Tag: yadda ake

  • Azumin Watan Ramadan 2

    Azumin Watan Ramadan 2

    Idan kuma mutum ya kusa haɗiye abinci ko abin shan, sannan kuma sai ya ji ana kiran sallah, idan lokaci ne, ma`ana shi ne wanda ya fara kiran sallah a lokacin ko kuma mutumin yana da saurin yin kiran sallah, saboda shi mutumin ya tashi da wuri ya yi sahur ɗinsa, to mutum zai iya yin sauri ya haɗiye wancan lomar ko abincin ko abin shan.

    Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ko amfani ga mai azumi haɗi da mai kiran sallah su san lokacin da alfijir yake fitowa ko alamar fitowar alfijir a kowace rana, saboda wasu ladanan suna kiran sallar asubah ko kiran sallah na biyu kafin alfijir ya fito, wasu kuma ladanan suna kiran sallah ne bayan alfijir ya fito da jimawa, wasu kuma masu yin azumi da su suke yin la`akari.

    Haka kuma ya kamata ladanai da masu yin azumi mu san hukunce-hukuncen na yin azumi haɗi da yadda alfijir yake fitowa da yadda rana take faɗuwa, saboda a nan ma ana samun wasu matsaloli da yawa ga wasu ladanan, saboda suna kiran sallah magariba kafin rana ta gama faɗuwa ko lokacin kiran sallah magariba ya yi, su kuma wasu mutane da su ke la`akari da zarar sun ji kiran sallah sai su ɗauki abin shan su ko abin cin su, sai su kama ci ko sha ba tare da yin la`akari da duba lokacin shan ruwa ba.

    Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga mai yin azumi, idan zai sha ruwa ya tabbatar lokacin shan ruwan ya yi, saboda da mutum ya yi gagggawar shan ruwa, kuma bai tabbatar lokacin shan ruwan ya yi ba, to gara ya jinkirta shan ruwa bayan an yi sallah, sai mutum ya sha ruwan, saboda idan ya sha ruwa kafin lokacinn shan ruwan ya yi, to ba shi da azumin wannan ranar, haka kuma idan mutum da gangan ko alfahari ko taƙama ya sha ruwan, to ya karya azuminsa, sannan kuma akwai kaffaran azimi a kansa guda sittin a jere haɗi da guda ɗayan can da ya karya.

    Saboda waɗannan misalan ya kamata ‘yan uwana musulmai mu tashi tsaye wajen ilimi addini da na zamani, saboda malam mai ” ahlari ” yace “bai kamata ba ga wani mutum ya aikata wani abu a cikin addinin musulunci, har sai ya san hukuncinsa ko abin da Allah (da manzom Allah) yace a kan abin da zai aikata a cikinsa”.

    Haka kuma wannan ƙa`idar take a cikin addinin musukunci, babu wani abu da wani mutum ya isa ya aikata har sai ya san hukuncinsa a addinin musulunci, saboda haka yana da matuƙar mahimmanci ga ladanai su koyi yadda ya kamata su dinga kiran sallah, saboda kaucewa wasu kura-kurai na kiran sallah.

    Bugu da ƙari kuma, idan mutum ya yi mafarki suna ganawa da rana da wani mutum (mace ko namiji), sannan kuma a cikin watan azumin Ramadan, yaya azuminsa yake ?, amsa, azuminsa yana nan matuƙar a wannan yanayin hakan ta faru.

    Amma kuma idan mutum tunanin wani abu ne ko kuma ya kalli wasu abubuwa ne, sai ya fitar da wani abu daga gabansa mai kauri-kauri, sannan kuma fari-fari kamar ruwan kwakwamba ko ƙurji, to hukuncinsa shi ne, hukuncin wanda ya karya azumi da gangan, zai rama azumi guda sittin a jere na kaffara, sai kuma guda ɗaya wanda ya karya.

    Danna nan don karanta Guzirin Ramada Daga Rayuwar Sahabbai Da Magabata Na Gari

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Tambayoyin Azumi Da Amsoshi

    Tambayoyin Azumi Da Amsoshi

    Tambaya :- Idan mutum ya fara yin azumin kaffara zai iya hutawa ?

    Amsa :- Idan mutum  ya fara yin azumin kaffara ba zai iya tsayawa hutawa ba, sai idan yana da wata cuta, misali mace mai jinin haila ko wani mutum mai cutar gyambon ciki (ulcer) ko wata cuta ko hatsari ya samu mutum, wanda kuma  ba zai iya yin azumin ba, to wannan ya halatta a wannan yanayin mutum ya ajiye azumi har izuwa lokacin da mutum ya samu lafiya.

    Misali idan mace tana yin azumin kaffara, sai kuma hailarta ta zo mata, sai ta ajiye azuminta, bayan ta ɗauke mata, sai ta ci gaba da azuminta daga inda ta tsaya, haka ma mutum mai ciwon gyambon ciki zai aikata ko wanda wata cuta  rashin lafiya ta same shi zai aikata.

    Amma idan mutum lafiyarsa ƙalau, sannan  kuma babu wani dalili da shari`ar musulunci ta amince da shi na jingine ko ajiye azimi, har sai ya gama azuminsa a jere, idan kuma ya ajiye azuminsa a wannan halin, to dukkanin azumin da ya yi a baya sun rushe, sai ya sake tun daga farko.

    Misali idan mutum ya yi azumi guda hamsin da tara, sai yace bari ya huta,  idan Allah ya kai mu jibi ya ƙarasa cikon azumin guda ɗaya, to azumin da ya yi a baya sun ruguje, dole ne sai ya sake lissafi tun daga farko. Saboda haka yana da matuƙar mahimmanci a kanmu mu yi la`akari sosai a kan irin waɗannan matsaloli da sauran su.

    Tambaya: Idan mutum yana saduwa da matarsa a cikin watan azumin Ramadan sai alfijir ya fito, to yaya hukuncin azuminsa yake ?

    Amsa : Idan wani mutm yana cikin ganawa da matarsa sai kuma alfijir ya fito, azuminsa ya karyer matuƙar ya yi Inzali, sannan kuma akwai kaffaran azumi a kan su guda sittin (60).

    Tambaya: Mutum ne yake kwance bayan alfijir ya fito  ko bayan an yi sallar Asubah, sai matarsa ta zakke masa ,to yaya matsayin azumin su yake ?

    Amsa: Azuminsu ya ruguje ko ya rushe, sannan kuma akwai kaffaran azumin guda sittin a kansu. Bugu da ƙari kuma malamai sun ce ” mace ba za ta iya zakkewa ɗa namiji ba kai tsaye kuma ta yi Inzali ba tare da shi namijin yana so ba, Allahu a`alamu.

    Tambaya : mace ce take yin azumi, to kuma ya rage saura kamar mintuna biyu a sha ruwa, sai hailarta ta zo mata, ko lokacin haihuwarta ya yi, to yaya matsayin azuminta yake?

    Amsa:  Duk wacce haka ta faru da ita, to azuminta na wannan ranar ya rushe, sai ta sake wani azimin bayan an sha ruwa, amma kuma babu kaffara a kan ta.

    Tambaya: Menene hukuncin mutumin da ya aikata wani abu wanda yake karya azumi, amma kuma shi a lokacin da yake aikata wannan abun, shi bai san hukuncin aikata haka ba?

    Amsa:- Duk wanda ya aikata wani abu, saannan kuma a lokacin da yake aikata abin shi kansa bai san hukunci aikata haka ba, babu laifi a kansa, saboda Allah (S.W.A) ba zai kama mu ba da abin da muka aikata bisa ga rashin sanin hukuncinsa ba. Sai ya roƙi Allah gafara a kan abin da ya aikata, sannan kuma yana da matuƙar mahimmanci a kan musulmi duk abin da zai aikata a rayuwarsa ya san hukuncinsa, Allah yasa mu dace.

    Domin karanta Azumin Watan Ramadan danna nan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Azumin Watan Ramadan

    Azumin Watan Ramadan

    Azumin watan Ramadan, wajibi ne a kan kowane musulmi, kuma wanda yake baligi, sannan kuma mai hankali, saboda mara hankali zai iya aikata duk abin da ya ga dama kuma a lokacin da ya so, ba tare da yin la`akari da halaccin ko haramcin abin da yake aikatawa ba, saboda babu hankali a tare da shi a lokacin da yake aikata haka.

    Haka kuma azumi yana zama ko tabbata ne, saboda cikar watan sha`aban (kwanaki ashirin da tara ko talatin) ko kuma saboda ganin jinjirin watan Ramadan da yamma, kafin ko bayan sallar magariba ta hanyar gani da ido ko samun labarin ganinsa (wata) a  wata jihar ko  garin ko unguwa, ta hanyar wasu mutane amintattu kuma masu halaye masu kyau haɗi da mu`amala mai kyau a tsakaninsu da mutane.

    Saboda haka da zarar mutane sun ga wata ko sun samu labarin ganin wata daga wajen irin waɗancan mutane, to azumi ya zama wajibi a kan mutum sai ya yi ko ya ɗauka, haka kuma za a aikata ko lura a lokacin ajiye azumi, ta hanyar ganin sabon tsayuwar watan shauwal ko ta hanyar cikar watan Ramadan kwana lokacin talatin(30).

    Bugu da ƙari kuma, ana iya ɗaukar niyyar azumin watan Ramadan ne, bayan ko a lokacin da mutum ya samu labarin ganin wata ko ya gani da idonsa kafin fitowar alfijir, saboda tabbatar tsayuwar watan Ramadan.

    Sannan kuma idan mutum ya ɗauki abincisa zai ci, to kafin ya fara cin abincin, dole ne sai ya tabbatar ya wanke hannunsa ko cokalin da zai ci abinci da shi haɗi da bakinsa, sannan kuma sai ya ƙulla niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko takatin.

    Misali, idan mutum ya ɗauki abincinsa ya ajiye a gabansa, kafin ya fara cin abincin, sai ya yi Bismillah,  sannan yace “Allahumma Inni nawaitus siyamu Ramadan tis`a wa ashiruna au salasuna” ko kuma mutum yace “Nawaitus siyamu Ramadan tis`a wa ashiruna au salasuna” .

    Ma`ana ya Allah na yi niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko guda talatin.

    Saboda haka idan mutum ba zai iya faɗar wancan kalma ba da larabci, to zai iya faɗar kalmar da harshen Hausa ko Fulatanci, Barbanci, Yarabanci ko harshen da yake iya magana da shi, hakan ya halatta, Misali “Na yi niyyar yin azumin watan Ramadan guda ashirin da tara ko guda talatin”,. amma kuma an fi so mutum ya faɗa da larabci.

    Bugu ƙari kuma, idan mutum ya yi niyyar yin azumin watan Ramadan tun a daren da aka ga wata, ma`ana tun niyyar da ya yi na azumin sa na farko,to wannan ya isar masa a cikin dukkanin azuminsa na wannan watan, saboda babu wani sharaɗi a kan mai yin azumi na sake yin niyya a cikin kowane azumi ko rana, matuƙar azumin na sa a jere zai yi, amma kuma idan ba a jere zai yi su ba, saboda wata matsala, to dole ne a kansa  sai ya sake yin niyyar azumin a duk lokacin da zai yi(azumi).

    Sannan kuma  yana daga cikin sunnah yin azumi gaggauta shan ruwa da jinkirta yin sahur, ma`ana da zarar mutum ya ji an kira sallar magariba, sai ya yi saurin shan ruwa (da dabino ko “yayan itatuwa ko ruwa) kafin mutum ya yi sallar magariba, saboda haka ne ma yake da matuƙar kyau ko ake buƙatar a samu kamar mintuna  huɗu ko biyar a tsakanin kiran sallah da yin sallah.

    saboda mutane su samu damar aikata wancan sunnah ta azumi kafin suyi sallah, amma kuma ba dole ba ne sai mutum ya aikata haka, amma kuma aikata haka yana da matuƙar kyau sosai, soboda sunnah ce ta annabi Muhammmad (Sallallahu alaihi wasallam).

    Sai kuma jinkirta yin sahur, ma`ana kada mutum ya tashi cikin dare ya yi sahur, ma`ana kamar misalin ƙarfe biyu na dare ko kafin a kira sallah na farko, amma kuma idan mutum ya aikata haka azuminsa ya yi, sai dai bai aikata sunnah ba.

    Haka kuma mutum ya nisanci cin abinci ko abin sha a lokacin da alfijir yake fitowa ko a lokacin da ake kiran sallah na biyu, saboda ana buƙatar a samu kamar mintuna goma  ko mintuna goma sha biyar(15) a tsakanin kiran sallah da gama yin sahur, amma idan mutum ya sa abinci a cikin bakinsa, sai kuma ya ji ana kiran sallah na biyu ko asubah, to sai ya yi sauri ya fitar da abin da yake bakinsa, saannan kuma ya kuskure bakinsa sai ya ci gaba da yin azuminsa.

    Danna nan don karanta Yaƙe-yaƙen Annabi SAW A Watan Ramadan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Chinese Rice

    Yadda Ake Chinese Rice

    Tukunyar Ramadan tare da ni Ummulkhair Sani.

    A yau za mu ga yadda ake haɗa Chinese Rice.

    ABUBUWAN BUƘATA:-

    Shinkafa.
    Karas.
    Peas.
    Albasa.
    Ƙwai.
    Tattasai.
    Butter.
    Gishiri.

    YADDA AKE HAƊAWA:-

    Da farko za ki fasa ƙwanki a cikin ƙaramin kwano sai ki yanka masa albasa, ki saka gishiri kaɗan ki ajiye a gefe. Sai ki kawo tattasai, albasa, karas, ki yayyanƙa ki ajiye a gefe.

    Ki ɗauko karas ɗinki ki samu abu mai kyau ki zuba masa ruwan zafi da baking powder ki rufe na wasu mintuna sai ki tace. Ki kawo peas ɗin ki, ki juye a kwano sai ki zuba masa ruwa sosai sannan ki tace. Bayan nan sai ki haɗa dukkanin kayan lambunki a wuri guda ki ajiye. Za ki samu non-stick pan ɗin ki ki ɗora a kan wuta ki samu butter ɗinki ki riƙa juyawa kamar dai yadda kike miyar ƙwai. Idan ya yi sai ki ɗauko kayan lambunki ki zuba a kai kina juyawa a hakali saboda kar ya kama. Sai ki kawo dafaffiyar shinkafarki ki zuba a ciki ki yi ta juyawa har sai ta soyu sai ki juye.

    Ki samu plate mai kyau ki juye a ciki. Ana ci da miya.

    Danna nan don karanta Yadda Ake Garin Kunun Aya

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Shawara Ga Masu Ciwon Suga

    Shawara Ga Masu Ciwon Suga

    Mutane masu larurar ciwon siga ku daure kullum musamman wajen alwalar safe ko la’asar kuke tsayawa ku lura da tafukan ƙafarku da tsakanin yatsu da kyau, saboda 60% kukan iya yin rauni ba tare da kun ji zafi ba ballantana ku sani, wanda a ƙarshe in aka yi rashin sa’a ƙwayoyin cutar da ke kan fata ko sarari, tsakar gida ko kan titi inda muke takawa suka sami damar hawa kan ciwom sai abu ƙarami ya zamto babba har ya yi muni.

    Da yawa ta inda matsalar gyambon ƙafa ke somuwa kenan a gareku, wanda ƙarshe sai an kai ga yanke kafa, A ƙalla duk awa 1 sai an yanke ƙafa dalilin ciwon suga, kimanin ƙafafu 24 ake cire wa a kullum cikin faɗin duniya.

    Don haka, muddin ka ga rauni a ƙafarka matsayinka na mai ciwon sugar, to ka hanzarta zuwa a duba a wanke a baka magani, kar ka kuskura ka ce ai zai warke da kansa tunda ba shi da girma.

    Haka nan wasu kan yi kuskuren cewa ai cin ruwa ne alhalin diabetic neuropathy ne don haka a lura da ƙafa, a lura da glucose control, Diabetes is not a joke. Banda yawo ba takalmi ko safa koda kuwa a tsakar gida ne, ake shafawa kafa mai sosai take santsi. Da an ji alamun ta fara yin dundurus, ko ba ta bari a iya bacci in dare ya yi to a nemi ɗaukin likita. A kuma dinga yanke farce koyaushe.

    Sannan a dinga rufe ido ana sa tsinken tsintsiya lokaci lokaci ana duddungurar tafin kafar musamman pressure points. ko kuma mutum ya rufe ido ya sa wani ya yi masa, ana jin cewa ba a jin sensation na taɓin ko kuwa in a taɓa mutum ba ya iya guessing yace guri kaza ne tunda idonsa rufe yake, to akwai buƙatar a je ga likita lallai kar a yi wasa, ba sai an jira an ga rauni ba.

    Allah shi taƙaitamana wahala, ya bai wa kowa lafiya.

    Domin karanta Ciwon Suga danna nan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Yanayin Damuwa (Depression)

    Yanayin Damuwa (Depression)

    Depression dai wani yanayi ne marar daɗi da mutum ke tsintar kanshi bayan wani abu marar kyau ya faru da shi, ko kuma haka kawai mutum ya tsinci kanshi cikin wani yanayi na rashin jin daɗin komai kuma ba ya sha’awar komai da kowa, wanda zai sa mutum ya riƙa tunanin ina ma ya mutu ya huta. Wani lokacin kuma mutum ya kasa bacci, aiki, cin abinci, kula da iyali, kula da jiki da sauran su.

    Depression shi ne a kan gaba wajen saka mutane su hallaka kansu da kansu, ko ta hanyar rataya ko shan guba ko cakawa kai wuƙa ko faɗawa ruwa.

    Wannan depression ɗin yana ɗaya daga cikin manyan matsalolin ƙwaƙwalwa ko in ce “PSYCHIATRIC EMERGENCY”.

    A duniya baki ɗaya a ƙalla mutum (miliyan 264) ke fama da depression kuma daga cikin su kashi 87% cikin ɗari mata ne ‘yan shekara 15 zuwa shekara 40. Ya danganta daga tsawon lokacin da mutum ke yi yayin da yake cikin damuwar kamar SHORT TIME (kwana ɗaya zuwa kwana uku) ko kuma LONG TIME (kwana 3 zuwa sati biyu har abin da ya fi haka)

    DEPRESSION YA KASU KASHI KASHI KANSHI, AKWAI:

    1. Endogenous_depression: Wato mutum zai tsinci kanshi cikin yanayi marar daɗi ba tare da dalilin komai ba, wannan ya samo asali ne daga:
    ✍Gado daga uwa (mafiyawa)
    ✍Rashin lafiyar ƙwaƙwalwa ko taɓuwar ƙwaƙwalwa
    ✍Rashin isasshen bacci
    ✍Wata rashin lafiya da ke damun hormones da sauran jiki

    2. Exogenous_depression ko kuma REACTIVE DEPRESSION: Wato idan wani abu ya faru da mutum na yau da kullum kamar:
    ✍Mutuwar miji ko mata/uba ko uwa
    ✍Sakin aure/ ƙara aure/kishiya
    ✍Rasa aiki/kora daga aiki
    ✍Wani bala’i na rayuwa
    ✍Faɗa ko rashin jituwa tsakanin ‘yan uwa, miji, mata, iyaye, dangin miji, dangin uwa ko uba da sauran su
    ✍Faɗuwa jarrabawa
    ✍Asarar dukiya ko faɗuwa takarar siyasa
    ✍Kamuwa da ciwo kamar HIV ko diabetes
    ✍Fyaɗe
    ✍Bayan haihuwa (peupherial blues)

    Waɗannan su ne kashe-kashen depression da muke da su. Amma wani lokacin ba koyaushe depression ɗin ke kasancewa ga mutum ba, yakan iya zowa mutum kamar haka:

    Biopolar: Da safe kana cikin damuwa amma da maraice ka kasance cikin farin ciki kamar ba kai ba.

    Unipolar: Ko ka kasance cikin baƙin ciki koyaushe ko kuma ka kasance kana cikin baƙin ciki amma komai kana iya yi ba ka gajiya.

    ALAMOMIN DEPRESSION

    Alamomin shi suna zuwa ta fuska biyu Wato, yanda mai depression ɗin ke ji a jikin shi:

    • Tsananin baƙin ciki da damuwa,
    • Mummunan tunani,
    • Tunanin mutuwa,
    • Mutum ya ji ba shi da amfani
    • Tunanin ba mai sonka
    • Jin haushin kowa da komai

    Don karanta Amfanin Aya Wajen Samar Lafiya A Jiki danna nan

    Alamar da mutane za su gane cewa wannan mutum yana cikin depression

    • Ramewa
    • Gumi (zufa)
    • Turowar idanuwa
    • Rashin bacci
    • Rashin cin abinci
    • Bugawar zuciya da ƙarfi
    • Hawan jini
    • Kaɗaita cikin ɗaki ko gida
    • Rashin son magana da kowa
    • Fushi
    • Rashin kula da kai kamar wanka
    • Kuka dare da rana

    MATAKIN DA YA KAMATA A ƊAUKA IDAN AN GA MUTUM CIKIN YANAYIN DEPRESSION /MATAKIN DA YAKAMATA KA ƊAUKAR WA KANKA

    1- Psychological care: Babban abu na farko da mai depression ke buƙata shi ne shawarwari masu kyau a kan yanayin da ya tsinci kanshi.

    • Kada ka danmu da kanka a kan abin da dole sai ya faru ga ɗan Adam kamar:
      -Mutuwa, mutuwar ɗan uwa da sauran su
      -Kishiya ko sakin aure
      -Kora ko rasa aiki
      -Asarar dukiya da sauran su

    Mutane da dama kullum sai sun fuskanci wannan matsalar kuma ba za a daina ba har duniyar ta ƙare, to don haka kada ki damu kanki a kan abin da ba za ki iya canjawa ba idan ya faru. Idan ke kaɗai ce ga mijin ki yace zai ƙara aure kada ki damu, 4 Allah yace ya yi kin ga ko yanzu akwai 2 zuwa. To meye na damun kai?

    Ya sani cewa rayuwar duniya ba komai kake so za ka samu ba, ko kuma ko me ka samu mai yiwuwa ne ya kuɓuce ma musamman idan ba rabon ki ba ne kuma idan mutuwa ce, to tabbas dole ce a kan kowa.

    Ki nemi amintacciyar ƙawa ki gaya mata matsalolin ki kada ki bar damuwa a cikin zuciyar ki, idan ba ki da ita, ki nemi ‘yan uwa ko wani wanda kika fi jin sanyi a wurin shi koda addu’a aka yi miki za ki ji sanyi sosai. Idan kuma babu, ki nemi ƙwararru a wannan ɓangaren wato GUIDANCE AND COUNCELING SERVICES insha Allah za a dace.

    • Yan uwa kuma ku saka mai damuwa a jiki kada ku bar shi ya kai ga hallaka kanshi ko ya kai shi ga wani ciwo daban
    • Kada mutum ya zauna shi kaɗai, ya riƙa shiga mutane da abokai ana hira, idan ma babu hali, ki/ka nemi masu irin matsalar ka ku zauna tare ku riƙa samun nishaɗi.

    2- Rehabilitation and care:

    • Idan aiki ne mutum ya rasa ko wani abu, ya nemi wani abun wanda ko bai kai ga wancan ba ya yi haƙuri da shi, rayuwar duniya ta ɗan lokaci ce, ba dole ne sai an sami abin da ake so ba 100%
    • ‘Yan uwa da abokai, ku kula da mai depression iya gwargwado kada ku watsar da mutum, sannna ku tabbata babu wuƙa ko kwalba ko wani mummunan abu kusa da shi ko ɗakin shi wanda aka san zai iya hallaka kanshi da shi. Ku sani, ba yin kanshi ba ne duk abin da ya yi.

    3- Spiritual care: Dukkan mu musulmi mun yadda da Allah kuma mun yarda da ƙaddara, a nunawa mutum cewa komai ya gani daga Allah ne, kuma jarrabawa ce, mai yuwa ne ta yi masa sanadin shiga aljanna.

    4- Diversion: Ka yi wa kanka maganin depression da abin da ka san ya fi faranta maka rayuwa kamar rawa da waƙa, sauraren music ko ƙuran, karatun littafan na nishaɗi ko soyayya, kallon films ko drama ko games da sauran su. Duniyar mai ƙarewa ce, don haka NO NEED TO WORRY ABOUT ANYTHING. An haife ka ba ka da komai, kuma ba za ka koma da komai ba, to meye don ka rasa wani abun?

    5- Drugs: Idan abun ya gagara, ana bai wa mutum magungunan da ke sa bacci, tabbas suna rage depression kuma suna sa mutum bacci, amma kada mutum ya dogara da magani, ya yi ƙoƙari ya fahimci rayuwar duniya kuma ya yi ƙoƙarin ƙauracewa wannna abin da ke sa shi damuwa, saboda maganin zai iya zame ma mutum addiction ko maganin ya daina aiki.

    Abu na ƙarshe: Ba kowacce damuwa ce depression ba, rayuwa dama an yi ta da farin ciki da baƙin ciki, don haka mu lura, damuwa idan an ɓata ma rai ko ka yi asarar abu ta ɗan lokaci ba matsala ba ce, matsala ita ce idan waɗancan alamomin da na lissafa sun faru da mutum.

    Domin karanta Cutar Damuwa danna nan 

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Tarihin Dr. Mujahid Abdullahi Kudan

    Tarihin Dr. Mujahid Abdullahi Kudan

    An haifi Mujahid Abdullahi a ranar 29/03/1987 a unguwar Zaɓi, wacce take kusa da unguwar Saidawa a garin Kudan, kuma cikin ƙaramar hukumar Kudan, a Jihar Kaduna. Ya fara karatun sa ne a Model Primary School Kudan a shekara ta 1995-2000. Ya yi karatu a Barewa Collage Zaria a shekara ta 2000-2006, ya yi karatun digirin sa na farko  a Jami’ar Jihar Kaduna (KASU) a shekara ta 2007-2012 ɓangaran Hausa.

    Haka kuma ya yi karatun digirin sa na biyu a jami’ar Ahmad Bello (ABU) ɓangaren Hausa a shekara ta 2014-2017. Bugu da ƙari kuma sashin addinin ma ya yi karatun sa dai-dai gwargwado.Har ila yau, ya koma jihar Katsina, don yin digirinsa na uku. Wanda a ranar Alhamis 20/02/2025, ya samu damar kammala digirinsa na uku (PhD).

    Koyarwa/aiki

    1.Ya yi aiki a sashin koyar da harsuna na jami’ar Kaduna (KASU) a matsayin mataimakin malami (assistant Lecturer) a watan takwas shekara ta 2018 zuwa yau (August 2018 to Date).

    2.Ya yi aiki na wucin-gadi da DFID/UKAID a matsayin mai tallatawa haɗi da wayar da kai (Mobilizing for Development Project) daga August 2013- December, 2017.

    3.Ya yi aiki a sashin koyar da harsuna na jami’ar Kaduna (KASU) a matsayin mai kula da ɗakin karatu na Jami’ar  daga watan September 2012 zuwa June 2013.

    4. Ya zama mataimaki na bincike akan harkan yaɗa labarai na yanar gizo-gizo ga shugaban Ƙaramar hukumar Kudan daga watan August 2016 zuwa March 2017. Da sauran su

    Muƙalolin sa

    1. Rubutaccen Wasan Kwaikwayon Hausa a ƙarni na Ashirin Da ɗaya.

    2. Bugun Gaɓa a Waƙoƙin Aminu Ladan Abubakar (Alan Waƙa).

    3. Ɓurɓushin Nakasa a Adabin Hausa: Tsokaci Daga karin magana”.

    4. Bara Cinikin Su Makaho.

    5. Tubalin Samuwar  Ilimin Boko Da Rubutaccen Zuben Hausa”. (haɗin gwiwa da  Malumfashi, I)

    6. “The Impact of International Organizations in Promoting Local Governance in Nigeria.

    7. Hankaka Mai Da ɗan Wani Naka.

    8. Adabin Bara.

    9. Salon Tallace-Tallacen Magungunan Gargajiya a Kasuwar Maƙarfi (wannan takardar ba a bugata ba).

    Lambobin yabo

    1.Kwamitin dattijan malamai na Jami’ar KASU sun ba shi lambar girmamawa da jajircewa wajen tsayawa tsayin daka da kawo ci gaba ga ɗalibai na ajin farko da na aji na biyu da kuma na aji na uku (100 Level, 200 Level and 300).

    2. Ɗalibi mafi ƙwazo a ɓangaran Hausa a makaranatar Barewa College Zaria, 2006.

    3. Ɗalibi mafi ƙwazo na biyu a makarantar Model Primary School Kudan, 2000.

    4. Ɗalibi mafi ƙwazo a ɓangaran harshen Hausa da Turanci, Model Primary School Kudan, 2000. Da sauran su.

    (Mun samu waɗannan jawaban ne daga bakin Mujahid Abdullahi Kudan ta hanyar rubutawa da ya yi ya turo min ta WhatsApp a ranar Alhamis 15/10/2020)

    Danna nan don karanta Manufar Rayuwar Duniya

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Tsayar Da Update Na Windows 8 Da Kuma 10

    Yadda Ake Tsayar Da Update Na Windows 8 Da Kuma 10

    So da yawa mutane na kukan cewar idan sun haɗa wayar su da computer; Domin yin amfani da yanar gizo (browsing). Suna ganin Data nasu yana saurin janyewa, musamman masu amfani da Windows 8 ko 10 da ma sauran makamanta su.

    Update : Saboda haka a wannan ɗan bayanin nawa zan faɗi yadda za a yi amfani da waɗannan hanyoyi domin tsayar da zuƙar Data a sakamakon Update da window 8 ko 10 yake.

    Ga Wasu Matakai Guda (4) Da Za su Taimaka;

    1. Danna Windows logo key + R a lokaci guda domin shiga wajen Search Run box.

    2. Sai a rubuta services.msc sai a danna Enter.

    3. Sai a yi ta tafiya ƙasa ko a nemo Windows Update, sai a danna kanshi sau biyu.

    4. A gurin da aka rubuta Startup type, sai a shiga domin zaɓar “Disabled”. Sai a zaɓi “Apply” sai a danna kan “OK” domin ajiye saitin da aka yi.

    Shikenan da waɗannan hanyoyi ka tsayar da zuƙar data da ake maka sakamakon kusan kowannne windows musamman window 8 da 10 suna ɗaukar abubuwan da suka san cewa za su taimaka wa tsare-tsaren computer su tai dai-dai lokacin da aka haɗa computer da tsarin shiga yanar gizo wato (Internet Data For Browsing).

    Domin Karanta cikakken bayani A kan Yadda Hashtag Yake danna nan

    Domin karanta bayani a kan Tarihin Komfiyuta (Computer) danna nan

  • Haƙƙoƙin Mabiya A Kan Shugabanni

    Haƙƙoƙin Mabiya A Kan Shugabanni

    Su kuwa mabiya suna da waɗannan haƙƙoƙi a kan Shugabanninsu:

    1. Tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi da mutuncin mabiyansa. Wajibi ne ya kula da tsaron kan iyakoki, ya yi maganin ‘yan fashi da ɓarayi da ‘yan ta’adda. Ya kula sosai da jin daɗin jami’an tsaro da iyalansu ta yadda za su samu ƙarfin gwiwa da kishin kare ƙasa.

    2. Kulawa da addini da bunƙasa shi ta hanyar jan managartan malamai a jiki da neman shawarwarinsu da fatawoyinsu da sauraron karatuttukansu da wa’azin su.

    Kada ya bar kafirci ko bidi’a ko lalata da masu yinsu su samu sakewa har su kafu a inda yake da iko. Ya ƙarfafa koyar da ingantacce sahihin addini bisa koyarwar ƙur’ani da sunna da fahimtar magabata na ƙwarai.

    3. Wajibi ne shugaba ya kula da al’amarin musulunci, kada ya yi sakaci da salloli biyar a cikin jama’a ya ringa halartar sallolin juma’a da na idi, ya kula da yadda limamai suke gabatar da huɗubobi, da karatuttukansu, ya kula da ladanai da kiran salla daidai.

    4. Ya naɗa alƙalai masana masu adalci da tsoron Allah da kamewa, ya sanya idanu sosai a kansu, saboda sai an tuhume shi kan duk shari’un da suka yi, zai kuma samu lada kan adalci da taimako da suke yi wa mutane.

    5. Wajibi ne a kan shugaba musulmi ya ringa fita jihadi da kansa, sannan kuma ya tura mujahidai suna yi a ƙalla sau ɗaya duk shekara. Gwargwadon ikonsa. Koda kuma ya yi sakaci da sauran nau’o’in jihadin.

    6. Aiwatar da Shari’ar Allah da hukunta masu laifi ba sani ba sabo kamar yadda Allah ya shari’anta da manzonsa, kada ya kuskura ya yi wani hukunci da ya saɓawa shari’ar Allah Ta’ala.

    7. Ya kula da tattalin arziƙin mabiyansa da jin daɗinsu da walwalarsu. Ya tabbatar yana bin hanyoyin da shari’a ta yarda da su domin samun kuɗin shiga kamar zakka, ganima da jizya, ya kuma sarrafa su ta hanyoyin da shari’a ta yi izini a sarrafa su.

    8. Kafa hukumar kula da waƙafi da tsara al’amarinsa ta yadda kowa zai amfana da shi, mutane kuma su samu ƙarfin gwaiwar bayar da kafa waƙafin.

    9. Yin adalci wajen rabon arziƙin ƙasa da gudanar ayyukan ci gaban al’umma.

    10. Wajibi ne shugaba ya kasance mai gaskiya da riƙon amana ya guji zalunci da nuna son kai da bambanci tsakanin mabiyansa.

    Shahararren malamin nan masanin siyasar musulunci Abul Hassan Almawardi Rahimahullahu ya faɗa a cikin sanannen littafinsa ‘Al- Ahkamus sultaniyya cewa akwai haƙƙoƙi goma a kan shugabanni.

    A taƙaice su ne;

    1. Kiyaye addini daga gurɓata.
    2. Tabbatar da doka da oda da bai wa kowa haƙƙinsa.
    3. Tabbatar da tsaro a birane da ƙauyuka.
    4. Tabbatar da hukuncin Allah ba sani ba sabo.
    5. Tabbatar da tsaron kan iyakoki.
    6. Yin jihadi domin ɗaukaka addinin Allah Ta’ala.
    7. Tattara kuɗin shiga da sarrafa su ta hanyar da shari’a ta yarda da su.
    8. Rabon arziƙin ƙasa da biyan ma’aikata albashinsu.
    9. Naɗa amintattu mutanen kirki masu gaskiya a kan muƙamai.
    10. Sanya idanu a kan dukkanin al’amuran mabiyansa da wanda ya naɗa su kula da ɓangarorin gudanarwa kada ya bari kowa yake cin karensa ba babbaka.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Halaye Da Siffofin Shugaba Nagari danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

     

  • Yin Kabbara Da Tasbihi Yayin Da Ake Tafiya

    Yin Kabbara Da Tasbihi Yayin Da Ake Tafiya

    “Allaahu akbar”. {Allah ne Mafi girma}.

    Idan kuma muka zo gangara sai mu yi tasbihi {wato mu ce}:

    “Subhaanal laahi”. {Tsarki ya tabbata ga Allah}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’ar Matafiyi Idan Ya Riski Ƙarshen Dare (Dai-dai Lokacin Sahur) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’o’i Domin Neman Tsari Daga Azzalumai danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Hausawa Da Al’adunsu danna nan.