Falalar Gaggauta Buɗa Baki

0
963

An karɓo daga Sahal Ibn Sa’ad (Radiyallahu anhu) Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce:

“Mutane ba za su gushe ba a kan alhairi mutuƙar suna gaggauta buɗa baki”. (Bukhari 1957 Muslim 1098).
Kuma an ruwaito daga shi (Sahal) ya ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce:”Al’ummata ba za su gushe ba a kan sunnata, matuƙar ba sa jiran fitowar taurari kafin su yi buɗa baki”. (Ibn Hibban 1957, Sahihut Targib 1074).
Waɗannan hadisai suna nuna cewa, jinkirin buɗa baki har sai an yi sallar magariba, ko har sai taurari sun fito bidi’a ne, kuma ɗabi’ar Yahudu da Nasara ce, kamar yadda ya tabbata a hadisin (Ibn Hibban 3562).

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yin Sahur danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceFalalar Dake Cikin Yin Sahur
Labarin na GabaFalalar Ciyar Da Mai Azumi