Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Wannan babi yana ƙunshe da bayanan da suka danganci farfajiyar ƙasar Hausa a jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa dangane da mutanenta da halin zamantakewa da shugabanci da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu. Daga nan sai aka yi bayani kan ƙaura da shigowar baƙi ƙasar Hausa da matsayin Hausawa a yau.

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya da Yau

    Yana da matuƙar mahimmanci kafin mu baje kolin wannan nazari mu yi waiwaye domin sanin wurin da ƙasar Hausa take a jiya da kuma a yau. Ƙasar Hausa ta asali tana a Afrika ta Yamma ne, a farfajiyar da take tsakanin hamadar Sahara da dazuzzukan da suka doshi gaɓar tekun Atlantika daga kudu. Kuma ana kiran ƙasar da sunan Sudan ta Yamma, wato tsakanin Tafkin Chadi da gwiwar Kogin Kwara a can Yamma (Alhassan, 1982:1).

    A wata faɗar kuma an bayyana cewa ƙasar Hausa tana shimfiɗe ne a can Arewacin Nijeriya da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar cikin Afrika ta Yamma. Daga Gabas ta yi iyaka da ƙasashen Borno. Daga Yamma ta yi iyaka da ƙasashen Dahomey a gaɓar Kogin Kwara. Daga Arewa ta yi iyaka da ƙasar Adar a cikin Jamhuriyar Nijar. Daga wajen Kudu kuma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari da kuma ƙabilun kudancin Zariya da na Kudancin Bauchi (Ibrahim, 1982:1).

    Ƙasar Hausa wadda tana shimfiɗe a shiyyar Sudan ta tsakiya, a tsari irin na gargajiya a iya cewa ta haɗa da ƙasashen sarakunan Katsina da Kano da Daura da Zazzau (idan aka ɗebe kudancin Zazzau) da Argungu da Gwandu da Gumel da Haɗejiya da Ƙwanni da Maraɗi da Tassawa.

    Ni kuma a nawa hasashen ina ganin a yau, ƙasar Hausa yanki ne wanda ya mamaye dukkan Jihohin Katsina da Kano da Zamfara da Sakkwato da Arewacin Jihar Kaduna da wasu ɓangarori na Jihohin Kabi da Bauchi da Gwambe da Neja da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar.

    Yanaye-Yanayen Ƙasar Hausa

    Mafi yawancin sassan ƙasar Hausa yana shimfiɗe ne kuma yana da yawan sarari, amma duk da haka akwai tsaunuka da tuddai a wasu wurare kamar Dutsin Dala da na Gwauron Dutse a Kano da Dutsin Dutsin-ma a jihar Katsina da Dutsin Kwatarkwashi a jihar Zamafara da Duwatsun Kufena a Zariya da sauransu.

    Akwai ‘yan dazuzzuka waɗanda suka haɗa da dajin Rugu wanda ya ratsa jihohin Katsina da Zamfara da dajin Falgore wanda ya ratsa jihar Kano da wani ɓangare na lardin Zazzau a jihar Kaduna. Yanayin dajin da yake a ƙasar Hausa iri biyu ne, da wanda ake kira “Sahel”, wato irin dajin da ake samu a arewa, da kuma dajin “Savanna” wanda ake samu a kudancin ƙasar.

    Akwai ƙarancin itatuwa a dajin “Sahel” kuma mafi yawancinsu gajeru ne. A lokacin rani da yawa daga cikin ganyayen da suke wannan daji sukan kakkaɓe, idan kuma damina ta kusa zuwa sai su fara tohuwa. Ciyawar da ake samu a wannan daji dabbobi kan cinye rabi su tattake rabin, amma da an yi ruwan tohon geza duk sai ta tsiro a ko’ina. Wuraren da wannan daji ya mamaye sun haɗa da dukkan kudancin Jamhuriyar Nijar da arewacin ƙasar Hausa a sassan jihohin Katsina da Kano da Jigawa da Zamfara da Sakkwato da Kabi.

    Daga dajin “Sahel” idan aka yi kudu kaɗan sai dajin “Savanna”. A irin wannan daji, itatuwa sun fi tsawo da kusanci da juna, haka kuma ana samun ganyaye da ciyayi da suke shekara cikin ɗanyantakarsu wato kore. Ana samun yanayin irin wannan daji a kudancin jihar Katsina da Lardin Zazzau a jihar Kaduna da Lardin Kabi da Yawuri a jihar Kabi da Kwantagora a jihar Neja (Alhassan, 1982:2-3).

    Duk faɗin ƙasar Hausa manyan koguna biyu ne suka ratsa ta cikinta da kogin Rima da kogin Haɗejiya. Kogin Rima shi ne ya taso daga ƙasar Zamfara ya malala ya yi Arewa zuwa cikin Jamhuriyar Nijar, daga nan sai ya karkata kudu ya bi ta yammacin Sakkwato ya je ya faɗa cikin kogin Kwara. Kogin Haɗejiya kuwa ya fara daga ƙasar Kano ya gangara ya yi gabas, ya bi ta Jama’are a jihar Bauchi, ya bi ta Gashuwa da Gaidam a jihar Yobe ya faɗa tabkin Chadi (Alhassan; 1981:3).

    Ta fuskar yanayin shekara ƙasar Hausa tana da yanayi iri biyu, lokacin damina da lokacin rani. Ana samun ruwan sama a lokacin damina wanda yakan fara daga watan bakwai na Hausa (Mayu) zuwa watan sha ɗaya na Hausa (Oktoba), kuma ruwan da ake samu ba mai yawa ne ƙwarai ba, amma duk da haka yana da albarka da biyan buƙatun manoma. Shi kuma lokacin rani yana farawa daga watan goma sha biyu na Hausa (Nuwamba) zuwa watan shida na Hausa (Afrilu), ya kuma rabu biyu wato lokacin ɗari da lokacin zafi ko bazara.

    Mutanen Ƙasar Hausa

    Mutanen ƙasar Hausa su ne ake kira Hausawa waɗanda masana da manazarta daban-daban suka kawo ra’ayoyinsu kan waɗanda suke ganin cewa su ne Hausawa. A ra’ayin wani masani ya bayyana cewa Hausawa su ne mutanen da suke zaune a ƙasar Hausa tun tuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa (Ibrahim, 1982:1)

    Wani masanin kuma yana ganin, Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi daga ƙasar Hausa zuwa wasu sassa da ke maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da ƙasar Hausa, ko da kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adun Hausawa sun ɗauka su Hausawa ne. Misali, Abakwariga da suke zaune a Jihar Taraba ta Nijeriya da kuma wasu da suke iƙirarin su Hausawa ne waɗanda suke zaune a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Faso da Mali (Adamu, 1974:3).

    Akwai kuma waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi zuwa ƙasar Hausa sun manta da harshensu da adabinsu da al’adunsu na asali sun ɗauki na Hausawa. A taƙaice sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’ada. Misalin ire-iren waɗannan mutane sun haɗa da Barebari da Kambarin Barebari da Barebarin Katsina da Buzaye da wasu Fulani (Adamu, 1974:4).

    Wani masanin kuma ya bayyana cewa Hausawa dai su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa, sannan dukkan al’adunsu da tadodinsu na Hausa. Haka kuma addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu (Magaji, 1986:3).

    Mutanen ƙasar Hausa suna tafiyar da hanyoyin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da tattalin arzikinsu don cimma burin rayuwarsu na yau da kullum daidai da yanaye-yanayen ƙasarsu. Wannan ne ya ƙara taimaka masu suka kai ga matsayin da suke a yanzu, ya kuma ƙara taimakawa wajen shigowar baƙi wannan ƙasa.

    Danna don karanta Sana’ar Wanzanci Da Sauye-sauyen Zamani Jiya Da Yau (Shimfiɗa) 

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    An haifi Alaramma Malam Salisu ɗan Malam Ahmad ɗan Usmanu ɗan Ahmad a garin Ruwantsa. An ce asalin zuriyarsu sun fito daga ƙasar Mali, Alaramma Malam Salisu ya taso a garin Ruwantsa a inda ya fara karatu a wurin Malam Abdul’Aziz ɗan Malam Ibrahim.

    Lokacin da ya ƙara datawa kuma idonsa ya yi ƙwari, sai tsananin kwaɗayinsa ga Alƙur’ani ya ƙaru, ya ƙara duƙufa. Malam Salisu ya kasance tun ƙuruciyarsa ba ya zama wuri guda face yana tsakanin wancan gari da waccan tsangaya izuwa waccan cibiya ta makaranta. Wannan ya ba shi damar huɗuwa da gwarazan malaman zamaninsa irin su Malam Haruna Ningi wanda a wurinsa ne ya haddace AIƙur’ani Mai Girma.

    Koda Alaramma Malam Salisu ya sami labarin bayyanar Gwani Hamad a garin Taura kuwa; sai ya zabura ya haɗa kayansa ya nufe shi kuma ya kamfata daga marmaron ilmin Gwani Hamad. Daga nan kuma ya wuce garin Malamawa wurin Bajimin malami Malam Abdullahi. Malam Sal ısu bai gushe ba yana kutsawa cikin kowane loko da saƙo na ƙasar Kano da kewayenta; har sai da ya dangana da garin Insharuwa cikin Jamhuriyar Nijar.

    Bayan Dawowar Malam Salisu daga ƙasar Nijar ne ya yi aure a mahaifarsa. Daga nan ne ya taso tare da Wani adadi na almajiransa ya dawo Kano ya sauka Unguwar ƙofar Wambai; wurin Malam AbdulKarim inda ya karanta ilimin Tajwidi da Fiƙihu. Manyan malaman Malam Ɗanruwantsa sun haɗa da Shehin Malami Rabi’u Ɗantinki da Shehu Mai Hula. Bayan nan ne kuma ya sake zabura izuwa garin Ɗabbatta wurin babban malami Malam Adam; don sanin ilimi littafin Shaɗibiyya da ilmin Rasmu.

    Sannan ya sake dawowa birnin Kano karo na biyu a inda ya sauka a wurin Malam Garba Tudun Nufawa.

    Ya zauna shekaru biyu a wurinsa yan karantar Alfiyyar ɗan Malik. A lokaci guda kuma, shi Malam Garba Tudun Nufawa (Malam Abubakar Ramadan) yana koyon ilmin Tajwidi da Kira’o’i a wurinsa; Daga nan ne ya koma Unguwar Yakasai ya kafa makarantarsa a shekarar 1945.

    Bayan ya tumbatsa da ilmi da Alƙur’ani; daga bisani kuma ya koma Gwauron Dutse kusa da Masallacin Juma’a na Sheikh Is’haka Rabiu a matsayin Na’ibin Limamin Masallacin.

    A takaice dai zamu iya cewa Malam Salisu Ɗanruwantsa shi ne magajin kambin Shehi Rabiu Ɗantinki a fagen ilmin Alƙur’ani; da ƙira’o’i a faɗin Kanon Dabo. Tsangayarsa ta shahara da tsare-tsare masu ban sha’awa tare da sanya cigaban zamani a Wasu ɓangarori daban-daban. Alal misali, akwai tsarin azuzuwa inda ake sanya yara goma sha bakwai; a Kowane aji ana biya musu rabin sumuni da safe har sai sun haddace. Da yamma kuma a ƙara musu rabi don a samu kyakkyawar haddar AIƙur’ani.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Gambon Takai danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Haramun Ne Mata Su Halarci Husainiyya

    Haramun Ne Mata Su Halarci Husainiyya

    A baya kaɗan mun kawo wasiyyar da Imamu Husaini ya yi wa mata a gab da shahadarsa har ila yau a cikin wasiyyar ya ce:

    “Yake ‘yar uwata, ya ke Ummu Kulsum, ya ke Fatima; ya ke Rabab ku nutsu idan na mutu kada ku yaga tufafinku, kada ku ya ƙushe fuskokinku.

    Sannan kuma Abul Hasan da Abu Ja’afar (Alaihis Salam) sun faɗa akan fassarar faɗin Allah Ta’ala; “Kuma kada Su (mata) su saɓa maka a kan wani abin aihair? ya ce: “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya gayawa Fatima (Alaihis Salam) cewa; “Idan na mutu kada ki yakushe fuskarki, kada ki cizge gashinki, kada ki yi min kururuwa, kada ki yi makoki. Sai ya ce wannan shi ne ma’anar “abin da Allah ya ke faɗa”.

    Abu Abdullah (Alaihis Salam) ya ce; “Ma’anar wannan ayar ita ce kada su yaga tufafinsu; kada su yakushe fiskokinsu, kada su yi ihu da kururuwa, kada su tsaya a kan ƙabari.

    An karɓo daga Abu Sa’id Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “ya la’anci mace mai rera-kuka da mai sauraro”

    To ‘yan uwa mata (sisters) kun ji abinda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam); da Imamai (Alaihis Salam) suka faɗa a kan matan da suke halartar Husainiyya. Shin ko za ku bi maganar Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da ta Imamai ku hutar da kawunanku daga zarya da kuke ba dare ba rana; domin ku kaucewa fushin Allah ta’ala da Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam). ‘Yar uwa ki bi gaskiya ki bi Allah da Manzo (Sallallahu Alaihi Wa Sallam); ba jagorori ba waɗanda su suna huce cikin raɓa suna kwasar girki ku kuma kullum kuna kan hanya.

    Ni dai nasiha nake yi miki. Kuma gyara kayanka…

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihi Da Falalar Husaini (Radiyallahu Anhu) A Taƙaice danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kanFalalar Ba wa Ɗan Uwa Sadaƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Ake Mandi Rice

    Yadda Ake Mandi Rice

    Matso kusa ki zauna. Yau na taho muku da yadda ake yin MANDI RICE.

    ABUBUWAN BUƘATA.

    • Shinkafa (Basmati rice).
    • Nama ko Kaza.
    • Albasa
    • tumatur
    • man zaitun ko man salak
    • tafarnuwa
    • citta
    • cinamon stick
    • curry
    • thyme
    • lemon tsami
    • seasoning.
    • Coal (gawayi).

    YADDA AKE HAƊAWA.

    Mataki na farko za ki wanke naman kazarki ko nama ki zuba ɗan gishiri, lemun tsami, tafarnuwa, citta, thyme. Ki dafa shi da ɗan ruwan zafi har sai ya yi laushi ya fara zarewa amma kar ya narke sosai.Kki ajiye ruwan naman don dafa shinkafar.

    Mataki na 2:

    Ki wanke shinkafar ki, ki barta ta jiƙu na minti 30. Ki soya albasarki da tafarnuwa a cikin mai, sannan ki zuba tumatur markaɗaɗe. Za ki saka kayan ƙamshi; kirfa, bay leaf, curry, thyme da gishiri.

    Ki zuba wannan ruwan naman ki bar shi ya tafasa sannan ki zuba shinkafar. Ki rufe ki kuma rage wuta har sai shinkafar ta dahu amma ba ta caɓe ko ta manne da jikinta ba.

    Mataki na 3:

    Bayan shinkafar ki ta dahu, ki jera naman kazar ki ko naman ki a saman shinkafar cikin tukunya. Ki kunna ƙaramin coal ki saka a cikin ƙaramin cokali ko dai wani abu da ba zai ƙone ba ki sa a tsakiyar shinkafar, ki zuba man zaitun a kan coal ɗin ki rufe na minti 5-10.

    Wannan shi ne sirrin ɗanɗanon mandi rice mai ƙamshi.

    Karanta Yadda Ake Faten Tsakin Masara

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Faten Tsakin Masara

    Yadda Ake Faten Tsakin Masara

    Assalamu alaikum! Barkanmu da wannan lokacin. Mun jima ba mu leƙa kichen ba. Yau dai na ce bara mu leƙa gargajiya. Dana laluba sai na ga bara mu taɓo FATEN TSAKIN MASARA.

    Abubuwan da ake baƙata idan za a yi faten tsakin masara su ne:

    • Tsakin Masara
    • Manja /Farin mai
    • Yakuwa
    • Attarugu
    • Albasa
    • Seasoning
    • Nama ko kifi
    • Kayan ƙamshi

    Yadda Ake Haɗawa:

    Da farko ki za ki wanke tsakin masara. Ki samu tukunya ki ɗora manja ko farin mai ki soya albasarki da attarugu da ɗan kayan ƙamshi yadda kike so ki ƙara ruwa bayan albasar ta dahu kaɗan sai ki zuba ruwa da ɗan dama.

    Bayan ruwan ya tafasa sosai ki zuba tsakin a hankali kina gaurayawa don kada ya yi guda (lumpy). Ki zuba kayan ɗanɗanon ki kamarsu curry,thyme in kina so amma. Ki zuba namanki ko kifi a ciki su ci gaba da dahuwa tare.

    Sai ki yanka yakuwa ki zuba a ciki. Ki bar shi ya dahu har ya yi laushi kina motsawa don kar ya ƙone lokaci zuwa lokaci, idan ya yi miki kauri sosai ki ƙara ruwa kaɗan.

    Idan ya dahu ya yi laushi kuma ya dahu sosai ,sai ki sauke. Za ki iya ƙara manja a saman don ƙamshi.

    Na barku lafiya. A gwada uwargida da amarya. Sace zuciyar mai gida ba na mai bacci ba ne.

    Don karanta Faten Doya Da Ƙwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Musa Ɗanƙwairo A Gayaunar Waƙa

    Musa Ɗanƙwairo A Gayaunar Waƙa

    Makaɗa Abdu Kurna yana daga cikin makaɗa na ƙungiya; waɗanda suka yarje wa wasu mataimakansu su dinga zuwa taɓe na yin waƙa; wato gayaunar kiɗa.

    A lokacin da Sarkin Kiɗa Abdu Kurna ya lura wazirinsa Musa Ɗanƙwairo ya laƙanci waƙar baka; sai ya ba shi faraga ya dinga fita da abokansa yawon rera waƙoƙi lokaci bayan lokaci wato sa’i da wata bukata.

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi waƙoƙin noma da yawa lokacin gayauna. Daga nan ne Abdu Kurna ya ba shi izini ya dinga haɗawa da waƙoƙin masu Sarauta, musamman ma ‘ya’yan Sarakuna.

    Waƙar Gayauna ta Sarauta wadda Musa Ɗanƙwairo ya fara shiryawa da aiwatarwa da rerawa da sadarwa; ita ce wadda ya yi wa Abubakar ɗan Sarkin Noma Usman na Birnin Ƙaya.

    Ga wasu ɗiya na waƙar:

    G/Waƙa: Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    Jagora: Ya tafi daji ba shi komawa,
    : Kullum daƙe duƙe sai duƙe,
    ‘Y/Amshi: Gyado mai ƙoƙarin gabce,
    : Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    Jagora: Mijin Ɗiya jikan Nomau,
    : Gwarzon Ango karsanin Ali,
    : Gungaman Iro ɗan Jatau,
    : Kullum daga duqe sai duqe,
    ‘Y/Amshi: Gyado mai ƙoƙarin gabce,
    : Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    (Waƙar Musa Ɗanƙwairo 30 ta Abubakar Birnin Ƙaya)

    Domin karanta cikakken bayani akan Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Gudumawar Waƙoƙin Baka na Situdiyo Wajen Haɓaka Tattalin Arziki danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shine daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Shehun Malami Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki (1897-1959)

    Tarihin Shehun Malami Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki (1897-1959)

    Malam Rabi’u ɗan Yunusa ɗan Alhasan ɗan Baru. An haife shi a garin Tinki a cikin ƙaramar hukumar Bici da ke Jihar Kano cikin shekarar 1897.

    Malam Rabi’u ya taso ciki ƙuruciya manisanciyar wargi da wasanni irin na matasa. Ya yi karatu a gaban mahaifinsa. Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki ya kasance mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da yawan sabo da jama’a. Ya haddace Alkur’ani tun yana ɗan shekara goma sha huɗu. Sannan ya fara karatun littatafai irin su Ahalari da lziyya.

    Daga nan ya nemi izinin muhaifinsa ya bi wani baƙon mashahurin malami da ake kira Malam Kunta. Bayan ya zauna tsawon lokaci a wurinsa, sai ya nemi izini zuwa wajen Mahiru Kalla mutumin Damagaram cikin Jamhuriyar Nijar.

    Ya zauna a wajensa tsahon lokaci har ya sauke litlatafai da yawa a fannin ilimin ƙira’a da Tawhid da litlafai irinsu Nuniyar Sakawiy da Hidayatussibiyan da Tuhfatul adfal da Mukaddimat Jazary, da Shadibiyya da Lamiyyatul Kira ‘at.

    Shaihun malamin bai gushe ba yana kutsawa cikin fagagen ilmai da gogayya da malamai har sai da ya dangana da garin Maiduguri ya yi karatu a wurin Mahiru Ahmad. Daga nan ya dawo Kano ya sauka Haɗejiya ya kara dukuta a gaban Malam Is’hak daga bisani ya dawo Kano ya cigaba da koyarwa.

    A lokacin da Malam Ɗantinki ya samu labarin Mahiru Hamid, sai ya nemi izinin ya zama almajirinsa. A nan ma ya karanta littafai da dama musamman fannin dabti wanda shi ma ɓangare ne na ilimin Rasmu da ilimin wasullan Alkur’ani.

    Abokan karatun Shehi Rabi’u wurin Gwani Hamid sun haɗa da Malam Ɗan Gunduwawa da Malam Aliyu Mai Kwaro da Malam Ɗan Karofin Yashi da Malam Yunus Ɗan Gumel da Malam Ɗan Kanuri da Malam Isah Ɗan Kwandarai da Malam Sabo Ƙofar Wambai da Malam Umar Ɗan Mai-Rigar-Fatu.

    A halin yanzu tsangayarsa ta cigaba da bunƙasa kuma ta yi rassa a hannun ɗan sa Halifa Sheikh Is’haka Rabi’u.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Gwani Saleh Danzargu danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yadda Falalar Karatun Al-Ƙur’ani Ya Ke

    Yadda Falalar Karatun Al-Ƙur’ani Ya Ke

    Karatun ƙur’ani ibada ce babba wacce babu sama da ita; musamman in ta haɗu da ikhlasi da lura da ma’anoni da manufofin abinda ake karantawa (Tadabbur) da karantawa dai-dai da ƙa’idodin karatun (Tajwidi); da kuma abinda ya fi komai muhimmanci wato aiki da abinda ake karantawa.

    Hadisai da dama sun zo kan bayanin Falalar Karatun Al-Ƙur’ani a jumlace; da kuma falalar karanta waɗansu keɓaɓɓun surori da ayoyi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Koyo Da Koyarwar Da Al-Ƙur’ani Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Zikiri danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Falalar Sadaƙar Mai Ƙaramin Ƙarfi

    Falalar Sadaƙar Mai Ƙaramin Ƙarfi

    An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu anhu) ya ce: “Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace: “Sadaƙar dirhami ɗaya ta rigayi sadaƙar dirhami dubu ɗari” Sai wani mutum ya ce; Kamar yaya Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam)?

    Sai ya ce: “Mutum ne yana da dukiya mai yawan gaske, sai ya tsakuro dubu ɗari ya bayar sadaƙa; kuma wani dirhami biyu ne kaɗai da shi. Sannan ya yi sadaƙa da dirhami ɗaya” (Nasa’I Ibn Khuzaimah), (Sahihul Targib 875).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Ciyarwa Da Shayarwa Da Tufatarwa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ratiban Nafiloli danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Gwani Saleh Ɗanzargu

    Tarihin Gwani Saleh Ɗanzargu

    An haifi Gwani Saleh ɗan Abdullahi jikan Abdullahi a Ƙasar Jahun. Mahaifin sa ya rasu yana ƙaramin yaro, don haka sai mahaifiyar sa ta koma da shi garin Zarga ta kuma kyautata tarbiyar sa.

    Gwani Saleh ya taso da kaifin basira da son Alƙur’ani. Don haka ya lazimci makarantan garin Zarga irinsu Malam Abdullahi har Ubangiji Ya hore masa Alƙur’ani ya haddace shi yana ɗan shekara tara (9). Gwanin Alƙur’ani ma’abocin ƙan-ƙan da kai da gaskiya da riƙon amana. An ce tun yana ɗan shekara sha biyu ya sha fari.

    Gwani Saleh ya yi tafiye-tafiye na neman karatu a inda yazo Kano ya sauka a tsangayar Gwani Nadudu. Daga bisani kuma ya lazimci mashahurin malami Malam Aliyu Basakkwace ya karanci Fiƙhu da Hadisi da tafsiri Shaharar da tsangayarsa ta yi ya sanya makaranta daga nisan duniya yin takakkiya don ɗosana daga haskenta. Manyan abokanen karatun Gwani Saleh sun haɗa da:-

    • Gwani ɗan Kwandarai
    • Gwani Ɗan birni
    • Gwani Daudu

    Game da yawan almajiran da suka samu Alƙur’ani a hannun sa kuwa, wannan ɗan littafi ba zai ɗauke ambaton su ba, sai dai mu yi ishara ga waɗansun su:

    • Malam Muktari Abdullahi
    • Yayan sa Gwani Yahuza da Gwani Lawi
    • Malam Husaini Rijiyar Lemo
    • Malam Sham’unu
    • Malam Ibrahim Maidarasu

    Gwani ya rayu cikin karamci da girmamawa daga maƙwabtan sa, musamman ma Alhaji Sunusi Ɗantata da al’umar Unguwar ƙoƙi da kewayenta. A halin yanzu wannan tsangaya tana ƙarƙashin kulawar ɗan sa Gwani Yahuza inda ta ƙara bunƙasa ta hanyar shigo da tsarin ilmin zamani, ɓangaren firamare da sakandare. A lokaci guda kuma, ga tsohon tsarin tsangaya na gudana da makaranta da mahaddata.

    Gwani Yahuza ya samu gogayya da wayewa ta zamani a inda ya dangana da ƙasar Masar don karatun sa na digirin farko. A halin yanzu Gwani Yahuza ɗaya ne daga manyan alƙalai na musabaƙar Alƙur’ani ta ƙasa. Gwani Yahuza shi ne ɗan Najeriya na farko da ya karɓi kyautar girmama mahaddata Alƙur’ani daga ƙasar Saudi Arebiya. Baya ga wannan rassa na makarantar akwai majalisai a unguwannin Gwammaja da Kurnar Asabe da Ƙoƙi.

    Ita wannan makaranta ta Gwammaja, Gwani Lawi ne ya kafa ta mai suna Ma’ahad Gwani Lawi Litahfizil Ƙur’anil Karim.

    Gwani Lawi ya yi babbar Diflomarsa a Jami’atul Ƙur’anil Karim da ke Sudan, kuma shi ne wan da ya kafa ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani ta farko a Najeriya, mai suna Rabiɗatul Huffazil Ƙur’ani, Nigeriya. Gwani Sale Ɗanzarga ya bar ‘ya’ya goma sha biyu, maza da mata.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Ɗankwandarai danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Farko Na Nijeriya (1500 BC- 500 AD) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.