Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Yadda Wanzamai Suke Tsaga

    Yadda Wanzamai Suke Tsaga

    Tsaga wata alama ce wadda Hausawa da kuma wasu ƙabilu na sassa daban-daban da suke cikin Nahiyar Afrika da wasu sassa na wannan duniya suke yi da aska a fuska ko a wani ɓangare na jiki, don a bambanta wata ƙabila da wata ko mutanen wata Daula da wata ko dangi da dangi ko zuri’a da zuri’a ko don riƙon al’ada ko don magance wata cuta ko kuma don yin kwalliya.

    A al’adar Hausawa tsaga ta kasu zuwa rabo uku kamar haka: Tsagar gado da tsagar magani da tsagar kwalliya. Kowace daga cikin waɗannan kashe-kashe na tsaga tana da dalilan da kan sa a yi ta, kuma kowane kaso ya sake kasuwa zuwa wasu rabe-raben.

    Tsagar Gado

    Tsagar gado ita ce wadda ake yi a fuska don nuna asalin mai ita ko sashin da ya fito. Ita tsagar gado tana bin gadon uba ne ba na uwa ba, watau ana yin tsagar gado ne don nuna asalin wajen uba ba na wajen uwa ba. Tsagar gado ta kasu zuwa kashi uku kamar haka: tsagar gado mai nuna asalin gari ko wurin zama misali, Katsinanci da Dauranci da Kabanci da Ƙwannanci da Gobirci da Zamfaranci da Arauci da sauransu.

    Akwai kuma tsagar gado mai nuna asalin ƙabilar da mutum ya fito misali, barbarci da buzanci da sauransu. Akwai kuma tsagar gado mai nuna ma’abota wata sana’ar gargajiya misali, mahauta da manoma da sauransu. Ana kuma kiran tsagar gado da sunan askar gado. A yanzu za a yi bayani cikakke kan ire-iren tsagar gado.

    Tsagar Gado Mai Nuna Asalin Gari ko Wurin Zama

    Irin wannan tsaga tana nuna asalin gari ko shiyyar da mai ita ya fito a ƙasar Hausa. A da can irin wannan tsaga tana nuna daga Daular da mai ita ya fito, watau ya fito daga ƙasar Katsina ko Daura ko Kabi ko Gobir ko Zamfara da sauransu. A wancan zamanin ta hanyar tsagar gado ne ake yaƙar abokan hamayya. Ana nufin ta hanyar tsagar gado ne idan ana yaƙi tsakanin Daular Katsina da ta Gobir, Katsinawa suke gane Gobirawa, su ma Gobirawa su gane Katsinawa.

    Haka kuma ta hanyar tsagar gado ne ake fahimtar masu irinta zuri’ar wane ne da yake zaune a wuri kaza. Akwai tsaga iri daban-daban a ƙasar Hausa waɗanda suke nuna mazauna wurare ko garuruwa waɗanda suka haɗa da Katsinanci a ƙasar Katsina da Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar, da Dauranci a ƙasar Daura ta Jihar Katsina, da Gobirci a ƙasar Gobir da Zamfaranci a ƙasar Zamfara da Kabanci a ƙasar Birnin Kabi da Arauci na Arawa mazauna Gundumar Dogon-Dutsi da kuma wasu ƙauyukan da suke cikin Gundumar Ƙwanni duk a cikin Jamhuriyyar Nijar da kuma Ƙwannanci a Gundumar Birnin Ƙwanni ta Jamhuriyyar Nijar. Yanzu za a bi ire-iren waɗannan tsaga da aka lissafa a sama domin yin cikakken bayani kan kowace da wurin da ake samun ta.

    Tsagar Katsinanci

    Tsagar Katsinanci tsagar gado ce wadda ake yi wa haɓen ƙasar Ƙatsina na asali ko maguzawan ƙasar Katsina, akan kira irin wannan tsaga da sunan bille ko maguzanci a ƙasar Katsina. Irin wannan tsaga gado biyu ce, gado na farko ana yin su ne a kumatu, gado na biyu bisa fuska. Akwai bambanci tsakanin yawan ‘ya’yan tsagar da ake yi wa saraki da talakawa.

    Ga talakawan ƙasar Katsina ana yin tsaga shida ga kuncin dama, tsaga bakwai a kuncin hagu. Ga ‘ya’yan sarautar haɓen Katsina ana yin tsaga bakwai a kuncin dama, shida a kumcin hagu. Abin nufi anan shi ne, ta hanyar yawan tsaga a kumatu ake bambance wannan saraki ne wannan talaka ne. A halin yanzu ana samun masu irin wannan tsaga a sassan arewaci da tsakiyar Jihar Katsina a ƙananan hukumomin Katsina da Kaita da Jibiya da Mashi da Mani da Dutsi da Ɓatagarawa da Rimi da Kurfi da Dutsin-ma da Safana da Batsari da Ɗan-musa da Charanchi da Ingawa da Kusada.

    Haka kuma ana samun masu irin wannan tsaga a masarautar Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar. Kamar yadda aka bayyana a baya masu irin wannan tsaga su ne haɓen asali na Daular Katsina, kuma su ne sarakunan haɓe na masarautar Katsina. A lokacin da Ummarun Dallaje ya kafa mulkin Fulani Dallazawa a Katsina, sai sarakunan haɓen suka yi ƙaura zuwa Maraɗi wadda da can ƙasar Katsina ce, suka kafa mulkinsu a wurin da sunan masarautar Katsina a Maraɗi.

    Wannan dalili ne ya sa tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu ake kiran Sarkin Maraɗi da sunan Sarkin Katsinan Maraɗi. A wannan sabuwar masarauta sun ci gaba da yi wa ‘ya’yansu irin wannan tsaga ta Katsinanci har zuwa wannan lokaci da muke ciki. Bayan ƙasar Katsina da ƙasar Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar duk wurin da aka ga mutum da tsagar Katsinanci to ƙaura ya yi daga waɗannan wuraren zuwa wannan wuri.

     Tsagar Gado Mai Nuna Masu Yin Sana’o’in Gargajiya

    Irin wannan tsaga tana nuna masu irinta suna yin wata sana’a daga cikin sana’o’in gargajiya na Hausawa.Ire-iren wannan tsaga akwai billen hannun dama, wanda yake nuna mai irinta zuri’arsu masu yin sana’ar fawa ne. Akwai kuma tsagar lezumanci wadda take nuna mai irinta masu sana’ar noma ne.

    Tsagar Billen Hannun Dama na Mahauta

    Tsagar Bille a hannun dama tsagar gado ce wadda ake yi wa mahauta a ƙasar Hausa. Ana yin bille ƙarami a ɓangaren fuska na hannun dama gefen karan hanci. Dukkan mai irin wannan tsaga zuri’arsu masu yin sana’ar fawa ne. A yanzu akwai wasu mahauta da kan yi wa ‘ya’yansu tsagar bille a hannun hagu maimakon hannun dama. Tsagar bille a hannun hagu ba ta mahauta ba ce, masu irin wannan bille asalinsu Fulani ne Sulluɓawa waɗanda a yanzu su ne sarakunan Katsina.

    Daga nan ne sai wasu mahauta suka ara suka yafa, suka mayar da shi nasu bayan kuwa ba asalinsu ba ne. Wurin da aka yi bille ne, watau a dama ko a hagu yake bambanta wannan mahauci ne ko kuma Bafulatani Basulluɓe. Irin wannan tsaga ta billen hannun dama ta mahauta ana samun masu irin ta a duk sassan ƙasar Hausa.

    Tsagar Lezumanci Ta Manoma

    Tsagar Lezumanci tsagar gado ce wadda take nuna mai irinta asalinsu manoma ne waɗanda ba su da wata sana’a idan ba noma ba. Tsagar Lezumanci gado biyu ce kuma ta yi kama da tsagar Katsinanci, wurin da suka bambanta shi ne, tsagar Lezumanci ana yin su ne da yawa caɓa-caɓa ba kamar Katsinanci ba da ake yin nan shida nan bakwai. Masu tsagen Lezumanci ana kiransu da sunan Lezumawa.

    Bincike da aka gudanar ya bayyana su Lezumawa asalinsu Zamfarawa ne, sai wani Bazamfare mai suna Jatau ya sayi ɗan uwansa Bazamfare ya sanya shi bauta, sai ya riƙa kiran shi da sunan ‘ZUMU’ watau ɗan’uwa. Sannu-sannu sai aka riƙa kiran sa ‘Lezumu’ watau aka yi ƙarin ɗafa-goshin ‘Le’. Da Jatau ya ga hankalin Lezumu da ƙoƙarinsa sai ya yarda da shi ya kuma ba shi amanar gidansa, sai ya kasance duk harkokin gidan Jatau Lezumu ne yake tafiyar da su.

    Yau da kullum Lezumu yana ta yin bauta a ƙarƙashin ɗan uwansa Jatau har ya gane dukkan asirin Jatau na tsafi. Wannan ne ya ba shi damar yin amfani da wannan asiri ya rinjayi ubangidansa Jatau, ya yi masa juyin mulki, ya amshe gidan sai mai doki ya koma kuturi.

    Daga nan ne aka sami zuri’arsa wadda aka riƙa kira da sunan “Lezumawa” daga sunan Lezumu da mai gidansa Jatau ya riƙa kiran sa. Saboda ƙoƙarin Lezumu da iya tsafin da ya taimaka masa har ya amshe gidan maigidansa ɗan’uwansa Jatau wanda ya yi wa bauta, ya sa ake yi wa zuri’arsa kirari kamar haka:

    “Lezumawan Jatau aska ba ki amana”

    “Lezumawan Jatau taba kashe mai ba ki ruwa”.

    (Hira da ASKS a ranar 3-6-96).

    Ma’anar kirari na farko shi ne, duk irin yadda ka saba da aska idan ka ba ta amana, to wata rana za ta ci amanar mutum domin idan ka yanka ta a jikinka za ta kama, kamar yadda duk da amanar da Jatau ya ba Lezumu, amma da ya gane asirinsa sai ya tumɓuke shi ya amshe gidan.

    Kirari na biyu kuma yana nufin duk wanda ya ba taba ruwa ta sha ta girma idan ya sha ta ba daidai ba, to tana shaƙe shi ya ƙware, ƙarshe ma ta kashe shi kamar yadda Lezumu ya yi wa ɗan’uwansa Jatau wanda ya riƙe shi har ya girma amma ya amshe masa gida.

    Daga lokacin da Lezumu ya amshe gida, sai ya canza tsagarsu daga tsagen Zamfaranci ya zuwa tsagen Lezumanci wanda ya ƙirƙiro wa zuri’arsa, ya kuma mayar da ita tsagarsu ta gado. Irin wannan tsaga ta Lezumanci da Katsinanci a Jihar Katsina ana kiran su da “Hatimin-Noma”. Wannan kuwa ya faru ne saboda shaharar masu irin wannan tsaga a sana’ar noma da kuma ƙwarewarsu wajen yin tsafe-tsafen da suka shafi sana’ar noma.

    A yanzu Lezumawa shahararrun manoma ne kuma matsafa a duk wurin da suke. Ana samun zuri’ar Lezumawa a ƙananan hukumomin Safana da Ɗan-musa da Dutsin-ma da Matazu da Musawa da Batsari da Kankiya da kuma wasu sassan na Jihar Zamfara. A saboda wannan tarihi nasu ya sa a yanzu idan wani biki ya same su sukan gayyaci dukkan danginsu daga ko’ina domin a taru wajen yin bikin (Hira da Sarkin Noma Babban- Kada, Shugaban zuri’ar Lezumawa na Jihar Katsina. A Lezumawar Babban-Kada Safana, a Ranar 11-6-97).

    Tsagar Magani

    Tsagar magani ana yin ta ne domin a fitar da jini daga jikin mutum saboda a sami sauƙi ko a warke daga wani ciwo wanda yake cikin jiki. Ana kuma yin ta don a fitar da mataccen jinin da yake cikin jikin mutum. Wasu Hausawa suna da ra’ayin mataccen jini a cikin jikin mutum kan yi sanadiyyar kamuwa da cututtuka iri daban-daban. Fitar da shi ko rage shi kan sa a sami sauƙi ko a warke daga ciwon. Akwai tsagar magani iri daban-daban da ake yi wa Hausawa, waɗanda suka haɗa da ƙaho da tsagar ɓalli-ɓalli da tsagar fitar- ruwa da tsagar maganin jiri da tsagar maganin kanne da tsagar ciki ga jarirai da tsagar murfi da sauransu.

    Ƙaho

    Ƙaho tsagar magani ce wadda wanzamai kan yi wa mai buƙata. Ana samun ƙaho na sa ko na saniya a gyara shi. Ana kafa ƙahon a bayan mabuƙacin ko a wurin da lalura take. Daga nan sai wanzamin ya yi ta tsotsa ƙahon da yake kafe a wurin da ake buƙatar yin sa. Zai yi ta yin haka har sai ƙahon ya kame sosai sannan ya liƙe ‘yar-ƙofar ƙahon da jijiyar da yake taunawa a cikin bakinsa.

    Yin haka ne zai sa ƙahon ya liƙe wurin da aka kafa shi. Bayan kamar minti goma zuwa sha biyar sai a cire ƙahon saboda a wannan lokacin mataccen jinin ko cutar da ake son fitarwa ta taru daidai wurin da aka kafa ƙahon. Daga nan sai a sanya askar tsaga a tsaga wurin da aka fitar da ƙahon, ana yin tsage daga tara zuwa goma sha biyar. Daga nan sai a sake mayar da ƙahon wurin da aka cire shi.

    Bayan kamar minti goma sha biyar sai a sake cire shi, a wannan lokaci mataccen jini ko cutar ta taru cikin ƙahon, sai a zuba a ramin da aka tona kafin a fara yin ƙahon. Haka za a sake yi kamar sau biyu ko uku, yin haka ya danganta da ƙarfin wanda za a yi wa ƙahon. Daga nan sai a zuba ƙasa a rufe ramin da aka zuba jinin. Shi ke nan an gama ƙaho sai wanda aka yi wa ya saka suturarsa idan ga baya aka yi masa.

    Ana yin ƙaho daga ɗaya zuwa huɗu, amma kafin a kafa wa mutum ƙaho fiye da ɗaya dole sai wanzamin ya tabbatar wannan mutum yana iya ɗaukar fiye da ɗaya. Idan jinin mutum ba shi da yawa, to idan aka yi masa ƙaho fiye da ɗaya ana iya ƙwararsa, maimakon abin ya zama na magani sai ya zama cuta. Wasu wanzamai kan shafa magani a wurin da suka yi ƙaho, wasu kuwa ba sa shafa wani magani matuƙar mataccen jini ya fita buƙata ta biya.

    Yana da muhimmamnci a nan a bayyana ire-iren cututtukan da kan sa a yi ƙaho.Yawan mutuwar jiki da kasala abubuwa ne waɗanda Hausawa suka ɗauka mataccen jini ne yake kawo su. Haka kuma idan mutum ya buge a wani ɓangare na jikinsa har jini ya taru a wurin kuma bai fita ba, ko ya yi targaɗe a wani wuri kuma wurin ya yi kumburi. Bayan an gyara sai a yi masa ƙaho a wurin don a fitar da jinin da ya taru.

    Haka kuma idan murfin ƙahon zuciyar mutum ya faɗa dole sai an yi amfani da ƙaho a jawo shi.Dukkan waɗannan matsalolin rashin lafiya da aka yi bayaninsu, wasu Hausawa sun ɗauka idan aka yi ƙaho za a sami sauƙi ko a warke daga ciwon.

    Tsagar Kwalliya

    Tsagar kwalliya ko jarfa ko shasshawa tana nufin ire-iren tsagen da mata kan sa wanzamai su yi masu a fuska ko a wani ɓangare na jiki domin ado ko kwalliya.Ita tsagar kwalliya an fi yi wa mata ita, domin da wuya a ga namiji ya ba da fuskarsa ko wani ɓangare na jikinsa ga wanzami don a yi masa tsagar kwalliya.

    Ire-iren waɗannan tsage sun haɗa da kalangai da takutuha da kwaluluwa da matakin-soro da ‘yar ƙirji da alluna da me-ka-ce maigida da ‘yarbaka da garɗin-gero da kwanciya-da-masoyi. Akwai kuma tsagen kwalliya waɗanda zamani ya kawo, ire-irensu sun haɗa da alamomin siyasa kamar fartanya mai nuna alamar jam’iyyar N.P.C. da tauraruwa mai nuna alamar jam’iyyar NEPU. Wasu kuma sukan sanya a tsaga masu hoton agogo ko sunan masoyi ga hannuwansu.

    A binciken da aka gudanar a sassan ƙasar Hausa an fahimci mafi yawancin ire-iren waɗannan tsage na kwalliya ana amfani da alamomi iri-ɗaya. Kuma ana kiransu da suna ɗaya, ɗan bambancin da akan samu bai taka kara ya karya ba.

    Lokacin Yin Tsagar Kwalliya

    A al’adance an fi yin tsagar kwalliya da kaka domin kuwa a wannan lokaci an kawar da amfanin gona, kuma sanyi ya fara sauka yadda idan an yi tsagar za ta yi saurin warkewa. Wannan kuma ya faru ne saboda Hausawa suna da ra’ayin a wannan lokaci jiki ya fi saurin tohuwa. A irin wannan lokaci ne wanzamai masu yin tsagar kwalliya ko jarfa suke barin gidajensu domin tafiya yawon jarfa, watau yin tsagar kwalliya a garuruwa da ƙauyukan ƙasar Hausa.

    Wani lokaci kuma da ake yin tsagar kwalliya shi ne watan takutuha. Idan wanzaman jarfa za su sauka a wani gari mafi yawanci sun fi sauka a ranar kasuwar garin don kowa ya san an yi baƙin wanzamai ‘yan jarfa. Kowane daga cikin ‘yan tawagar kan sami gidan da yake da budurwa ya saukar mata. Dukkan yawan kwanakin da za su yi a garin, a gidan da suka sauka ake ba su masauki da abinci har sai sun tashi daga wannan gari.

    A duk wurin da suka je suna tafiya da makaɗa da maroƙa waɗanda suke rera waƙoƙin yabo da na kushe ga ‘yan matan da suka yi masu kyakkyawar sauka da waɗanda ba su yi masu ba. Makaɗan wanzamai ana kiran su da ‘yan kurya ko makaɗan kurya.

    Ire-Iren Tsagar Kwalliya

    A lokacin da za a yi wa budurwa ko yarinya tsagar kwalliya, sai abokiyarta ta ɗauko turmi don wadda za a yi wa tsagar ta zauna ta jingina da wannan turmi. Daga nan sai wannan abiya ta zauna kusa da ita ta dafa kafaɗunta. Ana yin haka ne domin wadda za a yi wa tsagar kar ta nuna kasala. Ita abiyar wadda za a yi wa tsagar ce take gaya wa wanzamin irin tsagar da za a yi wa wannan abiya.

    Wasu kuma samarinsu ne kan zaɓa masu irin tsagar da za a yi masu. Daga nan ne sai wanzamin ya fara tsaga, ana yin tsagar ana kiɗa da waƙa, maroƙa kuma suna shelar a kawo kari. A wannan lokaci ne samari za su yi ta ƙoƙarin gwada bajinta ta hanyar bayar da kari.Su ma ‘yan’uwa da abokan arziki ba a barin su a baya, sai su ma su yi ta ba da nasu karin. Abubuwan da akan bayar na kari sun haɗa da kuɗi da sutura da dabbobi.

    Dukkan abubuwan da aka samu na kari wanzaman ne da makaɗansu da yaransu da maroƙansu suke rarrabawa. Bayan abubuwan da aka samu na kari sai kuma iyayen yarinyar da aka yi wa tsagar su ba da tasu sallamar ga wanzaman.Idan aka sauka gidansu yarinyar da take da dangi da yawa wadda a lokacin da aka fara yi mata tsaga an sami kari sosai, akan ɗauki kwanaki da yawa a wannan gida don ci gaba da yi mata tsaga, kamar misalin kwana biyu zuwa bakwai.

    A mafi yawancin lokaci a saboda kiɗa da waƙa da ake yi a lokacin jarfa waɗanda a cikin waƙar akwai yabo da kuma bayar da ƙarfin gwiwa ga budurwar da ake yi wa tsagar, yakan sa ‘yan mata nuna juriya da daurewa. Wasu kuma gudun kar a yi masu zambo kan sa su daurewa a lokacin da ake yi masu tsaga. Wannan kan sa har a gama yi masu tsagar ba sa nuna wata alama ta kasala ko raggwanci ko su yi kuka. Haka za a yi ta yi daga wannan gida zuwa wancan gidan inda ‘yan mata suke a garin da suka sauka don yi masu tsaga.

    Bayan sun gama a wannan gari sai kuma su ƙara gaba zuwa wani garin.Wanzaman jarfa kan ɗauki lokaci mai tsawo kafin su sake dawowa a garin da suka yi tsaga. A wani lokaci sukan ɗauki misalin shekara biyu zuwa uku ba su dawo a wannan gari ba, sai kuwa idan an bukaci su dawo.Wannan wata alama ce ta nuna kawaici da godiya bisa ga abubuwan da aka yi masu.

    Kalangai

    Kalangai tsaga ce wadda ake yi a fuska daidai saitin kunnuwa. Irin wannan tsaga ƙarama ce marar tsawo ƙwarai, tsawonta bai wuce daidai kunnuwa ba, wasu ana yi masu kalangu ɗaya-ɗaya wasu kuwa ana yi masu kalangai biyu-biyu a kowane ɓangare na fuska, wannan ya danganta da sha’awar wadda za a yi wa tsagar.

    Abin kula a nan shi ne, wasu samari kansa wanzami ya yi masu tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a kowace fuska domin sha’awa, ko kuma su ma ‘yan matansu kan bukace su da a yi masu kalangu ɗaya-ɗaya a kowace fuska.

    Akwai kuma waɗanda ake yi wa tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a fuska a matsayin tsagar gado. Misali, Fulani Dallazawa zuriyar Malam Ummarun Dallaje (wanda ya yi jihadin jaddada addinin Musulunci a ƙasar Katsina kuma Sarkin Katsina na farko daga zuri’ar Fulani) ana yi wa mazansu da matansu tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a fuska a matsayin tsagar gado.

    Tsagar ‘Yar Baka

    Tsagar ‘yar baka tsaga ce ta kwalliya wadda ake yi wa ‘yan mata a kumatu ta haɗe da wutsiyar baki. Wannan tsaga gado ɗaya ce kuma ana yin ta caɓa-caɓa a kumatu. Wasu kan kira irin wannan tsaga da sunan cika baki. Wannan kuwa ya faru ne saboda yadda ake yin ta caɓa-caɓa ga kumatu. An fi yi wa ‘yan mata masu kaurin kumatu irin wannan tsaga don a ƙara rage kaurin kumatun.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

     

  • Ire-Iren Ayyukan Wanzamai

    Ire-Iren Ayyukan Wanzamai

    Cire Belun-Wuya

    Belun-wuya tsokar nama ce wadda take tsirowa a cikin bakin mutum liƙe da ƙarshen dasashin sama kusa da maƙogaro.Wannan tsokar nama Hausawa sun ɗauka idan ba a cire ta ba, to idan mutum ya girma ciwo na iya kama ta. Idan kuwa ta kamu da ciwo zai sa mutum ya kasa cin abinci ko shan ruwa, ya kuma yawaita yin amai ya kuma rame. Idan kuma wani abu ya taɓa wurin, mutumin zai ji tsananin zafi. Wannan ne ya sa da an haifi jariri sai a kira wanzami domin ya cire ta (Hira da Alhaji Aliyu Sarkin Aski, a Safana, 16-6-96).

    Wasu daga cikin Hausawa ba a cire wa ‘ya’yansu belin wuya, a maimakon cirewa suna amfani da maganin da zai hana su kamuwa da wani ciwo.

    Ire-Iren Ayyukan da Wanzamai Kan yi a Farjin Mata

    Wanzaman gargajiya suna yin wasu ayyuka a cikin farjin mata domin a yi maganin wasu lalurori da sukan iya matsa masu bayan sun yi aure. Wasu daga cikin waɗannan ayyuka ana yin su tun mata suna jarirai, wasu kuma sai sun fara girma ake gane suna fama da lalurar sai a yi masu aikin.

    Akwai kuma waɗanda sai sun yi aure ne za a iya fahimtar suna da lalurin, misali wanzamai suna fahimtar yarinya mai fama da lalurar angurya tun lokacin da aka haife ta sai a cire. Amma lalurar sadadda da mahindi da sarƙa da turu duk sai in yarinya ta girma ne za a iya fahimtar su.

    Domin aiwatar da wannan aikin cikin sauƙi da nasara ba tare da samun sha’awa ba wajen yin waɗannan aikace – aikace wanzaman da suke yin aikin suna shan magani, ko amfani da layu da gurayen da za su kawar masu da sha’awa a lokacin da suke yin waɗannan ayyuka. Misali,a lokacin da za a yi aikin wanzamin da zai yi aikin da wanda zai taimaka masa kan shafa farar ƙasa a dukkan gefen idanunsu, kuma su sanya ta cikin baki suna taunawa suna haɗe ruwan har sai sun gama aikin sannan sai su wanke fuskokinsu da bakunansu.

    Wannan yana taimakawa ƙwarai wajen kawar da sha’awa ga shi wanzamin da mai taimaka masa. Mutane suna yaɗa jita-jita wai idan wanzami ya zo yin ire-iren waɗannan ayyuka idan azzakarinsa ya tashi, to idan ya kwanta ba zai sake tashi ba. To wannan ba gaskiya ba ne, ana amfani da maganin sha’awa domin kar ɓarna ta faru a lokacin da ake yin wannan aikin, saboda wasu mutane ba sa iya riƙe sha’awa su yi haƙuri idan ta kama su.

    Cire Angurya

     Angurya wani tantanin nama ne wanda ake haihuwar mata da shi a cikin farjinsu, wasu kuma sai sun girma yake fito masu. Idan ba a cire shi ba yana iya hana mace saduwa da namiji idan ta girma. Wanzamai suna gane mata masu fama da angurya a lokacin da suka zo cire beli ko hakin-wuya. A nan ne idan budurwa ce sai su binciki farjinta su ga idan tana da angurya sai su cire shi.

    Wasu wanzamai suna amfani da yatsa domin cire angurya. Suna sa babban yatsansu ne su tallabo shi daga tushensa sai su sa ‘yar tsaga su cire shi. Wasu kuma suna amfani da allura da zare domin cire shi. Ana tsiro shi da allurar ne da zaren sai a ɗaga sama a sanya askar aski a yanke shi. Wasu wanzaman kuma suna amfani da hantsaki domin cire shi, ana sanya hantsakin a kamo tushensa sai a sa askar aski a yanke shi.

    Wasu kuma suna amfani da akaifar babban yatsansu su kama shi daga tushensa sai su sa askar aski su yanke shi. Bayan an cire shi sai wanzamin ya tauna ‘ya’yan bagaruwa ya furza a wurin, daga nan kuma sai ya barbaɗa maganin da zai tsayar da jini da wanda zai hana shi sake tuƙowa.

    Gyara Sadadda

    Mace mai lalurar sadadda ana haihuwar ta da wannan lalura, domin ana samun ƙofar farjinta ‘yar ƙarama ce wadda fitsari ne kawai yake iya fita ta wurin, amma can daga cikin farjinta lafiya lau yake. Matsalar a wurin ƙofar farjin take. Wasu kuma ana haihuwarsu lafiya lau, amma saboda rashin tsabta da rashin kula daga wurin iyayensu ko masu riƙonsu sai ƙofar ta sake toshewa.

    Matan da suke da irin wannan matsala idan za su yi fitsari sai ya riƙa fita kamar na namiji. Idan iyayensu suka fahimci haka sai su sanar da wanzamin gidansu domin ya binciki yarinyar don ya gyara ta. Ana yin irin wannan gyara ne ta yadda aka fahimci matsalar.

    Ga waɗanda aka haifa da matsalar, sai an sanya askar aski a ƙara buɗa ƙofar farjin, daga nan sai a barbaɗa maganin da zai tsayar da jini da wanda zai sa wurin ya yi saurin warkewa. Ga kuma waɗanda suka sami matsalar sakamakon rashin kula ko rashin tsabta, ana amfani da hannu ne a sake buɗa ƙofar, daga nan sai wanzamin ya gargaɗi iyayen yarinyar ko masu kula da ita da su riƙa tsabtace farjinta ta hanyar wanke mata a duk lokacin da ta yi fitsari ko ta tashi daga barci.

    Gyara Sarƙa

    Sarƙa lalura ce da ake samu a farjin mace a inda za a tarar leɓatun farjinta sun sarƙe yadda ba za ta iya ganin ƙofar farjinta ba. Irin wannan matsala ba kasafai ake samun ta ba, akan daɗe ba a sami mace mai fama da irin wannan matsala ba. Idan an sami mace da lalurar sarƙa aka kai wa wanzami domin ya gyara yana amfani da hikimar da ya gada kuma ya ƙware a kanta domin gyara ta.

    Ba dukkan wanzamai ne suke iya gyara mace mai matsalar sarƙa ba, ko a cikin wanzaman gado sai waɗanda suka koya wajen tsofaffin wanzamai suke iya gyara mace mai matsalar sarƙa. Wanzamai suna gyara mace mai matsalar sarƙa ta amfani da hannuwansu su raba leɓatun farjin su kawo magani su shafa a wurin yadda kowane zai tsaya a wurin da yake ba tare da ya sake sarƙewa da ɗan uwansa ba. Wanzamin zai yi ta yin haka har sai wurin ya zauna daidai ƙofar farjin ta fito sosai.

    Cire Mahindi

    Mahindi shi ma wata lalura ce wadda ake samu ga farjin mata wadda ta yi kama da angurya amma suna da bambanci. Shi mahindi tsokar nama ce take tsirowa ta toshe ƙofar farjin mace ta hana ta saduwa da namiji. Wajen cire shi ana amfani da askar aski ne ko askar tsaga (‘yartsaga), a sanya akaifa a ɗago shi sama, sai a sanya askar a yanke shi.

    Gyara Turu

    Wata matsalar wadda wanzamai suke gyarawa a farjin mace, ita ce ta turu. Shi turu ana samun matsalar shi ga mata ƙalilan. Matan da suke da wannan ciwo idan suna saduwa da namiji azzakarin ba ya wucewa duka a cikin farjin saboda turun da yake ciki ya tare ƙofar.

    Mata masu irin wannan lalura suna iya ɗaukar ciki, sai dai idan sun zo haihuwa sukan fuskanci matsalar da kan kai ga sai an yi masu yankan gishiri, wanda wani al’amari ne mai haɗari. Ita ma wannan matsalar ba dukkan wanzamai ne suka iya gyara ta ba, sai wanzamai da suka koya ga wanzamai na da can.

    Wanzamai suna gyara turu ta hanyar sanya yatsunsu biyu manuni da na kusa da shi a cikin farjn mace mai wannan matsala, su kama shi da yatsun su buɗe shi yadda ba zai tokare azzakarin namiji a lokacin da ake saduwa da matar ba.

    Kaciya

    Kaciya tana nufin yanke ko cire fatar da ta rufe kan azzakarin mutum. A ƙasar Hausa wanzamai ne suke yin kaciya, kuma mafi yawanci an fi yin kaciya a lokacin sanyi. Dalilin da ya sa aka fi yin kaciya a lokacin sanyi shi ne, a wannan lokaci jikin mutum ya fi saurin tohuwa, don a wannan lokaci ko rauni mutum ya yi zai yi saurin warkewa.

    A lokacin sanyi kuma an kai ga amfanin gona, abinci ya wadata, yaran da aka yi wa kaciya za su sami wadataccen abincin da za su ci, jikinsu ya tohu da sauri su yi saurin warkewa, kuma a wannan lokaci aiki ya yi sauƙi za a sami wanda zai tsaya ya riƙa kula da su.

    A al’adar Hausawa yawanci sai yaro ya kai shekara bakwai abin da ya yi sama da haka nan za a yi masa kaciya. Hausawa ba su faye yi wa yaro kaciya yana da shekara takwas da haihuwa ba. Saboda an camfa wai idan aka yi wa yaro kaciya yana da shekara takwas, to wani bala’i na iya faɗa masa. Wannan ne ya sa idan ba a yi wa yaro kaciya yana da shekara bakwai ba, to ba za a yi masa ba, sai ya kai shekara tara ko goma.

    A da idan za a yi kaciya ana tara yaran unguwa ɗaya a gida ɗaya domin yi masu kaciya, a sanya mutum ɗaya ya tsare su yana kula da su don kar su fama kaciyar. Amma a yanzu wasu suna yin haka, wasu kuwa da sun tashi yi wa ‘ya’yansu kaciya, sai su kira wanzami ya yi kaciyar ba tare da sun gaya wa kowa ba.

    A ranar da za a yi wa yaran kaciya wanzamin da zai yi kaciyar tare da yaransa masu taimaka masa kan yi sammako zuwa gidan da za a yi kaciyar. A al’adar Hausawa an fi son a yi sammako domin a wannan lokaci yaran da za a yi wa kaciyar ba su farka daga barci ba.

    An fi son a yi kaciyar da sun farka sun wanke idanunsu, watau ba su kai ga motsa jikinsu ya tashi ba. Wani dalili da yake sa a yi kaciya tun da sassafe shi ne, a wannan lokaci rana ba ta fito ba bare ta yi zafin da zai sa jinin yaron da za a yi wa kaciyar ya tashi, wanda zai sanya idan an zo yi masa kaciyar ya zubar da jini da yawa.

    Idan za a yi wa yara kaciya ba a gaya masu ranar da za a yi don kar su sami fargaba ko su gudu su ɓuya. Haka kuma a lokacin da za a yi masu kaciya an fi son wani daga cikin ‘yan’uwansu ya riƙe su don kar su yi tsammanin cuta masu za a yi. Ana kuma ba su wani abu mai daɗi kamar alewa da makamantanta wadda za ta ƙara kwantar masu da hankali su ƙara yarda da ba cutar su za a yi ba. A lokacin da za a yi kaciyar ana rufe wa yaron da za a yi wa kaciyar idanu don kar ya ga jini na zuba daga jikinsa hankalinsa ya tashi.

    A lokacin da za a yi wa yaro kaciya idan ya nuna kasala abokan wasansa da kakanninsa kan riƙa yi masa dariya, a wani lokaci sukan tambaye shi, idan ba ya son a yi masa kaciya ya ba da wani abu a ƙyale shi. A irin haka wasu kan ce sun ba dukkan dabbobin da ke gidansu da gidan duka, wasu ma kan ce sun ba da wani daga cikin ‘yan gidansu ko wani daga cikin mahaifansu.

    Idan wanzami ya yi kaciya, bayan kuɗin kari waɗanda ‘yan uwa da abokan arzikin iyayen yaron da aka yi wa kaciya suka bayar, su ma iyayen yaron suna ba wanzamin tasu sallamar. Irin wannan sallama ta haɗa da kuɗi daidai arzikin iyayen yaron, bayan kuɗi ana kuma ba da damen dawa da zakara domin wanzamin ya sami hatsin da za a riƙa yi ma abinci ba tare da ya sha wahalar neman abinci ba.

    Shi kuwa zakara da ake bayarwa ana ba da shi wai ladar jinin da ya fitar a jikin ɗan kaciyar. A da can idan aka yi wa yaro kaciya ya zama dole a ba wanzamin damen dawa da zakara, amma a halin yanzu saboda juyawar zamani wannan al’adar ta fara ƙaura, wurare kaɗan ne ake bayarwa. A maimakon su ana ba da kuɗi gwargwadon arzikin iyayen yaron da aka yi wa kaciyar.

    Bayan waɗannan kuma a da can kayan da suke jikin yaron da za a yi wa kaciya idan an tuɓe su, bayan wanzamin ya gama kaciyar, sai ya ɗauke su ya kai wa ‘ya’yansa.

    Kaciyar sa-Wandonka

    Wannan kaciya ƙarin hikima ce da wanzamai suka samu a gargajiyance, wadda ake yi wa yaro kaciya da an gama ya sanya wandonsa ya yi tafiyarsa ya ci gaba da yin harkokinsa na yau da kullum. A irin wannan kaciya ba a tsare yaro domin yin jinya kamar yadda ake yi kafin zuwan wannan hikima. A taƙaice a iya cewa kaciyar sa-wandonka ci gaba ne wasu wanzamai suka samu a gargajiyance.

    Ita wannan kaciya babu wani bambanci wajen yin ta da irin kaciyar da wanzamai suke yi, wurin da bambancin yake shi ne wajen sanya magani. A wannan kaciya ba a tauna bagaruwa a furza ruwan, a maimakonta ana shafa ruwan magani mai mai, sai kuma a naɗe kaciyar da wani farin ƙyalle kamar yadda ake yi wa kaciyar asibiti.  Wannan farin ƙyalle da ake naɗawa ba zai fita ba sai a lokacin da kaciyar ta warke.

    Karanta Yadda Askin Sarauta Yake

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Askin Sarauta Yake

    Yadda Askin Sarauta Yake

    Askin sarauta na nufin askin da ake yi wa sarakuna ko wasu masu riƙe da sarauta a ƙasar Hausa. Ga al’ada ba kowane wanzami ne yake yi wa sarki aski ba, kowane sarki yana da wanzamin da yake yi masa aski, kuma wannan wanzami shi ne sarkin aska ko magajin askar wannan sarki.

    Kowane sarki akwai ranar da yakan keɓe wadda ake yi masa aski. Mafi yawancin sarakuna an fi yi masu aski a ranar Litinin ko Talata. Dalilin da ya sa ake ware waɗannan ranaku shi ne, shi wanzamin ya san da wannan rana da kuma lokacin da zai riƙa zuwa, to a ranar ba zai yi tafiya zuwa wani wuri ba domin kar ya saɓa. Wasu kuma suna yin aski a waɗannan ranaku ne saboda camfe-camfe.

    Kuma kowane sarki yana da askar da ake yi masa aski wadda ba a yi wa kowa aski da ita sai shi. Sai kuwa idan bayan rasuwarsa a ci gaba da yi wa wanda ya gaje shi aski da ita. Bugu da ƙari, ba a kowane wuri ake yi wa sarki aski ba, sarkin askarsa ko magajin askarsa yake tarar da shi a gidansa ya kai shi bargarsa domin ya yi masa aski. Dalilin da ya sa ake bin waɗannan sharuɗɗa na yi wa sarakuna aski shi ne, domin kariya daga maƙiya kar su harbe su, ko su yi masu wasu surkulle ta hanyar aski da zai yi dalilin su rabu da sarautunsu ko wani sharri ya same su, ko rashin lafiya, ko ma dai su mutu.

    Game da ladar da sarakuna suke biyan wanzamansu bayan sun gama masu aski, ba a lokacin da suka yi askin suke biyansu ba. Su sarakuna a lokacin da suka bukata sukan aika wa sarakunan askarsu da kyauta mai yawa. Ire-iren kyaututtukan da sarakuna kan ba sarakunan askarsu sun haɗa da manyan riguna da kuɗi da abinci (gero da dawa da makamantansu) da dawaki. Haka idan wani biki na aure ko na haihuwa ya sami wanzamin sarkinsa kan taimaka masa sosai.

    Aski da Gyaran Fuska

    Aski na nufin amfani da askar aski mai kaifi domin a aske sumar da ta tsiro a kan mutumin da ya bukaci a yi masa askin.A ƙasar Hausa masu yin sana’ar aski ana kiransu da sunan wanzamai. Gyaran fuska na nufin amfani da irin askar da ake yin aski domin aske gashin da ya tsiro a fuskar mutumin da ya bukaci a yi masa gyaran fuska.A al’adar Hausawa maza ne kawai ake yi wa aski da gyaran fuska.

    Ga kuma wanda ya ajiye gemu sai a gyara gemun ya fito sosai. Gyaran fuska yana da matuƙar muhimmaci ga rayuwar Hausawa, domin kuwa ana kiran wanzamai yin gyara saboda masu gashi da yawa ko ƙasumba su ji daɗi ga fuskarsu. Ga wasu suna nuna, idan gashi ya tsiro masu a fuska yana yi masu ƙaiƙayi sosai har sai in an aske shi sannan za su ji daɗi ga fuskarsu.

    Akwai aski iri daban-daban da ake yi wa Hausawa, kuma kowane daga cikinsu akwai dalilan da kansa a yi shi. Ire-iren waɗannan aski sun haɗa da askin ƙwaryar molo da gyaran fuska da askin sarauta da askin jarirai na suna da askin tuba da zanko da tukkaye da bawale da askin muzantawa da kuma tsayar da gemu.

    Askin Ƙwaryar Molo

    Askin ƙwaryar molo aski ne wanda ake yi wa Hausawa da wasu al’ummomi. A irin wannan aski ana aske dukkan suma ne tas har idan rana ta haskaka kan wanda aka yi wa askin sai mutum ya ga kan yana ƙyalli. Idan za a yi askin ƙwaryar molo da fari ana fara jiƙa sumar da ruwa sai ta jiƙa sosai daga nan sai a bi da sabulu domin ta ƙara laushi.

    Yana da muhimmanci a fahimci cewa, duk sumar da ba ta jiƙa da ruwa sosai ba, idan aka yi saurin shafa sabulu, ba za ta yi laushi kamar wadda ta jiƙa sosai ba. A irin wannan gaggawar ce za a tarar idan ana yi wa mutum aski zai ce da zafi. Idan ta jiƙa sosai aka shafa sabulu ta fi sauri da daɗin aski ga wanda yake yin askin da kuma wanda ake yi wa.

    Bayan suma ta jiƙa, sai a fara aski daga ɓangaren fuska kusa da kunnen dama a nufi wajen ƙeya. Ana bi ana askewa tare da la’akari da bin kwanciyar sumar, wato ana bin yadda sumar ta kwanta ba tare da tarbar kan gashin ba. Idan an aske dukkan gashin da yake baya, sai a juyo tsakiyar kai a nufo wajen goshi domin shi ma a aske shi.

    Bayan duk an aske gashin da yake bisa kai, sai a sake shafa ruwa domin a maimaita askin tare da bin hanyoyin da aka bi lokacin aka fara yin askin.Haka kuma idan babban mutum ne mai gashi a fuska, sai kuma a yi masa gyaran fuska.

    A’al’adar Hausawa askin ƙwaryar molo yana da muhimmanci sosai, domin kuwa al’ada ta mayar da shi dole, har ma Hausawa a da can sun ɗauka dukkan wanda ya bar suma da yawa bisa kansa tamkar mahaukaci ne, mai yin koyi da ɗabi’a marar kyau. Wannan ne ya sa iyaye kan tilastawa ‘ya’yansu yin askin ƙwaryar molo, wasu ‘ya’yan ba cikin suna buƙata ba. Maroƙan Hausawa na gargajiya suna yi wa wanzamai kirari kamar haka:

    “In ba domin ku ba,

    Da mahaukata sun yi yawa”

    Ma’ana, in ba don wanzamai suna yi wa mutane aski ba, da yawan mutane masu gashi duguzun kamar mahaukata sun yi yawa cikin duniya.

    Askin Jarirai na Suna

    Askin jarirai na suna shi ne askin farko da ake yi wa jarirai bayan an haife su, ana yi wa jarirai maza da mata aski. A al’adar Hausawa ana yin wannan aski a ranar da aka raɗa wa jaririn suna. A da can kafin zuwan addini Musulunci a ƙasar Hausa ana yin wannan aski ne a lokacin da dangi na wajen uba da dangi na wajen uwa suka taru domin raɗa wa jariri suna.

    Misali, a al’adar Kaina-Fara Arnan Birci da suke zaune a Ƙauyen Goda ta Birci a Ƙaramar Hukumar Kurfi ta Jihar Katsina, sai jariri ya kwana arba’in da haihuwa sannan za a yi masa aski, kuma a wannan rana ne za a raɗa masa suna. A halin yanzu ana yi wa jarirai askin suna a rana ta bakwai da haihuwa. A wasu ƙauyuka ana yin askin jariri da maraice lokacin da dangi mata na wajen wadda ta haihu da dangin wanda ya haihu duk sun haɗu a wannan lokaci ne wanzami zai yi askin. Dalilin haka kuwa shi ne, don kowa ya ba da tasa gudummuwar wajen yin askin

    Dangane da ladar da ake biyan wanzami idan ya yi askin jariri na suna za mu ga a gargajiyance a ƙasar Hausa kafin samuwar kuɗin zamani ana biya ne da hatsi da dabbobi da kuma tsuntsayen gida irin su kaji. A nan dangin masu haihuwa na maza da na mata duk suna ba da nasu ga wanzamin.

    Bayan an gama aski sai a fitar da kushekara ko karfata daga ragon suna a ba wanzamin. Daga nan kuma sai a ba wanzamin ƙwaryar aski. Dukkan waɗannan kayayyaki da ake ba wanzami, Hausawa sun ɗauka ba su biya shi ladan aikin da ya yi ba, domin in ba shi ba, babu mai iya yin ayyukansa. Wannan dalilin ne ya sa ake haɗa wa wanzami dukkan waɗannan kayayyakin abinci, saboda kar rashin abinci ya sa shi tafiya neman abinci, haka ka iya jawo idan an haihu aka zo neman sa ba za a same shi ba, don ya tafi neman abinci.

    Tukkaye

    Tukkaye ana yin su ne bisa kan yara maza ɗaya-ɗaya. Abin nufi a nan shi ne, su tukkaye ana barin gashi a lokacin da ake aski kaɗan-kaɗan a wasu wurare bisa kan yaron da ake yi wa aski waɗanda a mafi yawancin lokaci ba a aske su sai lokacin da za a yi wa yaro kaciya. Wasu tukkayen kuwa manya ne, waɗanda masu wasan fage suke sanyawa a yi masu domin kwalliya a bisa kawunansu.

    Ire-iren masu wasan fagen da suke yin tukkaye sun haɗa da ‘yan kokowa da ‘yan dambe da ‘yan kwarako da ‘yan dadale da gardawa da sauransu. Su tukkaye da ma can asalinsu na Hausawa ne, sauran baƙi da suka shiga cikin Hausawa su ma sun zo da irin nasu tukkaye, misali, Buzaye da a yanzu sun koma Hausawa, ana yi wa ‘ya’yansu tukkuwa ɗaya a bisa ƙeya, har sai ta kai ga matakin da gashin tukkuwar ya yi tsawo sai a yi masa kitso.

    Shi ma ba za a aske shi ba sai lokacin da za a yi wa yaron kaciya. Wasu kuma daga cikin Hausawa kan yi wa ‘ya’yansu tukkuwa ɗaya bisa tsakiyar kai, wasu kuma a kusa da goshi. Ita wannan tukkuwa ta kusa da goshi an fi yi wa almajirai ita, don har ana kiran wannan tukkuwa “leƙa tukunya”. Dukkan waɗannan tukkaye da aka yi bayani a sama ana aske wa yara su ne lokacin da za a yi wa yaron kaciya.

    Su kuwa waɗannan da suke yin tukkaye domin wasan fage suna yin tukkayen ne a lokacin da za su fara wasan fagen, ba kuma za su aske su ba sai lokacin da suka manyanta suka tuba da yin wasan fage, a lokacin ne za su yi askin tuba.

    Ana yin wasu tukkayen domin a muzanta mutum, watau idan aka kama wani mutum ya yi sata ko wani mummunan laifi wanda ya saɓa wa al’ada, idan ana son muzanta shi a idon jama’a, sai a sanya wanzami ya yi masa tukkaye da yawa a bisa kansa, a shafa masa baƙin tukunya a fuska, sai a sami makaɗi a zagaya da shi cikin kasuwa da wasu wuraren da mutane suke zama, ana yi masa kiɗa yana rawa tare da faɗar irin laifin da ya aikata wanda ya sa aka yi ma sa irin wannan aski.

    Ana kuma yin irin waɗannan tukkaye a lokacin wasan kalankuwa, idan wani ɗan kallo ya yi laifi aka kama shi.Idan aka yi masa tara ba shi da kuɗin biya, sai a kira sarkin askar wasan ya yi masa tukkaye da yawa bisa kai, a kuma shafa masa baƙin-tukunya a fuska. Daga nan sai a sanya shi ya goya wata budurwa a riƙa zagayawa da shi a cikin filin da ake yin wasan kalankuwa. Ana yi masa kiɗa yana rawa da wannan budurwa a goye, har sai ya zagaye ko’ina, sannan ya zo gaban Sarkin Samari ya ajiye budurwar ya yi godiya shi ke nan an sallame shi.

    Haka kuma ana yin tukkaye a lokacin da ake yi wa jariri askin suna, idan iyayen jariri da abokan arziki ba su biya kuɗin ana aski ba, ko kuma ba su ba wa kakanni kuɗin ana aski ba, sai su kakannin su biya kuɗin askin, daga nan sai su riƙa yi wa iyayen jaririn gorin cewa sun sayi jaririn, ya zama ɗansu ke nan, idan ana son a fanshe shi dole a nunka yawan kuɗin da kakanni suka ba da na ana aski a mayar masu.

    Tsayar Da Gemu

    A al’adar Hausawa, mutum ba ya ajiye gemu, sai ya kai wasu shekaru na haihuwa, ko kuma sai ya kai lokacin da al’ada ta ƙayyade mutum ya ajiye gemu. Yawanci lokacin yakan zo idan matar ɗansa ta ko ‘yarsa ta haihu, watau ya ɗauki jika ke nan, ya isa ya ajiye gemu.

    Idan kuwa ba shi da ɗa ko ‘ya wadda ta isa aure har ta haihu, to sai a kwatanta da haihuwar ɗan abokin haihuwarsa ko ‘yarsa. Ba za a sa gemu ba sai a lokacin wani biki na aure ko na suna a gidan. Tun kafin zuwan ranar ake sanar da ‘yan ‘uwa da abokan arziki da wanzamin gidan wanda shi ne zai yi wa wanda za a sanya wa gemu aski da tsayar da shi.

    Karanta Sana’ar Wanzanci A Jiya

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Wannan babi ya duba sana’ar wanzanci a jiya wato yadda aka gudanar da wannan sana’a kafin al’ummar Hausawa su sami shigar al’adun wasu baƙi cikin al’adunsu. A nan an yi bayani a kan matsayin sana’ar wanzanci a al’adar Hausawa da kayan aikin wanzanci da kuma yadda ake gudanar da ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da aski da gyaran fuska da cire belun-wuya da na mata da kaciya da tsaga da bayar da magungunan gargajiya.

    Matsayin Sana’ar Wanzanci a Al’adar Hausawa

    Kowane irin al’amari wanda ya danganci yadda ɗan Adam yake tafiyar da rayuwarsa ta yau da kullum yana da irin nasa matsayi a idanun masu yin sa da waɗanda ake yi wa. Wannan ne ya sa aka ga ya dace a duba matsayin sana’ar wanzanci a al’adance da irin yadda al’ummar Hausawa suke kallon wannan sana’a da masu yin ta.

    Sana’ar wanzanci tana da babban matsayi a al’adar Hausawa, wannan kuwa ya faru ne saboda ire-iren muhimman ayyukan da wanzamai suke aiwatarwa. Haka kuma al’ummar Hausawa suna girmama wanzamai, wannan ne ya sa Alhaji Sale Gambara a cikin bakandamiyarsa yake cewa, a duk gari akwai manya uku waɗanda su ne kamar haka; shugaban da yake jagorancin mutanen garin, sai limamin garin daga nan sai wanzamin garin.

    Haka kuma a fannonin adabin Hausawa akwai wurare da dama waɗanda aka bayyana muhimmancin wannan sana’a. Misali, a cikin littafin da Alhaji Nuhu Bamalli ya rubuta mai sunan “Mungo Park Mabuɗin Kwara”, wanda aka yi bayani a kan tafiye-tafiyen Mungo Park a sassan Afrika ta Yamma a shafi na 42-43 an yi bayyanin inda wannan matafiyi ya bayyana ya zama wanzami.

    Haka su ma makaɗan ƙasar Hausa suna bayyana muhimmancin wanzami a idon Hausawa. A iya ganin haka a waƙar da Ɗan’anace ya yi wa Shago inda yake cewa:

    “Ɗan Abdu Gazaguru,

    Ai na faɗa maka goga,

    Wanga kashi da kay yi ba dawa ne ba,

    Kar ka kashe Na’ila wanzami na,

    Ai shi ka yo muna gyara,…”

    Kuma kasancewar wanzaman gargajiya masana tsubbace-tsubbace da sihirce-sihirce ne masu ban mamaki da al’ajabi da ban tsoro ya sa al’ummar Hausawa suke ɗaukar su kamar wasu dodanni ko wasu mutane da ake tsoro. Wannan ne ma ya sa ba a yi wa wanzamai gardama ko gatse ko shisshigi dangane da yadda suke aiwatar da ayyukansu, don tsoron kar su yi wa mutum wani abu da zai cuce shi.

    Haka kuma al’ummar Hausawa sun ɗauki wanzamai a matsayin wasu mutane masu bayar da taimako idan wata lalura ta rashin lafiya ko bukatar maganin gargajiya ta taso. A nan ma makaɗan Hausawa sun bayyana irin rawar da wanzamai suke takawa wajen yin ire-iren waɗannan tsatsube-tsatsube.

    Misali, a waƙar da Alhaji Mamman Shata Katsina ya yi wa Ciroman Aski na Jalingo ya bayyana irin yadda wanzamai suke harbin ‘yan uwansu a lokacin da suka zo yin aski sai su riƙa yin kyarmar hannu wadda take yin dalilin a riƙa yankar wanda ake yi wa aski. Ga irin yadda ya bayyana haka cikin wannan waƙa:

    “Ga wani ya zo aski,

    Sun harbai hannu nai na karkarwa,

    Da ya zo gun aski,

    Sai na ga jini na ta zubowa…”

    Haka kuma karin maganar Hausawa ya ƙara fito da matsayin wanzami a idon Hausawa kamar haka:

    Kowa ya ci ladar kuturu, dole ya yi masa aski.

    Kushekarar jaki sai wanzamin kura.

    Wanzami ba ya son jarfa.

    Waɗannan dalilai ne suka sa al’ummar Hausawa suke matuƙar kyautata wa wanzamai da dukkan abin da ya dace na kyautatawa, kuma kowane mutum ya yarda da dukkan ayyukan wanzanci, ana yi masa da dukkan iyalinsa. Idan bukatar aikin wanzami ta kama matuƙar bai zo lokacin da ake buƘatar ya zo ba, ana tarar da shi har gidansa don a gani ko lafiya? Wannan dalili ya sa yin ayyukan wanzanci a wurin Hausawa a jiya wani al’amari ne wanda ya zama dole a yi shi.

    Kayan Aikin Yin Wanzanci

    Wanzamai suna amfani da kayayyaki iri daban-daban domin yin ayyukan wanzanci. Ire-iren waɗannan kayayyaki sun haɗa da askar aski da kwanon aski da kalaba da ƙoshiya da ‘yaR tsaga da hantsaki da tankolo da zabira da ƙaho da kura ta cire haƙori da sauransu.

    Askar Aski

    Askar da ake amfani ita wajen yin aski ƙarama ce madaidaiciya kuma ba ta da tsawo sosai. Akwai bambanci tsakanin wadda ake askin jarirai da wadda ake yi wa manya aski.Ta askin jarirai ba ta kai girman wadda ake yi wa manya aski ba. Da kuma askar aski ake amfani wajen yin kaciya, ana amfani ne da irin wadda ake yi wa manya aski wato mai kaifi da nauyi wajen yin kaciya. Kafin zuwan wannan zamani ana amfani da askar baƙin ƙarfe wajen yin aski da kaciya, irin wannan aska ita wanzamai suka gaji amfani da ita, kuma maƙeran Hausawa ne suke samar ta ita ga wanzamai.

    Wani muhimmin abu da ya kamata a sani a nan shi ne, askar baƙin ƙarfe ta fi kowace irin aska riƙe kaifi. Idan wanzami ya wasa askar baƙin ƙarfe sai ya yi wa mutane da yawa aski ko gyaran fuska ba tare da ya sake wasa ta ba. Akwai maƙera na daban waƙanda suke ƙerawa da kuɗar asaken aski.

    Dutsin Washin Asaken Aski

    Dutsin washin asaken aski dutsi ne ƙarami mai sulɓi da ake amfani da shi domin yin washin asaken aski idan kaifinsu ya dakushe, wato idan kaifinsu ya ragu. Idan kuwa kaifinsu ya dakushe duka, to sai a kai ga maƙeri domin a sake koɗa su. Ana amfani da dutse ta hanyar goga askar bisa dutsen sannu a hankali har sai an tabbata askar ta wasu.

    Hanyar da ake gane aska ta wasu ita ce, sai a ɗan fera fatar hannu, idan askar ta fere fatar sosai aska ta wasu ke nan. Kafin zuwan wannan zamani duwatsu iri biyu da ake amfani da su wajen wasa asaken aski. Na farko shi ne na gatarin aradu, watan dutsen da yake faɗowa idan an yi tsawa lokacin ruwan damina.

    Hanyar da ake bi domin samun dutsen gatarin aradu ita ce, da zarar an yi tsawa, aka kuma yi dacen ganin wurin da ta faɗi, sai a yi gaggawa a je a zuba madara ko nonon shanu a wurin da tsawar ta faɗi. Idan an tona sai a tarar da dutsin da ya faɗo, don kuwa madara ko nonon da aka zuba zai hana shi yin ƙasa da nisa. Dutsi iri na biyu da ake amfani da shi domin washin asaken aski shi ne na ƙanƙara mai sulɓi da ake samu a kogi ko wurin da yake da duwatsu. 

    Fatar Washin Asaken Aski

    Fatar wasa asaken aski fatar dabbobi ce ake samu daga wajen dukawa wadda aka jeme. Ana amfani da mai faɗin misali inci ɗaya da rabi, tsawonta kuma misalin inci goma sha biyar zuwa ashirin. An fi amfani da mai kauri irin ta manyan dabbobi domin kuwa ta fi inganci da ƙara wa aska kaifi.

    Amfanin fatar washin asaken aski shi ne, idan aka wasa askar da dutsi kaifinta ba zai kai sosai ba, sai an wasa da fata. A nan ne sai a shafa ruwa ga fatar a bi da askar ana shafawa bisa fatar sannu a hankali. Wannan ne zai daidaita kaifin askar yadda idan an zo yin aski askar za ta tuje gashin da sauƙi. Mafi yanwancin wanzamai suna ɗaura fatar wasa asaken askin wurin zabira daga gefe.

    Kwanon Aski

    Kwanon aski ana amfani da shi ne domin zuba ruwan da za a riƙa amfani da shi wajen yin aski da gyaran fuska da kaciya da tsaga. A da can kafin zuwan Turawa wanzamai suna amfani da ƙoƙo domin zuba ruwan aski. Wannan ne ma ya sa ake kiran wanzaman da suke yin aski da gyaran fuska da sunan ‘wanzaman ƙoƙo’. A halin yanzu ana amfani da kofin roba ko na ƙarfe domin zuba ruwan aski

    Kalaba

    Kalaba ƙarfe ne ƙarami wanda tsawonsa misalin inci shida zuwa bakwai, kuma ba shi da kauri sosai. Maƙera ne suke ƙera kalaba, ba kuma dukkan maƙeri ne yake ƙirar kalaba ba, akwai maƙera na daban masu ƙera ta. Ana yin ta ne da kaifi a gefe ɗaya na kanta sai a lanƘwasa kan ya zamo kaifi ciki. Ana yi wa gindinta kauri domin a ji daɗin riƙewa idan za a yi aiki da ita. Amfanin kalaba wajen ayyukan wanzanci shi ne a riƙa cire belin- wuya da ita.

    Ƙoshiya

    Ƙoshiya itace ne ƙarami ake sassaƙawa da ɗan faɗi ga kai da kuma kauri ga gindi. Tsawon ƙoshiya misali inci shida ne zuwa bakwai, faɗin kanta kuma bai kai inci ɗaya ba. A taƙaice tsawon ƙoshiya ɗaya yake da na kalaba. Ana amfani da ƙoshiya wajen wanzanci domin taushe harshen jariri a lokacin da za a cire belun-wuya. Ita ƙoshiya masassaƙa ne suke samar da ita ga wanzamai, akwai kuma wasu wanzamai da suke iya sassaƙa ƙoshiya.

    ‘Yar Tsaga

    Yartsaga aska ce ƙarama da maƙera suke ƙerawa, tsawonta ya kai misalin inci huɗu zuwa biyar, kanta kuma ana yin sa da faɗi da tsini da kaifi. Ana amfani da ‘yartsaga wajen ayyukan wanzanci domin yin wasu ayyukan da wanzamai suke yi a farjin mata kamar cire angurya da yanke linzami da cire haƙoran shuwa.Ana kuma amfani da ita domin yin tsagar gado da ta magani da kuma ta kwalliya.

     Hantsaki

    Hantsaki ƙarfe ne da maƙera suke ƙerawa da baki a gindi da kuma tsini a kai. Ba shi da kauri sosai, kuma tsawon sa misalin inci huɗu ne. Ana amfani da hantsaki wajen wanzanci domin cire angurya a farjin mata.

    Ƙaho

    Wanzamai suna amfani da ƙahon sa ne domin yin ƙaho. Ana amfani da ƙaho madaidaici wanda ba babba ba ƙwarai, ba kuma ƙarami ba, ana yanka misalin tsawon inci biyar ko shida. Ana yi wa wajen tsininsa ‘yar ƙaramar ƙofa. Ana amfani da ƙaho ne domin yin ƙaho. Mahauta ne suke samar da ƙaho ga wanzamai, su ne suke fitar da shi daga kan sa da aka yanka sai su sayar wa wanzaman da suke yin ƙaho.

     Jijiya

    Wanzamai suna amfani da jijiyar agarar ƙafar akuya ko tunkiya domin a riƙa liƙe ƙofar tsinin ƙahon da aka kafa wa mutum domin ya liƙe a wurin da aka kafa shi a jikin mutum. Wanzamin zai sanya wannan jijiya a cikin bakinsa yana taunawa sai ya liƙa ta a wurin ƙofar, da an liƙa shi ke nan sai ƙahon ya liƙe a wurin da aka kafa shi, ba zai fita ba sai in an cire wannan jijiya. Ita ma jijiya mahauta ne suke samar da ita ga wanzamai.

    Kura ta Cire Haƙori

    Ita kura ƙarfe ne ake samu domin cire haƙori, yanayinta ya yi kama da abin da kafintoci suke cire ƙusa a wannan zamani, amma ita kura ba ta kai girman abin cire ƙusa ba. Wanzamai suna amfani da kura ne domin cire haƙori. Wanzami yana amfani da kura ne ya kama haƙori mai ciwo ko mai girgiɗa sai ya cire shi daga wurin da yake.

    Tankolo

    Tankolo ‘yar jaka ce wadda dukawa suke ɗinkawa da fatar akuya ko tinkiya domin wanzamai su riƙa sanya askar aski ɗaya ko kuma babba wadda za a sanya asaken aski masu yawa.

    Zabira

    Zabira jaka ce babba mai aljihuna da yawa misali uku ko huɗu. Ana yi mata maratayi domin a riƙa ratayawa. Ita ma dukawa ne suke ɗinka ta da fatar akuya ko tinkiya domin yi wa wanzamai jakar da za su riƙa sanya dukkan kayan aikin wanzanci waɗanda aka yi bayaninsu a baya.

    Don karanta Matsayin Hausawa A Yau danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

  • Matsayin Hausawa A Yau

    Matsayin Hausawa A Yau

    Wannan duniya da muke ciki tana ƙunshe da al’ummomi daban-daban masu magana da harsuna da adabi da al’adu mabambanta. An ƙiyasta a yanzu akwai al’ummomi masu magana da harsuna daban-daban kimanin dubu shida da ɗari shida da sittin (6660) a wannan duniya tamu, kuma kowane daga cikin su na cin gashin-kansa. Misali, akwai Larabci da Turancin Ingilishi da na Faransanci da na Jamusanci da Sinanci da Indiyanci da dai sauransu.

    Kowane daga cikin waɗannan harsuna suna da masu yin magana da shi, kuma kowane yana da sigogin yaɗuwarsa. Daga cikin su za a tarar wani harshen masu yin magana da shi ‘yan ɗaruruwa ne a wani tsukin wuri, wani kuma za a tarar mutane ne dubbai suke yin amfani da shi, wani kuma miliyoyi ne waɗanda suka barbazu a wurare na nahiyoyin da suke cikin wannan duniya (Yahaya, 1991:3).

    Idan muka dawo nan gida Afrika akwai al’ummomi daban-daban waɗanda suke magana da harsuna kimanin 1850 wanda harshen Hausa na daga cikinsu. Yana daga cikin harsunan Afrika irinsu Swahili da Mande da Wolof da Ashanti da Yoruba da Bambara da sauransu. Daga waɗannan harsuna 1850 da suke Afrika an tantance an gano akwai kimanin harsuna 394 waɗanda ake yin amfani da su a sassa daban-daban da suke cikin Nijeriya.

    Duk da kasancewar waɗannan harsuna suna da dangantaka da wasunsu kowane daga cikinsu yana zaman kansa a matsayin harshe. Daga cikin harsunan da ake amfani da su a Nijeriya baya ga harshen Hausa akwai Yarbanci da Ibo da Fulatanci da Barbarci da Efik da Nufanci da Ibibio da Tiv da Angas da Edo da Bade da Igala da Idoma da Igbirra da Mandara da Karekare da Kanakuru da sauransu. A halin yanzu ana amfani da waɗannan harsuna a tsakanin al’ummomin da suke magana da su don yin hulɗoɗin rayuwa na yau da kullum (Yahaya, 1991:3-4).

    Hausawa suna daga cikin manyan al’ummomin da suke a wannan duniya a wannan zamani, kuma harshen Hausa wanda Hausawa suke magana da shi a matsayin harshen uwa na daga cikin manyan harsunan wannan duniya. Idan aka ɗebe harshen Larabci, masu magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Nahiyar Afrika, harshen Swahili ne kaɗai yake yi masa cin dudduge.

    Haka kuma harshen Hausa ne harshen da kowa yake yin magana da shi a mafi yawancin sassan arewacin Nijeriya ciki har da waɗanda ba Hausawa ba (Schuh, 1982:1). A Jamhuriyar Nijar mafi yawancin mutanen wannan ƙasa na magana da harshen Hausa (Hira da AHSA, a garin Agadez, a ranar 8/5/2005).Wannan ya bayyana mana ke nan, masu magana da harshen Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika.

    Idan muka dawo kan batun da muke son magana a kansa watau matsayin Hausawa a yau, za mu ga kamar yadda aka yi bayanai a baya, kasancewar al’ummar Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika, ya taimaka ƙwarai wajen yaɗuwa da haɓakar harshe da adabi da al’adun Hausawa da kuma mamaye na maƙwabtan ƙasar Hausa. Kamar yadda wani ɗan ƙabilar Babur ta jihar Borno ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce wadda take mamaye dukkan wata al’umma da ke kusa da ita” (Hira da AYB, a ranar 24/9/2004).

    Wani Badakkare daga Zuru ya bayyana min cewa: “Al’ummar Hausawa da harshensu da al’adunsu da adabinsu suna ƙara haɓaka a kullum, don kuwa ba wani wuri da mutum zai shiga a cikin Nijeriya da kuma ƙasashen waje da ba a san Hausawa ba”(Hira da IIPZ, a garin Zuru, a ranar 18/9/2005).

    Ga kuma ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ibo mutumin jihar Anambra kan matsayin Hausawa a yau: ”Al’umma ce mai harshe wanda ake magana da shi a duk faɗin Nijeriya ta Arewa da maƙwabtanta ciki har da ma waɗanda ba Hausawa ba, kuma Hausawa mutane ne masu saurin karɓar baƙi, kuma masu son zaman lafiya”(Hira da DIJ, a Birnin Kabi, a ranar 16/9/2005).

    Haka kuma wani ɗan ƙabilar Ibo daga jihar Abia ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce mai yawan gaske, kuma suna samun bunƙasa a duk harkokinsu na rayuwar yau da kullum”(Hira da MAO, a Birnin Kabi, a ranar 16/10/2004).

    Wani Banufe bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne da suka yi fice a dukkan al’amuran duniya, wannan ne ya sa suke da manyan mutanen da duniya ta san da zamansu a wannan zamani”(Hira da MNM, a garin Bida, a ranar 23/9/2004).

    A ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ekoi ta jihar Cross Riɓer bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne masu gaskiya da riƙon amana da kuma karɓar baƙi cikin mutunci. Kuma mutane waɗanda suke bin dokokin addininsu sau da ƙafa. Haka kuma harshensu ya yaɗu a kowane lungu da saƙo da yake cikin Nijeriya da maƙwabta (Hira da EEO, a garin Gusau, a ranar 10/9/2005).

    Wata Bayarabiya kuma bayyana min ra’ayinta ta yi kan matsayin Hausawa a yau kamar haka: “Al’ummar Hausawa mutanen kirki ne wanda a yanzu yana da matuƙar muhimmanci ga dukkan ‘yan Nijeriya su koyi harshen Hausa don samun sauƙin tafiyar da harkokin rayuwarsu ta yau da kullum”(Hira da MGAA, a garin Zariya, a ranar 30/9/2004).

    Bisa la’akari da waɗannan ra’ayoyi da waɗanda ba Hausawa ba suka bayar kan matsayin Hausawa a yau, na tabbata za a amince da ni al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani a idanun mafi yawancin mutanen da suke cikin Nijeriya da ma waɗanda suke a ƙasashen da suke maƙwabta.

    Haka yake a idanun mutanen da suke ƙasashen da suke nesa da ƙasar Hausa don kuwa a wata hira da na gudanar da wani wanda ya ziyarci Ingila ya bayyana min cewa “A ƙasashen Turai al’ummar Hausawa suna da babban matsayi, kuma ana duban su a matsayin mutanen kirki saboda halayensu masu kyau sun sanya da wuya ka same su suna aikata munanan laifuffuka irinsu sata da zamba cikin aminci da fashi da makami da rashin gaskiya” (Hira da AASD, a garin Katsina, a ranar 14/12/2005.

    Saboda matsayin al’ummar Hausawa da harshensu a wannan zamani ya sa harshen Hausa ya zama na farko daga cikin harsunan Afrika ta Yamma da aka fara rubuce-rubuce da shi. Haka kuma shi ne harshe na farko da aka fara gabatar da labarai da shirye-shirye a gidajen Radiyon ƙasashen waje kamar a Sashen Hausa na BBC London da Muryar Amirka (ƁOA) da Muryar Jamus (Radiyo Deutche Welle) da Radiyo China da Radiyo Alƙahira da Radiyo Iran da dai sauransu (Yahaya, 1991:10 – 11).

    A nan gida kasancewar Hausawa suna da tsararren mulki wanda suka riƙa tafiyar da harkokin rayuwarsu lokaci mai tsawo tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka, ya sa sun mamaye fagen siyasar Nijeriya a wannan zamani. A halin yanzu duk wani mai son mulkin ƙasar nan dole sai ya haɗa kai da Hausawa zai ci nasara.

    Saboda haka ne Hausawa a wannan zamani suka shahara a fagen tafiyar da harkokin mulki cikin nasara da kwanciyar hankali, kuma suka zama jagora ga dukkan al’ummomin da suke a cikin wannan ƙasa. A iya ganin haka idan aka waiwaya aka duba waɗanda suka shugabancin Nijeriya tun daga samun mulkin kai zuwa wannan zamani. Daga cikin shugabanni goma sha biyu da suka shugabanci Nijeriya shida ko bakwai daga cikinsu Hausa/Fulani ne.

    Na farko Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa da Janar Murtala Ramat Muhammad da Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari da Janar Muhammadu Buhari da Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Janar Sani Abacha da Janar Abdulsalam Abubakar da kuma Alhaji Ummaru Musa ‘Yar’aduwa.

    Haka kuma a ƙasashe maƙwabta waɗanda Hausawa suka yi ƙaura suka koma, sun sami babban matsayi a waɗannan ƙasashe. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon ire-iren gudummuwar da suke bayarwa don ci gaban waɗannan ƙasashe. A ire-iren waɗannan ƙasashe akwai Hausawa da daman gaske waɗanda suka yi fice a harkokin tafiyar da mulki da na soja da na tattalin arziki da na ilimi da dai sauran fannonin rayuwa.

    Misali, a yanzu Mataimakin Shugaban Ƙasar Ghana Alhaji Aliyu Muhammad Bahaushe ne wanda asalinsu mutanen Talatar Mafara ta jihar Zamfara ne. Bayansa akwai ‘Yan Majalisar Dokoki ta Ghana waɗanda Hausawa ne (An samo wannan bayani daga wani rahoto da Idi Ali, Wakilin Sashen Hausa na BBC London a Accra, Ghana).

    Duk da kasancewar al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani akwai matsalolin da suke neman dakushe wannan matsayi. Wannan kuwa ya faru ne saboda wasu daga cikin waɗanda suke jagorancin al’ummar Hausawa da kuma wasu waɗanda ake jagoranta na neman su watsar da kyawawan al’adu waɗanda aka san Hausawa da su kamar nuna ƙauna da ‘yan’uwantaka da kara da alkunya da haɗin kai da nuna gaskiya da riƙon amana da dai sauran ire-iren waɗannan kyawawan al’adu.

    A yanzu ire-iren waɗannan Hausawa suna son su zama marasa gaskiya da nuna son kai da son tattara abin duniya da rashin taimaka wa al’umma da rashin haɗin kai da dai sauran munanan abubuwa. Saboda haka matuƙar ba a gyara waɗannan matsaloli ba, to matsayin Hausawa na jagorancin al’ummar Nijeriya zai fita daga hannunsu kuma mutuncinsu ya zube.

    Kamar yadda aka gani, wannan babi an yi bayani a kan farfajiyar ƙasar Hausa jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa da mutanenta da halin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu da bayani kan ƙaura da shigowar baƙi a sassa daban-daban na ƙasar Hausa da dalilan da suka sanya su zaɓar ƙasar Hausa don yin zama na ci-rani ko zama na dindindin da kuma matsayinsu a yau.

    Don karanta Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Tun cikin shekarun 1960 zuwa wannan lokaci masana da manazarta da ɗalibai masu binciken tarihi suke ta kai-kawon nazari kan ƙaura da shigowar baƙi da kuma sakamakon da wannan ƙaura ta haifar ga al’ummomi daban-daban da suke cikin faɗin Nijeriya.

    Saboda haka ne ire-iren waɗannan masana da manazarta da ɗalibai suka kawo irin tasu fassarar kan kalmar ƙaura. Misali,”ƙaura na nufin tashin mutane daga ƙauyuka ko garuruwa zuwa manyan birane, wasu na wani ɗan lokaci (ci-rani), wasu kuma sun koma don su yi zama na dindindin a wannan sabon wuri” (Osaghae, 1994:20).

    Wani masanin kuma yana ganin ƙaura a matsayin “tashi daga wata gundumar mulki zuwa wata, wadda sakamakon wannan ƙaura yake samar da sabon wurin zama na dindindin” (Prothero, 1981:51).

    A wata fassarar kuwa ana ganin ƙaura a matsayin “mutum ko ƙungiyar mutane masu yawa su yi sauyin wurin zama su koma wani wuri na daban wanda za su yi zama na dindindin, amma ba irin sauyin wurin da makiyaya ko ‘yan ƙodago ko ‘yan ci-rani da makamantansu suke yi ba waɗanda ba sa yin zama na dindindin a sabon wurin da suka koma” (Bello, 1999:1).

    Dangane da haka ne wannan nazari ya yi ƙoƙarin kawo bayani kan ire-iren baƙin da suka yi ƙaura daga ƙasashensu na asali waɗanda suke maƙwabtaka ta kusa da ƙasar Hausa. Waɗannan baƙi sun haɗa da Fulani da Nufawa da Barebare da Buzaye da Yarabawa. An kuma kawo bayanan dalilan da suka sa sanya su zaɓar ƙasar Hausa a matsayin wurin da suka ga ya dace su zauna don ci-rani ko don su yi zama na dindindin.

    Idan muka dubi ire-iren baƙin da suke zaune a ƙasar Hausa kuma aka waiwayi tarihi, za a fahimci sun shigo ƙasar ne a lokuta daban-daban. Dangane da wannan nazari an kasa waɗannan lokuta zuwa biyu. Lokaci na farko ya fara daga ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas. Lokaci na biyu kuma ya fara daga farkon ƙarni na goma sha tara zuwa ƙarni na ashirin.

    Idan muka ɗauki lokaci na farko watau ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas lokaci ne da ƙasashen da a yanzu ake kira ƙasar Hausa kowace daga cikinsu take cin gashin kanta. A wancan zamani babu abin da a yanzu ake kira haɗaɗɗiyar ƙasar Hausa, kowane Sarki na mulkin iyakar riƙonsa,tsakaninsa da sauran sarakuna danginsa maƙwabta na kusa da na nesa sai yaƙi.A lokacin kuma hamayya a tsakanin waɗannan sarakuna don mallakar hanyoyin kasuwanci da tattalin arzikin wannan ƙasa ya zama ruwan dare.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda dukkan ƙasar da ta mallaki babbar kasuwa za ta jawo baƙin ‘yan kasuwa daga sassa daban-daban.Wannan irin damar ce Katsina ta samu a wajajen tsakiyar ƙarni na goma sha biyu, inda fatake Larabawa da Azbinawa da Wangarawa suka riƙa haɗuwa.A wannan lokaci saboda yawan yaƙe-yaƙe da sarakunan Kano suka yi fama da shi ta rasa wannan dama (Ibrahim,1982:74-75).

    Haka abubuwa suka yi ta faruwa sannu a hankali baƙi suna ta shigowa cikin ƙasar Hausa a wannan lokaci daga ƙasashe maƙwabta na kusa don yin kasuwanci da wasu hulɗoɗi. Daga cikin ire-iren waɗannan baƙi akwai Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa.

    Lokaci na biyu da baƙi suka shigo ƙasar Hausa watau farkon ƙarni na goma sha tara zuwa na ashirin, shi ne lokacin da aka yi jihadin Shehu Usman Ɗanfodiyo a cikin shekarun 1804 zuwa 1809. Wannan jihadi da kuma kafuwar Daular Sakkwato ya taimaka ƙwarai wajen ƙara shigowar baƙi ƙasar Hausa, misali Buzaye da Adarawa daga arewacin ƙasar Hausa (Hammani, 1975:197-198).

    A babi na biyar da na shida za a bi diddigin shigowar waɗannan baƙi ƙasar Hausa da kuma yadda wasu al’adunsu suka yi naso cikin al’adun Hausawa musamman sana’ar wanzanci a wannan zamani.

    Domin Karanta Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Ƙasar Hausa kamar kowace ƙasa tana da manyan hanyoyi da dama waɗanda suke taimaka wa tattalin arzikinta bunƙasa. Daga cikin waɗannan hanyoyi akwai waɗanda aka gada tun iyaye da kakanni, wato su ne na asali. Ire-irensu sun haɗa da noma da kiwo da fatauci da sana’o’in gargajiya. Bayan waɗannan akwai waɗanda aka samu sakamakon cuɗanya tsakanin Hausawa da wasu baƙin al’ummu kamar sana’ar kanikanci da kafinta da ɗinkin keke da mesin da dai sauransu.

    Noma

    Hausawa suna yi wa noma kirari da suke cewa “noma na duƙe tsohon ciniki kowa ya zo duniya kai ya tarar”. Wannan kirari na bayyana sana’ar noma daɗaɗɗiya ce a wannan duniya ba wai ga Hausawa kaɗai ba. Wannan ne ya sa idan ana maganar tattalin arzikin ƙasar Hausa, noma ne za a fara kawowa don kuwa shi ne ƙashin bayan tattalin arzikin wannan ƙasa.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda sana’a ce wadda kowa-da-kowa yake yi talaka da saraki, attajiri da matalauci, maza da mata, babba da yaro don a sami abincin da za a ci da kuma wanda za a sayar don yin hidimomin yau da kullum. Saboda haka ne manoma a dukkan faɗin ƙasar Hausa da kewayenta suke samun wurare masu nagarta waɗanda suka haɗa da fadama da jigawa don noma amfanin gona mai kyau.

    Al’ummar Hausawa na yin noma iri biyu, na abinci da na kasuwa. Kayan noma na abinci sun haɗa da gero da dawa da masara da maiwa da dai sauransu, na kasuwa kuma sun haɗa da auduga da gyaɗa. Haka kuma ƙasar Hausa tana da albarkar da ake noma wasu abubuwan kamar rogo da dankali da sauransu (Nadama, 1977:90 – 92).

    Kiwo

    Kasancewar ƙasar Hausa shimfiɗaɗɗiya ce ga kuma sarari da ciyayi a ko’ina ya sa kusan a kowane gida ana kiwon dabbobi ko tsuntsaye. Hausawa na tsare dabbobi da tsuntsaye a gidajensu ta hanyar ba su abinci ko kuma a kora su zuwa daji don su nemi abinci a can. Ire-iren dabbobin da Hausawa suke kiwo sun haɗa da shanu da tumaki da awaki don cin namansu da kuma sayarwa.

    Haka kuma ana sayar da fatunsu da ƙiragansu don yin amfani da su. Ana kuma ɗaukar kashin da suka yi don kaiwa gona a matsayin takin da zai ƙara wa gona albarkar ƙasa. Bayan waɗannan dabbobi, Hausawa na kiwon dawaki don hawa na ƙawa da jin daɗi. Haka kuma suna kiwon jakuna da alfadarai don ɗaukar kaya da yin wasu ayyuka irinsu fatauci. Ire-iren waɗannan dabbobi dukkansu ana kiran su da sunan dabbobin gida.

    Bayan dabbobi Hausawa suna kiwon tsuntsaye irin su kaji da agwagi da zabi don cin namansu da ƙwayayensu da kuma sayarwa. Haka kuma saraki da attajirai suna kiwon tsuntsaye na alfarma irin su aku da ɗawisu da kanari don sha’awa da nishaɗi.

    Fatauci

    Tun kafin wannan zamani al’ummar Hausawa suna da irin nasu tsari wajen tafiyar da harkokin kasuwanci. Wannan tsari ana iya dubansa ta fuska biyu, kasuwancin cikin gida da kuma na waje. A cikin gida akwai kasuwanni na garuruwa waɗanda ake tafiyar da harkokin kasuwanci ta hanyar furfure. A irin wannan kasuwanci ana musayar abubuwan sayarwa ne, misali manomi ya ba masaƙi kayan gona don ya amshi kayan saƙa, ko ya ba makiyayi don ya amshi wata dabba da sauransu.

    An daɗe ana yin irin wannan tsari na cinikayya a ƙasar Hausa har zuwa cikin ƙarni na goma sha takwas da aka shigo da hanyar yin amfani da kuɗin wuri da biringizau don yin saye da sayarwa a duk faɗin Afrika ta Yamma (Nadama, 1977:137 – 138). Ta fuskar kasuwancin wajen ƙasar Hausa ‘yan kasuwa daga ƙasar Hausa na yin fataucin kayayyaki daga wannan ƙasa zuwa garuruwan Adar da Azben da Nufe da ƙasashen Yarabawa da Gwonja.

    Bayan sun sayar da kayayyakinsu a can, suna kuma sawo wasu kayayyakin daga waɗannan ƙasashe su kawo ƙasar Hausa don su sayar. Ire-iren kayayyakin fatauci da suka riƙa saye daga ƙasar Hausa suna kaiwa waɗannan ƙasashe, sun haɗa da daddawa da kayayyakin sutura irin waɗanda aka saƙa a ƙasar Hausa da kuma shunin gadi da baba da dabbobi da sauransu.

    Haka kuma suna sawo kayayyaki irinsu bindigogi da kayan albarushi da riguna girken Nufe da kayan ƙarau daga ƙasar Nufe. Suna kuma sawo balma da kanwa da dabino da dawakin Azbin da awaki da tumaki da raƙuma daga ƙasashen Adar da Azbin da kuma Borno.’Yan kasuwar da suke zuwa fatauci kudu watau ƙasashen Yarabawa da Gwonja suna sawo goro don kawowa ƙasar Hausa da maƙwabtanta na arewa don sayarwa (Nadama, 1977:142 – 143).

    Sana’o’in Gargajiya

    Kafuwar garuruwa a ko’ina cikin ƙasar Hausa da kuma bunƙasar da noma ya samu ya ƙara taimakawa wajen samuwar sana’o’in gargajiya inda ake ƙera da kuma sarrafa kayayyaki iri daban-daban domin amfanin mutanen ƙasar Hausa da maƙwabtansu na kusa da kuma na nesa. Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ƙira da saƙa da rini da jima da dukanci da sassaƙa da sauransu.

    Akwai kuma sana’o’in da ake yin ayyukan taimaka wa rayuwa kamar wanzanci da fawa da ɗori da sauransu. Bayan waɗannan akwai ƙananan sana’o’i waɗanda mata suke tafiyar da su kamar kaɗi da kitso. Waɗannan sana’o’i na gargajiya sun taimaka matuƙa gaya wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Yanzu za a ɗauke su ɗai-ɗai da ɗai-ɗai domin ganin yadda suka taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Ƙira

    Ƙira sana’a ce wadda aka fi yi a lokacin rani domin tanadar kayan aikin noma, amma duk da haka ana yin ta a kowane lokaci na shekara domin samar da kayan amfanin gida na yau da kullum. Maƙera sun kasu zuwa kashi biyu, akwai maƙeran baƙi da maƙeran fari. Maƙeran baƙi su ne suke tono tama su narka ta don ta zama ƙarfe wanda suke amfani da shi domin yin nau’o’in kayan ƙira.

    Ire-iren kayayyakin da maƙeran baƙi suke yi sun haɗa da fartanya da masassabi da gatari da lauje da sungumi da adda da dai sauransu domin yin ayyukan gona. Haka kuma maƙeran baƙi suna ƙera takubba da gariyo da tsitaka da masu da kibau da sauran kayayyakin da ake amfani da su wajen yin farauta da yaƙi.

    Bayan waɗannan suna yin kalaba da wuƙaƙe ƙanana da manya waɗanda ake amfani da su wajen yin ayyukan cikin gida na yau da kullum. Haka kuma su ne suke samar da kayan aikin wanzanci waɗanda suka haɗa da asake domin yin aski da kaciya da kuma kalaba wadda ake amfani da ita wajen cire belun-wuya. Suna kuma yin askar tsaga wadda ake amfani da ita wajen cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya da sauransu.

    Saƙa

    Saƙa sana’a ce wadda ake sassarƙa zare ko gashi ko ɓawo ko kaba don a mayar da su wani abu mai faɗi kamar tufafi ko shimfiɗa. Saboda haka a iya cewa, saƙa ta kasu zuwa iri biyu, ta tufafi da ta kayan shimfiɗa. Ana amfani da zaren auduga ne wanda mata suke kaɗawa domin saƙar tufafi.

    Masaƙa wato masana’antar da ake sarrafa zare domin yin sutura ita ma ta kasu zuwa iri biyu. Akwai masaƙar tsaye wadda mafi yawanci mata ne suke amfani da ita don yin saƙar gwado ko zanen kujera ko ɗan goyo wanda ake goya jarirai. Akwai kuma masaƙar zaune wadda maza ne suka fi yin amfani da ita wajen yin saƙar sauran abubuwa.

    Hakika wannan sana’a tana da matuƙar muhimmanci a ƙasar Hausa domin kuwa ba domin ita ba da an riƙa tafiya tsirara. Wannan a fili yake, sutura ita ce alamar da take bayyana bambanci a tsakanin mutum da dabba. A cikin mutane ma da sutura ake iya rarrabe bambancin al’adu.

    Da ita ake gane cikakken mutum da akasinsa. Haka kuma da ita ake sanin mawadaci da mabuƙaci. Masana’antar saƙa ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Wannan kuwa ya samu ne sakamakon kayayyakin da ta riƙa samarwa waɗanda ake sayarwa a kasuwannin cikin gida da na ƙasashe maƙwabta (Alhassan, 1982:52-54).

    Jima

    Jima sana’a ce wadda ake sulluɓe fata don a fitar da gashin da yake jikinta. A irin wannan masana’anta da ake kira majema ana sauya fata daga halinta na asali na gashi da kaushi a sarrafa ta, a gyara ta yadda za ta yi laushi kamar sutura.

    Bayan an gyara fata ta yi kyau ana sayar da ita ga dukawa, kuma mafi yawancin fatar da aka gyara tana daga cikin manyan muhimman hajoji da ake safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashe maƙawabta na kusa da na nesa. Ana yin wannan safara tun lokaci mai tsawo da ya gabata kafin shigowar Turawa wannan ƙasa.

    Irin wannan fata na daga cikin kayayyakin da aka riƙa fataucinsu daga Kano da Katsina da Zamfara da Sakkwato ana ƙetare hamadar Sahara da su ana kaiwa Morocco da sauran ƙasashen da suke arewacin Afrika ana sayarwa. Daga nan ne kuma Turawa suke sayen ta su kai ƙasashensu inda suke sarrafa ta domin yin jikunkuna da takalma da riguna maganin sanyi da sauran abubuwa waɗanda kuma suke kawo wasu daga cikinsu zuwa ƙasashen Afrika da sauran ƙasashen duniya don sayarwa.

    Dukanci

    Dukanci sana’a ce wadda ake sarrafa fata don mayar da ita wani abu na amfanin yau da kullum. Ire-iren abubuwan da dukawa suke yi sun haɗa da jikunkuna da takalman fata da igiyar linzamin doki da burgami da zabira wadda ake zuba kayan wanzanci da jakar zuba ma dawaki dawa ko dusa. Haka nan kuma suna yin warki da gafaka da tandun kwalli da kuben wuƙa da na takobi da sauran abubuwa.

    Bayan dukawa sun yi waɗannan abubuwa suna sayar da su ne ga waɗanda suke buƙata da kuma masu yin sari waɗanda suke kaiwa kasuwanni na cikin gida da na waje. Haka kuma ‘yan kasuwa na waje na shigowa cikin ƙasar Hausa don sayen ire-iren waɗannan kayayyaki da dukawa suka sarrafa.Wannan masana’anta ta dukanci ta bayar da gagarumar gudummuwa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Rini

    Rini na nufin sauya launin tufa ko zare don ya zama wani iri. Ana kiran masana’antar da ake yin rini marina. Abubuwan da ake amfani da su wajen yin rini sun haɗa da muciya da kwatarniya da guga da itace da ƙaiƙayi da ɗan kutuɓu da baba da katsi da shuni da zarta da marina da ruwa.

    Wannan masana’anta ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. An fahimci haka ne kuwa ta la’akari da kayan rini irin na ƙasar Hausa na daga cikin muhimman abubuwan da fatake suke yin safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashen maƙwabta don sayarwa.

    Sassaƙa

    Sassaƙa sana’a ce wadda ake gyara icce don a mayar da shi wani abu na amfani. Masassaƙan ƙasar Hausa na sassaƙa turmi da taɓarya da kujerar zama ta mata da kujerar gwado ta maza da ƙotar fartanya da ta masassabi da ta gatari da ta garma. Haka kuma masassaƙa suna sassaƙa akushi da ƙoshiyar dama fura da ludayin itace da allunan karatun Alƙur’ani mai girma da dai sauran abubuwa masu yawan gaske.

    Wannan sana’a ta sassaƙa tana taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa matuƙar gaske. A iya ganin haka ta yadda take samar da wasu kayan aiki ga sauran masana’antun gargajiya. Misali, manoma na amfani da ƙotoci, wanzamai na amfani da ƙoshiya don cire belun-wuya, makaɗa na amfani itacen da ake yin kayan kiɗa, masaƙa na amfani da gwafa wadda ake kafa masaƙa ta zaune da ta tsaye da sauran abubuwa.

    Wanzanci

    A Hausance, sana’ar “wanzanci” tana nufin amfani da askar aski domin yin aski da gyaran fuska da yin kaciya da kuma amfani da kalaba da ƙoshiya don cire belun-wuya. Sana’ar wanzanci ba ta tsaya a nan ba don kuwa ana amfani da ‘yar tsaga don yin ƙaho da cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta kwalliya da ta magani.

    A sana’ar wanzanci dai ana yin hujen kunne da yanke yatsan cindo (shiddaniya) da yanke linzami a cikin bakin jarirai da wasu ayyuka da dama. Haka kuma masu yin sana’ar wanzanci na bayar da magungunan gargajiya ga waɗanda suke buƙata.

    A taƙaice a iya cewa sana’ar wanzanci ta taɓo aikin likita a ƙasar Hausa kafin zuwan asibitin zamani. Dalili kuwa shi ne wani daga cikin ayyukan wanzanci shi ne kula da lafiya musamman ta jarirai da ƙananan yara, ta wani fannin ma har da lafiyar manya. Masu yin ire-iren waɗannan ayyuka ana kiran su wanzamai waɗanda dole su kasance masu cikakkiyar lafiya, masu hankali da natsuwa.

    A mafi yawanci maza ne suke yin sana’ar wanzanci, amma ana samun wasu mata waɗanda saboda rashin wani namiji a gida, ko kuma don wani dalili sukan koyi wannan sana’a daga mahaifansu. Ana gadon wannan sana’a a wajen iyaye ko kakanni na wajen uba. A gargajiyance yana da matuƙar wuya a sami wani mutum wanda bai gaji wannan sana’a ba yana yin dukkan ayyukan wanzanci.

    A wannan zamani ana samun waɗanda kan koyi yin askin zamani na saisaye wanda suke yi da kayan askin zamani, amma iyakarsu askin don kuwa ba sa iya yin sauran ayyukan wanzanci. Haka kuma wajen yin ayyukan wannan sana’a gado na taka muhimmiyar rawa, don kuwa kowane wanzami yana da gidajen da yake zuwa don gudanar da ayyukansa. Wani wanzami daban ba ya zuwa gidan da wani wanzami ɗan’uwansa yake yin aiki ya yi.

    Kowane gida ko zuri’a suna da wanzamin da suka gada wanda yake yi masu aiki, daga shi sai ‘ya’yansa ko wani da ya wakilta ne kaɗai suke iya zuwa waɗannan gidaje nasa don yin waɗannan ayyuka. Haka su ma masu gidajen ba sa kiran wani wanzami daban don yin ayyukan wanzanci a gidajensu dole sai wanda suka gada tun asali daga iyayensu.

    Wani tsari mai ban sha’awa dangane da aiwatar da sana’ar wanzanci shi ne, wanzami ba shi da iyakar ƙasar da zai riƙa gudanar da ayyukansa. Yana iya fita daga garinsu ko ƙasar dagacinsu ko hakiminsu ko sarkinsu, kai a wannan zamanin har jiharsu ya tafi wuraren da mutanensa suke domin yi masu ayyukan wanzanci.

    Misali, idan Bahaushe ya auri Bafulatana wadda ita a al’adarsu mace ba ta yin haihuwar fari a gidan mijinta, sai dai ta tafi goyon-ciki gidan mahaifanta. To, idan ta haihu ba mahaifanta ne za su kira wanzami ba, mijinta ko mahaifansa ne za su kira wanzaminsu na gida don ya yi ayyukan. Haka kuma a wannan zamani idan mutum na aikin Gwamnati a wani gari, idan matarsa ta haihu sai ya aiko garinsu don wanzaminsu na gida ya je domin yin ayyukan.

    Misali, lokacin da nake gudanar da wannan bincike, da na ziyarci Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na sadu da Dr.Kabir Chafe wanda shi ne Shugaban Sashen Koyar da Tarihi kuma Shugaban Tsangayar Fasaha da Zamantakewa na wannan Jami’a. A lokacin da nake tattaunawa da shi ya bayyana min cewa, a duk lokacin da aka haihu gidansa nan Zariya, yana aikawa garinsu Tsafe don wanzaminsu na gida ya zo ya yi ayyukan wanzanci.

    Ni ma a halin yanzu mutanen da nake yi wa aikin wanzanci waɗanda kuma muka gaji juna waɗanda suke aikin Gwamnati a Katsina da Abuja da Kaduna da sauran wurare, idan matansu suka haihu suna aikowa don in je waɗannan garuruwa da suke don yin aikace-aikacen wanzanci.

    A wani lokaci takan kama a sauya wanzamin da aka gada. Dalilan da kan sa a yi wannan sauyi sun haɗa da sauyin wurin zama. Wato idan mai gida ya tashi daga garinsu ya koma wani gari da yake nesa da garinsu na asali, to a sabon wurin da ya sauka idan aka yi masa haihuwa, ko yana bukatar a yi wa wasu yaransa kaciya ko dai wata bukata ta aikin wanzanci a gidansa, sai ya nemi wani wanzami don ya yi masa waɗannan ayyuka. Daga wannan lokaci shi wannan wanzami ya zama na gidansa, sai kuwa idan wani dalilin ya tilasta a sauya shi.

    Haka kuma idan wanzamin gida ya rasu ko wata lalura ta rashin lafiya ta same shi, idan ba shi da mai gadonsa sai waɗanda yake yi wa aiki su sami wani wanda zai maye gurbinsa. Shi ma daga nan ya zama wanzamin waɗannan gidaje. Idan kuma rashin fahimtar juna ko wani saɓani ya shiga tsakanin wanzamin gida da mai gidan da yake yi wa aiki, misali maita ko siyasa ko aure da sauransu sukan tilasta a sauya wanzami.

    Idan ba ta waɗannan hanyoyi da aka yi bayaninsu ba, matuƙar wani wanzami ya yi shisshigi ya shiga gidajen da wani wanzami yake yin aiki ba tare da izininsa ba, ɓarna na iya shiga. Domin kuwa kowannensu zai yi ta ƙoƙarin yin ire-iren surkulle da sihirce-sihircen da ya iya domin nakasa abokin hamayyarsa ko ya lalata ayyukan da ya yi.

    Wanzaman Hausawa sun kasu zuwa rabo biyu. Akwai wanzaman gado da wanzaman ƙoƙo. Wanzaman gado su ne waɗanda suka gaji yin sana’ar wanzanci a wajen iyayensu da kakanninsu, kuma suna yin dukkan ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da yin aski da kaciya da cire belun-wuya da cire angurya da bayar da magungunan gargajiya da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya.

    Ire-iren waɗannan wanzamai ne suke gadon gidajen da za su riƙa yin ayyukan wanzanci. Haka kuma daga cikin irinsu ne ake naɗa Sarkin Aska ko Magajin Aska. Idan buƙatar aikinsu ta tashi a mafi yawancin lokaci a gidajensu ake zuwa don a sanar da su wuri da lokacin da ake bukatar su je don yin ayyukansu.

    Kuma a mafi yawancin lokaci ire-iren waɗannan wanzamai ba su da rainuwa domin kuwa duk abin da aka ba su a matsayin ladar aikinsu, sai su karɓa suna masu yin murna da godiya. An bayyana cewa dalilin haka shi ne suna yin waɗannan ayyuka ne don gado ba don ladar da ake biyan su ba.

    Su kuma wanzaman ƙoƙo ba sa yin dukkan ayyukan wanzanci, iyakar ayyukan da suke yi sun haɗa da aski da gyaran fuska. Wanzaman ƙoƙo barorin wanzaman gado ne. A wani lokaci irinsu na yin ƙaho, kuma irinsu ne suke yawo da zabira rataye a kasuwanni da cikin garuruwa suna neman wanda za su yi wa aski ko gyaran fuska ko ƙaho.

    Haka kuma ire-iren waɗannan wanzamai ne suke yin rumfuna a kasuwanni da shaguna a cikin garuruwa domin yi wa mabuƙata aski da gyaran fuska. Idan suka yi wa mutum ayyukansu suna gaya masa adadin kuɗin da zai biya ba kamar wanzaman gado ba. Hausawa na yi wa ire-iren waɗannan wanzamai kirari kamar haka:

    Wanzaman ƙoƙo a ci tuwo a yi aski,

                                     Cire belun-wuya da belun-mata sai ‘yan gado”.

    Ba a tsakanin Hausawa kaɗai ake yin sana’ar wanzanci ba, akwai al’ummomi da ƙabilu masu yawa waɗanda ake yi masu ire-iren ayyukan wanzanci. Wasu ana yi masu dukkan ayyukan ne, wasu kuwa ana yi masu waɗansu ne daga cikin ayyukan kawai.

    Wannan dalili ne ya sa kowace al’umma ko ƙabila tana da sunan da take kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzanci. Misali, Larabawa suna kiran wanzami da sunan al-Hallaƙ. Fulanin da suke zaune a ƙasar Hausa suna kiran sa da sunan wanzamijo, su kuma Fulanin da suke zaune a gabacin ƙasar Hausa a Yola da Gwambe suna kiran sa da sunan wanjam ko wanjamjo.

    Turawan Ingilishi suna kiran sa da sunan barber, su kuma na Faranshi suna kiran sa da sunan coiffure ko coifere. Barebari suna kiran wanzami da sunan diyeji ko wanzama, shugaban wanzamai kuma suna kiran sa da sunan Zanna Ɗambusuma. Buzaye kuma suna kiran wanzami da sunan aghachaou, su kuma Adarawa na kiran sa da sunan wanzami. Su kuma Yarabawa na kiran wanzami da sunan bonjamo, wanda yake yin aski kawai kuma suna kiran sa da sunan fari-fari ko akola. ’Yan ƙabilar Ekoi waɗanda suke zaune a Jihar Cross Riɓer suna kiran wanzami da sunan anu-uka.

    Nufawa kuma suna kiran sa da sunan gozan. Su kuwa ‘yan ƙabilar Ibo suna kiran mai yin aski da sunan okpa-isi, wanda yake yin kaciyar maza kuwa suna kiran sa obe-ugwu, wanda yake yin tsagen gargajiya kuma suna kiran sa da sunan ogbu-ichi. Dakarkari waɗanda suke zaune a ƙasar Zuru da kewaye a Jihar Kabi na kiran wanzami da sunan sah’pana ko u’oro.

    Idan muka ƙetara a ƙasashen da suke Afrika ta Gabas za mu ga akwai wasu ƙabilun waɗannan ƙasashe waɗanda suke aiwatar da ire-iren ayyukan wanzanci da ake yi a ƙasar Hausa kamar yadda Hausawa suke yi. Wasu daga cikin al’ummomin waɗannan ƙasashe na cire belun-wuya da belun-mata da yin askin suna ga jarirai da dai sauran ayyuka irin waɗanda wanzaman Hausawa suke yi.

    An ce kamar yadda wanzaman Hausawa suka gaji yin wannan sana’a, al’ummomin waɗannan ƙasashe masu yin waɗannan ayyuka suna yin gado ne a wurin mahaifansu. Akwai waɗanda suke koyon yin waɗannan ayyuka bayan sun girma, ire-irensu suna bayyana cewa iskoki ne suka sanar da su hikimomin yin waɗannan ayyuka (Hira da JMT da PMT da KMK da AGU a ranar 20/12/2004 da MEHT a ranar 22/12/2004). A Uganda ƙabilun Sabiny da Kapchori, a Kenya kuwa ‘yan ƙabilar Kisii, a Tanzania kuma ‘yan ƙabilar Wakurya ne suke yin ire-iren ayyukan wanzanci na Hausawa.

    A gabacin Afrika ana amfani da harshen Swahili a matsayin harshen ƙasa a ƙasashen Uganda da Kenya da Tanzania don yin hulɗoɗin gwamnati da harkokin yau da kullum a tsakanin al’ummomin waɗannan ƙasashe. A saboda haka akwai sunayen da ake kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzami a waɗannan ƙasashe. Misali, ana kiran mai cire belun-wuya da sunan kukata-kilimi, mai yin aski kuma kinyozi.

    Shi kuma mai yin kaciyar maza ana kiran sa da sunan tohara ya wanaume, mai yin kaciyar mata kuwa tahora ya wanawake ko ngariba. Shi kuma mai yin tsagar gado ana kiran sa da sunan ndonya ko makonde, mai yin tsagar kwalliya kuwa alama za nyuso (Hira da AGU, a ranar 20/12/2004 da kuma MEHT], a ranar 22/12.2004).

    Bayan waɗannan sana’o’i waɗanda mafi yawancinsu maza ne suke aiwatar da su, akwai waɗanda mata ne kawai suke yin su kamar kaɗi wanda ake yi don samar da zare da abawa ga masana’antar saƙa. Haka kuma mata ne suke yin sana’ar kitso ga ‘yan uwansu mata. Suna yin salon kitso iri-iri don yin kwalliya ga kan mata wanda suke ƙara masu kyau da jawo hankalin maza.

    Akwai kuma sana’ar tauri ko koda wadda mata suke amso hatsi don yin dakau na fura ko garin da za a yi amfani da shi don yin abinci. Waɗannan sana’o’i waɗanda mata suke yi suna taimaka wa matan yin hidimominsu na yau da kullum da kuma yin bikin dangi ba tare da sun dogara da wani ba.

    Shigowar baƙi ƙasar Hausa wato Larabawa da Turawa sun taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa ya ƙara bunƙasa.Wannan kuwa ya faru ne ta yadda aka sami shigowar wasu sababbin sana’o’i waɗanda wasun su ci gaba ne ga waɗanda Hausawa suke yi kafin zuwan waɗannan baƙi.

    Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ta makanikanci don yin gyaran kekuna da babura da motoci da rediyo da rikoda da talabijin da kwamfyuta da wayar hannu da dai sauransu. Akwai kuma masana’antar kafinta wadda ci gaba ce ga sana’ar sassaƙa ta gargajiya. Kafintoci na sassaƙa kujerin zama na zamani da tebura da tagogi da ƙofofin ɗaki da yin rufin ɗaki wanda ake amfani da katako da kwanon rufi da dai sauran ayyuka don a ƙara sauƙaƙa rayuwar yau da kulllum.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Hanyar bauta wa wani abu wanda mutum yake tsammanin shi ne zai biya masa bukatun rayuwar yau da kullum shi ne addini. Addinin farko na mutanen ƙasar Hausa shi ne addinin gargajiya, wato tsafi ta hanyar bautar iskoki ko mutanen ɓoye da kuma bori da camfi.

    Irin wannan addini ya faru ne ta bin wasu hanyoyi da mutane suka ƙaga wa kansu ta bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan buƙatunsu na rayuwa. Wannan hanyar bauta ta daɗe ƙwarai a dukkan sassan duniya ba ƙasar Hausa kawai ba. Mutanen da suka fara zama a duniya ne suka ƙirƙiro ta, daga nan sai abin ya zama al’ada ga sauran ƙabilun da suke biye da su har ya zo ga Hausawa.

    A sakamakon shigowar addini Musulunci cikin ƙasar Hausa da kuma karɓar sa da mafi yawancin Hausawa suka yi, irin wannan addini ya sami rauni. Amma duk da haka ba a bar yin wasu abubuwa waɗanda suka danganci addinin gargajiya na Hausawa ba. Don kuwa za a ga yana yin tasiri a kan wasu al’amuran da suka shafi rayuwar wasu Hausawa ta yau da kullum.

    Idan muka waiwaya muka duba yadda al’ummar Hausawa suka gudanar da addininsu na gargajiya, za mu ga ba wai suna sassaƙa wani gunki ne suna bauta masa ba, a a, suna yin bautarsu ne ta hanyar yin tsafi. Bauta ta hanyar tsafi tana nufin bauta wa wani iska da aka ɗauka yana zaune a wani wuri na daban. Ire-iren wuraren da aka ɗauka iskoki suna zama sun haɗa da wata kwankwamar dutsi ko cikin wata sarƙaƙƙiya ko wurin wata tsohuwar bishiya, irinsu kuka da tsamiya da marke da dai sauransu.

    Misali, a Kano an bauta wa iska Tsumburbura wanda aka ɗauka ya zauna a Dutsen Dala, Kainafara-Arnan Birchi suna bauta wa iska Ɗantalle wanda suka ce yana zaune a cikin Dutsin Birchi. Arnan Kwatarkwashi kuma suna bauta wa Ƙunƙurutu wanda suka ɗauka yana cikin Dutsin Kwatarkwashi, arnan Sauna kuma suna bautar Magiro.

    Haka kuma a duwatsun Kufena ta Zariya mazaunan farko a wannan wuri sun ɗauka akwai wasu iskoki da suke zaune a wannan wuri. Saboda suna biya masu buƙatunsu shi ya sa suke bauta masu. A ƙasar Katsina ma akwai wasu arna da suke bautar Magiro a Safana da Ɗan-musa da Ƙanƙara da Dutsin-ma wanda suka ce yana zama a wurin tsamiya mai sarƙaƙƙiya da duhu, kuma ba mai iya zuwa wurin da yake sai masu yi masa hidima

    Bayan addinin gargajiya sai addinin Musulunci wanda addini ne da Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) don ya zama hanyar shiriya ga al’ummomin duniya, ya kuma zama hanya madaidaiciya a gare su. Wannan kuwa ya faru ne a cikin shekara ta 610 Miladiyya.

    Addinin Musulunci ne ya biyo bayan addinin Kirista wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Isa, Allah ya ƙara yarda da shi. An sami shekaru ɗari shida a tsakanin waɗannan addinai (Ibrahim, 1982:63 da Gusau, 2005:18-19). Ba kamar sauran addinan da suka gabace shi ba, addinin Musulunci an aiko da shi zuwa ga dukkan al’ummomin duniya don ya zama hanyar shiriya ga kowa.

    Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) ya fara da kiran ‘yan’uwansa zuri’ar Banu Hashim don su karɓi wannan addini. Wasu suka karɓa wasu kuwa suka ƙi. Sannu a hankali yana wa’azi shi da waɗanda suka fara ba shi goyon baya, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci sai da dukkan ƙasashen Larabawa suka amshi addinin Musulunci.

    Wannan ne ya sa aka kafa Ƙungiyar Al’ummar Musulmi wadda take da cibiya a Birnin Madina, Annabi shi ne shugaban wannan al’umma. Dukkan abin da zai zartar, sai ya yi shawara da sahabbansa. Wajen tafiyar da wannan al’umma ba a nuna ƙabilanci ko fifiko a tsakanin jama’ar da suke cikinta. Abin da ta sa gaba shi ne haɗin kai da son juna da nuna ‘yan’uwantaka a tsakanin Musulmi. Babban tsarin mulkin wannan al’umma shi ne shari’ar Musulunci. Kafin Annabi ya yi ƙaura, ya bar wa al’ummar Musulmi Alƙur’ani mai tsarki da kuma Hadisai don su yi masu jagora dangane da addininsu (Ibrahim, 1982:63).

    Manyan shika – shikan addinin Musulunci biyar ne:

    • Shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) bawansa ne kuma manzonsa ne.
    • Tsayar da salla.
    • Bayar da zakka.
    • Yin azumin watan Ramalana.
    • Ziyartar ɗakin Allah don yin aikin Hajji ga wanda ya sami iko.

    Bayan ƙaurar Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) da kuma zaɓaɓɓun halifofi huɗu da suka biyo bayansa. An sami wasu daga cikin sahabbai da wasu malamai da suka biyo bayansu, sun kawo hanyoyin da suke ganin ya dace a riƙa yin aikace-aikacen addini don samun sakamako mai kyau a duniya da lahira. Wannan ne ya sa aka sami ɗariƙu da ƙungiyoyin addini mabambanta masu yawa waɗanda suke da magoya baya a ko’ina.

    Daga cikin ire-iren waɗannan ɗariƙu akwai Ƙadiriyya da Tijjaniyya da dai sauransu da dama. Haka kuma akwai ƙungiyoyin addini waɗanda suka haɗa da Ƙungiyar Jama’atu Izalatul Bid’a wa Iƙamatus Sunna wato Ƙungiyar Kawar da Bidi’a da Tsayar da Sunna. Akwai kuma Ƙungiyar ‘Yan’uwa Musulmi (Shi’a). Waɗannan ɗariƙu na Ƙadiriyya da Tijjaniya suna da magoya baya sosai a cikin ƙasar Hausa. Haka su ma waɗannan ƙungiyoyi suna da nasu magoya baya a sassa daban-daban na ƙasar Hausa (Ibrahim, 1982:98-99, ‘Yanɗaki, 1997:46-50 da Suleman, 1997: 58-59).

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Hanyoyin Zamantakewar Hausawa

    Hanyoyin Zamantakewar Hausawa

    Al’ummar Hausawa ba haka nan suke zaune kara-zube ba, wato zama irin na ba-kai-ba-gindi, suna da tsararriyar ingantacciyar hanya wadda ta shafi yadda suke tafiyar da harkokin rayuwarsu na yau da kullum.

    A gaskiya ma ko da addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa ya tarar da Hausawa suna tafiyar da harkokin rayuwarsu bisa ingantaccen tsarin da ya shafi harkokin aure da haihuwa da mutuwa da sauran ma’amalolin rayuwa. Wannan ne ya sa ba a sami wata matsala ba a lokacin da Hausawa suka karɓi addinin Musulunci wajen tafiyar da rayuwarsu kamar yadda shari’ar addinin Musulunci ta tsara wa mabiya addinin.

    Dangane da haka tsarin zaman Hausawa na yau da kullum an tsara shi daga kafuwar iyali. Daga iyali ne al’umma ko jama’a suke faruwa har su zama babban gida (gidan-gandu) daga nan sai ‘yar unguwa. Ire-iren waɗannan unguwanni ne suke haɗuwa su kafa ƙauyuka, ta haka ne kuma aka sami garuruwa da birane waɗanda sarakuna suke mulki (Smith, 1957:241- 42).

    Domin tafiyar da rayuwarsu ta yau da kullum cikin sauƙi, al’ummar Hausawa suna tafiyar da rayuwarsu bisa tafarkin cuɗan-in-cuɗe-ka, watau taimakon-kai-da-kai. Ta wannan fuska idan abin arziki ya sami wani mutum a wannan unguwa ko ƙauye ko gari, misali aure ko haihuwa, sai ‘yan’uwa da abokan arziki su taru don taya shi murna. Kuma kowa kan kawo irin tasa gudummuwa wadda wasu kan kawo hatsi ko abinci ko kuɗi ko sutura da sauran abubuwan arziki.

    Dalilin yin haka shi ne don a taimaka wa wannan ɗan’uwa da abin da zai yi wannan hidima ba tare da ya fuskanci wata matsala ba. Irin wannan halayya ce ta haifar da ƙungiyoyin taimakon kai-da-kai domin a ƙara taimaka wa juna. Za a tarar ‘ya’yan waɗannan ƙungiyoyi akwai maza da mata da ma waɗanda ba Hausawa ba a cikinsu, kuma ana yi wa kowane ɗan ƙungiya dukkan abin da ya dace a yi wa wani ba tare da la’akari da jinsi ko ƙabila ba.

    Haka kuma idan abin baƙin ciki ya sami wani mutum misali, rashin lafiya ko mutuwa ko wata masifa ‘yan uwa da abokan arziki na kusa da na nesa suna zuwa wurinsa don su yi masa jaje da taya shi jimamin wannan hali da ya shiga ko wani nasa ya shiga. Idan rashin lafiya ya kama mutum, a nan ma za a tarar cikin masu zuwa don jajantawa akwai maza da mata da ma waɗanda ba Hausawa ba, duk suna zuwa ne saboda zaman lafiya da mutuntaka da take tsakaninsu da Hausawa a wuraren da suke zaune.

    Bayan wannan al’ummar Hausawa suna tafiyar da ayyukan gayya don taimaka wa kansu-da-kansu. Ana yin ayyukan gayya a gidaje inda ake yin sababbin ɗakuna da gyara tsofaffi da yin darnin gida ko na garka da ɗora ɗan bisan ɗaki da na rumbu da sauransu. Su kuma mata suna yin ayyukan gayya don yin daɓen ɗaki da shafen jangargari da na farar ƙasa da sauransu.

    Ana kuma yin ayyukan gayya a gonaki inda ake yin sassabe da huɗa da shuka da noma da girbi da ɗaurin amfanin gona da kawo shi gida. Haka kuma a cikin ƙauyuka da garuruwa ana yin ayyukan gayya wajen gyara masallatai da maƙabartu da magudanun ruwa da mashayar ruwa da gyaran hanyoyin da ake bi don kawo amfanin gona gida da kasuwa.

    A wannan zamani ire-iren waɗannan ayyukan gayya da Hausawa suke yi sun yi rauni saboda tasirin zamananci a kan wannan al’umma. A yanzu mafi yawancin mutane suna zaune a bisa tafarkin kowa-tasa-ta-fisshe-shi, amma duk da haka ana samun ɗaiɗaikun al’ummomi a wasu wurare cikin ƙasar Hausa da suke aiwatar da ayyukan gayya a garuruwansu.

    Tsarin Shugabanci a Tsakanin Hausawa

    Shugabanci na nufin yi wa mutane jagora a halin zamantakewarsu na yau da kullum. A nan duk wanda aka ba ragamar tafiyar da mulkin al’umma, nauyi ya hau kansa na tsare lafiyarsu da dukiyarsu da mutuncinsu. Su kuma waɗanda ake shugabanta haƙƙinsu ne su ba mai mulkinsu haɗin kai, su kuma riƙa bin umurninsa don ya sami sauƙin tafiyar da mulkinsu cikin kwanciyar hankali.

    A ƙasar Hausa shugabanci yana farawa daga gida ne, don kuwa a kowane gida wanda yake ƙunshe da mutanen da suka kai biyu ko waɗanda suka wuce haka, akwai maigida wanda nauyin dukkan mutanen wannan gida ya rataya a wuyansa. Shi yake jagorancin wannan gida a dukkan wasu harkokin rayuwar yau da kullum.

    Dukkan mutanen gidan waɗanda suka haɗa da matansa da ‘ya’yansa da matan ‘ya’yansa da ƙannensa da matansu da ‘ya’yansu da jikokinsa da barorinsa da ‘yan cin arziki da dai sauran duk wanda yake ƙarƙashinsa na bin ummurninsa. Shi yake yi masu kome wanda ya shafi sutura da abinci da tsaro da kare mutuncinsu da nema masu magani idan sun kamu da wata rashin lafiya.

    Idan ire-iren waɗannan gidaje suka yi yawa sai su kafa unguwa. Daga cikin masu gidajen sai a sami wani mai kwarjini daga cikin su wanda ya iya tafiyar da harkokin al’ummarsa, a ba shi mai unguwa. Mutanen wannan unguwa ne tare da amincewar dagacinsu suke zaɓar sa, daga nan shi kuma nauyi ya hau wuyansa na mulkin al’ummar wannan unguwa. Shi kuma ne zai riƙa wakiltar su a duk wasu hidimomi da kuma yin sasanci a tsakanin talakawansa (Usman, 1972:176).

    Samuwar unguwanni da yawa yake samar da dagaci wanda dukkan masu unguwanni suke ƙarƙashinsa. Dukkan abubuwan da suke faruwa a waɗannan unguwanni sai an sanar da shi, kuma duk wani sasanci da ya gagari mai unguwa wurin sa ake zuwa don ya yi sasanci. Dagaci yake wakiltar al’ummominsa da suke unguwanni a wasu ma’amalolin rayuwa.

    Garuruwan dagatai da yawa suke samar da ƙasar Hakimi wanda shi yake shugabancin dukkan garuruwan dagatai da suke ƙarƙashinsa. Dukkan abubuwan da suke faruwa a garuruwan dagatai sai an sanar da shi, kuma shi yake wakiltar su a duk wata hidima. Idan dagatai sun gaza wajen yin wani sasanci, sai su miƙa maganar gare shi, don ya yi tasa hikimar ya sasanta saɓanin.

    Waɗannan garuruwa na hakimai ne suke taruwa su yi ƙasar sarki. Sarki shi ne wuƙa da nama a duk harkokin da suke faruwa a wannan masarauta. Dukkan mutanen wannan ƙasa suna ƙarƙashin mulkinsa, kuma hakimai na sanar da shi dukkan abubuwan da suke faruwa a ƙasashensu. Idan hakimai sun gaza wajen yin sasanci a tsakanin talakawansu, sai su kai ga sarki wanda ta hanyar shawartar ‘yan majalisarsa zai yanke hukunci ko da daɗi ka ba daɗi. Wanda hukuncin bai yi wa daɗi ba dole sai ya yi haƙuri, wannan ne ya sa ake yi masu laƙabi da ‘wuƙar yanka’ (Usman: 1972:176).

    A kowace masarauta akwai ‘yan majalisar wannan sarki, su ne suke taimaka wa wannan sarki da shawarwarin da za su taimaka a aiwatar da mulkin wannan ƙasa cikin nasara da adalci. Waɗannan ‘yan majalisa sun haɗa da Waziri wanda shi ne babban mai ba sarki shawara kuma shi yake wakiltar sarki a lokacin da ya fita daga masarautarsa. Bayansa akwai Alƙali da Magatakarda da Shamaki da Shantali da Ma’aji ko Ajiya da Sarkin Fada da Galadima da Sarkin Gida da dai sauransu da dama.

    Bayan waɗannan sarautu akwai kuma sarautun da ake ba masu sana’o’in gargajiya. Kowace sana’a akwai wanda ake ba jagorancin mutanen da suke gudanar da irin wannan sana’a don ya yi sasanci a tsakanin ma’abota sana’ar da kuma tafiyar da ita bisa ingantaccen tsari. Ire – iren waɗannan sarautu sun haɗa da sarkin noma ga masu yin noma da sarkin maƙera ga masu yin ƙira da sarkin aska ga masu yin sana’ar wanzanci da sarkin makaɗa ga masu yin sana’ar kiɗa da sanƙira ko sarkin roƙo ga masu yin sana’ar roƙo da sarkin fawa ga masu yin sana’ar fawa da sauransu da dama (Adamu, 1978:5).

    Dukkan waɗannan sarautu da aka yi bayani a kansu tun daga mai unguwa zuwa ga sarki da ‘yan majalisar sarki da masu riƙe da sarautun sana’o’in gargajiya, an tsara su ne bisa tafarkin gado. Wato idan wanda yake riƙe da sarautar ya mutu ko ya yi murabus ko aka tuɓe shi, a mafi yawancin lokaci ana zaɓar wani daga cikin ‘ya’yansa don ya gaje shi, wani lokaci kuma ana ba ƙanensa ko wani ɗan uwansa don ya gaje shi.

    Wannan na faruwa ne saboda irin ƙima da mutunci da martaba da muhibbar kowane daga cikin ‘ya’yan sarkin ko danginsa. Hanyar da ake bi wajen zaɓar sarki a ƙasar Hausa kafin jihadin Shehu Ɗanfodiyo ba tsari ne na bai ɗaya ba. Akwai bambanci a tsakanin wannan masarauta da waccan. Daga kafuwar Daular Usmaniyya zuwa mulkin mallakar Turawa an sami canji dangane da yadda ake tafiyar da wannan tsari.

    Don kuwa dukkan sarkin da aka zaɓa, a fadar Mai Martaba Sarkin Musulmi ne za a yi naɗinsa, kuma Sarkin Musulmi ne yake amincewa da zaɓensa kafin a naɗa shi, saɓanin tsarin da suke bi kafin wannan lokaci. Kafuwar mulkin mallaka kuma, sai ya ƙara sauya tsarin don kuwa dukkan sarkin da za a zaɓa sai Gwamna ya amince kafin a naɗa shi ya hau gadon sarauta.

    Kafin jihadin Shehu Ɗanfodiyo a shekarun 1804 zuwa 1809 dukkan ƙasar Hausa tana rarrabe ne masarauta-masarauta. Kowane sarki na mulkin iyakar garuruwan da suke ƙarƙashin ikonsa. A babban birnin wannan masarauta ne ake gudanar da harkokin mulki da na tattalin arziki. Wannan dalili ne ya sa ba a sami dunƙulalliyar ƙasar Hausa wadda take ƙarƙashin mulkin sarki ɗaya ba. Sai bayan da aka yi jihadi kuma aka kafa Daular Usmaniyya, sannan ne aka haɗe su a ƙarƙashin daula ɗaya mai cibiyar mulki a Sakkwato. A wancan zamani tsakanin su sai dai yaƙe-yaƙe da kai hari don kamen bayi.

    Tun daga mulkin Hausawa har zuwa mulkin Fulani a ƙarƙashin Daular Sakkwato zuwa mulkin mallaka na Turawa, tsarin sarautar ƙasar Hausa bai sauya ba. To, amma ayyukan da sarakunan suke yi ya sauya, kuma a wajen mulki ba su da izinin aiwatar da wasu hukunce-hukunce kamar yadda suke yi a da can. A yanzu an ɗauke su iyayen ƙasa kawai, ba su da cikakken iko da ƙasa da talakawa, duk sun koma ƙarƙashin gwamnati.

    Idan ma za su yi wani abu, sai sun nemi izini daga gwamnatin ƙaramar hukumar da suke ko jiha ko gwamnatin tarayya idan abin mai ƙarfi ne sosai. A wannan zamani sarautun gargajiya an mayar da su ƙarƙashin ikon ma’aikata mai kula da ƙananan hukumomi da masarautun gargajiya ta kowace jiha a faɗin Tarayyar Nijeriya. A Jamhuriyar Nijar ma suna da tsari irin nasu wanda shi ma dai sarautun gargajiya na wannan ƙasa suke ƙarƙashin irin wannan ma’aikata wadda take kula da yadda suke tafiyar da harkokinsu.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Huɗubar 07/02/1447H 01/08/2025M

    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Yasir Ibn Rashid Addausari

    Mai fassara: Malam Salisu Alhaji Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo tabbata ga Allah, Wanda Ya koyar da alƙalami. Ya koyar da mutum abin da bai sani ba. Muna gode Masa bisa ni’imominSa masu bibiyar juna, da baiwarwakinSa waɗanda ba a iya ƙirga su ko a ƙididdige su. Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, Ya kewaye dukkan komai da iliminSa, kuma Ya sanya iyaka ga kowane abu.

    Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, mafi alherin wanda ya bi tafarkin shiriya, kuma ya gargaɗi al’umma game da bin hanyoyin halaka.
    Tsira da amincin Ubangijina su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa ma’abota hankula, da Tabi’ai da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Bayan haka, ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronSa, kuma ku hararo kulawarSa gare ku a sarari da yayin ganawa, kuma kada rayuwar duniya ta ruɗe ku.

    Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: (To, amma duk wanda ya yi ɗagawa () Kuma ya fifita rayuwar duniya () To lallai wutar Jahimu ita ce makoma () Kuma duk wanda ya ji tsoron tsayuwa a gaban Ubangijinsa, kuma ya hana zuciya bin abin da take so () To lallai Aljanna ita ce makoma).

    Ya ku mutane:
    A zamanin nan namu, bil’adama na fuskantar cigaba na ban mamaki ta fuskar rayuwa, da bunƙasa ta musamman a fagage na fasaha da na’urori masu ƙwaƙwalwa, da kafafen sadarwa na dijital, da su ne sadarwa ta sauƙaƙa, kuma nesa ta zo kusa, kuma aka taƙaita lokuta, kuma aka aiwatar da ayyuka, aka kuma inganta hidindimu, kuma aka sauƙaƙa isa ga ilimi ta kafafen zamani, don haka, sai fasahar zamani ta zama wani ɓangare da ba zai iya rabuwa da rayuwarmu ba.

    Kuma idan al’ummu suna yin gasa a fagen fasaha, to lallai ƙasarmu mai albarka ta bambanta da hangen nesanta, kuma ta yi fice a matakan da ta ɗauka, sai ta zama jagora a wannan fanni, tana ribatar fannin fasaha kuma tana amfani da ita wurin hidimtawa al’umma da ɗan’adam, har ta zama abin kwaikwayo da ake yabawa kuma ake koyi da ita a cikin wani yanayi mai ban sha’awa da ke tabbatar da matsayinta a mataki na duniya a fannonin fasahohin zamani masu zurfi.

    Kuma haƙiƙa ƙasarmu ta tabbatar da cewa cigaba ba ya cin karo da ɗabi’u na ƙwarai, kuma ba ya saɓa wa al’adu, bari-dai, yana gina su ne kuma yana dogaro da su, sai ƙasar ta daukaka ba tare da ta manta da tushenta ba, kuma ta cigaba ba tare da ta yi watsi da tabbatattun al’adunta ba.

    Madalla da wannan a matsayin wata ni’ima daga Ubangiji, kuma kyauta daga Allah, wadda take wajabta yabo da godiya, don haka, dukkan yabo ya tabbata ga Allah da Ya hore mana waɗannan hanyoyi, kuma Ya buɗe mana kofofin alheri da sauƙi, kuma Ya datar da jagororimmu shiryayyu zuwa ga amfani da su da kuma inganta su.

    Ya ku bayin Allah
    Kuma idan har wannan ni’ima na daga cikin manyan ni’imomi, kuma na daga alamomin samun rinjaye a wannan zamani, to lallai ita ni’ima idan aka sanya ta a inda bai dace ba, sai ta koma azaba da bala’i.

    Kuma a yayin da fasahar zamani take rasa alƙiblarta, kuma aka rasa wayewar addini tattare da masu amfani da ita, to a wannan lokaci sai na’urori su koma tarko, hanyoyin kuma su koma ababen da suke zamarwa, daga nan ne wata cuta da aka jarrabi wasu mutane da ita ta bayyana, duk da bambancin shekarunsu da wayewarsu da jinsinsu, wannan kuwa ita ce cutar ɗamfaruwar zuciya da kafafen sadarwa na zamani, da nutsewa a cikin duniyar yanar gizo da ba ta da iyaka, har ma a wajen wasu wayoyi suka sauya daga kasancewarsu hanyoyin sada zumunci zuwa hanyoyin kaɗaici da yanke alaƙa.

    Sai ka ga mutum cikin jama’a tamkar gangar jiki ne da babu zuciya da hankali a tare da shi; yana kai-komo tsakanin kafafen sadarwa, yana shiga manhajoji sai shafukan yanar gizo su riƙa fizgar sa, kuma yana kallon bidiyoyi masu yawa, bai ma san abin da yake nema ba, kuma bai samu wani abu mai amfani ba.

    Wannan wata fitina ce mai hallakarwa, mutum yana rayuwa a cikinta cikin ruɗani ba tare da wasu manufofi ba; kamar ƙaramin kwale-kwale ne a tsakiyar teku ba tare da na’urar gane hanya ko abin tuƙa shi ba, kuma kamar matafiya ne wanda bai isa inda zai je ba kuma ga shi ya halakar da abar hawansa. Tir da shekaru da ke wucewa kamar gajimare, kuma suke ƙarewa ba tare da wani guzuri don ranar hisabi ba.

    An karɓo daga Ibn Abbas Allah ya ƙara musu yarda ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Akwai wasu ni’imomi guda biyu da ake yi wa yawancin mutane kamunga a cikinsu, su ne lafiya da lokaci). Bukhari ne ya rawaito shi.
    Ibnul-Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce: “ɓata lokaci ya fi tsanani fiye da mutuwa; domin mutuwa tana raba ka ne da duniya, amma ɓata lokaci yana raba ka ne da Allah da kuma rabauta a lahira”

    Ya ku Musulmi:
    Lallai zuciya idan ba a shagaltar da ita da ayyukan ɗa’a ba, to sai ta shagaltu da saɓo, musamman ma a wannan zamanin na kafafen sadarwa na zamani, da yawan bibiyar hotuna da labaran yau da kullum, da ƙawata shafuka, sai ka ga mutum ya nutse cikin ruɗanin da ba shi da ƙarshe, da burace-burace waɗanda ba sa ƙarewa, kuma abin da ya fi wannan muni shi ne wanda yake rayuwarsa cikin bibiyar rayuwar wasu kuma yake ɓata lokutansa, kuma yake sa ido a rayuwar mutane amma yake manta tasa rayuwar.

    Kuma haƙiƙa lallai gargaɗi ya zo daga shari’a game da irin wannan shagaltuwa abar zargi, kuma ɗabi’a mai guba, wadda ke lalata wa mutum addininsa, kuma ta ɓata masa lokacinsa. An karɓo daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Yana daga cikin alamomin kyawun Musuluncin mutum, barin abin da bai shafe shi ba” Tirmizi ne ya rawaito shi.

    Kuma Abubakar Allah ya ƙara masa yarda ya ce: “Lallai wasu mutane sun sadaukar da rayuwarsu ga wasunsu, kuma sun manta da kawunansu, saboda haka, ina hana ku ku zamto kamar su”.

    Kuma ya kamata a sani, ya ku bayin Allah, cewa: Lallai kafafen sada zumunta na zamani a mafi yawan lokuta sun zama matattarar rayuwa ta ƙarya, kuma wajen gasa marar amfani, sai cutar hassada da ƙiyayya ta shiga zukatan wasu, kuma fushi da ƙin juna ya yi naso a zukatansu, sai godiya da yabo ga Allah bisa nani’imominSa da baiwarwakinSa su yi ƙaranci.

    Kuma daga cikin sharrori da masifu akwai shafukan ƙarya na bogi da ke fesa gubarsu cikin al’umma, kuma suke yaɗa fitintinu da ƙarairayi, suna ƙirƙirar maganganu da jita-jita, kuma suna fatawowi na ƙarya da sunan malunta, a cikin wasu shirye-shirye da aka ɗau nauyinsu, da kuma ɓatanci da ake yi da gangan, waɗanda ba sa la’akari da addini ko kyakkyawar ɗabi’a.

    Abin mamaki baya ƙarewa game da wanda ke bibiyar irin waɗannan shafuka ba tare da tantancewa ba, yana gaggauta yaɗa abin da suka wallafa ba tare da jinkiri ba, kuma ba tare da komawa ga majiyoyin hukuma da amintattun tashoshi ba.
    Allah Maɗaukaki Ya ce:

    (Ya ku waɗanda kuka yi imani! Idan wani fasiki ya zo muku da wani labari, to ku yi bincike, don kada ku cuci mutane cikin rashin sani, sai ku wayi gari kuna masu nadama game da abin da kuka aikata)

    Ya ku mutane,
    Kuma akwai wata fitina da ke lalata zukata a lokutan kaɗaici, lokacin da mutum ya ke keɓancewa da wayarsa a wuraren da babu kowa, sai ya keta alfarmar addini, yana kallon haramtattun abubuwa, yana raina umarnin Allah, ba ya damuwa da abin da Allah Ya hana, yana mai manta irin cututtuka da annoba da irin waɗannan abubuwan kallo ke jawowa, da keta mutunci, da ɓata shekaru da lokuta, da kuma salwantar da kyawawan ayyuka.

    An karɓo daga Sauban Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Lallai ina sane da wasu mutane daga cikin al’ummata, za su zo a ranar alkiyama da kyawawan ayyuka masu girma kamar manyan duwatsun garin tihama farare, amma sai Allah Ya mayar da su ƙura abar sheƙewa)

    Sauban ya ce: Ya Manzon Allah, ka siffanta mana su, ka fito mana da su fili mana, saboda kada ya zama muna cikinsu alhali ba mu sani ba, sai ya ce: (Lallai su ‘yan’uwanku ne kuma daga cikin danginku, kuma suna ibada a wani sashe na dare kamar yadda kuke yi, sai dai su wasu irin mutane ne waɗanda idan suka keɓe da dokokin Allah sai su keta su) Ibn Majah ne ya rawaito shi.

    Ya ku bayin Allah, Allah Ya mana albarka cikin Alƙur’ani mai girma, kuma Ya amfanar da mu abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato mai hikima, ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu, don haka ku nemi gafaraSa, lallai Shi Mai yawan gafara ne da jinƙai.

    Huɗuba Ta Biyu

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda Ya shiryar da mu zuwa ga hanyar samun rabo, kuma Ya nusantar da mu zuwa ga hanyar tsira, kuma Ya saukar da haske da rahama a cikin littafinSa, kuma Ya sanya shiriya da hikima a cikin sunnar AnnabinSa, kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba shi abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa, tsira da aminci da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa da wanda ya bi tafarkinsa zuwa ranar ƙarshe.

    Bayan haka, Ya ku ‘yan’uwa Muminai!
    Lallai daga cikin mafiya girman ni’imomin Allah akwai cewa mutum ya faɗaku game da tasgaronsa kafin ƙurewar lokaci, kuma ya lura da zuciyarsa kafin rufi ya mamaye ta, sau dayawa muna buƙatuwa ga maganin wannan alaƙa mai cutarwar a wannan duniya ta dijital da fasaha, hakan zai kasance ne ta hanyar ɗaga kafa, wanda da shi ne za mu daƙile guguwar amfani da waɗannan na’urori, ba wai don mu ƙaurace wa rayuwa ba, bari dai, sai don mu sabunta daidaito game da tasgaro da aka samu a rayuwarmu.

    Ibnul Jauziy ya ce: Ban taɓa ganin abin da ya fi amfani ga zuciya ba, fiye da ƙauracewar da mutum zai gano aibobinsa kuma ya riƙa nazari cikin makomar al’amuransa).

    Ya ku bayin Allah!
    Lallai addininmu addini ne na tsaka-tsaki da daidaito, don haka, ku ware wa ibada lokaci, haka rai ma a ba shi nasa kason, kuma iyalai ma a ba su rabonsu, haƙiƙa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya gaskata maganar Salman ga Abu Darda’i Allah Ya ƙara musu yarda cewa: (Lallai Ubangijinka Yana da hakki a kanka, kuma kai kanka kana da hakki a kanka, kuma iyalanka suna da hakki a kanka, don haka ka ba wa duk wani ma’abocin hakki hakkinsa) Bukhari ne ya rawaito shi.

    Kuma ku sani Allah Ya muku rahama cewa: Lallai fasaha ni’ima ce mai girma idan aka fuskantar da ita zuwa ga alheri kuma aka dabaibaye ta da dabaibayin shari’a da hikima, don haka ita ba tsagwaron sharri ba ce, kuma ba abar ƙyama ba ce a asalinta, bari dai, ita kamar takobi ne mai kaifi biyu, saboda haka ka zamto wanda yake amfani ba wanda ake amfani da shi ba, kuma na’urarka ta kasance hadima ba shugaba ba, kuma gada zuwa ga ɗa’a ba ramin da zai kai ka zuwa ga saɓo ba, kuma ta kasance tsani na samun ilimi da fahimta ba filin wasa na son zuciya da jahilci ba.

    Saboda haka ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku yi riƙo da sabbuban tsira, kuma ku riƙa tunawa koda yaushe cewa lallai za a tsayar da ku a gaban Ubangijinku, kuma za a tambaye ku game da gaɓɓanku, haƙiƙa Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: (Lallai ji da gani da kuma tunani, duk waɗannan sun zama abin tambaya ne game da su).

    Don haka, ku ribaci shekarunku kuma ku mori lokutanku, domin duk wanda yaƙininsa ya gaskata, to zai yi da gaske kuma zai yi ƙoƙari, kuma duk wanda burinsa ya taƙaita, to zai yi guziri da tanadi, ya zo cikin Sahihu Muslim daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Ka yi kwaɗayi kan abin da zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah kada ka yi ƙasa a gwiwa).

    Ya ku bayin Allah,
    Wannan kenan,
    Kuma ku yi salati da sallama ga wanda aka aiko shi da hikima da kuma shiriya, mafi alheri cikin halittu kuma mafi darajar wanda ya taka ƙasa, kamar yadda Ubangijinku Mai girma da ɗaukaka Ya umurce ku da hakan cewa: (Lallai Allah da Mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati, ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa).

    Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammad Manzo amintacce, da Alayen Annabi Muhammad, kamar yadda Ka yi salati ga Annabi Ibrahim da Alayen Annabi Ibrahim cikin talikai, lallai Kai Abin yabo ne Mai girma, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammad da Alayen Annabi Muhammad kamar yadda Ka yi albarka ga Annabi Ibrahim da Alayen Annabi Ibrahim cikin talikai lallai Kai Abin yabo ne Mai girma.

    Ya Allah Ka yarda da Halifofi huɗu shiryayyu, jagorori masu shiryarwa, Abubakar da Umar da Usman da Aliyu, ya Allah Ka yarda da Sahabbai baki-ɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako, Ka haɗa da mu cikin baiwarKa da karamcinka da kyautatawarKa ya Mafi karamcin masu karamci.
    Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi, Ka kare shingen addini, Ka sanya wannan ƙasa ta kasance mai aminci da lumana da yalwa, tare da sauran ƙasashen Musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah muna roƙon Ka dace da gamonkatar ga shugabanmu kuma majiɓincin al’amarinmu hadimin Masallatai biyu masu alfarma da magajinsa amintacce, kuma Ka saka musu da mafi alherin sakamako game da ƙasa da mutane da Musulunci da Musulmi. Ya Allah Ka taimaki jami’an tsaronmu da sojojinmu a kan iyakoki, Ka kare su da kariyarKa, Ka jiɓince su da kulawarKa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka yaye damuwar waɗanda suke cikin damuwa, Ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiyarmu da na sauran Musulmi. Ya Allah Ka jiƙan mamatanmu da na sauran Musulmi, Ka taimaki masu rauna daga cikin Musulmi a kowane wuri, da kuma ƙasar Falasɗinu, ya Allah Ka ba su waraka daga dukkan damuwa, da mafita daga dukkan ƙunci, da kuɓuta daga dukkan bala’i, ya Allah Ka warkar da masu rauninsu, Ka tsare jinanensu, Ka tabbatar da zukatansu, ya Allah Ka kare Masallacin Ƙudus, Ka sanya shi ya zamto mai ɗaukaka da buwaya har zuwa ranar Alƙiyama.

    Ya ku bayin Allah
    Lallai Allah Yana umurni da yin adalci da kyautatawa da kuma bai wa makusanta taimako, kuma Yana hana alfasha da mummunan aiki da zalunci, Yana gargaɗin ku don ku wa’azantu, don haka ku ambaci Allah Maɗaukaki mai girma, Shi ma Zai ambace ku, kuma ambaton Allah shi ne abin da ya fi girma, kuma Allah yana sane da abin da kuke aikatawa.

    Don karanta Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke danna nan

    Edita@rumasau-kallamu