Rabiu Musa Adam
“Sannan mun yi wasiya ga mutum da ya kyutata wa mahaifansa, mahaifiyarsa ta yi goyon cikinsa cikin wahala sannan ta haife shi cikin wahala…” (Q 46:15)
Wata rana cikin watan satumba na shekarar 2024 na je jihar Legas ɗan halartar wani horon aiki. Bayan na isa ne, na hau motar haya dan ƙarasawa inda zan halarci horon, da yake da safe ne, a kan hanyar mu sai na hango wani yaro ɗan makaranta da bai wuce shekara goma (10) ba da mahaifiyarsa a gefen titi suna jiran abin hawa, mahaifiyar tana ta gyara wa yaron takalminsa da safarsa, sannan tana ta ƙoƙarin shafa masa wani abu kamar man shafawa, a zato na yaron ne ya shafa man shafawan amma bai yi yadda ya kamata ba, mahaifiyar take gyara masa.
Duk wannan abin da mahaifiyar ta ke yi, yaron yana tsaye kamar ba da shi ta ke ba. Wannan abinda ya faru ya sani tunani sosai game da lamarin iyaye da ‘ya’ya.
Allah maɗaukakin sarki saboda girmama sha’anin iyaye bai taƙaita lamarinsu ga masu Imani ko musulmi kaɗai ba, za mu iya fahimtar haka ne a ayar da take cikin Suratul Ahkaf, aya ta 15 in da Allah ya yi kira ga “mutum” kowa da kowa ke nan, ba wai wasu gungun mutane na musamman ba.
Kalmar da Allah ya yi amfani da ita na “mutum” ya ƙunshi musulmi, mumini, fasiƙi, munafiki, kafiri da duk wani jinsi na mutum, sannan ya umurce shi da ya yi wa iyayensa biyayya. Biyayyar iyaye ana buƙatar ta ne daga duk wani mutum. Mahaifiyar da na gani da ɗanta, daga yanayin shigarta babu alamar musulma ce, amma ku dubi yadda ta ke yi wa ɗan ta. Shi ya sa Allah a aya ta 23 ckin Suratu Isra’i, ya yi kira ga mutum da ya bauta masa, ya kuma jingina hakan da yi wa iyaye biyayya.
Kira zuwa ga bautar Allah kira ne ga kowa da kowa, toh haka ma kira zuwa yi wa iyaye biyayya ta shafi kowa da kowa. Iyaye suna yin duk abinda za su iya ne wurin su ga sun kyautata rayuwar ‘ya’yan su a nan gaba, suna ƙarar da ƙarfinsu, abinda suke da shi, su na haƙura da jin daɗinsu, su ma sa kansu a wahala don kyautata rayuwar ‘ya’yansu, idan ta kai su rasa rayuwarsu ma iyaye a shirye suke su rasa rayuwar su don ‘ya’yansu. Babu wanda zai iya yin wannan in ba iyaye ba. Duk waɗannan abubuwa ba su taƙaita ga wani mai addini ba, duk an haɗu a kan wannan babban lamarin.
A aya ta takwas cikin suratul ankabuut Allah ta’ala cewa ya yi “ mun yi wasiya ga mutum da ya kyautata wa iyayensa, da za su yi maka umarni da ka yi shirka da Ni kan abinda ba ka da ilimi, toh kada ka yi musu biyayya (kan wannan umarnin na yin shirka)” A wannan ayar ma Allah kai tsaye ya kira mutum bai ware wani ba, sanan ya ba da wasiyar yi wa iyayye biyayya da kyautatwa.
Ya kuma nuna ko da kuwa iyayen nan kafirai ne, ba a bai wa mutum dama ya saɓa musu ba. Idan iyaye waɗanda ba musulmi ba, suka umurci mutum da ya yi shirka da Allah, toh sai ya ƙi musu biyayya kan wannan umurnin na yin shirka da Allah, amma haƙƙin biyayya yana nan a wuyan sa dole.
Wannan ayar tana ƙara nuna mana ce wa iyaye ko suna saɓa wa Allah, to wajibi ne a yi musu biyayya a dukkan ɓangarori na rayuwarsu. Inda kawai ba za a yi musu biyayya ba shi ne inda su ka yi umarni da a saɓa wa Allah. A abin da ya shafi biyayya wanda yake kan kowane mutum, Allah ne a gaba, sannan iyaye ba tare da babancin imani ko rashin sa ba.
Iyaye wasu mutane ne na musamman da Allah ya zaɓa kuma ya fifita, ba wai dan haihuwar mutum da suka yi ba kaɗai, har ma da irin gudumawar da suka bayar a cikin rayuwarsa.
Shi yasa a hadisin Manzon Allah SAW wanda Amr bin Shu’aib daga Babansa daga Kakansa ya ce wani mutum ya zo wurin Manzon Allah SAW ya ce: Mahaifina yana da buƙata da dukiyata, sai Manzon Allah SAW ya ce: “kai da dukiyarka duk na mahaifinka ne” Wannan ya ƙara tabbatar mana da matsayin iyaye a wurin mutum, ba wai ma shi kansa kaɗai ba har ma abinda ya mallaka na iyayensa ne, suna da damar yin abinda sukaga dama a ciki.
Amma yanzu sai ka ga mutum yana yi wa iyayensa rowa kawai don Allah ya yi masa arziƙi. Shi bai san arziƙin nan da Allah ya ba shi da shi kansa duk na iyayen sa ne ba. Idan kuma ya ƙi musu abinda suke so a cikin dukiyarsa ba tare da yin almubazarranci ba, toh ya sani yana da laifi mai girma a wurin Allah.
Waɗanda ba musulmi ba, idan ba su yi wa iyayensu biyayya ba, toh bayan laifin shirka da Allah akwai kuma na ƙin bin umarnin Allah dangane da ƙin yi wa iyayesu biyayya. Shi kuma musulmi da ya saɓa wa iayayyensa, ko da yana da wasu ayukan laheri sai an kama shi da laifin ƙin wa iyayensa biyayya.
Allah ya hore wa kowane mutum bin iyayensa da kyautata musu, wannan yasa za a ga wanda ba musulmi ba, yana kyautata wa iyayensa, a kuma sami musulmi mai ƙin biyayya ga iyayensa. Babu abinda ya kai wannan takaici. Kamata ya yi a ce wanda ya fi kowa bin umarnin Allah, shi ne wanda ya fi yi wa iyayensa biyayya da kuma kyautata musu.
Haka kuma, Allah ya tsara idan mutum ya kyautata wa iyayensa, toh shi ma sai ‘ya’yansa su kyauatata masa.
Rabiu Musa Adam
Deceember 25th, 2024.
Danna nan don karanta Ni’imar da Allah Ya Yi Wa Mutane Ba Tare Da Sun Fahimta Ba
Edita:@rumasau-kallamu