yabo ko murna, takan ɗauki ma’anar ‘Allah ya sa albarka. Haka kuma takan nufi tubarkalla ko madalla ko sanya albarka (CNHN, 2006:386).

    Waƙoƙin Hausa suna cike da harshe cikin kalmomi masu yabo ko yabau ko bege, kalmomi na nuna sambarka, kalmomi masu saka jin daɗi, kalmomi na ayyana soyayya ko ƙauna, kalmomi masu nuna yanayi na farin ciki ko sakin fuska ko sakin jiki ko farar zuciya ta yin magana kwakkyawa, ta baza alheri, ta baza kyauta, ko nuna hannun baiwa da sauran maganganu masu saka wa jiki annashuwa, ita kuma zuciya ta faranta har a wani lokaci ta ɗimauta, idanu su dinga zubar da hawaye domin daɗi.

    Harshe mai saka tsima ta sambarka ya ƙarfafa a waƙoƙin baka na Hausa waɗanda ake yi wa masoya da waɗanda ake ƙauna kamar malamai da sarakuna da attajirai da iyaye, maza da mata, da sauran mutane masu ayyukan bajinta, masu ɗaukaka darajar al’ummar Hausawa.

    Mai waƙa Yakubu Muhammad ya yi ishara wadda ya nuna yabo, ta amfani da kalmomin sambarka, yakan saka daɗin zance ya jaddada ƙauna a inda ya ce:

    Jagora: Imbambaliba imbambalibo,
    : Biyayya daraja ce,
    : Yabo daɗin zance,
    : Ƙauna ai ƙima ce,
    : Son ki gare ni ai hujja ce,
    ‘Y/Amshi: Alambiyo-biyo yaran badali,
    : An yi bibiyo sai in da dalili.
    (Yakubu Muhammad: Waƙar ‘Imbambaliba’)

    Wannan fage mai faɗi ne wanda yake da waƙoƙi masu ɗimbin yawa, kila waɗanda ma baza a iya gane adadi na yawansu ba. Wasu daga cikin waƙoƙi na harshen nuna sambarka su ne waqar ‘Abdullahi shugaban sahu’ da waƙar ‘Mai yawuri bangon daniya’ da waƙar ‘Babban bijimi Muhammadu Sama’ na Aliyu Ɗandawo da waƙar ‘Amadun Bubakar gwarzon Yari’ da waƙar ‘Gogarman Tudu jikan Sanda’ na Ibrahim Narambaɗa da waƙar ‘Mai dubun nasara garnaƙaƙi sardauna’ da waƙar ‘Zaki ba a ja ka wasa ba’ da waƙar ‘Babban jigo na Yari’ na Musa Ɗanƙwairo da waƙar ‘Bijimin gidan Bello Mamman na Yari’ da waƙar ‘Tsakin Tama na Abashe’ da sauransu.

    Sa’idu Faru ya gaya wa Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Macciɗo wasu halaye nasa tun a lokacin da yake riƙe da sarautar Sarkin Kudun Sakkwato har yake gaya masa Sarkin Musulmi ne na wata rana. Ga abin da ya ce:

    Jagora: Maganag ga da za ni faɗa maka,
    : Gagarau ɗan Aliyu kai mana gafara,
    : Wada duk aka gadon ƙasura,
    : Wada duk aka gadon ɗaukaka,
    : Wadda duk aka gadon ci gaba,
    : Mamman ka gaji Abubakar
    : Ko da sayen halin nan akai,
    ‘Y/Amshi: Baba halin da ka kai kuɗɗi shikai.

    Ya ci gaba da cewa:

    Jagora: Diba ƙafarka zuwa bisa hannuwa,
    : Zaman Shaihu na ba wata sa’ida,
    : Sarkin Musulmi wataran kake,
    : Da imani da mu’ujjiza,
    ‘Y/Amshi : Na nan ga Malam Macciɗo,
    Jagora: Tun ga Aliyu Maisango naj jiya,
    : Halin ga da Bubakar yar riƙa,
    ‘Y/Amshi: Macciɗo kai ka shirin gado haka.
    (Gusau, 2009:154).

    4.8 Harshe na Tarihi

    Tarihi wani fannin ilimi ne wanda yake ba da labarin al’amura da suka faru a zamanin da ya wuce wato labarin abubuwan da suka shuɗe (CNHN, 2006: 49).

    Makaɗan baka na Hausa sukan yi amfani da harshe mai nuna tarihi su gina waƙoƙinsu. Misali, Alan waƙa ya rera wata waƙa a kan, tarihin cinikin bayi a tsakanin Hausawa mai gindi ‘Rayuwar Afirkawa, ga waƙar ‘Mu so Allah Sarkin makaɗa ‘ta Danmungai Daura wadda ya rera game da tarihin, zuwan Bayajidda ƙasar Hausa. Dubi kuma waƙar ‘Ga darajjar Amadu Bello’ ta Sarkin Taushi Salihu jankiɗi wadda ya bayyana tarihin zaman Turawa Nijeriya ta Arewa da hanyoyin da suka biyo da shekarun da suka yi kafin su miƙa mulki a 1960 da kuma bayan tashinsu.

    Dubi abin da yake faɗa a wani ɗa:

    Jagora: Zakkuwar Turawa nan Tudu,
    ‘Y/Amshi: Shekara hamsin da tara,
    : Ta inda sunka biyo Bidda,
    : Sai Kafin-Ɗanyumusa da Makurɗi,
    : Kwantagora garin Ibrahim,
    : Gwanga ya yi faɗa da Nasara,
    : Ga darajjar Amadu Bello,
    : Da arziki na mazan jiya yay yi.

    Jagora: Dagga Zariya sai Birnin Kano,
    ‘Y/Amshi: Ƙoramar Zorori wajen faɗa,
    : San Kano ya tarbi Nasara,
    : Ga darajjar Amadu Bello,
    : Da arziki na mazan jiya yay yi.
    (Gusau, 2012:119-120)

    4.9 Harshe na Koyar da Addini

    Addini hanya ce ta yi wa Allah bauta, ko kuma kamar yadda Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006:3) ya bayyana, addini shi ne hanyar bauta wa Ubangiji. Akwai dabaru iri-iri waɗanda al’ummu suke amfani da su wajen yi wa Allah bauta. Mutum, ɗan’adam, ya shirya wa kansa wasu hanyoyi na bautar ubangiji na maguzanci, Allah kuma ya saukar wa ɗan’adam da daidaitacciyar hanya ta yi masa bauta a inuwar addinin Musulunci.

    Addinin Musulunci yana ƙunshe da sharuɗɗa da hukunce-hukunce da ake neman kowane mutum Musulmi ya san su, ya yi aiki da su wajen yin wannan bauta ko ibada (Gusau, 2008:389). Haka kuma dole ne a sami wasu mutane daga cikin al’umma waɗanda za su tsayu a wajen koya wa sauran jama’a hanyoyi waɗanda suke yin jagoranci ga sanin matsayin bauta da kaifiyyarta da siffofinta da hanyoyin gudanar da ita.

    Bisa wannan aiki ne aka sami wasu suka himmatu wajen koyar da abubuwan da suka shafi bauta ko ibada a addinin Musulunci tun daga Manzanni da Annabawa da malamai da sauransu.

    Makaɗan baka na Hausa sun sami dama ta baiwar waƙa wadda suka dinga koyar da ayyukan ibada ta harshen waƙa domin ilmantar da mutane wasu sassa na sha’anin addininsu na Musulunci. Misali, waƙar ‘Fara ba mu ye Allah’ ta Uwaliya Mai’amada an zuba ta a kan harshe mai neman a kaɗaita Allah, waƙar ‘Mu je mu je ba mai yi kamar Allah’ ta Uwaliya ita kuma tana koyar da aikin hajji da kuma waƙar Ɗanyaya ta ‘Allah kai ni Madina’.

    Ita waƙar ‘Don salla da Salatil-Fati’ ta Alhaji Mamman Shata Katsina ya gina ta ne bisa harshe na sunnar aure. Dubi kuma waƙar ‘Azumi watan bautar Allah’ ta Alan Waƙa wadda ya sarƙa ta bisa harshe mai yin bayani a kan ibadar Azumi ta watan Ramalana. Ga waƙar ‘Allah ba ku mu samu Alhaji Alhajiya’ har wa yau ta Alan waƙa wadda take karantar da matsaloli na almajirci irin na Ɗankulodu. Kila ko wannan ne ya sanya Alan Waƙa ya ba ta suna Muhajira wato waƙa wadda take ƙaurace wa bara da almajirci irin na ɗanƙolo domin ta zama wata hanya ta koyarwa cikin harshen waƙar baka, da sauransu.

    4.10 Harshe na Bara-Gurbi

    A hikimar magana ta Bahaushe ne yake kiran sauran ƙwai wanda kaza ta yi kwanci, bayan ta gama ƙyanƙyasa ta bar su da bara-gurbi. Irin ƙwai bara gurbi yakan zama ya ruɓe ko ya ƙafe ko ya zama gunya ko dai wata illa ko lalura ta same shi (Bargery, 1934&1951:81). Ƙwai bara-gurbi yana fita ne daga ƙwayaye masu lafiya waɗanda ake ƙyanƙyashewa su zama ‘yan tsaki.

    Harshe bara-gurbi, harshe ne maras kyau, maras daɗi, mai ban haushi wanda wasu makaɗa suke jefawa a cikin wasu waƙoƙinsu. Abincin harshe bara-gurbi a waƙa shi ne zagi da batsa da baɗala da alfasha da munanan kalmomi, musamman irin na bara a kufai (Alan Waƙa: ‘Gara nai bara da bulayi, bara a kufai) da wasa da nassi na Alƙur’ani ko Hadisa ko musanta wani hukunci saukake ko ƙarfafa al’adu munana waɗanda suke kauce wa tubalai kyawawa na gina ingantacciyar al’ummar Hausawa. Lalataccen harshen waƙar baka tamkar lalataccen ƙwai ne wanda yake zama bara-gurbi (CNHN, 2006:37) a cikin ƙwayaye.

    Wasu misalai na harshe bara-gurbi a waƙoƙin baka na Hausa sun haɗa da wani ɗa wanda Muhammadu Gambo ya rera inda yake cewa:

    Jagora: Ba azumi nika wa gudu ba,
    : Yawan sallan nan yau da gobe,
    : Ba sallan nan nika wa gudu ba,
    : Yawan duƙin nan yau da gobe,
    : Ba shi barin mai rai da wando.
    (Gambo mai waƙar Ɓarayi)

    A wani ɗa ma yana cewa:

    Jagora: Ba Allah nika wa tambaya ba,
    : Wai laihin mutuwa ɗaukar ɓarayi,
    : Ta bar mai kurɗi lahiya lau,
    :Shin Allah mis sa hakan ga?
    (Gambo mai waƙar Barayi)

    A wani ɗa ma yana cewa:

    Jagora: Ni dai in ga asara danya-danya,
    : Ko ba a ban ko sisin kwabo ba,
    : In ishe tsohi sun yi lanƙwat,
    :Sai in ji kamar na taki Arfa.
    (Gambo Fitilar Sarri mijin Kulu)

    Wasu daga cikin waƙoƙi da aka yi su bisa harshe bara-gurbi su ne waƙar ‘Buwayi gasa na Shehu’ ta Ɗangaladima Labbo, Magajin Jankiɗi (Gusau, 1980:57) da waƙar ‘Ɗan’ali’ ta Muhammadu Bawa Ɗan’anace da waƙar ‘Gagaragadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa’ da waƙar ‘Habu na Habu’ da waƙar ‘A sha ruwa ba laihi ba ne’ na Alhaji Mamman Shata da waƙar’ Yau huɗu ga wata’ da waƙar ‘Jirgin sama za ya wuce’ na Aliko Makaho da wasu waƙoƙin Illon Kalgo da wasu na Isa Ɗanmakaho da wasu na Ɗanqurji da wasu na Musa Ɗanƙwairo tun ma ba wasu waƙoƙinsa na noma ba da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Waiwaye Kan Harshen Makaɗi A Zubin Waƙar Baka; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakkken Littafin danna nan.

  • Wasu Daga Malamai A Ilori

    Wasu Daga Malamai A Ilori

    Malam Musa Akalanbi

    Shi ne mashahurin Malami, Musa Ɗan Abubakar Ɗan Hassan Alkasinawiy. An ce iyayensa sun je Ilori daga Katsina don yaɗa Addinin Musulunci. An haifi Malam Musa a garin Ilori.

    Ya yi karatu a wurin mahaifinsa har ya haddace Alƙur’ani kuma ya shiga fannonin ilmi har ya tumbatsa a fannin Tafsiri da Hadisi. Makarantarsa cike ta ke da ɗalibai sama da ɗari Uku. Bai gushe ba yana koyarwa har ya rasu a shekarata 1970.

    Malam Muhammadul Ghali Ilori

    An ce zuriyarsa sun zo daga ƙasar Mali. An haifi Muhammad Ghali a garin Ilori kuma ya yi karatu a hannun mahaifinsa har ya zama malami masanin Alƙur’ani. Malam Ghali ya yi tafiye-tafiye Izuwa ƙasashen Yarabawa kamar Ibadan da Ikirun don koyar da Addini. An ce mafiya yawan Malaman Yarabawa sun yi karatu a hannunsa, kamar su Alhaji Ibrahim Giɗaɗo da Alhaji Sulaiman Limamin Juma’a Na Ikirun. Malam Ghali ya rasu a shekara ta 1974.

    Alpa Anla

    Shi ne Alhaji Abubakar Alkasinawiy, Wanda aka fi sani da Alpa Anla, ma’ana, babban Malami. An haife shi a cikin shekara ta 1913. Ya haddace Alƙur’ani tun da yarintarsa. Har ya zama hamshaƙin malami. Ya cigaba da koyarwa har rasuwarsa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin

    Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin

    Malaman ƙarni na ashirin sun haɗa da:

    – Alhaji Umar Egan Bidda

    – Alhaji Alpa Darajta Bidda

    – Alhaji Umaru Banwuya Bidda

    – Alaramma Malam Zubairu Kuba Bidda

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Malaman Yarabawa A Ƙarni Na Goma Sha Tara danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Malam Buhari Siriddawa (Sarkin Malaman Sakkwato)

    Tarihin Malam Buhari Siriddawa (Sarkin Malaman Sakkwato)

    An haifi Malam Buhari, Sarkin Malaman Sakkwato a Unguwar Siriddawa da ke Sakkwato a shekara ta 1934. Ya yi karatu wurin mahaifinsa Malam lbrahim da Malam Na Ta’ala Gidan Kanawa Sakkwato da Malam Mujeli Garge da Malam Shehu NaLiman (Limamin Masallacin Shehu).

    A halin yanzu tsangayarsa cike ta ke da almajirai da makaranta sama da ɗari biyar, baya ga ɗumbin masu karatun littatafai kowace rana a wurinsa. Babbar baiwar Malam Buhari ita ce ƙwarewar da Ubangiji Maɗaukaki Ya ba shi a fagen ilmin Fiƙhu.

    A yanzu shi ne ya ke riƙe da ragamar Jagorancin malaman Sakkwato a fadar Sarkin Musulmi. Makarantarsa na gudana ne tare da taimakon ɗansa Malam Sambo da wasu daga almajiransa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Muhammadu Na Ta’ala danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Sahabbai Suka Yi Koyi Da Annabi Muhammad (S.A.W) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Cikin Molo (Molar Pregnancy)

    Cikin Molo (Molar Pregnancy)

    Cikin Molo wani nau’in alamun juna biyu ne da wasu cikin mata kan samu kansu da shi wanda kuma a zahiri gaskiya ba ciki ne na haihuwa ba kamar yadda suke tsammani duk da abun ya tattara dukkan alamomin samuwar ciki na zahiri.

    Bisa ƙididdiga a dukkan mata dubu “1000” masu ciki akan sami guda ɗaya “1” ya zamto cikin molo ko cikin ƙarya, wanda 999 su ne ke ɗauke da ciki me ƙunshe da jariri. Viable Pregancy.

    SHIN YA CIKIN YAKE, ME KE JAWO SHI KUMA ?

    Wani cikin ne da ke faruwa sakamakon tangarɗar ƙwan haihuwa wanda wata ƙwayar halitta da ake kira TROPHOBLAST a turance da aikinta samarwa da jariri sinadaran abinci da rayuwa a cikin mahaifa kan rikiɗe ta hau girma a karan kanta ya zamto ta yi girman da ya mamaye cikin mahaifa ta samar da ƙaton tsiro me ƙunshe da ruwa ko tsauri WATO cysts ko TUMOR sakamakon waɗancan ƙwayayen haihuwa marasa rai ko inganci da suka shigo cikin mahaifar mace daga kututar ƙwayaye wato OVARY.

    Wanda wannan yasa a farkon samuwar abun duk wani alamu na ciki mace za ta ji ta fara fuskantarsa kama daga tashin zuciya, zazzaɓi ba me tsanani ba, rashin son warin abu, zubar da miyau, kasala da sauransu. Wani abu ma da za ta yi gwajin ciki na fitsari ko jini kai tsaye za ta ga ya nuna POSITIVE alamun ta samu ciki saboda HcG ɗin is High.

    Kuma zai cigaba da girma kamar yadda ciki ke girma a hankali har a ga tasowar cikin. Shi yasa da yawa in aka ce musu ba ciki ba ne ba sa yadda. Wasu sai a yi ta fama da su su ƙi, har su riƙa kiransa da kwantacce a lokacin da suka ga girman ya dakata. Ko kuma lokacin watannin haihuwa ya zo ya wuce har sun ƙara shekara sai ka ji ana kwantaccen ciki.

    SHIN DUK IRI GUDA NE KO YA RARRABU ?

    Ya kasu rukuni biyu ne kacal; akwai COMPLETE wato me gaba ɗaya, da kuma INCOMPLETE me ragayya.

    RUKUNI NA FARKO [COMPLETE]

    A irin wannan ainihin shimfiɗar cikin mahaifa wato (uterus layer) inda jariri ke kwanciya ciki ya zauna ita kanta shimfiɗar takan rasa ingancinta ma’ana takan tattare ta murmuɗe ta yi tudu da ƙwari, domin daga cikin ƙwayoyin halittun gado chromosomes 46 da Maxa suke saki wato 23 daga mace, 23 wanda ke ba da total na 46.

    Akan samu Chromosome ɗin mace ne kurum zai iya zamowa jariri wato viable egg. Shi MIJIN empty sperm cell ya saki. WANDA tunda kuwa sai da ƙwan namiji ciki zai tabbata amma ga shi sai mace ce ke da normal egg toh irin wannan ke sa zubin shimfiɗar mahaifar ya jirkice shi kuma wancan tumor ɗin na trophoblast sai ya yi amfani da wannan viable egg na macen ya girma ya cika cikin mahaifar mace (uterus). A riƙa ganin kamar ciki gareta. kuma ko yaushe in an duba HCG za a ga high kamar dai mai ciki, yadda dai kuka ji na faɗa a baya.

    RUKUNI NA BIYU [PARTIAL]

    A partial shi kuma cikin 23 pairs ɗin na chromosome MACE tana sakin normal egg tare da 1 pair na chromosome, shi kuma NAMIJIN sai ya saki 2 pairs na chromosome maimakon 1 wato shi kaɗai ya samar da 46pairs maimakon 23pairs wanda in ka haɗa da 23pairs ɗin na matar sun tashi 69 pairs maimakon a sami total na 46.

    Hakan shi ke sa ga cikin ya shiga akwai ciki na gaske ba tumor ba toh amma fa ba zai ta6a rayuwa ya zama cikakken jariri ba, kuma a daidai wannan lokacin ga growth ɗin trophoblast ɗin da ya kusa cika mahaifar mace, don haka nan ma za a yi ta ganin HCG high amma fa ba zai taɓa zama ciki ba.

    Sai dai a PARTIAL ɗin akwai kuma Partial me Normal Karyotype wato chromosome ɗin daidai ne kowa ya samar da 23 ana da total 46 amma kuma ga trophoblast ya samar da tumor kusa da jaririn. To a irin wannan ne yakan girma ya zama ciki a haifi jariri koda kuwa bai da cikakkiyar lafiya.

    A irin wannan ne ake jin hausawa na cewa kwantaccen wance dai ya tashi, duk da cikin kan shafe shekaru. Amma gaskiya ba a cika samun irin wannan ɗin sosai ba, sai dai dama irin wannan tun a ultrasound ake iya bambance shi.

    Domin karanta Cutar Maƙoƙo dannan nan

    ME KE JAWO HAKAN LIKITA ?

    Abubuwan da kan jawo haka sun ƙunshi;

    1. Akwai shekaru musamman macen da ke kusa ko kuma ta haura shekaru 35

    2. Kasancewar mace ta taɓa samun hakan a baya, akwai yiwuwar ƙara maimaitawa

    3. Sai rashin daidaiton sinadaran halitta (hormonal imbalance)

    Wannan matsala musamman a me COMPLETE MOLAR likitoci kan kalle ta a matsayin ɗaya daga cikin cuttukan cancer na mahaifa wato choriocarcinoma. Duk abin da ke iya ƙara girma a karan kansa tabbas ko dai ya zamo cancer ko kuma benign tumor wato wanda ba cancer ba amma in aka bar shi zai iya zama cancer.

    Domin idan har bayan an cire cyst ɗin kuma HCG ya cigaba da tsayawa High akwai zargin ya riga ya zama cancer dole a ɗora mace a kan CHEMOTHERAPY, kuma ana warkar da cancer ɗin cikin ikon Allah in an farga da wuri.

    Idan kuwa aka bar shi to ka san cancer tana iya yaɗuwa zuwa wasu sassan kuma hakan ce za ta faru wanda a ƙarshe mace za ta iya mutuwa a dalilin cancer hanta ko huhu ko hanji alhalin tushen ciwon a mahaifa ne. Wannan tasa da zarar likita yace miki cikin MOLO ne to kar ki ɓata lokaci kurum a cire shi.

    ALAMOMIN CIKIN MOLO

    Alamomin sun ƙunshi;
    Ganin Fitar jini me duhu ta gaba
    Ciwon baya ko mara
    Ganin jini na fita kamar dunƙulen grapes fruits da kuma
    Matsanancin tashin zuciya da amai.

    WAƊANNE GWAJE-GWAJE AKE YI

    Akan yi gwajin jini domin duba hemoglobin level saboda tunanin ƙarancin jini, sannan a kuma duba HCG wato hormone ɗin juna biyu da kuma ultrasound scan.

    MATAKIN ƊAUKA

    1. Kai tsaye bayan tabbatar da molar pregnancy ne abin da ake kira Dayilteshin & kyuritaj wato manuwal bakyum Asfireshan SHI NE abin yi, a cire tissue ɗin baki ɗaya, domin barinsa ba zai taɓa zama jariri ba, dama ba ciki ba ne kuma ko da partial ne wanda ke ƙunshe da ciki shi ma ba girma zai ba.

    Bayan kuma an cire ɗin ba a kuma barin mace ta ɗauki ciki, a ƙalla sai bayan shekara. Saboda ana so a cigaba da auna HCG level ɗin lokaci lokaci har zuwa shekara bayan cire molar ɗin domin idan ya cigaba da zama HIGH kamar de akwai ciki to alama ce ta PERSISTENT GESTATIONAL TROPHOBLASTIC NEOPLASIA wato ya tabbata cancer. Don haka dole a yi maza a fara mata chemotherapy a kashe shi, in ba haka ba za ta yaɗu zuwa sauran organs, kunga ko hakan is deadly.

    2. Ko kuma idan dama mace ba ta da sha’awar ƙara haihuwa tana jin ta gama shi kenan sai a cire mahaifar baki ɗaya kurum. Duk da nan gaba kuma lokacin menopause in estrogen ɗinta ya yi low wasu suna samun hot flashes wato premenopausal symptoms wanda ake musu hormone replacement therapy to amma fa macen da ba ta da mahaifa ita ba za a yi mata wannan ba, domin zai zame mata matsala tunda ya ƙunshi estrogen alhalin ba ta da uterus. Progesterone only method shi ne therapy ɗin da za ta iya amfani da shi.

    Don haka ake son ko yaushe in likita ya tambayi mace wani abu to ba ɓoye-ɓoye ko da dangane da mu’amalar auratayya ne ta faɗa masa gaskiya ba a yi wa likita ƙarya ko da kuwa kina yi wa mijinki shi likita in aka yi masa ƙarya kanki kika cuta.

    Wannan shi ne molar pregnancy a taƙaice.

    Danna nan don karnta Saiƙo Ko Sanƙo

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Saiƙo Ko Sanƙo (Baldness)

    Saiƙo Ko Sanƙo (Baldness)

    Saiƙo inji sakkwatawa, ko sanƙo inji zage-zagi da katsinawa, shi ne ake kira “alopecia” a likitance. A turance kuwa ana kiransa “baldness” ko “bald headedness”. Saiƙo yanayi ne wanda yake sanya zubewar wani ɓangare na gashi (partial loss of hair) ko kuma zubewar dukkan gashi (complete loss of hair) a saman kai (scalp) ko sauran sassan jiki.

    A likitance ba a ɗaukar saiƙo a matsayin wata cuta, sai dai ana ganinsa a matsayin yanayin da abubuwa masu yawa suke iya haddasawa. Mafi yawan saiƙon da yake samun namiji ko mace ana kiransa “androgenetic alopecia”, wanda yake faruwa saboda mutum ya yi gado daga iyayensa da kakanninsa.

    Wani lokacin kuma saiƙo yana faruwa ne sakamakon rashin daidaiton zubar ruwan sinadarai (hormonal imbalance), ko nisan shekaru (ageing), ko rashin lafiya ta dogon lokaci (chronic illnesses), ko damuwa (stress), ko rashin cin abinci mai gina jiki (nutritional deficiencies), ko laulayin magunguna (medication side effects), ko matsalolin garkuwar jikin (autoimmune disorders), ko salon gyaran gashin kai (hairstyles), ko amfani da mayukan gyaran gashi (hair treatment creams), da sauransu.

    Saiƙo yana aukuwa ne idan ƙofofin gashi (hair follicles) suka matse, wanda haka zai sanya gashi ya riƙa fitowa da kyar, har daga ƙarshe ya daina fitowa gaba ɗaya.

    SASSAN JIKI DA SAIƘO YAKE KAMAWA (BODY PARTS AFFECTED BY BALDNESS)

    Anfi samun saiƙo a kai (scalp) daidai saman goshi, ko tsakiyar kai, ko keya. Amma wani lokacin saiƙo yakan kama wasu sassan jiki daban kamar gira (eye brows), da gashin ido (eye lashes), da gashin gemu (beard), da gashin baki (moustache), da gashin hammata (armpit hair), da gashin mara (public hair). Idan mutum ya ga sassan jikinsa da na lissafa ba su yin gashi, to, akwai yiwuwar cewa saiƙo ne ya kama su.

    RABE-RABEN SAIƘO (CLASSIFICATION OF BALDNESS)

    Saiƙo ya rabu gida uku kamar haka:

    1. Saiƙon da yake aukuwa ga maza (androgenetic alopecia): wannan shi ne saiƙon da aka fi sani. Alamarsa ita ce rashin gashi mai yawa ko kuma rashin gashi kwata-kwata a kai ko wani ɓangaren kai.

    2. Saiƙo ga mata (androgenetic alopecia): sunansa ɗaya da na maza a likitance. Bambancinsa da na maza shi ne gaba ɗaya gashin yake zubewa, ba tare da farawa daga goshi ba (without receding hairline).

    3. Saiƙo wanda yake sanya gashin kai ya yi cibiri-cibiri (alopecia areata): a wannan saiƙon, gashin kai zai yi dabbare-dabbare. Ma’ana, wani wurin akwai wani wurin babu. Matsalolin garkuwar jiki ne suke haddasa shi (autoimmune disorders).

    MUTANEN DA SAIƘO YAKE KAMAWA (PERSONS AFFECTED BY BALDNESS)

    Saiƙo yana aukuwa ga kowane irin mutum, mace ko namiji, yaro ko babba. Amma an fi ganinsa a jikin mutanen da suka kai shekarun balaga ko shekarun tsufa.

    KARIYA DAGA SAIƘO (BALDNESS PREVENTION)

    Mawuyaci ne mutum ya iya ɗaukar wani matakin da zai hana shi samun saiƙo, domin alaƙarsa da gado da kuma sinadaran jiki. Amma ana kyautata zaton cin abinci mai gina jiki tare da kaucewa yawan yin amfani da chemicals a gashin kai za su taimaka wajen rage hatsarin samun saiƙo.

    MAGANI (TREATMENT)

    Idan mutum ya samu saiƙo, to, sai ya tafi asibiti domin ganin likitan fata. Likitan zai binciki mutumin domin gane abinda ya haddasa samun saiƙon. Daga nan zai ɗora shi a kan magani bisa la’akari da abinda ya samar da saiƙon.

    Magungunan da akan yi amfani da su wajen magance saiƙo sun haɗa da minoxidil da finasteride. Sa’annan akan yi amfani da hasken na’urar computer (lazer treatment), ko dashen gashi (hair transplant). Idan kuwa ba a yi nasara ba, to, sai mutum ya riƙa yin amfani da hular gashin roba (wig) domin ɓoye saiƙonsa.

    Domin karanta Cututtukan Haƙori danna nan
    Edita:@rumasau-kallamu

  • Matasa

    Matasa

    Allah SWT ya ce:
    “Lallai su matasa ne, sun yi imani da ubangijinsu sai muka kara musu shiriya”

    MATASHIYA: WANENE “MATASHI”
    Majalisar ɗinkin duniya dangane da abinda ya shafi shekaru, ta faɗi waye matashi. “Matashi shi ne wanda bai yi ƙasa da shekara goma sha biyar ba kuma bai wuce shekara ashirin da huɗu ba”. Idan muka dubi yanayi, cimaka da yankuna na duniya, za mu ga banbanci tsakanin masu waɗannan shekaru a zubi, yanayin girman jiki, wayewa, ilimi har ma da tunani.

    Haka ma abin da ya shafi dokokin ƙasa zuwa wata ƙasar, za mu iya samun bambance banbance na masu waɗannan shekaru. Misali wasu ƙasashe daga shekara 18 shi ne matashi yake samun damar yin zaɓe ko izinin zaman kansa. A ƙasashe kamar Koriya ta Kudu, sai matashi ya kai shehara goma sha tara ko ma ashirin.

    Tarayyar Afrika a nata ɓangaren, ta bayyana matashi shi ne wanda ya ke tsakanin shekara goma sha biyar zuwa talatin da biyar. Daga shekara goma sha biyar ɗabi’a, tunani da wasu halayyar mai wannan shekaru sukan canza.

    Mai waɗannan shekaru yana taka wasu matakai masu mahimmanci a rayuwa, wanda ake buƙatar a kula sosai, sannan shi kansa matashi ya kula da su, ya yi ƙoƙarin yin amfani da su dan cin moriyar su nan gaba. Wasarairai da su da yin abin da ba shi ya dace ba a wannan lokacin ya na sanya mutum babbar nadama bayan shekarun sun wuce.

    MATSAYIN MATASHI A WANNAN LOKACI A NAJERIYA

    Najeriya ta na da tsare tsare masu kyau game da matasa amma a rubuce kawai. Kamar sauran ƙashashen duniya masu tasowa musamman na Afrika da Asiya. Gwamnatoci ba su fiye damuwa da abin da ya shafi matasa ba, ko dai saboda rashin sannanin mahimmancin su, gudumawarsu a gina al’umma da ci gaban ƙasa, ko kuma dan wani dalili na ƙashin kansu na siyasar su ta cikin gida.

    Matashi a wannan ƙasa kusan shi ya ke tanadar wa kansa da kansa duk wani abu na gina rayuwarsa. Hukumomi ba sa ba da mahimmanci sosai dangane da abinda ya shafi wannan ɓangaren. Misali, abinda ya fi komai mahimmanci a rayuwar matashi babu kamar ilimi. Makarantun mu na sakandire kowa ya san hali da yanayin da suke ciki, babu wani kyakkyawan tsari da zai ƙarfafa gwiwar ɗalibi don zamowa wani abu nan gaba. Makarantun sakandire sun zama madakata ga da yawa daga cikin matasa musamman ‘ya’yan talakawa waɗanda ba sa iya karatu a makarantun kuɗi.

    Matasa sun gama sakandire amma sun faɗi jarabawar gamawa, babu wani tanadi da hukumomi suke da shi na yadda za a yi da waɗannan matasan, daga nan sai su kiɗime, su rasa yadda za su ci gaba da rayuwa ga kuma buri. Wannan ya ke janyo wasu su fara shaye shaye don rage raɗaɗin zaman banza da yawon banza, wasu kuma su faɗa ayyukan ɓarna na yau da kullum. Kaɗan ne ake samu su nemar wa kansu sana’a don dogaro da kai.

    A halin yanzu, ina makarantun mu na vocational da technical, suna nan, amma an yi watsi da su. A Arewa tun 1909 aka buɗe makarantar koyar da sana’a a Nasarawa inda ake koyar da saƙa, aikin kapenta da sauransu. A 1946 an sami bunƙasar wuraren koyar da sana’o’i inda aka buɗe wurare har goma sha huɗu a Arewa.

    Na kawo wannan ne don kawai in nuna yadda makarantun koyar da sana’a suke da mahimmanci a da da yanzu. Za a iya amafani da waɗannan makarantu wurin saitawa da inganta rayuwar matasa a wannan ƙasa, don ba su damar komawa waɗannan makarantu in ba su sami damar yin nasara a jarabawar gama sakandire ba don su koyi san’a don dogaro da kai da kuma ɗauke musu kewar zama da yawon banza.

    IRIN TANADE-TANADEN DA YA KAMATA A YI WA MATASHI:

    Hukumomi a Najeriya suna da tanade-tanade masu yawa da inganci game da matasa a wannan ƙasa, amma ba a ba su mahimmanci wurin aiwatarwa, saboda wasu dalilai na shugabanni. Wani lokaci ana kallon aiwatar da waɗannan tanade-tanade da ba abin da za a iya ganin alfaninsu ne a yanzu yanzu ba. Su kuma ‘yan siayasa abin da suke so, shi ne sha yanzu magani yanzu, a gani a ƙasa don yaɗa manufofinsu da ɗorewar siyasar su.

    Akwai tanade-tanaden da hukumomi suke da su na ilimantar da matasa, koya musu sana’o’i da abinda ya shafi wasanni. Abin da ya shafi ilimi da koyar da sana’o’i kullum hukumomi da ‘yan siyasa suna yin abinda za su iya, amma dai bai taka kara ya karya ba.
    Abin da ya shafi wasanni shi ne har yanzu kamar an bar mu a baya musamman a nan Arewa.

    A yanzu duk da addini da al’adar mu suna da tasiri mai yawa a rayuwar mu ta yau da kullum, amma dai a yanzu duniya ta ci gaban da ya kamata a ce mun tsunduma cikin abinda ya shafi wassani da motsa jiki wanda yanzu ya zama sana’a mai tagomashi a duniya. Banda ƙwallon ƙafa, akwai wasanni kamar ƙwallon kwando, ƙwallon hannu, ƙwallon raga, table tenis, badminton, guje guje, tsalle –tsalle, kokawa, iyo da sauran wasanni da ake gudanar da su ƙarƙashin kulawar hukumar wasanni ta duniya wato (Olympics).

    A shekarun nan matasa ‘yan ƙalilan da sunayensu suka fito fili daga Arewa waɗanda suke buga ƙwallon ƙafa a duniya, an ga yadda suka samu ɗaukaka. Amma sauran ɓangarorin wasanni an yi buris da su, da ƙyar za ka sami ‘yan Arewa a sauran wasanni da na ambata a sama.

    Idan hukumomi da ‘yan siyasa za su bai wa sauran ɓangarori na wasanni kulawa ta yadda za a samar da wuraren horar da matasa waɗannan wasanni, kamar yadda a Kano ɗaya daga cikin gwamnatocin da suka wuce aka gina makarantar horarwa kan wasanni. Faɗaɗa tunani wurin samar da ƙwararrun masu horar da wasanni iri–iri, a riƙa nemo matasa masu baiwar waɗannan wasanni ana ba su horo na musamman, sannan hukumomi su taimaka musu wurin shiga gasar wasanni na cikin gida da kuma na ƙasa da ƙasa.

    Wannan wani tanadi ne mai kyau da zai rage wa matasa zaman banza, sannan za a samar musu da wani abin yi wanda ba lallai sai sun yi karatu mai zurfi ba, zai ba su dama su riƙe kansu da ‘yan uwansu ta hanyar abin da suke samu na kudade. Ƙari a kan haka shi ne, sauran matasa za su yi sha’awar waɗannan wasanni dan abinda suka ga ‘yanuwansu suka zama. Idan ba a manta ba akwai wata matashiya Tobi Amusan da ta lashe gasar tseren mita 100 a shekaran 2022.

    Wannan abinda ya shafi wasanni an kawo shi ne a babin misali kawai, amma akwai damammaki da yawa da hukumomi suke wasarairai da su wanda zai ba wa matasa dama mai yawa a rayuwarsu don zama wani abu nan gaba ba tare da dogaro da gwamnati ba.

    ABIN DA MATASHI YA KAMATA YA YI WA KANSA

    A ƙashashen da suka ci gaba, hukumomi su suke yi wa matasa tanadi tun farko don a ɗora matashi a kan hanya, a ba shi ilimi mai kyau, a ba shi dama na koyon sana’a da sauransu. Amma a ƙasashen mu masu tasowa kamar yadda na faɗa, abin ba haka yake ba. Toh shin matashi don bai samu waɗannan tande-tanaden ba sai ya zauna ya kashe kansa da kansa yana ji yana gani? Shekarun samartaka wasu shekaru ne da yake bai wa wanda yake wannan mataki damammaki waɗanda ba su da iyaka.

    Matashi yana da ƙarfin jiki, lokaci da ƙarancin tsoro, wanda ba a wannan shekarun yake ba yana da ƙarancin waɗannan abubuwa. A wannan shekarun matashi ji yake kamar ya ɗau duniya a ka saboda ƙarfin da yake ji jikinsa, ba wasu nauyi na yau da kullum a kansa da zai cinye masa lokaci, kamar hidimar iyali. Sannan matashi yana da ƙaracin tsoron yin duk abinda ya ke so, zai iya yin tafiye-tafiye masu nisan gaske, zai iya shiga ko yin duk wani abu mai haɗari ba tare da yin dogon tunani ba.

    Waɗannan su suke bai wa matashi damar zama wani abu a rayuwarsa. Idan mutum ya girma ƙarfinsa ya fara ƙarewa wasu abubuwan ba zai iya yin su ba, lokacin sa kuma na aikinsa ne ko sana’arsa da kuma iyalansa, sannnan tsoron abinda zai iya kai wa ya komo. Misali tsoron mai zai faru ko wani hali iyalansa da ‘yanuwansa za su shiga idan ba ya nan duk waɗannan suna daƙile wanda ba matashi ba.

    Ɗaya daga cikin manyan abubuwa da Najeriya ta ke da shi wanda ƙasashe da yawa babu, shi ne, duk ɗan Najeriya zai iya zama komai a ƙasar nan, abin nufi a nan, shi ne duk abin da kake so ka zama a Najeriya za ka iya zamowa, misali zama babban ɗan siyyasa, attajiri, babban jami’in gwamnati da sauransu.

    Kullum muna gani waɗanda ba ‘ya’yan kowa ba, kuma su kansu ba kowa ba, suna zama manyan mutuane a ƙasar nan, ba za ka taɓa samun haka ba a wasu ƙashashe. A waɗannan ƙasashen idan ka taso a gidan takalawa, a haka za ka girma ka gama rayuwarka a wannan layin. Babu tsallake zuwa wani layin, wato abinda ake cewa “social mobility”.

    Saboda haka, wannan dama ce mai kyau ga duk wani matashi da ya taso a Najeriya da ya yi ƙoƙarin samun ilimi ko da ba mai zurfi ba ne, ya sami sana’a ya riƙe, musamman idan a gidan su akwai sana’a, kada ya raina ta duk ƙanƙantar ta. Yanzu zamani ya canza za a iya zamanantar da duk wata sana’a, a tallata, kambama ta. Kada matashi ya kallafa wa kansa sai ya sami aikin gwamnati a yanzu, kada kuma ya yaudaru da abinda wasu suke samu ta hanya mara kyau a gwamnati.

    Matashi ya rage wa kansa dogon buri. Duk arziƙin da Allah ya ƙaddara wa mutum sai ya same shi a duniya. Shi arziƙin ɗan Adam ana rubuta masa shi tun yana cikin mahaifiyarsa. Kamar yadda ya tabbata a hadisin Manzon Allah SAW da ga Abdullahi ibn Mas`ud, Bukhari da Muslim suka fitar da shi. Sannan babu wanda zai mutu har sai arzikinsa ya same shi, babu wanda ya isa ya tare masa shi.

    Kawai a daure a nema ta hanyar halas, kada matashi ya yi gaggawar neman arzikinsa ta hanyar haramun. Manzon Allah SAW ya ke cewa, “Mala’ika Jibril ya faɗa min cewa babu wata rai da za ta mutu face ta sami arziƙin gaba ɗaya sannan kuma sai ta kai ajalinta. Ku ji tsaoron Allah ku kyautata nema. Kada ɗayan ku ya yi gaggawar neman arziƙinsa ta hauyar haram.

    Kawai matasa ku tashi ku nema, Allah zai bayar. “Waɗanda suka yi gwagwarmaya za mu shiryar da su kan tafarkin mu, lallai Allah ya na tare da masu kyautatawa”

    January 17th, 2025.

    Danna nan don karanta Biyayya Ga Mahaifa

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Falalar Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)

    Falalar Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)

    Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; wanda ya yi salati ɗaya a gare ni, Allah zai yi salati goma a gare shi’.

    Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘kada ku mai da ƙabarina idi; ku yi salati a gare ni ko ina kuka kasance’.

    Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Marowaci shi ne wanda aka ambace ni a wurinsa amma bai yi mini salati ba’.

    Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Allah yana da waɗansu mala’iku matafiya a bayan ƙasa; suna isar mini da sallama daga al’ummata’.

    Sannan kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Babu wani wanda zai yi mini sallama face Allah ya dawo mini da raina na amsa sallamarsa’.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Ya Raɗa Wa Manzon Allah(S.A.W) Suna Muhammad? danna nan.

     

  • Yadda Ake Garin Kunun Aya

    Yadda Ake Garin Kunun Aya

    A yau za mu koyi yadda ake yin Garin Kunun Aya. Kunun Aya kamar yadda muka sani kunun aya yana da matuƙar amfani ga lafiyar mu musamman ma ma’aurata.

    Abubuwan da ake buƙata:

    Aya.
    Dabino.
    Kwakwa.
    Citta.
    kanumfari.

    Yadda ake haɗawa:-

    A tsinci aya a cire dattin ciki. Ki soya ayar sama-sama yadda za ki ji daɗin niƙawa ya koma gari don kar ya yi saurin lallacewa.

    Ki samu kwakwarki (dry coconut) da dabino ki zuba a cikin ayar nan. Sai ki daka cittarki da kanumfari ba da yawa ba saboda kar yawanshi ya ɓata miki ɗanɗanon garin yayi yawa ɗan daidai za ki zuba ki kai a niƙa miki. Bayan nan kafin ki yi packaging ɗinsa ki baza ya sha iska sannan ki saka a cikin mazubinki saboda kar ya sha iska sosai.

    Danna nan don karanta Yadda Ake Wainar Semovita

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Biyayya Ga Mahaifa (Iyaye)

    Biyayya Ga Mahaifa (Iyaye)

    “Sannan mun yi wasiya ga mutum da ya kyutata wa mahaifansa, mahaifiyarsa ta yi goyon cikinsa cikin wahala sannan ta haife shi cikin wahala…” (Q 46:15)

    Wata rana cikin watan satumba na shekarar 2024 na je jihar Legas ɗan halartar wani horon aiki. Bayan na isa ne, na hau motar haya dan ƙarasawa inda zan halarci horon, da yake da safe ne, a kan hanyar mu sai na hango wani yaro ɗan makaranta da bai wuce shekara goma (10) ba da mahaifiyarsa a gefen titi suna jiran abin hawa, mahaifiyar tana ta gyara wa yaron takalminsa da safarsa, sannan tana ta ƙoƙarin shafa masa wani abu kamar man shafawa, a zato na yaron ne ya shafa man shafawan amma bai yi yadda ya kamata ba, mahaifiyar take gyara masa.

    Duk wannan abin da mahaifiyar ta ke yi, yaron yana tsaye kamar ba da shi ta ke ba. Wannan abinda ya faru ya sani tunani sosai game da lamarin iyaye da ‘ya’ya.
    Allah maɗaukakin sarki saboda girmama sha’anin iyaye bai taƙaita lamarinsu ga masu Imani ko musulmi kaɗai ba, za mu iya fahimtar haka ne a ayar da take cikin Suratul Ahkaf, aya ta 15 in da Allah ya yi kira ga “mutum” kowa da kowa ke nan, ba wai wasu gungun mutane na musamman ba.

    Kalmar da Allah ya yi amfani da ita na “mutum” ya ƙunshi musulmi, mumini, fasiƙi, munafiki, kafiri da duk wani jinsi na mutum, sannan ya umurce shi da ya yi wa iyayensa biyayya. Biyayyar iyaye ana buƙatar ta ne daga duk wani mutum. Mahaifiyar da na gani da ɗanta, daga yanayin shigarta babu alamar musulma ce, amma ku dubi yadda ta ke yi wa ɗan ta. Shi ya sa Allah a aya ta 23 ckin Suratu Isra’i, ya yi kira ga mutum da ya bauta masa, ya kuma jingina hakan da yi wa iyaye biyayya.

    Kira zuwa ga bautar Allah kira ne ga kowa da kowa, toh haka ma kira zuwa yi wa iyaye biyayya ta shafi kowa da kowa. Iyaye suna yin duk abinda za su iya ne wurin su ga sun kyautata rayuwar ‘ya’yan su a nan gaba, suna ƙarar da ƙarfinsu, abinda suke da shi, su na haƙura da jin daɗinsu, su ma sa kansu a wahala don kyautata rayuwar ‘ya’yansu, idan ta kai su rasa rayuwarsu ma iyaye a shirye suke su rasa rayuwar su don ‘ya’yansu. Babu wanda zai iya yin wannan in ba iyaye ba. Duk waɗannan abubuwa ba su taƙaita ga wani mai addini ba, duk an haɗu a kan wannan babban lamarin.

    A aya ta takwas cikin suratul ankabuut Allah ta’ala cewa ya yi “ mun yi wasiya ga mutum da ya kyautata wa iyayensa, da za su yi maka umarni da ka yi shirka da Ni kan abinda ba ka da ilimi, toh kada ka yi musu biyayya (kan wannan umarnin na yin shirka)” A wannan ayar ma Allah kai tsaye ya kira mutum bai ware wani ba, sanan ya ba da wasiyar yi wa iyayye biyayya da kyautatwa.

    Ya kuma nuna ko da kuwa iyayen nan kafirai ne, ba a bai wa mutum dama ya saɓa musu ba. Idan iyaye waɗanda ba musulmi ba, suka umurci mutum da ya yi shirka da Allah, toh sai ya ƙi musu biyayya kan wannan umurnin na yin shirka da Allah, amma haƙƙin biyayya yana nan a wuyan sa dole.

    Wannan ayar tana ƙara nuna mana ce wa iyaye ko suna saɓa wa Allah, to wajibi ne a yi musu biyayya a dukkan ɓangarori na rayuwarsu. Inda kawai ba za a yi musu biyayya ba shi ne inda su ka yi umarni da a saɓa wa Allah. A abin da ya shafi biyayya wanda yake kan kowane mutum, Allah ne a gaba, sannan iyaye ba tare da babancin imani ko rashin sa ba.
    Iyaye wasu mutane ne na musamman da Allah ya zaɓa kuma ya fifita, ba wai dan haihuwar mutum da suka yi ba kaɗai, har ma da irin gudumawar da suka bayar a cikin rayuwarsa.

    Shi yasa a hadisin Manzon Allah SAW wanda Amr bin Shu’aib daga Babansa daga Kakansa ya ce wani mutum ya zo wurin Manzon Allah SAW ya ce: Mahaifina yana da buƙata da dukiyata, sai Manzon Allah SAW ya ce: “kai da dukiyarka duk na mahaifinka ne” Wannan ya ƙara tabbatar mana da matsayin iyaye a wurin mutum, ba wai ma shi kansa kaɗai ba har ma abinda ya mallaka na iyayensa ne, suna da damar yin abinda sukaga dama a ciki.

    Amma yanzu sai ka ga mutum yana yi wa iyayensa rowa kawai don Allah ya yi masa arziƙi. Shi bai san arziƙin nan da Allah ya ba shi da shi kansa duk na iyayen sa ne ba. Idan kuma ya ƙi musu abinda suke so a cikin dukiyarsa ba tare da yin almubazarranci ba, toh ya sani yana da laifi mai girma a wurin Allah.

    Waɗanda ba musulmi ba, idan ba su yi wa iyayensu biyayya ba, toh bayan laifin shirka da Allah akwai kuma na ƙin bin umarnin Allah dangane da ƙin yi wa iyayesu biyayya. Shi kuma musulmi da ya saɓa wa iayayyensa, ko da yana da wasu ayukan laheri sai an kama shi da laifin ƙin wa iyayensa biyayya.

    Allah ya hore wa kowane mutum bin iyayensa da kyautata musu, wannan yasa za a ga wanda ba musulmi ba, yana kyautata wa iyayensa, a kuma sami musulmi mai ƙin biyayya ga iyayensa. Babu abinda ya kai wannan takaici. Kamata ya yi a ce wanda ya fi kowa bin umarnin Allah, shi ne wanda ya fi yi wa iyayensa biyayya da kuma kyautata musu.
    Haka kuma, Allah ya tsara idan mutum ya kyautata wa iyayensa, toh shi ma sai ‘ya’yansa su kyauatata masa.

    Rabiu Musa Adam
    Deceember 25th, 2024.

    Danna nan don karanta Ni’imar da Allah Ya Yi Wa Mutane Ba Tare Da Sun Fahimta Ba

    Edita:@rumasau-kallamu