Tag: yadda ake

  • Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya samar da ƙungiya ta aiwatar da kiɗa mai zurfin tunani wadda kuma ta amsa sunanta. A wannan ƙungiya Ɗanƙwairo shi ne Jagora, kuma yana ba ‘Y/Amshi nasa damar yin ƙari da ajewa da sauka da saukar sauka da takidi da rakiya ko karɓeɓeniya, wani bi ma da bayayyeniya, sannan da yin takidi na G/Waƙa.

    Haka kuma a rera wasu waƙoƙi Alhaji Musa Ɗanƙwairo yakan tafi da Sanƙirori da wasu hadiman waƙa duk a ƙungiyar kiɗa ta Musa Ɗanƙwairo.

    Da kansa Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya nuna yadda yake aiwatarwa da ƙullawa da rerawa da sadar da ɗiya a waƙoƙinsa a wannan ɗa na waƙarsa ta ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II, mai G/Waƙa:

    Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe:

    Jagora: Duk Makaɗan da at Tsahe nai jam’i,
    : Hab baƙi ha ‘yan gida su duka,
    ‘Y/Amshi: Babu mai shirya waƙa kamat tawa,
    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla wuƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    : In nuk ƙulla waƙa a ƙara man,
    : Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki raini ba.
    Jagora: Ga mu hwa! Ga mu hwa!!

    (Ɗan’ƙwairo, Waƙar Musa Ɗanƙwairo ta ‘Yandoton Tsahe Aliyu & Gusau, 2003: sh. ɗi)

    Domin haka, Musa Ɗanƙwairo yana ƙullawa da rera ɗiya na waƙoƙinsa a yayin sadarwa kamar haka:
    +Ƙungiya
    + Jagora (+Ƙulli)
    + ‘Y/Amshi (+Ƙari +ajewa +sauka +saukar sauka +takidi +rakiya +karɓeɓɓeniya +/-Bayayyeniya +ciko ko maimaita ko takidin G/Waƙa)
    + Sanƙira (Mai Kalato Ƙarin Bayanai)
    + Hadiman Waƙa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa ƊanƘwairo Maradun ta Kiɗan Kotso ta haɗa da:

    i) Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun = Jagora

    ii) Muhammadu, Daudun Kiɗa na Farko, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iii) Garba, Zawacin Kiɗa, Marafan Kiɗa,
    Daudun Kiɗa na Biyu (2), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iv) Audu, Wakilin Kiɗa = Kiɗa da Amshi

    v) Ali, Sabon Kiɗa (ɗan Sa’idu Shayi, Wani Ƙanin Musa Ɗanƙwairo) = Kiɗa da Amshi

    vi) Sani, Zaƙin Murya, Marafan Kiɗa, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    vii) Abubakar (Garba), Ciroman Kiɗa (ɗa), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    viii) Ibrahim Sarkin Fada (Ƙane) = Kiɗa da Amshi

    ix) Muhammadu Jikka (Jikka, Halifa 3) = Kiɗa da Amshi

    x) Sani (Jika) = Kiɗa da Amshi

    xi) Muhammadu Gambo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xii) Malam (Bara) = Sanƙira, Kwandon Ɗanƙwairo

    xiii) Ƙanƙahu (Bara) = Tsaron Kaya

    xiv) Sada (Bara) = Sanƙira

    xv) Rabo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvi) Nabuba (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvii) Bucaca ‘Yarkohji (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xviii) Amadu Bakura (Bara) = Sanƙira

    xix) Sallah Kwana (Bara) = Hadimin Gidan Ɗanƙwairo

    xx) Daudu Ɗangaladima (Bara) = Kula da Doki da Gona

    Domin karanta cikakken bayani akan Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    A lokacin da makaɗi ya zo yin waƙar baka tun a ƙwaƙwalwarsa da tunaninsa yake fara tsara ta. Wannan tsari shi ne na baɗini, wanda yake a rattaɓe a zuciyarsa kuma a cikin jumlolinsa.

    To, tun daga wannan lokaci ne ya riga ya yi waƙarsa ta baka ta bin waɗannan matakai:

    – Matakin Ƙullawa
    – Matakin Kiɗa
    – Matakin Rauji
    – Matakin Kalmomi
    – Gindin Waƙa
    – Layuka ko Saɗaru a Ɗiya 
    -Nuna Farin Ciki
    – Nuna Baƙin Ciki
    -Faɗakarwa
    -Gargaɗi
    -Ilmantarwa
    -Nasihantarwa
    – Isharantarwa
    -Yabawa
    -Yin Zambo
    -Yin Habaici

    Da Sauransu Kamar Kalmomin Azancin Magana

    Matakin Ƙullawa

    Makaɗan baka sukan ƙulla waƙoƙinsu ta azanci da fasahar da suke da su.
    Ma’anar ƙulli ta ƙamus:

    A ƙamus na Hausa-English (Awde, 1996: 102) ya nuna Ƙulli shi ne (1) to knot (2)to plan (3) to conspire; wato (1)ya ƙulla (2) ya shirya ko ya yi dabara (3) ya haɗa kai. Shi kuma Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 285) cewa ya yi ƙulla, ita ce ɗaura ko ƙudura.

    Ma’anar Ƙulli ko Ƙulla ko Ƙullawa ta isɗilahi wato ta fannin ilimin waƙar baka. Ita ce:

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya faɗi yadda yake ƙulla waƙarsa a inda yake cewa:

    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla waƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    Jagora: In naƙ ƙulla waƙa a ƙara man,
    ‘Y/Amshi: Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa Maigida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki reni ba.

    (Ɗanƙwairo, Waƙar ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II (1960-1991)

    Ƙullawa ta waƙoƙin makaɗan baka tana da matakai biyu. Akwai ƙullawa ta makaɗan ƙungiya, sannan akwai ƙullawa ta makaɗan kaɗaita. Ga su kamar haka:

    i) Ƙullawar Makaɗan Ƙungiya

    Waƙoƙin baka na Hausa waɗanda ake ƙullawa ta ƙungiya, waƙoƙi ne waɗanda ake tunaninsu ta tsakanin Jagora da kuma ‘yan amshinsa. Ita ƙungiya ita ce wadda ta ƙunshi Jagora da kuma yaransa masu yi masa amshi na waƙar baka da kuma yin kiɗa.

    Har wa yau, ƙungiya ta ƙunshi ‘yan ma’abba ko san-ƙirori ko masu kirarin baki. A wannan lokaci, za a haɗa ƙarfi da ƙarfe tsakanin Jagora da ‘yan amshinsa, a dinga tunanin yadda za a shirya waƙa, musamman ta kawo jumloli da yadda za a tsara saɗaru ko layuka, sannan ana yi ana dakatawa ko lumfasawa. Wannan shi ne ƙulla waƙa ta makaɗan ƙungiya.

    Su kuwa makaɗan kaɗaita, su ne waɗanda Jagororinsu kawai za su dinga ƙulla kalmomi da jumloli, amma yaransu, za a sami waɗanda suke yin amshi wato +ciko kawai, sai dai ba su yi musu kowane irin ƙari a waƙa. Akwai wasu jagororin da ba a ce musu ko ƙala, Jagora ne zai ƙulla waƙarsa kuma ya ƙare ta shi kaɗai. Irin wannan ƙulli jagora ne kawai zai yi tunanin waƙa a baɗininta idan ya gama ƙulla ta sai ya zo cikin yaransa ya rera ko ya je wani wuri ya sadar da ita. A irin wannan waƙa, Jagora ne kawai ake jin muryarsa yana rera waƙa, yana sadar da ita ga jama’a.

    A bisa waɗannan matakai ne ake bi, ake ƙuƙƙulla, waƙoƙi na gargajiya ko waƙoƙi na zamani na baka da Hausawa suke yin tunaninsu a baɗini, daga baya su rera su a yayin da suke sadar da su.

    Matakin Kiɗa

    A Ƙamusun Hausa an nuna kiɗa yana nufin bugun ganga ko kalangu ko abun bugawa ko bugun ƙwarya ko goge ko garaya ko taushi ko kotso da hannu ko da makaɗi ko da wani abu (CNHN, 2006: 243).

    A ilimin fannin waƙar baka, kiɗa yana nuni ne da wani amo ko sauti da ake samarwa ta gwama ko haɗa abubuwa biyu kamar dutsi + dutsi ko tafi + tafi ko baki + ƙahon dabbobi ko ganga + gula (makaɗi) ko wani abu + wani abu ko sauransu. Kiɗa kuma yakan zama wani amo ne wanda yakan shiga jikin mai sauraro, ya sa masa karsashi har ya dinga rausayawa, yana tattakawa ko jujjuyawa.

    Gusau (2008: 54) yana ganin kiɗa shi ne wanzar da amo mai shiga jiki wanda kuma ake aiwatarwa ta haɗa abubuwa biyu ta matakin busawa ko tafawa ko bugawa ko kaɗawa ko gogawa ko girgizawa ko kuma wasun waɗannan.

    Akwai kayayyakin kiɗa da dama. Wasu na gargajiyar Hausawa ne, wasu kuma na baƙin wasu al’ummu ne waɗanda Hausawan suka aro, suna amfani da su. A wajen Hausawa akwai kiɗa zallarsa kawai, ba tare da haɗawa da waƙa ba, ko kirari ko kaɗa take. Akwai kuma kiɗa ta amfani da kayan kiɗa wanda ake haɗawa da waƙa, wanda kuma ake yi wa waƙoƙin da makaɗan baka suke yi.

    Kiɗa a wajen Hausawa ya rarrabu zuwa: Kiɗa

    -waƙa +take -take +waƙa
    -Waƙoƙin Gaɗa
    -Waƙoƙin Samartaka
    -Waƙoƙin Manyan Mata
    -Waƙoƙin Manyan Maza
    -Waƙoƙin Makaɗa

    A wajen aiwatarwa ta waƙar baka akan gwama ta da amon kiɗa wanda za su dinga tafiya a tare tsakanin muryar makaɗi da sautin gangar da makaɗin yake amfani da ita. Bisa mahangar makaɗa, akwai wasu hanyoyi da ake ɗora kiɗa na waƙoƙinsu na baka domin su yi daidai da yadda ake sadar da su. Waɗannan hanyoyi sun haɗa da:

    – sadar da kiɗa daidai da nauyi na muryar makaɗi da kuma raujin da aka zaɓa wa matanin waƙa;
    – Dacewar amon kiɗa da gaɓoɓin murya bisa gurabunta na hawa da sauka da kuma faɗuwa;
    – Ƙarfafa madirar gaɓoɓi;
    – Wani bi a kaurara amon kiɗa;
    – Wani bi a sassauta amon kiɗa;
    – Wani bi a ja amon kiɗa;
    – Wani bi a matse ko a tauye amon kiɗa;
    – Wani bi a qwairanta amon kiɗa;

    Sannan kuma yanayin kiɗan yana iya zama:

     Mai diri
     Mai ƙarfi
     Mai kauri
     Mai zaƙi
     Mai kumbura
     Mai kaurara
     da sauransu

    Matakin Rauji

    Ƙamus na Hausa a ɓangaren Hausa-English (Awde, 1996: 131) ya bayyana kalmar rauji da clapping wato yin tafi ko ban tafi (Awde, 1996, 131 & 210). A kuma littafin Ƙamus na Keɓaɓɓun kalmomi wato Hausa Metalanguage ya fassara Rauji da Ingilishi da Rhythems wato Kari ko karin murya (Awde, 1996:361).

    A fannin ilimin waƙar baka kuwa, rauji wani sauti ko amo ne wanda yake tashi a sama ko ya sauka ko ya faɗi. Rauji yana iya zama murya ta wata halitta mai rai ko sautin wani abu maras rai kamar ƙara ko doka ƙafafu a bisa ƙasa ko wani tsando ko sauti daga kukan tsuntsaye. Har wa yau kuma akwai rauji mai ɗaɗi, mai zaƙi da kuma rauji maras daɗi, mai-ta-da-hankali, kamar kukan kanari (rauji mai zaƙi) da kuma kukan jaki (rauji maras zaƙi, mai ɗaukar hankali).

    Wata ma’anar isɗilahi kuma, rauji na iya zama masaukar murya a gaba.

    A yayin da aka gwama rauji a waƙar baka ta Hausa ana ɗora shi bisa muryoyi na gaɓoɓi na kalmomi ne waɗanda akan sarƙa su a tayar da saɗara a ɗa na waƙa. Rauji wanda aka zaɓa, aka ɗora wa saɗara ko layi a ɗa na farkon waƙa, shi ne zai dinga daidaita rauji a dukkan layuka da ake ƙullawa a ɗiya na waƙar.

    Nauyin rauji a waƙar baka ta Hausa gajere ne, shi ya sa yake tafiya bisa gaɓoɓi na kalma gwargwadon hawansu da saukarsu da faɗuwansu. Matakai waɗanda ake bi a wajen samar da rauji a waƙar baka ta Hausa sun haɗa da:

    – Rauji mai dogon zango
    – Rauji mai gajeren zango
    – Rauji mai matsakaicin zango

    Sannan gaɓa ta rauji za ta iya zama mai nauyi wadda za ta ƙunshi [bww] ko [bwb], ko kuma ta zama mai sauƙi wadda za ta iya zama gaɓa mai [bw] kawai.

    A wajen furta rauji na waƙar baka ana yi masa waɗannan abubuwa kamar haka:

    – Kaurara gaɓa mai nauyi;
    – Jan gaɓa mai nauyi ko mai sauƙi;
    – Daidaita amsa-amon kari (hawa ko sauka ko faɗuwa) a ƙarshen kowace saɗara ko layi.

    Haka kuma ana yin rauji ne na waƙar baka daga karin murya (na hawa da sauka da faɗuwa) da kuma amon kiɗa tun daga tunanin makaɗi a zuciyarsa. Domin haka, ana samar wa waƙoƙin baka rauji ne ta waɗannan hanyoyi:

     Karin murya daga makaɗin waƙar;
     Amon kiɗa daga kayan kiɗan da makaɗi yake amfani da su, ta la’akari da madiransu na hawa da saukar amo ko kuma faɗuwarsa.
     Daga nan sai a fitar mata da raujinta;
     Rauji zai samar wa waƙar baka wani amo wanda zai fitar da ita kaɗai daga sauran waƙoƙin baka na makaɗin.

    Matakin Kalmomi

    Kamar yadda aka nuna a baya, idan makaɗin baka ya tashi aiwatar da wata waƙa ta baka, yakan fara aiwatar da waƙar ne a cikin zuciyarsa da kuma ƙwaƙwalwarsa tun kafin ya furta waƙar a waje. Haka kuma tunanin makaɗi na kalmomi da yadda zai sarrafa su cikin azanci da hikima shi ne wani abu da zai biyo biyo baya a aiwatar da waƙar baka.

    Sannan kuma dukkan makaɗi na ƙungiya da kuma makaɗi na ƙire duk suna yin aiwatarwa a wajen daidaita waƙoƙinsu da tsawaita su. Matakin kalmomi yakan bambanta dangane da kalmomi da makaɗi ya yi tunaninsu ko kuma ya zaɓo su wajen tsawaita waƙar da zai yi. Wasu daga cikin kalmomi da ake zaɓa a shirya waƙar baka sun haɗa da:

    Kalmomin Shirya Gindin Waƙa

    Gindin waƙa furuci ne na wasu kalmomi masu ma’ana masu nauyin saƙo, masu hikima da balaga da azanci waɗanda ake shiryawa don a gabatar da waƙar baka. Ta gindin waƙa ne ake rarrabe ɗa da ɗa a waƙar baka. Waƙoƙin baka sun kasu kashi biyu. Akwai waɗanda ake yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Abdu Karen Gusau. Sannan kuma akwai waƙoƙin da ba a yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Babangida Kakadawa.

    Ga Misali na Gindin Waƙa:

    G/Waƙa: A lula ɗan haya,
    : Mai gyaran kekuna.
    (Abdu Karen Gusau; Waƙar Alhaji Alula Ɗanhayar Kekuna, Fagge, Kano)
    Har wa yau kuma, Gindin waƙa yakan bayyana abin da waƙa take nufi tun kafin a shiga cikinta. Gindin waƙa wani ginshiƙi ne ko babban matangali na ginin waƙar baka. Wani kuma harsashe ne ko majingini na farko a waƙar baka, inda duk bai zauna ba, waƙa ba za ta ba da sha’awa ba, balantana har ta yi wani armashi.

    Idan makaɗi ya sami zaunuwar Gindin waƙa, to, zai sami haske ya buɗu a gare shi, ya sami walwala ta zaɓo kalmomi waɗanda suka dace ya saka a waƙa waɗanda za su ba shi damar samun sauran ɗiyan waƙar. Makaɗin baka yakan yi tunani a zuciyarsa idan kuma wanda suke a ƙungiya ne sukan haɗa ƙarfi da azama su samo kalmomi zaunannu kuma mafi girkuwa a waƙar da suke shiryawa ta baka su samar da Gindinta.

    A wajen shirya Gindin waƙa makaɗa sukan yi amfani da waɗannan matakai:

    Yawanci Gindin waƙa bai shige layuka biyu (2) zuwa huɗu (4) ba;
    – Yakan ƙunshi kalmomi masu nauyi da ake sarrafa su cikin azanci da hikima;
    – Gindin waƙa yakan ƙunshi sunan mai waƙa ko laƙabinsa ko alkunyarsa ko wata ƙarina da ke nuna Mai waƙa;
    – Sannan ana wakiltar Gindin waƙa da harafin [X] na ABCD;
    – Ana kuma wakiltar adadin saɗaru ko layuka a Gindin waƙa da alkalumma na [1,2,3,4] kamar haka: [X1] ko [X2] ko [X3] ko [X4] da sauransu;

    – Ga misalai:

    i) Gindin Waƙa; (mai layuka huɗu (4)
    X1: Ka bawai maza,
    X2: Na Magajin Gari Bubakar,
    X3: Kai ad da yanzu,
    X4: Allah ya ba ka Sarkin Kabi.
    (Mamman Inyaga Argungu; Wakar S/Kabi Muhammadu Mera. Wato kalmomin nuna farin ciki).

    ii) Gindin Waƙa; (mai layuka biyu (2)
    X1: Tankwafau namijin zaki,
    X2: Sa’idu bai taɓa tsoro ba.
    (Idi Ɗangiwa Zuru: Waƙar Sarkin Sudan Sa’idu, Kwantagora. Wato kalmomin nuna farin ciki)
    – Yawancin kalmomi masu nauyin ma’ana da hikimar zance da makaɗa suke tsarawa a Gindin waƙa sun ƙunshi na nuna farin ciki ko na nuna baƙin ciki. Misalin Gindin waƙa na kalmomin nuna baƙin ciki:
    G/Waƙa: X1: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa
    (Shata: waƙar ‘Gagarabadau, Mp3)

    – Kuma wani Gindin waƙar yakan ƙunshi kalmomin yabawa ko na zambo ko na habaici da na zugugutawa da makamantansu. Misali:

    G/Waƙa: X1: Ya ci maza ya kwan yana shirye,
    X2: Gamda’aren Sarki Tudu Alu.
    (Narambaɗa, Waƙar Tudu Alu; Kalmomin zuga da kururantawa da yabawa).
    Akwai kuma a wani G/Waƙa:
    X1: Madogara na Malam,
    X2: Iro Uban Bawa,
    X3: Maigida Shinkahi.
    (Narambaɗa, Waƙar Magajin Garin Shinkahi, Ibrahim; Kalmomin zuga da yabawa).

    – Haka kuma wani Gindin waƙar yakan ɗauki kalmomin faɗakarwa ko gargaɗi ko ilimtarwa ko isharantarwa ko nasihantarwa da sauransu. Misali:
    G/Waƙa: X1 “Yan Nijeriya sai Hausa
    (Abdu Karen Gusau; waƙar Harshen Hausa-kalmomin kishin Hausa da na gargaɗi da na ilimantarwa. Gusau, 2015: 64-75).

    G/Waƙa: X1 Mu kama sana’a ‘yan Nigeriya,
    X2 Zaman banza ba namu ne ba.
    (Abdu Karen Gusau, Waƙar Gargaɗi kan riƙo da sana’a – kalmomin gargaɗi da na faɗakarwa da na isharantarwa, Gusau, 2015: 75-78).
    G/Waƙa: X1 Shegiyar ƙafa ke kika saba da gulando,
    X2 Ki tallafe ni, ɗaukar ni ƙafa kar ki gaza ni.
    (Abdu Karan Gusau, Waƙar Shegiyar ƙafa – Kalmomin faɗakarwa da na gargaɗi da na isharantyarwa. Gusau, 2015: 96-97).

    Layuka ko Saɗaru a Ɗiya

    Layuka jam’i ne na layi (tilo). A Ƙamusun Hausa (CNHN, 2016 206-304) an faɗi ma’anarsa kamar haka: (i) Miƙaƙƙen zane (ii) miƙaƙƙiyar hanya ta cikin gari, ko jerin rumfunan kasuwa ko wani abu (iii)majalisar alƙalai ko kotu ko ɗakin shari’a. Amma kuma a ƙamus (Hausa-English) na Awde (1996:106) ya bayyana Layi (p/layuka) da harshen Inglishi da Line. A kuma ɓangaren ƙamus ɗin na English-Hausa, Awde

    (1996: 295) ya fassara line da noun=n=: (1) layi (2) Baiti (3) Telephone line wato waya. Ta Fuskar Saxaru (Jam’i); saɗara (tilo) kuwa – Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 381) ya fassara ta da layi cikakke na rubutu.

    A cikin layuka ne ko saɗaru waƙar baka take shirya saƙonni tun a ƙwaƙwalwa, sannan ta rera su, ta sadar da su ga al’umma; ta amfani da mataki na kalmomi waɗanda suka haɗa da nau’o’i daban-daban.

    Kuma har gami da kalmomi na maganganun habaici da isharantarwa da gargaɗi da ilimantarwa da tunasarwa da faɗakarwa da makamantansu da yawa.

    A waƙoƙin baka na Hausa akan shirya layuka ko saɗaru masu sauƙi a ƙagi ɗa na waƙar baka wanda zai ƙunshi saƙo ɗaya kawai. Akwai kuma layuka ko saɗaru da ake shiryawa masu tsauri, waɗanda za su haɗu su tayar da ɗa ɗaya na waƙar baka. Shi ɗa ɗaya mai tsauri yakan ƙunshi saƙonni da yawan gaske kamar guɗa huɗu (4) ko ma fiye da haka waɗanda ake wakiltarsu kamar haka:

    Ɗa ɗaya mai tsauri:
    A1:
    A2:
    B1:
    B2:
    B3:
    C1:
    C2:
    C3:
    C4:

    Da sauransu. Za a ba da misali na ɗan waƙa mai sauƙi (Mai saƙo guda ɗaya kawai) kamar haka:
    A1: Ni kam lafiya nit taho salla,
    A2: Lafiya ni ishe Sarki,
    X1: Amadun Bubakar gwarzon Yari,
    X2: Dodo na Alƙali.
    (Narambaɗa, waƙar Sarkin Gobir Ahmadu Bawa (1935-1975).

    Shi kuma ɗan waƙa ɗaya mai tsauri (mai Saƙonni da yawa fiye da ɗaya), ga wani misali kamar haka:

    A1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    A1.1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    B1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B 1.1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B3 Da kyauta da ilimi da neman dalili,
    B4 Da gode ma Allah da istingfari,
    B5 Da su Bello ɗan Shehu yat tsarmo kowa,
    B6 Ka kai kamar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa yak kai,
    B6.1 Ka kai ka mar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa ya kai,
    X1: Bajinin gidan Bello Mamman na Yari,
    X2: Sarki Kudu Macciɗo ci maraya.

    (Sa’idu Faru, waƙar Muhammadu Macciɗo lokacin yana a matsayin Sarkin Kudun Sakkwato, ya rasu a 1995 yana Sarkin Musulmi).

    A layi na ɗan waƙa ana wakiltar sa da alƙalumma na [1-0], da haruffa na ABCD ban da [X] kamar yadda aka gani a misalan da suka gabata. Har wa yau kuma ana iya wakiltar ɗan waƙa ta jan layuka kawai. Misali:

    Ɗanwaƙa mai layuka biyu ko uku
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    3 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Ko ɗa mai layuka biyu
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Saƙonni a ɗa na waƙa, bisa yawanci ba su shige layuka guda biyar (5). Misali: A1, B1, C1, D1, E1, wato saɗo na ɗaya (1) zuwa na biyar (5).

    A layuka ne kuma ko saɗaru ake tunani a zuciya a gina saƙo na farin ciki ko na baƙin ciki ko na faɗakarwa ko na tunasarwa ko na gargaɗi ko na ilimantarwa ko na isharantarwa ko na yabawa ko na zambo ko na habaici ko na wani saƙo da makaɗi yake son ya gaya wa al’ummarsa a harshen waƙar baka.

    Alalmisali:

    Jarora: Yara farau-farau farar tabarma,
    : Farin cikin mai baƙunta,
    Y/Amshi: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    (Shata, Gagarabadau; Gusau, 2018:20)
    Akwai kuma
    Jarora: Ga wani ya yi ilimi babu hankali,
    : Ga dai ilimi babu nutsuwa,
    : An kira shi Dabtan ya amsa,
    : Da ganin ƙurji sai ya yaɓa wuƙa,
    Y/Amshi: Na gode wa Amadun Gaya.

    (Shata, Waƙar Amadun gaya; Gusau, 2018: 23)

    A lokacin da makaɗa suke yin tunanin baɗini na wata waƙa da za su shirya sukan bambarta a wajen yin wannan tunani da kuma samo kalmomi na waƙa.

    i) Wasu makaɗan sukan zauna a ƙarƙashin wata inuwa kamar ta wata bishiya, su kwanta su lulluɓe kansu, suna tunanin wata waƙa. Alalmisali, Alhaji Ibrahim Narambaɗa, idan yana tunanin waƙa har zana tunanin nasa yake yi a ƙasa, ya dinga shata wani zani ko zane-zane kamar zai zana wani hoto na musamman. Zai dinga zanawa a ƙasa a cikin layuka, ya dinga yin zane-zane, yana tsara saɗaru na waƙa.

    ii) Wasu kuma makaɗan sukan dinga jefo wasu kalmomin suna sarƙawa suna kuma zubar da wasu, suna warwarewa, har su haɗa kalmomin da suke buƙata na waƙar. Wasu makaɗan, kamar Salihu Jankiɗi, har tattaka ‘yan amshinsa yake yi, suna zazzaune, idan sun jefo wasu kalmomi da ba su dace ba.

    Ta haka dole ɗan amshi ya yi taka-tsantsan da abubuwan da yake ba da tasa gudummawa.

    iii) Wasu makaɗan, musamman makaɗan ƙire (kaɗaita) sukan sami saulin yin tunani ne a yayin da ‘yan amshinsa suke maimaita kiɗa, su kuma makaɗan sukan yi shuru, suna numfasawa. A lokacin da kuma sanƙirorinsu suke ba da tasu gudunmawa, su kuwa makaɗan (Jagororin) suna yin shuru, suna saurarensu. Da sauran halayen makaɗan kaɗaita. A duk lokacin da makaɗan suka yi shuru suna tunani ne a kan abubuwan da za su ƙara ƙulla waƙoƙinsu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Sadarwa a Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita, RMK

  • Hutun Alhamis Da Juma’a A Tsangayu

    Hutun Alhamis Da Juma’a A Tsangayu

    Saboda irin himmar makaranta a tsarin tsangaya, alarammomi kan lazimtawa almajiransu yin karatu a wasu lokutan daban-daban bayan karatun safiya da maraice kamar haka:

    Tashe:-

    Akan tashi almajirai cikin dare jim kaɗan bayan fara barci da niyyar cigaba da kwami ko kuma tilawa. Wannan shi ne tashe ko jadare. Yanayin karatu a tsangaya kuwa kan ɗauki siffofi da dama musamman ma don ƙarfafa juna misali:-

    Musaffa:- Makarantan da suka tara tilawa kan haɗu a wasu lokuta musamman da dare su yi ta karatu a yanayin karɓa-karɓa ma’ana ana zagaya da’ira da tilawar sumuni-sumuni ko rubu’i-rubu’i. Da haka har a sauke ko kuma zuwa wurin da ya sauwaƙa. Da yawa makaranta kan kwana suna zuba tilawa a yanayi irin na musaffa ko tuƙuri.

    Ranakun Al’hamis da Juma’a su ne ranakun hutu a tsangaya. Wannan kuwa ya samo asali ne tun farkon Musulunci a lokacin da Sayyadina Umar ya yi tafiya ƙasar Sham kuma ya Jima Bai dawo ba. Wannan ya sa mutanen Madina cikin damuwa. Ko da labarin isowarsa ya iske su, sai kowa ya fito zuwa tarbo shi. Wannan ya sa yara ‘yan makarantar allo ba su yi karatu ba yini guda.

    A ranar Juma’a kuwa Amirul Muminina ya iso. Don haka aka ba su hutu kuma ya Zama hutun makarantunmu na Alƙur’ani.

    Domin karanta cikakken bayani akan Azuzuwa Da Kashe-Kashen Makaranta A Tsangaya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ma’anar Tsangaya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Asalin Samuwar Goni

    Asalin Samuwar Goni

    Asalin kalmar Gwani/Goni kalmar Barbarci ce “Luhranni Gonni” ma’ana wanda ba ya kuskure in yana karanta Alƙur’ani.

    Kalmar Gwani dai-dai ta ke da Al’mahir da kalmar Al-Mukri, ma’ana ƙwararren makarancin Alƙur’ani. Kamar yadda mai irin wannan matsayi ake kiransa Fakih a Masar ko kuma Karmako a Senegal.

    Yaɗuwar amfani da matsayin Gwani tsakanin makaranta ya samo asali ne tsakanin ƙarni na goma sha zuwa ƙarni na goma sha tara a Maiduguri bisa sharaɗin makaranci ya sanya allo a gaban malaman Marte ko Gawala ko Konduga. To a nan ne za su ga can-cantar a naɗa makaranci a matsayin Gwani.

    A baya-bayan nan makaranci ba ya zama Gwani har sai ya sa allo gaban Goni Dala a Monguno ko kuma marigayi Goni Ƙashim cikin Maiduguri.

    Ga misalin ɗaya daga sarƙa ko silsilar naɗa Gwani tun kimanin sama da shekara ɗari huɗu da goma sha shida a Barno, wadda ta ke tuƙewa kan Goni Musa Dongol, farkon wanda aka fara kira Goni a tsohon birnin Ngazargamu. Wannan silsila ita ce “Daga Imam Mahir Sheikh Goni Isa ɗan Sayyid Adam wanda aka fi sani da Walda Am jileji daga Mahir Alwali Salih Goni Hamid Kidik daga Goni Bukar Konduga daga Mahaifinsa Goni Mustafa Yabe daga 120 Musa Afgalbiyama daga mahaifinsa Goni Nukabi Bardi daga mahaifinsa Goni Kadai daga Goni Mele daga Goni lbrahim Al’aysar daga Mahaifinsa Goni Umar Jundi daga Mahaifinsa Goni Musa Dongol”

    Tsokaci:

    Akwai saɓani a wasu lokutan wurin wasu malamai game da matsayin Gangaran. Shin wane ne gaba tsakaninsa da Gwani? Wannan ya biyo bayan wani shahararren makarin zance “gangaran ka fi gwani”. Ala ayyi halin Gwani shi ne mafi karɓuwar ajin ƙoli a azuzuwan makaranta, kamar yadda ya gabata. Amma fa a yanzu ba a ɗabbaƙa sharuɗan da a da sai makaranci ya cika su sannan ya samu matsayin Gwani.

    Shi kuwa Gangaran har yau sai wanda karatunsa ya bushe raƙayau sannan za a kira shi da wannan laƙabi. Ma’ana dai a yanzu in har ka ga wanda makaranta ke kira Gangaran to kusan za a iya cewa ya fi gwanin da aka naɗa ba tare da ya cika sharuɗan ba.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ɗabi’un Makaranta da Halayensu Cikin Zamantakewar Tsangaya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Kasance A Cikin Zikiri Kowane Lokaci danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Ƙalubale Ga Makarantun Tsangaya

    Ƙalubale Ga Makarantun Tsangaya

    Kamar yadda tarihi ke maimaituwa kullum, cikin kowane al’amari mai kyau ba ka rasa baragurbi ko zare. Tsarin tsangaya ma bai tsira ba.

    Tarihin musulunci da rayuwar sahabbai (Radiyallahu Anhuma) ya isa ishara, domin kuwa tun sahabbai (Radiyallahu Anhuma) ba su ƙare ba aka samu wasu mutane waɗanda ke da’awar Musulunci sun fito sun kishiyanci musulmi na ainahi. Irin waɗannan mutane sun haɗa da Khawarijawa da ‘yan Hururiyah da Murji’awa da Mu’utazilawa.

    Aƙidun waɗannan mutane sun ci karo kai tsaye da aƙidun musulmi. Don haka dukkan musulmin da yake son ya wanzu cikin musulmin ƙwarai dole ya kauce wa aƙidu da ta’adun waɗannan mutane da muka ambata.

    Makaranta cikin tsangaya su ma ba su kuɓuta daga irin waɗannan mutane da aƙidu ba. Da yawa mutane na kallon ma’abota tsangaya gaba ɗayansu a matsayin wani ɓangare na wani gungu na irin waɗansu jama’u da suka yi ƙaurin suna. Yin hakan rashin adalci ne ga nagartaccen tsarin mu na tsangaya.

    Za mu ɗauki irin waɗannan gungu na makaranta masu waɗannan aƙidu domin mu ƙara nazari:-

    1. ‘Yan Tatsine: Tatsine ko ‘yan Tatsine wasu mutane ne da ke da’awar su musulmi ne, masu karatun Alƙur’ani a yanayin irin na ma’abota tsangaya. ‘Yan tatsine sun samo asali ne ko sun ƙara fitowa fili a lokacin da wani mutum wai shi Muhammadu Marwa daga Marwa da ke ƙasar kamaru, ya tara gardawa masu neman karatun ƙur’ani ta hanyar sihiri da yaudara da yin da’awar annabtar ƙarya. Wanda daga ƙarshe ya haddasa rikicin da ya jawo asarar rayukan dubunnan mutane da dukiyoyi a birnin Kano.

    Dukkan wanda ya rayu a birnin Kano ko a Najeriya ta Arewa a dai-dai wannan lokaci to kuwa ya san irin barazanar da Tatsine ta haifarwa al’ummar jihar Kano. Wannan al’amari ya jawo har yau ɗin nan akwai ɓurɓushin irin waɗannan ‘yan Tatsine masu aƙidun ƙin yarda da komai na Hadisi ko Tafsirin Musulunci daga bakin magabata, idan ba bisa irin fassarar son ransu ba.

    In ba a manta ba gwamnatin wancan lokaci ta kafa wani kwamiti sakamakon wannan rikici na mai Tatsine a shekarar 1981 mai suna Kwamiti Kan Almajirai (Almajirai Committee 1987) ƙarƙashin jagorancin Malam Isa Waziri da Mambobi guda goma.

    Ayyukan wannan kwamiti sun haɗa da:-

    1. Duba yadda za a inganta tsarin karatun almajiranci duba ga abubuwan rashin daɗi da suka faru.
    2. Nazari kan dokokin da za su kula da zirga-zirgar almajirai da shawarwarin yadda za a ɗabbaƙa su.
    3. Aunawa da gano irin yadda tsarin almajirai ke haddasa gurɓatar ɗabi’un almajirai da sauransu.

    Bayan kammala aikin wannan kwamiti, gwamnatin Guruf Kyaftin Muhammad Ndatsu Umaru ta fitar da matsayarta game da shawarar kwamitin wadda suka haɗa da:-

    1. Yin doka kan zirga-zirgar almajirai.
    2. Yi wa makarantun Alƙur’ani Rajista ta hanyar mai Unguwa ko Dagaci ko Hakimi.
    3. Damar ƙwace izinin kafa makaranta ko zirga-zirgar malami da almajirai da sauransu.

    Wannan ya sa mutane da yawa har zuwa yau ɗin nan suna kallon tsarin tsangaya a matsayin wani tsari da ke da haɗari kuma suna kallon almajirai da gardawa ko ma alarammominsu a matsayin masu alaƙa da tatsinanci.

    2. ‘Yan Ƙala-Ƙato: Wannan wani reshe ne na tatsinanci wanda mafi yawan mabiyansa ma’abota tsangaya ne. ‘Yan ƙala-ƙato mutane ne masu son yin bayani game da ma’anonin Alƙur’ani; bisa son zuciya da rashin ilimin fannonin musulunci da harshen Larabci. Ma’abota tsangaya kan ruɗu da bin ‘yan ƙala ƙato da riƙe aƙidunsu saboda:-

    i- Rashin neman ilmin fiƙihu da sanin ilmin harshen larabci wanda sai da shi ne za a iya fahimtar saƙon Ubangiji maɗaukaki bisa sahihiyar ma’ana sanin kowa ne makaranta a tsarin tsangaya a arewacin najeriya suna da tawaya ta rashin neman ilmi fannonii fiƙihu don gyaran Sallah da fahimtar sauran mas’aloli.

    Da yawa za ka ga gardi wanda ya rubuta alƙur’ani bai san hukuncin ƙabil da ba’adi ba hakan takan sa; wasu makaranta na ganin idan mahaddaci ya shiga fagen neman ilmin karatunsa ba zai yi inganci ba. Wannan matsala game da makaranta a tsangayun arewacin Najeriya ta zama ruwan dare. Saɓanin tsangayu a ƙasahen Gambiya da Senegal da Mali da Sudan; waɗanda ke da ɓangare guda na ɗaukar ilimai da sauran fannoni kamar su; Ahlari da Ishimawi a Fiƙhu da Alfiyya da Kaɗarun Nada a Nahwu da Lamiyya a ilmin Sarfu da Jawahir a fannin Balaga.

    Wannan ya taimaka da gaske wajen samun mahaddata masu wayewa da gogewa a ilmi daban-daban a irin waɗannan ƙasashe ta yadda ba za a iya yaudararsu ko a ruɗe su ba.

    ii. Da yawan makaranta musamman gardawa sun fi nuna ƙwaɗayinsu; wajen neman laƙani da asiri don samun shuhura tsakanin abokan hamayya da kuma samun jama’a. Wannan ya sa duk wanda ke da wani abu irin wannan to kuwa za su sallama masa; kuma duk wanda zai yi musu tsawa a kan wannan ba kasafai suke samun jituwa da shi ba. Don haka da yawa suke son laƙani ko da kuwa zai kai su ga fita daga Musulunci.

    3. ‘Yan Magaru: ‘Yan Magaru wasu mutane ne da ake danganta su da ma’abota tsangaya. ‘Yan magaru sun shahara da tsafi da surkulle. Su ma aƙidunsu abin ƙyama ne kuma ba adalci ba ne a danganta duk wani matsafi da AIƙur’ani ba ko da kuwa ya haddace shi ko ya rubuta shi. A lokaci guda kuma ba adalci ba ne yi wa ma’abota tsangaya dukkaninsu kallon irin waɗannan mutane.

    Duba da irin manyan Gwanayen Alƙur’ani kuma gwaraza a fagen fannonin ilmi irin su Gwani Hamad da Shehu Rabi’u Ɗantinki da makamantansu. Waɗanda ke kwaɗaitar da mahaddata kan su tsunduma cikin fannonin ilmi. Babu shakka an yanke hanzarin duk wani ɗan tsangaya, sai dai in son zuciya ne ya halaka shi.

    Matashiya

    Akwai wata ta’ada da ta yi gurbi a zukatan ma’abota tsangaya masu yawa; irin wannan ta’ada shi ne rashin gwama karatu da sana’a ko kasuwanci. Da yawa ma wasu malamai kan ce “in ka ga mahaddaci na sana’a ai karatu bai albarka ba”. Don haka za ka ga mahaddata Alƙur’ani sun fi son su yi tsibbu.

    A wasu lokutan ma’ana kyarar su a wajen sauke Alƙur’ani a gidajen masu kuɗi. A gaskiya idan da makarantanmu za su yi ƙoƙarin koyi da magabata; da ba a bar su kullum a raɓe a soraye ana yi musu kallon raini ba. Alhali Ubangiji Maɗaukaki Ya ba su abin da bai ba wa kowa ba.

    Ya kamata a samu alarammomi Teloli da Kafintoci da Ma’auna da ‘Yan kasuwa da dai duk wata sana’a da ba za ta hana malam yin karatunsa ba. Labarin Malam Na Maiganji a Sashe Na Huɗu na wannan littafi ya ishe mu ishara.

    Domin karanta cikakken bayani akan Hanyoyin Farfaɗo Da Tsangayun Alƙur’ani danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Asalin Tsibbu A Tsangayun Alƙur’ani danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Rashin Kogon Al’aura Ga Mata (GYNAETRESIA)

    Rashin Kogon Al’aura Ga Mata (GYNAETRESIA)

    Duk halittu sukan faro ne mataki bayan mataki har zuwa cikar halitta. Haka abin yake ko a mu mutane! Matakin farko shine bayan shigar ciki muna farawa da matakin “Ɗan tayi” wato ’embryo’ wanda a karshe wannan embryo din ne zai girma a sami dukkan sassan jiki dake nuna cikar halitta walau na jinsin Mace ko Namiji.

    Wasu muhimman sassa da ke rarrabe Namiji da Mace shi ne zubin al’aurarsu da bayyanar nonuwa a ƙirji in an cimma lokacin balaga.

    Sashin halittar al’aura, mazantaka da iya yi wa Mace juna biyu a namiji shi ake kira da “Mel rifurodoktib sistem” yayin da sashin zubin halittar mace, haila, da goyon ciki ake kiransa da “Fimel Rifurodoktib Sistem”

    Shi wannan sashi na FIMEL RIFURODOKTIB ya ƙunshi sassa irin su: Ƙwayayen haihuwa, mahaifa wato uterus, bakin mahaifa, bututun wucewar ƙwai da kuma can cikin farji…. Wannan sassa suke haɗuwa su samar da ɗa a gaba.

    Toh sai dai ina son mu sani wannan sashin yakan zamto an sami tangarɗar halitta tun sanda mace take jaririya a ciki amma sam ba a san da matsalar ba sai bayan da ta girma ko kuwa ta yi aure ma.

    KU SANI:

    1. Akwai macen da ke zamtowa tana da mahaifa wato uterus amma sam ba ta da ovaries. Sashin da ke samar da su bai tsiro ba, ta waje za ka ga kyakkyawar mace da nonuwa da komai to amma fa ta ciki tana da wannan naƙasun, don haka wannan macen ba za ta taɓa iya haihuwa ba. Shi yasa galibi sai bayan aure an ji ba labari an zo gwaji ake ganowa.

    2. Akwai macen da ke kasancewa maimakon kwanson ƙwayayen haihuwa guda biyu na hagu da dama…ita ɗaya gareta, Amma ba ta da mahaifa, ko kuwa mahaifar wani yanki ne ba complete ba ce… Wannan ma komi kyanta ta waje ba za ta taɓa iya haihuwa ba sai haƙuri.

    3. Akwai macen da akan haife ta da mahaifa ƙwaya biyu wato Biconuate. Wanda hakan ke nuna ko an sami ciki to aljihu ɗaya zai shiga kuma akwai hatsarin cewa cikin ba lallai ya zauna zuwa haihuwa ba, akwai hatsarurrukan da ka iya sa a rasa shi.

    4. Akwai macen da akan haife ta da rabin mahaifa, ita ma wannan sai can gaba ta gane ba za ta iya ciki ba ballantana ta haihu.

    5. Akwai me ƙofar farji biyu.

    6. Akwai macen da ba ta da farji, Eh ga shape da komi amma gajere ne, babu zurfi, ba hanya. Irin wannan in miji ya matsa mace ta hau kuka saboda azaba ya zaci ko a matse take tunda mutanen mu akwai wawan tunani wani lokacin. Bai san “Blind ended” vagina gareta ba.

    Mace ga nonuwa ga komi amma babu hanyar farji, musamman wannan na daga abinda ke janyo ciwo ko azaba yayin saduwa a mace me sabon aure. Sai daga baya a gane ba hanya ne kuma ba ta da cikakkiyar mahaifa don haka ba za ta iya ɗaukar ciki a haihu da ita ba, wanda galibi wasu Mace ba ta iya faɗawa miji wannan don ba lallai auren ya ɗore ba. Sai dai irin wannan mukan yi aiki Vaginoplasty mu ƙirƙiri hanyar farjin da za a ji daɗi da ita, amma dai ba batun haihuwa.

    Wannan matsalolin duk ta waje ba za ka iya sanin akwai su ba. Domin ta waje za ka sami mace cikakkiya a tsaye, a dire, nonuwa, hips, da kuma farjin in ka kalla da ido. Abin ta can ciki ne. Illa iyaka sai dai wasu da akan samu duk da ga Nonuwa ga cikar sura ta mace amma sam za su zo nema akan ba su taɓa ganin haila ba.

    Sun kai shekaru 17, 18, ko 20 amma mace tace har yau ba ta fara haila ba, ko kuwa ga alamu tana ji duk wata a keɓantattun kwanaki kamar haila amma babu jinin. Galibi wannan daga nan ne sai mun bincike sai mu gano ba ta da uterus. Infact wasu a nan muke tantance ta waje mata ne amma ta ciki maza ne.

    Wannan matsalar na ga ana ɗan samunta kwanan nan, gwanin ban tausayi, mutum yana ganin ya auri kyakkyawar matarsa amma ƙarshe farjin ne kurum ta ciki bayan scan za ka samu ba ta da mahaifa, ko ga mahaifa amma ba ovaries, ko kuma ga farji ta waje ras amma ba zai shigu ba. Duk ba abubuwa ba ne masu daɗi domin ba yadda za kai su haihu. Mai dama-dama ita ce me ovaries. Don akan iya cirar ƙwan a dasa a mahaifar wata macen ta haife mata. Duk da mu Musulmai hakan ya haramta garemu.

    Don haka kafin ka cewa babyn nan Yes akwai tarin abubuwan nazarta, ba iya Genotype ba ne, kasancewa mace na haila wannan ka kore wasu abubuwan da dama. Amma hakan bai kore matsalar. Haka abin yake ga wanda kan zo da ƙorafin rashin haihuwa sai bayan gwaji a gano mace ba ta cika ba a halitta ta ciki. Irin wannan yanayi na mace shi muke kira da GYNAETRESIA ko MÜLLERIAN AGENESIS.

    SHI YASA NAKE JAN HANKALINMU

    Lallai Yan-uwa mata ku dena watsi da magungunan FOLIC ACID da ake bai wa mata a watanni ciki na farko komi rashin daɗin warin su a daure a sha, daga cikin aikinsa shi ne ba da kariya daga irin wannan matsalolin dama sauran larurori da kan shafi jarirai.

    Domin karanta Mata Ku Ba Ni Kunnenku danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Ma’anar Alphanci da Simpanchi

    Ma’anar Alphanci da Simpanchi

    Amsa ga waɗanda ke tambaya a kan ALPHA DA SIMP

    Shi dai ALPHA wani mutum ne da yake da tunanin cewa mace ba ta da ‘yanci ko wata kima ko daraja a wajen namiji da ya wuce ta masa bauta, yana zare mata ido. Alpha yana ganin cewa bai kamata ana yi wa mace hidima ba, mace ba ta cancanci soyayyar namiji ko kulawa ba. Ko aurenta ya yi a wajensa ba ta da wani amfani daga gari ya waye ta gaishe shi sai ta masa girki ta wanke masa kaya ta goge, shikenan.

    A wajen Alpha ko dariya mace ba ta cancanci namiji ya mata ba sai bisa alfarma. ALPHA bai yarda da sakarwa mace fuska ba, kuma bai yarda cewa mace za ta iya komai ba, yana ɗaukar mace a matsayin wacce yake da ikon yi wa hawan ƙawara da mulkin mallaka yanda ya ga dama.

    Shi kuma SIMP, mutum ne da ya yarda mace na buƙatar kulawa da tattali da nuna tsantsar soyayya a gare ta, SIMP ya yarda ya zama dolo sakarai, wawa akan mace don kawai ya faranta mata rai, ya yarda zai iya kashewa mace ko nawa ne don kawai ya saka ta dariya, Simp bai yarda mace ta yi rayuwa cikin rashin ‘yanci da walwala ba, bai yarda mace ta zama baiwa walau a waje ko gidan aure ba.

    Simp mutum ne mai tausayin mace da son ganin rayuwarta ta inganta ta kowace siga. Sannan SIMP a wajensa mace ko ita ce da laifi ita ke buƙatar rarrashi da ban baki saboda raunin ta. Wannan shine bayani a takaice. Zaɓi ya rage wa mai shiga rijiya ko ALPHA ko SIMP.

    Saifullahi Lawal Imam.
    Jagoran Simpawa na Nozan

    Danna nan don karanata Iƙirarin Simpanci

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Sunnonin Ranar Juma’a

    Sunnonin Ranar Juma’a

    Ranar Juma’a, rana ce ta musamman a wurin Musulmai, rana ce babba, mafi daraja daga sauran ranakun mako. Rana ce da Allah ya zaɓa, kuma aka farlanta ibada ta sallah mai daraja a cikin ta. Rana ce da Allah SWT ya saukar da surah guda da sunanta.

    Saboda muhimmancin ranar, akwai wasu ɗabi’u da halaye da ladubba da ake so musulmai su riƙa aikatawa a kowacce ranar Juma’a.

    1. Yin wanka
    2. Sanya Turare
    3. Sanya tufafi masu kyau
    4. Yin asuwaki
    5. Neman dacewa da lokacin amsar addu’a
    6. Karanta Suratul Kahf
    7. Tafiya masallaci da wuri.
    8. Yawaita salati ga Annabi S.A.W.

    Allah ya ba mu albarkar ranar Juma’a.

    Danna nan don karanta Shakku a Cikin Sallah

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

     

  • Gudunmawar Mawadata Da Ɗaiɗaikun Jama’a Ga Tsangayu

    Gudunmawar Mawadata Da Ɗaiɗaikun Jama’a Ga Tsangayu

    Sanin kowa ne cewa ba kasafai gwamnatoci ko al’umma kan samu isassun kuɗaɗen da za su iya gamsar da buƙatun jama’ar da ke ƙarƙashinsu ba. Wannan wani al’amari ne da za a iya cewa ruwan-dare-gama-duniya.

    Koda ƙasashen Turai da suka shahara wajen cigaba, ba duka ne ke da irin wannan wadata ba. Kodayake mu mutanen Najeriya mun ginu bisa tunanin komai sai hukuma ta yi mana. Ta kai ta kawo abubuwan da za mu iya haɗa hannu da juna mu yi wa kanmu maganinsu; ba ma yi sai dai mu zauna har matsalar ta illata mu.

    Bisa wannan ne na ke son bayyana wa mai karatu wani abin ban sha’awa game da; yadda al’umar ƙasashen Sudan da na Gambiya suke sharewa tsangayunsu hawaye. Ta yadda babu wata tsangaya a ƙasar Sudan da ke zaune cikin gini ruguzajje ko ka ga wani almajiri na bara a faɗin ƙasar. Wani abin mamaki game da ƙasar Gambiya kuwa shi ne; jama’arsu da ƙasarsu ba su kama ƙafar Najeriya da ‘Yan Najeriya wadata da arziki ba.

    Amma duk da haka suna samar wa da tsangayunsu buƙatunsu na yau da kullum. Mawadaci ɗaya a irin waɗannan ƙasashe kan gina ilahirin tsangaya daga aljihunsa; gini irin wanda za ka ce wata hamshaƙiyar ma’aikata ce ta gwamnati. Ashe da abin a zuci yake. Tsangayar Wadil Fadni da tsangayar Umadawwanban ko tsangayar Shiekh Ɗaha da ke Umdurman sun isa misali.

    Domin suna da gidan gona kamar wani katafaren kamfani ga shanu ga amfani tsibi-tsibi, ga Alaramma kamar wani Sarki.

    Binkice ya nuna cewa kaso arba’in cikin ɗari na tallafin da tsangayunsu ke samu na zuwa ne daga jama’ar gari; kaso talatin zuwa arba’in kuma na zuwa daga gwamnati.

    Don haka ya zama wajibi gare mu da mawadatanmu da ma’aikatanmu da ‘yan kasuwarmu da mazanmu da matanmu, yaranmu da manyanmu mu kwaikwayi mutanen ƙasashen Sudan da Gambiya wajen jiɓintar al’amarin tsangayu da almajirai ta hanyar:-
    – Ciyar da su
    – Gina musu wuraren kwana
    – Girmama su da karrama su.

    Domin karanta cikakken bayani akan Koyo Da Koyar Da Alƙur’ani Zamanin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Da Sahabbai danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ɗabi’un Annabi (S.A.W) Suke danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Wa Ya Kashe Husaini (Radiyallahu Anhu)?

    Wa Ya Kashe Husaini (Radiyallahu Anhu)?

    Shin Ahlussunna ne suka kashe Husaini (Radiyallahu Anhu)? Ko Mu’awiyya ne? Ko Yazidu ne?

    Amsar wannan tambayar ba ta buƙatar dogon bayani, saboda shi da kansa Husaini (Radiyallahu Anhu) ya ba da amsar wannan tambaya; haka nan ma Aliyu ɗan Husaini (Radiyallahu Anhu) wato Zainul Abidina da Ummukulsum ‘yar sayyidina Au (Radiyallahu Anhu) wato ƙanwar Husaini waɗanda a gabansu komai ya faru; sannan kuma akwai waɗansu manyan malaman shi’a cikinsu har da masu muƙaman ayoyi duk sun ba da amsar wannan tambaya.

    Dukkansu bakinsu ya zo ɗaya a kan cewa ‘yan shi’a ne suka kashe Husaini! Ga maganganunsu daga amintattun littatafansu babu ƙari babu ragi.

    1-Maganar Husaini (Radiyallahu Anhu)

    Imam Husaini (Radiyallahu Anhu) ya tabbatar da cewa waɗannan ‘yan shi’ar da suka gayyato shi sun yaudare shi sun warware mubaya’ar da suka yi masa, sun koma bayan rundunar da suka zo domin yaƙarsa sai ya ce: “Idan kuma kun ƙi (mara baya, kun saɓa alƙawari, kun warware mubaya’a da kuka yi min, na rantse ba wannan ne farau ba a cikin mugwayen ayyukanku.

    Irin haka kuka yi wa baba na da ɗan uwana, da dan Baffa na Muslim, haƙiƙa duk wanda ya yarda da ku ya yaudari kansa”. Kuma tun da farko shi da kansa ya ɗan yi tababa dangane da yawan wasiƙun da suka aiko masa ya sha jinin jikinsa inda ya ce: “Haƙiƙa waɗannan suna tsorata ni, ga kuma wasiƙun mutanen Kufa, kuma ina jin kashe ni za su yi”.

    Kuma ya yi addu’a ya ce:

    “ya Allah ka shiga tsakanin mu da mutanen da suka gayyato mu domin su taimake mu, amma suka zo suka karkashe mu”. A ƙarshe dai Imam Husaini (Radiyallahu Anhu) ya yi musu baki, ya yi musu baƙar addu’a inda ya ce: “Ya Allah in ka raya su ka rarraba kawunan su, ka tarwatsa su ƙungiya-ƙungiya, kada ka sa shugabanni su yarda da su har abada, saboda sun gayyato mu domin su taimake mu, amma kuma sai suka afka mana da kisa”. Waɗannan kaɗan ne daga ikrari da Imam Husaini ya yi kan bayanin waɗanda suka kashe shi.

    2-Maganar Zainul Abidin (Radiyallahu Anhu)

    Shi Aliyu ɗan Husaini (Radiyallahu Anhu) ne, yana daga cikin waɗanda suka kuɓuta daga cikin iyalan Husaini (Radiyallahu Anhuma) a Karbala saboda shi ganau ne ba jiyau ba, ga abinda ya faɗa:

    “Ya ku mutane (Mutanen Kufa) ina haɗa ku da Allah shin ba ku ne kuka rubutawa mahaifi na wasiƙu ba, amma kuka yaudare shi, kuka yi alƙawarin yi masa mubaya’a da biyayya amma kuka yaƙe shi kuka tozarta shi, Allah wadaranku, tur da tunaninku, shin da wane ido za ku yi tozali da ma’aikin Allah ranar lahira idan ya ce da ku shi ne kuka kashe iyalansa, kuka keta alfarma ta?”

    Sai mata suka ɓarke da kuka, su kuwa mazajen suka rinƙa zagin junansu suke cewa: “kun halaka ba ku sani ba”.

    Shi kuma (Zainul Abidin) sai ya ce: “Allah ya yi rahama ga duk wanda zai karɓi nasiha ta, ya yi aiki da wasiyya ta akan Allah da manzonsa da iyalansa saboda mu masu koyi ne da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam).

    Gaba ɗayansu sai suka ce:

    “Mun yi alƙawari za mu bi duk umarnin da ka ba mu, za mu tsare ka, za mu bi duk umarnin da ka faɗa Za mu yaƙi wanda ka yaƙa, mu yi shiri da wanda ka yi shiri da shi. Sai mun kamo Yazidu, mun yi bara’a da waɗanda suka zalunce ka, suka zalunce mu”. Sai ya ce da su:

    “Haba mayaudara, makirai, ai wannan ihu ne bayan hari, son zuciyarku ba zai bar ku ku iya aikata hakan ba. Wato so kuke ku yi min irin yadda kuka yi wa babana? Wallahi ba za ta yiwu ba jiya jiya kuka kashe mahaifina a cikin iyalansa, alhali zuciya ta ba ta rabu da baƙin cikin rabuwa da shi ba, da rabuwa da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da ‘yan uwa na ba.

    A lokacin da Zainul Abidin (Radiyallahu Anhu) yake wucewa sai ya ga ‘yan shi’ar Kufa suna ta kururuwa da koke-koke sai ya dube su cikin murya rarrauna ya daka musu tsawa ya ce: “Kuna wani koke-koke wai saboda mu, to su wane ne suka kashe mu in ba ku ba?”

    3-Maganar Ummu Kulsum ‘Yar Ali (Radiyallahu Anha)

    Ƙanwa ce ga Husaini (Radiyallahu Anhuma) ita ma ganau ce ba jiyau ba, ga huɗubar da ta yi ga ‘yan shi’ar Kufa:

    “Bayan haka, ya ku mutanen Kufa ya ku maha’inta mayaudara, makirai, kada Allah ya tsayar da hawayenku, kada Allah ya kawar da kukanku. Ku dai kun yi kama da mahaukaciyar nan da take yini tana saƙa, sai kuma ta zo ta tsittsinka abinda ta saƙa gutsun-gutsun.

    Kuma rantsuwa don kawai biyan buƙatunku. Babu abinda kuka iya sai girman kai da jiji-da-kai da gaba, da mugunta da ƙarya, ga kwaɗayi irin na kuyangi, da tsanin riƙo da gaba, aikinku ya munana Allah ya yi fushi da ku, kuma za ku dawwama a cikin wuta.

    Kuna wani kuka saboda an kashe ɗan uwa na? Za ku yi kuka mai yawa, za ku yi dariya kaɗan, kun yi abin faɗar da ba zai rabu da ku ba, ba kuma za ku ga sauƙinsa ba har abada, shi ne kuka kashe ɗan cikamakon annabawa, wanda ya fito daga tsantson tushen manzanci, shugaban samarin Aljanna, wanda kuke fakewa da shi in ana yaƙi, wanda shi ne gatanku, tir da aikinku, zunubin ku ya munana ranar ƙiyama, kun shiga uku kun lalace kun yi asara kun gamu da fushin Allah, za ku gamu da ƙasƙanci da wulaƙanci.

    Ko kun san yadda kuka ɓatawa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) rai?
    Ko kun san girman alƙawarin da kuka karya?
    Ko kun san matsayin alfamar da kuka keta?
    Ko kun san darajar jinin da kuka zubar?
    Haƙiƙa kun yi taɓargazar da ta kusa sanya sammai su kece, ƙasa ta tsage, duwatsu su rumurmushe”

    4-Maganar Zainab ‘Yar Ali (Radiyallahu Anha)

    Ita ma ‘ya ce ga sayyaydi Ali (Radiyallahu Anhu) kuma tana cikin ‘yan kaɗan da suka tsira daga kisa ranar Karbala. A lokacin da suke wucewa a kan raƙuma sai ta ji mata suna ta karuruwa sai ta leƙo daga darbuka (rumfar da ake yi akan raƙumi) ta yi tsaki tace:

    “ku mutanen Kufa, mazajenku suna kashe mu, matanku suna yi mana kuka, sai ranar sakamako Allah zai yi hukunci tsakanin mu da ku”

    Ya ɗan uwa mai karatu, ka ji maganganun waɗanda abin ya faru akan su, yanzu kuma ga maganganun manya-manyan malaman shi’a da kuma sunayen litattafan da suka yi bayani ƙarara cewa ‘yan shi’a su ne suka kashe Husaini.

    Wani abin lura shi ne waɗannan malamai ‘yan zamani ne waɗansu suna nan da ransu, Waɗansu kuma ba wani daɗe wa suka yi da mutuwa ba.

    Kazim Al-Ihsa’i Annajfi

    Ya ce: “waɗanda suka yaƙi Husaini su dubu ɗari uku ne, dukkaninsu ‘yan Kufa ne, babu mutumin Sham a cikinsu, babu mutumin Hijaz, babu mutumin Indiya ko Fakistan ko Sudan ko Misra ko Afrika, ƙabilu ne daban-daban daga Kufa”

    Ayatullahil Uzma Muhsinul Amin

    Ya ce: “Sai kuma mutane dubu ashirin daga Iraki suka yi wa Husaini (Radiyallahu Anhu) mubaya’a, amma suka yaudare shi suka kashe shi”

    Husaini Karani

    Ya ce: “Su mutanen Kufa, ba wai tarwatsewa kawai suka yi daga bayan Husaini ba, a a saboda tsabar munafurcinsu sai suka rinƙa gaggawar zuwa Karbala suna ba da sunayensu domin a sa a cikin sojoji masu yaƙar Husaini don kawai su farantawa shaiɗan rai.

    Misali akwai wani mai suna Amr binul Hajjaj wanda ya rinƙa nuna goyon bayansa ga Husaini da kare alfarmar Ahlul Baiti har ma ya haɗa runduna domin ya kare Hani ɗan Urwah, amma sai ga shi ya canja yana kiran Husaini da sunan ɗan tawaye yana ma cewa da jama’arsa: “Ku yaƙi wanda ya fice daga addini ya rabu da jama’a”!

    Wani misali na irin wannan munafurci shi ne Abdullahi Ibn Hauzah Attamimi wanda mutumin Kufa ne, ɗan shi’a ne tun zamanin sayyidina Ali, ta yiwu ma yana daga cikin waɗanda suka rubutawa Husaini wasiƙar gayyata, amma sai ga shi ya tsaya a gaban rundunar Husaini (Radiyallahu Anhu) yana cewa: “Ya Husaini ina yi maka bushara da wuta” Subhanallah! Wa iyazubillah!

    To ɗan uwa ka ji yadda gaskiyar magana take, amma kuma daga baya su waɗannan mutane sai suka dawo suna koke-koke suna zage-zage da tsine-tsine suna jifan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba da laifinsu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Allah Ta’Ala Ya Yi Maganin Makasa Husaini (Radiyallahu Anhu) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Tasu’a Da Ashura danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu