Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Yadda Ɗabi’ar Tsotson Ɗan Yatsa Take (FINGER SUCKING)

    Yadda Ɗabi’ar Tsotson Ɗan Yatsa Take (FINGER SUCKING)

    Tsotson ɗan-yatsa, musamman babban ɗan-yatsansa (thumb), ɗabi’a ce wacce Jarirai suke yi da ƙananan yara ‘yan wata 6 zuwa shekara 5. Wannan ɗabi’a tana faruwa ga Jarirai tun suna cikin mahaifa, idan aka yi awon Ultrasound akan iya ganin jariri yana tsotson babban ɗan yatsansa.

    Yara da Jarirai sukan yi tsotsan ɗan yatsa ne domin su jiyar da kansu daɗi, ko barci mai daɗi. Wannan ba matsala ba ne. Suna ɗaukarsa kamar suna shan nono ne, don haka sai su sami nutsuwa idan suna yi.

    Amma idan yaro ya wuce shekara 5 yanayin ɗabi’ar tsotson ɗan-yatsa, to, za ta iya haddasa masa matsalolin daidaituwar haƙora (orthodontics issues), kamar:

    • gantso (dental misalignment),
    • ko rashin daidaiton tsawon haƙora (open bite teeth),
    • ko matsalar girman ƙashin muƙa-muƙi (jaw growth issues),
    • ko matsalar magana yadda zai sha wahala wajan furta wasu kalmomin irinsu “S” “the,
    • ko matsalar tsaftar (hygiene problem)

    Tsotsan yatsa yana iya kawo yaɗuwar ƙwayoyin cuta daga hannu zuwa baki, sannan zai iya haddasa cuttutuka kamar ciwon ciki, gudawa, ko maƙogwaro, da sauransu. Iyaye za su iya ƙarfafawa ‘ya’yansu gwuiwar daina tsotson ɗan-yatsa ta hanyar:

    1. Yin musu bayanin rashin amfanin tsotson ɗan-yatsa.

    2. Samar musu da kayan wasa waɗanda za su ɗauke musu hankali daga tsotson ɗan-yatsa.

    3. Sanya musu safar hannu ko abubuwa masu ɗanɗanon ɗaci (bitter) amma ba masu cutarwa ba, kamar ganyen shuwaka, ganyan maina a hannu, saboda ɗacin ya hana su tsotson ɗan-yatsan.

    Kodayake wannan ba dole ba ne ya yi tasirin hana wani yaron tsotson ɗan-yatsa, saboda a lokacin yaye wasu matan sukan shafa abu mai ɗaci a nipples ɗinsu, amma hakan ba ya hana wani yaron shan nonon.

    Karanta Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)

    Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)

    Malam Imam Ahmad da sauran malaman sunan sun rawaito daga Abi Darda` (RA) ya ce: Manzon Allah SAW ya ce: “Lallai Malamai magada Annabawa ne, Su Annabawa ba su bar dinari ko dirhami ba, sai dai sun bar ilimi. Wanda ya yi riƙo da shi lallai ya yi riƙo da rabo babba”

    A cikin wannan rubutun duk inda aka faɗi malami ko malamai ana nufin malamin addinin musulunci wanda aka yarda da iliminsa da kuma tsoron Allahan sa. Irin waɗannan malaman su ne magada Annabawa, saboda suna yaɗa shiriya ga mutane (Wanda aiki ne annabawa). Ko kuma don su (malamai) suna ɗauke da wani abu (ilimi) wanda yake daga wurin Allah wanda aka samu ta hanyar Annabawa. Duk ɓangare biyun sun cancanci girmamawa.

    Malanta wata hanya ce da ta ƙunshi kyautata niyya, tsoron Allah, gwagwarmaya, haƙuri, jajircewa, ladabi da girmama wanda ake neman ilimi wurinsa, dan neman sanin abinda ya shafi addini, wanda ya ke ɗaukan lokaci mai tsawo. Duk mai neman ilimi yana ba da lokacinsa ne gaba ɗaya, ya lizimci malami, ya jajirce, tare da yi wa malami ladabi, da haƙuri ga duk abinda zai iya bijirowa ta ɓangaren malamin ko ta ɓangaren karatun ko yau da gobe.

    Duk wanda ya bi wannan hanyar, bayan wani lokaci ana sa ran ya sami wani abu na ilimi, har ma ya amsa sunan malami. Sanin kowa ne shi ilimi ba a daina nemansa kuma ba a iya ƙure samunsa. Sai dai mutum ya yi iya yinsa kawai. Sannan ba kawai don mutum ya sami ilimi shi ke nan ba, sai an cigaba da bincike, karatu da nazarce nazarce.

    A ƙarni na Sha-shida (16) a Arewacin ƙasar nan, Jami`ar Gobarau da kuma `yandoto ta Katsina sun zamo wurare da suka tara masana a kowani fanni na ilimi wanda manyan malamai daga duk faɗin nahiyar Afrika da ma wasu wuraren suke zuwa dan neman ilimi da ilimantarwa.

    Bayan jihadin Babban Malami, Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo, cikin jama`ar Shehun malamin, manyan malamai irin su ƙaninsa, Abdullahi Ibn Muhammad Ibn Fodiyo (Abdullahin Gwandu), Malam Mustapha (Ɗan Tafa), Waziri Ɗan Laima da kuma irinsu ɗan Shehu Usman bin Fodiyo wato Muhammad Bello da ƙanwarsa Nana Asma`u da ɗanta Abdulkadir Ɗan Tafa da sauran manyan malamai sun yi ta ba da gudunmawa wurin karantar da mutane, rubuce rubucen littatafi da ƙasidu na ilimin addini, lugga da sauransu.

    Duk lokacin da aka sami tarin malamai a wuri, ko a lokaci ɗaya, sau da yawa akan sami wata mas`ala ta addini wadda za a iya samun saɓani a tsakanin malamai. Wannan yana faruwa ne sakamakon yawan bincike a kan mas`aloli na addidni daban daban da malamai su ke yi. Sabani ba wani abu ba ne da zai sa a ta-da jijiyar wuya ko a ɗau makami, tun da su masu ilimi ne, toh a ilmance ake komai ta hanyar rubuce rubucen ƙasidu, littattafai da wasiku da fitar da fatawa.

    MISALAI GUDA UKU KAƊAI DAGA MAGABATA.

    Misali na farko shi ne: Lokacin da Turawan mulkin mallaka suka shigo yankin Arewa, Sarakunan mu na musulunci sun ƙi miƙa wuya, kamar yadda turawan suka nema. Da yawa sun zaɓi su yaƙi waɗannan turawan.

    Sarkin Muslumi Attahiru I da sanyin safiyar ranar 15 Maris 1903 bayan an gwabza tsakanin jama`arsa da turawa na kimanin sa`o`i biyu, sai ya fahimci yaƙi da turawan nan babu nasara, saboda a ƙalla an kashe mutane kusan 100 cikin mutanen sa, a ɓangaren turawa ko mutum guda ba a kashe ba, saboda bindigogi na zamani da suke amfani da su a wancan lokacin.

    Ganin haka, ya yanke shawarar yin hijira zuwa gabas, bayan ya yi shawara da wasu daga cikin muƙarrabansa. A ranar 27 Yuli, 1903 aka yi yaƙin ƙarshe a wani gari da ake kira Burmi ranar Juma`a Sarkin Musulmi Attahiru I da kusan mutane 600 suka yi shahada a cikin masallacin juma`a. Wannan jajircewa da Sarkin musulmi da yayi, ɗaya daga cikin sojojin taurawan Ingila William Wallace ya tabbatar da haka.

    Ba tarihin Sarkin Musulmi Attahiru I zan bayar ba, amma ana cikin wannan taƙaddama bayan fitar Sarkin musumi daga birnin Sakkwato ranar 21 Maris, 1903 aka zaɓi Muhammad Ibn Ali Ibn Bello (Attahiru II) a matsayin sarkin Musulmi. A wannan lokacin Wazirin Sokoto Muhammadu Buhari ya nemi fatawa a wurin Alkalin Gwandu Ahmad Bin Sa`id kan maslaha ga musulmi; A miƙa wuya wa turawa, ko a ci gaba da yaƙarsu ko a yi hijira? Wanda wasu suna ganin ba bu wata maslaha da ta wuce a miƙa wuya wa turawa kawai.

    Wannan fatawa ta a miƙa wuya ta samu karɓuwa sosai musamman dalilin takardar da Wazirin Sokoto Muhammadu Buhari ya yi “Risalatil Wazir Ila Ahlil Ilmi Wat Tadabbur” ta yadda suka yi amfani da ilimin usul wurin bayanin hukuncin abinda ya kamata shugabannin musulmi su yi na miƙa wuya da yarda da turawan mulkin mallaka. Akwai waɗanda suka saɓa musu a ra`ayi suma da hujjojinsu, amma cikin rubuce rubuce na ilimi kowa ya fito da hujjarsa, ba hayaniya ko zage –zage da cin mutunci.

    Misali na biyu: Shi ne Lokacin da aka sami taƙaddama kan saka karatun Qur`ani a gidan rediyo a 1955 zuwa 1960 wanda Sheikh Ibrahim Nyass ya ba da fatawar ya halatta a sa karatun Qur`ani a gidan rediyo, shi kuma Sarkin Zazzau Malam Jafaru Ɗan Isyaku ya ba da fatawa sɓanin haka.

    Dukkansu (Sheikh Ibrahim Nyass da Sarkin Zazzau Malam Jafaru Dan Isyaku) kowa ya yi amfani da ilimi mai zurfi na Usulul Fiqh da hujjoji masu ƙarfi wurin bayanin hukuncin wannan mas`ala. Sheikh Ibrahim Nyass ya ba da fatawarsa ne sakamakon tambaya da wasu daga cikin malaman Kano suka yi masa. Sarkin Zazzau Malam Jafaru Ɗan Isyaku ya ba da nasa fatawar ne sakamakon tambayar da Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi I ya tura masa duk da cewa shi ma Sarkin Kano Malam Muhammadu Sasusi I babban malami ne.

    Abin sha`awa a nan shi ne Shiekh Ibrahim Nyass har wani littafi ya yi wanda aka buga shi a shekaran 1956 a ƙasar Masar mai suna “Alhujja albaligha fi kawn Idha`at alQur`an fir radiyo Sa`igha”. Wannan mas`alar ita ma haka aka ƙarƙareta ta hanyar ilimi ba hayaniya da harigido.

    Misali na uku, a ƙarni na 19, an sami taƙaddama a kan Sadalu da Qabalu a sallah, wannan taƙaddama ta samo asali ne saboda bayyana da yaɗuwar tajdidin ɗarikar Tijjaniya da Sheikh Ibrahim Nyass ya kawo wanda kafin zuwan wannan tajdidi, ɗarikar Ƙadiriyya ita ce aka fi sani kuma ta fi daɗewa a ƙasar Hausa tun bayan jihadi.

    Malaman ɗarikar Kadiriyya sun tafi a kan sadalu cikin sallah. Sheikh Ibrahim Nyass da wasu malamai a Kano suka zo suka warware wancan fahimta ta sadalu da hujjoji. Wannan ya sa `yan Kadiriyya suke ganin `yan Tijjaniya sun zo da wani sabon abu har aka riƙa kiran `yan Tijjaniya masu bin wannan fatawar da “`Yan Ƙabalu”

    Shehunan malamai irin su Malam Muhammadu Salga (r. 1938), Malam Tijjani Usman Zagon Barebari (r.1970), Malam Shehu Maihula (r1988) da sauransu sun yi rubuce rubuce dan tabbatar da ingancin yin ƙabalu a sallah. A ɗayan ɓangaren na Qadiriyya wanda Malam Nasiru Kabara ya ke jagoranta sun yi na su rubuce rubuce kan ingancin yin sadalu a sallah.

    A nan ma wani abin sha`awa, shi ne duk rubuce rubuce na ilimi aka rinƙa yi, har yau waɗannan rubuce-rubuce suna nan. An sami irin wannan taƙaddama ta faru a sokoto har Malam Abubakar Atiku Gwandu (r. 1913) ya rubuta wani littafi mai Irshad al-ikhwan ila bayan hukm as-salat bis-sadlu wa al-kablu.

    A kwai misalai masu yawa kan taƙaddama ko saɓani da ake samu tsakanin malamai tun tuni, amma abin zai birge ka idan ka kalli hanyar da ake bi wurin bayyana ra`ayi da hujjoji da fito da komai fili, hanya ce ta rubuce rubuce na ilimi, ba soki burutsu da hauragiya da shirme ba. Kuma malamai su suke kayansu ba kowani kare da doki ba. Hargowa da hayaniya da shiga fagen ilimi daga ko wani kare da doki ya samu asali ne dalilin yaɗuwar hanyoyin sada zumunta.

    Wanda shi ne za mu tattauna a rubutu na gaba.

    Rabiu Musa Adam

    Whatsapp: 08039290267

    September 12, 2025

    Karanta Ayyukan Ta’addancin Matasa A Kano: Aure, Yawan Haihuwa Da Tarbiyya A Wata Mahanga

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Da farko Khadeeja ta yi tunanin idan ta sami ciki Mustapha zai yi ɗoki kuma ya ba ta kulawa ta musamman kamar ko wacce amarya, sai dai ga mamakinta hakan ba ya samuwa. Wani lokacin ma sai ta ga kamar bai san ma tana da ciki ba ko kuma ba da son ransa ta sami cikin ba; halin ko in kula ɗin da yake nuna mata ya yi yawa.

    Tunda aka saka lockdown sai ya zamana kullum suna gida ita da shi da yara, ta so sosai ta je gida ta wuni kafin a kulle garin amma ba ta sami dama ba. Duk da haka kullum sai sun yi waya da Mommy da Yaya Mama; don tun satin da za a fara lockdown su Nabila suka zo mata wuni da suka je gida suka gaya wa Mommy ciki ne da ita. Don haka kullum da safe sai ta kirawota ta duba ta.

    Hayaniyar da su Afaf suke yi a gidan ba kaɗan ba ce don haka idan gari ya waye ko gyangyaɗi ba ta samu ta yi; ko ta fara baccin ma haka za a yi wata hayaniyar a tashe ta. Ba ta gane yanayin da jikinta yake ciki, ita dai kawai ta san tana shan wahala. Kullum jikinta babu ƙwari ga shi ba ta son cin abinci, ga shi kullum cikin jin bacci take. Ga hidimar yara, wadda duk ranar da ta nuna ba za ta iya ba haka Mustapha zai yi ta ƙunci yana kin kula ta.

    Haka take dagewa ta yi duk wani abu da ya kamata. Kullum wuni suke kallon TV saboda ana samun wuta sosai, idan dare ya yi kuma Abbansu ya tada inji su cigaba da kallo. Ita dai ba ta isa ta canza channel ba don da ta canza za a fara kuka wanda ba ta son ji sanna kuma a take ubansu zai fito ya yi magana. Ta gaji da zaman haka barkatai don haka ta daure take saka yaran a gaba su yi karatun kur’ani.

    Da safe a jagwale take tashi don haka ta san ba za ta iya da safe ba. Amma kullum bayan sallar azahar idan sun ci abincin rana sai ta kashe TV ɗin kowa ya ɗauki kur’ani ta biya masa. Nasreen ce kawai ba ta son zama don haka sai Khadeeja ta ƙyale ta saboda a halin yanzu ba za ta iya ba. Amma har Shukra ake biyawa karatun.

    Duk wani motsinsu idonsa a kai, da zarar ya ji wata hayaniya ko ya ji su shiru zai leƙo ya duba. Kullum yana kwance yana faman latsa waya. Yau ma haka suka tashi tun asuba suke ta guje-guje, TV kuma dama tana kunne don da zarar wani ya kashe ta za a yi ƙorafi. Shinkafa da wake ta dafa da manja da yaji; bayan sun gama cin abinci kowa ya yi Sallah ta saka su a gaba kowa da kur’aninsa. Sai da suka yi tilawa sannan ta ƙarawa kowa aya biyar amma banda Nasreen.

    Ba za ta iya surutu ba saboda yanayin jikinta da kuma yanda yawu yake yawan taruwa a bakinta, sannan kuma idan ta ɗaga murya tana mata faɗa Abbansu ba ya so. Don haka sai ta ƙyaleta, suna zaune gaba ɗayansu sun kewaye Khadeeja suna karatu, har da Shukra; amma Nasreen tana zaune a kan kujera ta zuba kayan wasa a gaba tana yi wa ‘yar tsanarta kitso.

    Shiru ya ji sai muryoyinsu kaɗan-kaɗan suna karatu don haka ya taso ya fito parlor ɗin. Ya kare musu kallo sannan ya sami waje ya kwanta a kan 3-seater. Ya dubi Khadijan yace ‘Ita Nasreen ba a biya mata karatun?’ ‘Tace sai ta gama yi wa ‘yar tsanarta kitso.’ ta ba shi amsa ba tare da ta dube shi ba. Nasreen tace ‘Na ma iya karatun Abba, kitson nan nake so na gama tukunna.’

    Ya yi dariya ya cigaba da danna wayarsa. Bayan sun gama karatun ta koma ɗaki ta kwanta su kuma suka cigaba da kallonsu na TV.

    A kwance take a gefen gadon da alawar tomtom a bakinta saboda yawu, ya zauna a kan kujera. Ta juyo ta kalle shi ta koma ta cigaba da kwanciyarta don ba ta son magana. Jimawa kaɗan ya kirawo sunanta, ta amsa sannan ta juyo. Ya kalle ta yace ‘Wai me yasa bakwa karatun ne da Nasreen?’ Tace ‘Bata so ne, ni kuma ba daɗi nake ji ba shi yasa ba zan iya surutu da ita ba kawai na kyale ta.’

    ‘Ya kamata idan ma wani abu kika saka a ranki game da Nasreen ki cire, duk abinda za ki yi wa yaran nan ki yi musu gaba ɗaya kuma ki yi musu adalci. Ina kula komai za ki yi sai ki ƙyale Nasreen, idan banda haka ya za a yi a ce Shukra ma da ba ta shiga islamiyya ba kina biya mata karatun amma ita Nasreen kin yi banza da ita.’

    Tun da ya fara zancen ta miƙe ta zauna a kan gadon tana kallonsa, maganganun da take so ta faɗa masa suna da yawa sai dai tana buɗe bakinta yawu ya cika bakin. Ta taune ‘yar guntuwar tomtom ɗin ta haɗiye da ƙyar, ta taɓe baki ta kawar da kai kawai tace ‘Ka yi hakuri za a gyara.’ ‘Ya kamata dai ki dinga yi musu adalci don dukansu ‘yayana ne.’ ya faɗa.

    Ta zame ta kwanta zuciyarta har turiri take saboda takaici; shi yake hanata takurawa Nasreen, shi yake nuna ba ya son a dinga yi musu faɗa amma kuma yanzu yana mata maganar ba a karatu da ita. To ya za ta yi da ita? Ita adalci ne wannan yake mata da zai ce ta dinga yi wa ‘yayansa adalci? Ta share ƙwallar da ta gangaro a idonta tayi ƙwafa. Jimawa kaɗan ya tashi ya fice daga dakin.

    Wannan wunin da kowa yake yi a gida ba ƙaramin takurawa Khadeeja yake yi ba; tana cikin laulayi sannan ga hidimar gida da ta yara. Wuni suke cin abinci don haka gidan kullum kaca-kaca ga wanke-wanke ba ya yankewa. Wasu lokutan tana samu ta ɗan gyara amma wasu lokutan haka take ƙyalewa saboda ba za ta iya ba.

    Yau kwana biyu kenan dan almajiri da ta ɗauka yake zuwa ya yi mata wanke-wanke da sharar tsakar gida bai zo ba; ba ta sani ba ko suma lockdown ɗin ya shafe su don da dai suna fitowa tunda makarantarsu nan cikin unguwa take. Gidan gaba ɗaya yayi kaca-kaca don kitchen har warin lalatacce abinci yake yi.

    Suna gama cin abincin safe Abbansu ya miƙe ya shige ɗaki. Nan da nan ta saka yaran a gaba suka taya ta suka fitar da wanke-wanken suka kai fanfon waje, ta turasu waje ta gyara cikin gidan tsaf. Tana yi tana hutawa tana tofar da yawu, zuwa ƙarfe goma na safe ta gama.

    Ta fito tsakar gidan ta tara yaran a waje ɗaya, ta dube su tace ‘Afaf mu je fanfo ni da ke mu wanke kwanukan can, kai kuma Yaya Habib ɗauki tsintsiya ka share compound ɗin nan, ka fara daga kan baranda. Nasreen da ke da Shukra ku tsince toys ɗinku ku zuba a kwando, duk wadda ba ta tsince ba ba zan ba ta sweet ba.’

    Nan da nan kowa ya fara aiki. Ta saka kujera a bakin famfo tana wanke kwanukan Afaf tana mata ɗauraya. Sai da suka cika ƙaramin kwando da kwanukan ta kirawo Habib wanda ya kusa gama sharar tace ‘Ya Habib zo ka ɗauki wannan kwandon ka kai kitchen ka kwashe kwanukan a kan sink sai ka dawo da kwandon mu cigaba da zubawa.’

    Ya ɗauka a nufi cikin gidan; a kan baranda suka ci karo da Abbansu yana fitowa. Ya ɗan ja baya don ya ba wa Abban hanya ‘Kai ina za ka da kwanuka haka.’ ‘Anti ce ta wanke zan kai mata cikin gida.’ Yana ɗaga kansa ya hango Afaf a tsakiyar kwanuka suna ta wanke-wanke ita da Khadeejan. A fusace ya ƙarasa wajen, cikin tsawa yace ‘Ke Afaf me kike a nan? kalli yanda kike jiƙa jikinki sai kin gama ki yi ta mura.’ Ya dubi Khadeeja yace ‘Ina yaron naki?’

    Ta tofar da yawun bakinta a gefe sannan tace ‘Kwana biyu bai zo ba, ni ma ban san dalili ba.’ Ya dubi Afaf wadda ta cigaba da aikinta ba tare da ta kula da shi ba, ya daka mata tsawa yace ‘Ki fita daga cikin ruwan nan nace, me kika iya? Sai sanyi ya kama ki kina ta faman jiƙa jiki. Fice ki je ki canza kaya kuma kada ki sake fitowa nan.’Ta dube shi tace ‘Kwanukan ne da yawa, ni ɗin kuma ba daɗi nake ji ba idan muka gama gaba ɗaya za ta canza kayan ai.’

    Habib ya ƙaraso ya ajiye kwandon yana cewa ‘Anti ga shi.’ Ya juya ya cigaba da shararsa. Abbansu ya sake dakawa Afaf tsawa don haka ta fice daga wajen wanke-wanken ta shige gida. Har ya buɗe baki zai cigaba da magana ya hango Habib yana kwashe shara ‘Kai Habib wa ya saka sharar nan?’ Yace ‘Anti ce Abba, ai na ma gama kwashewa zan yi.’

    ‘Ajiye tsintsiyar nan ka shige cikin gida ka ba ni waje.’ ya faɗa a fusace. Ya jefar da tsintsiyar ya shige gidan. Ya juya kan Khadeejan wadda take cigaba da wanke-wankenta yace ‘Wai me kika mayar da yaran nan ne? Habib ne zai iya share wannan tsakar gidan ga ƙura ga komai. Ita ma Afaf ɗin wannan uban ruwan ai sai ta yi mura. Ke kika ce a bar mai aikinki ta tafi gida, da kin bari ai da yanzu tana nan; sannan kuma ki dinga ba su aikin da ya fi ƙarfinsu?

    Ba na son irin wannan; ba na son ki dinga yi wa yaran nan kallon wasu manya, ki ɗauke su kamar ke kika haife su shi ne za ki iya yi musu adalci. Idan an ji wani almajirin yana bara sai a kirawo shi ya ƙarasa wannan aikin ko kuma tunda kun kusan gamawa ki ƙarasa zuwa gobe a sami wani almajirin.’ Ko kallonsa ba ta yi ba ta cigaba da wanke-wankenta, ya ja tsaki ya juya ya nufi cikin gidan.

    Ta share hawayenta ta cigaba da wanke-wankenta. Ba za ta iya dogon surutu ba sannan kuma ba ta son tana biye masa suna faɗa a gaban yara, ita yanzu duk wani abu da zai sa a yi magana ma ba ta so; shi yasa ta gwammace ta yi masa shiru. Sai da ta gama wanke-wanken nan tsaf sannan ta kwashe sharar, ta ɗebi kwanukan ta shigar cikin gida.

    Suna zaune a parlor suna kallon TV. Tana kitchen ɗin tana kife kwanukan Afaf ta shigo ta same ta, ta ɗauki kwanukan ta fara kifewa. Ta dube ta tace ‘Afaf je ki zauna ai na kusa gamawa.’ Tace ‘Bari na taya ki Anti, ai nan babu ruwa.’ Ba don ta so ba ta ƙyale ta sai da suka kife kwanukan gaba ɗaya ta mayar da komai inda yake sannan ta wuce ɗaki su kuma suka cigaba da kallonsu. Can wajen 1pm bayan sun yi sallar azahar ta fito daga ɗaki ta shiga kitchen; tuwon alkama da miyar ɗanyar kuɓewa ta dafa jiya da daddare amma duk sai suka ƙi ci.

    Da yake akwai biscuits da cake sai kowa ya ci ya sha lemo, ita da abbansu ne kawai suka ci tuwon ga shi ta dafa shi da yawa. Da safe kuma da kwaɗayi ta tashi don haka wainar fulawa ta soya kowa ya ci. Wannan ragowar tuwon shi ta ɗauko daga fridge ta ɗumama shi, ta ɗumama miyar wadda ta sha kaza da nama. Ta zuba wa kowa abincinsa sannan ta kirawosu kowa ya ɗauki nasa suka zauna a table.

    Kallon tuwon kawai Habib yake yi yana juya shi amma ya ƙi ya fara ci, tana kallonsa ta yi banza da shi ta cigaba da kai lomarta tana ba wa Shukra don ita tuwon ya yi mata daɗi. Jimawa kaɗan ya dube ta yace ‘Anti tuwon jiya ne fa?’ ‘Eh, shi ne, ko ci ko bari.’ ta faɗa a gajarce ta ci gaba da cin abincinta.

    Daidai nan Abbansu ya fito ya zauna a table ɗin, ta tura masa flask da plate. Ya buɗe flask ɗin ya kalli fuskokin yaran sannan ya kalle ta yace ‘Wannan ai tuwon jiya ne, ba a yi abincin ranar ba ne?’ ‘Shi ne abincin ranar ai, ɗumamawa aka yi tunda babu abinda ya yi.’ Nasreen wadda ita ma take ta juya nata tuwon tace ‘Abba wallahi tuwon ba daɗi, ni bana son baƙin tuwo gaskiya.’

    Shi ɗin yana son tuwon alkama don shi ne ma ya sa aka yi tuwon da daddare, don haka ya zuba malmala guda ya fara ci. Ya sake duban fuskokin yaran, bayan ya haɗiye lomar da take bakinsa yace ‘Yanzu ba wani abu da za a iya dafawa yaran nan, Afaf ce kawai take cin tuwon nan.’ Ba tare da ta kalle shi ba tace ‘Babu.’

    Ta cigaba da cin tuwonta kamar ba ta san da su ba a wajen. Jimawa kaɗan Nasreen tace ‘Abba ni a haɗa min cornflakes.’ Ya dubi Khadeeja yace ‘Akwai cornflakes ko?’ Cikin halin ki in kula tace ‘Akwai.’ ‘Da Allah a haɗa mata ta samu ta ci kafin a yi abincin dare.’ Tace ‘To.’ Ta ci gaba da cin tuwonta tana ba wa Shukra a baki, yayin da ita kuma Nasreen ta tashi ta koma gaban TV.

    Jimawa kaɗan Habib ma ya mike, ya ɗauki kwanonsa da na Nasreen yana cewa ‘Abba ni ma na sha cornflakes ɗin kawai. ’Ya wuce ya kai kwanukan kitchen ya dawo shi ma ya zauna a gaban TV. Bai daɗe da tashi ba kuma ita ma Khadeejan ta gama cin nata tuwon, ta ɗauke kwanonta ta kai kitchen. Ta fito daga kitchen ɗin ta wuce ɗaki ba tare da ta kalle su ba. Tana shiga ta saka pillow ta kwanta a tsakiyar gadonta, da yake ta gaji sannan kuma ta koshi tana rufe ido bacci ya kwashe ta.

    Ba ta sani ba ko ta daɗe da kwanciya ko ba ta daɗe ba, kamar a mafarki ta ji Mustapha yana ɗan buga ƙafarta yana cewa ‘Khadeeja, Khadeeja, barci ma kike yi? Kin bar yara da yunwa fa ki zo ki haɗa musu cornflakes ko ki dafa musu indomie.’ Ta ɗan janye kafarta tana ƙoƙarin tashi; kafin aurensu fa ba ya kiran sunanta sai dai yace ‘yan mata, mekyau ko kuma yace babe.

    Ta yi zaton idan sun yi aure next level za su shiga a ƙara mata matsayi amma za ta iya cewa tunda ta shigo gidan nan sau ɗaya ya kirawota da babe a daren da suka tare. Yanzu kam ya ci dubu sai ceto don gatsal yake kiranta Khadeeja. Ta gyara zama tace ‘Me kake cewa?’

    ‘Ba ki ba wa yara abinci ba kin zo kin kama bacci.’ Tana jijjiga kai tace ‘Kowa fa na ba shi abinci ba ka gani ba ne?’ ‘Habib da Nasreen nake magana fa.’ ‘Oh, ba sun ce cornflakes za su sha ba, ai akwai a kitchen ɗin.’ ta faɗa tana ƙoƙarin kwanciya. ‘To ai sai ki zo ki haɗa musu ko?’ Ta gyara kwanciyarta a cewa ‘Wallahi babe na gaji, idan ban yi baccin nan ba ko abincin dare ba lallai na iya dafawa ba.

    Su je su haɗa cornflakes ɗin mana ko su ci tuwon da kowa ya ci.’ ‘Ya ina miki magana kina kwanciya Khadeeja, haka za ki bar min yara da yunwa.’ ya faɗa a fusace. Ta gyara kwanciyarta ta yi banza da shi. ‘Ina miki magana kina ji na fa Khadeeja bana son wulaƙanci.’ Ta tashi zaune, lokacin ya riga ya miƙe tsaye. Ta gyara zama tace ‘To me zan ce maka?’ ‘Ba za ki zo ki haɗa musu cornflakes ɗin ba kenan?’

    ‘Haɗa cornflakes ɗin ba wani aiki ba ne shi yasa nace su haɗa kawai, wallahi kaina ciwo yake.’ Ta ture abinda ta rufa da shi ta sauko daga kan gadon ta wuce banɗaki saboda yanda bakinta ya cika da yawu, ta mako kofar banɗakin ta tsaya a gaban sink; wallahi babu wani abinci da za ta haɗa sai dai ya yi duk abinda zai yi. Tana ji Nasreen ta leƙo tace ‘Abba yunwa nake ji.’

    Ya ja tsaki ya kama hannun Nasreen suka fice daga ɗakin bayan ya maka mata kofar a fusace. Haka ya je ya haɗawa yaran cornflakes ɗin suka zauna suka ci. Tun da ya haɗa musu cornflakes ɗin nan kuma sai ya shiga share Khadeeja, gaba ɗaya ya ƙi kula ta ko zama inda take. Ta kula da hakan don haka ita ma sai ta ja jikinta, domin ba ta cikin yanayin ma da zata iya saurarensa.

    Ko da dare ya yi ma har ta kwanta a ɗakinta sai kuma ta ga rashin dacewar hakan, tunda dai bai kore ta ba kuma ita ba fushi take yi da shi ba shi kaɗai yake fushinsa. Don haka bayan ta kwantar da yara sai ta shirya ta wuce ɗakinsa ta kwanta. Can wajen sha biyun dare motsin shigowarsa ya tashe ta, yana tsaye a gaban wardrobe yana saka kayan bacci. Ta sauko daga kan gadon ta wuce banɗaki don ta yi fitsari ta kuskure baki.

    Tana fitowa ta wuce ta kwanta, ta kalle shi yana zaune a gefen gadon yana dannan waya; so take ta ce masa “good night Babe” kamar yanda ta saba amma bakinta ya ƙi furtawa saboda yanda take cike da haushinsa. Don haka sai kawai ta juya masa baya ta kwanta. Kamar wanda yake jira ta kwanta sai ya gyara zama a kan gadon yace ‘Tashi mu yi magana Khadeeja.’

    Ta juyo ta kalle shi sannan ta tashi zaune ta jingine da jikin gadon; tana baƙin cikin yanda yake kiranta Khadeeja gatsal sai kace shi ya yanka mata ragon suna. Bayan ta zauna ya ƙara tsuke fuska sannan yace ‘Bana son yanda kike yi min taurin kai da neman kawo min raini a gaban yara, idan ma wani abu ne a ranki gara ki fito ki gaya min.’ Da mamaki take kallonsa don gaba ɗaya ma ta manta me ya kawo wannan maganar; ta yi zaton ma zai tambaye ta dalilin da yasa ba ta ci abincin dare ba ne domin taliya ta dafa kuma ta kasa ci don haka ruwa kawai ta sha ta kwanta.

    Ta yi murmushin yake tace ‘To, sai dai ban san lokacin da na yi maka taurin kan ba.’ ‘Dazu nace ki haɗawa Habib da Nasreen cornflakes kin ƙi, nan kika shige banɗaki kika bar ni a tsaye ina miki magana.’ Ta kalle shi suka haɗa ido ta kura masa ido har sai da shi ya kawar da kansa, ta buɗe bakinta wanda ya fara tara yawu tace ‘To in sha Allah zan kiyaye, amma ni ma don Allah ka dinga sauƙaƙamin rayuwa a gidan nan. Idan ba ka yi min saboda ƙauna ba to ka yi min saboda yanayin da nake ciki tunda ni ma ba lafiya ce ta ishe ni ba duk abinda ka ga ina yi daurewa nake yi.’

    Ya ɗan fara saukowa yace ‘Duk don na nema miki sauƙin ne ai nace a kawo mai aiki, kuma da ta dawo za ta cigaba da taya ki. Ita ma mahaifiyarsu haka take kula da su ko da kuwa tana da ciki don wannan ba wani abu ba ne a wajen macen da ta san me take yi. Bana son ki dinga yi musu abubuwan da za su ji maraicin uwarsu, ki riƙe su kamar ke kika haife su. Shi ne abinda zai samar da zaman lafiya tsakanin mu.’

    Ta gyaɗa kai tana kallonsa cike da tsananin mamaki tace ‘To.’ Ta sauka daga kan gadon ta shiga banɗaki ta tofar da yawun bakinta ta ɗaurayo bakinta ta fito ta kwanta bayan ta kashe fitila. Tana kwanciya hawaye ya fara bin idonta; wannan wace irin rayuwa ce? Wai dama haka ake aure ko kuwa ita ce ba ta dace ba? Shikenan shi da ‘yayansa ne kawai mutane? Ƙiri-ƙiri sai a ƙirƙiri laifi a ɗora mata kuma a saka ta ba da haƙuri.

    Da ya bar ta da yaran tabbas ta yi niyyar ta riƙe su kamar ita ta haife su, domin har addu’a take yi kada Allah ya ba ta ikon cutar da su. Sai dai zuwa yanzu gaba ɗaya sun fice daga ranta, duk wata ƙauna da ta tana da don ta nuna musu ba ta jin za ta iya tunda ga dukkan alamu ma ba zai bar ta ba. Shi ba so yake ta nuna musu ƙauna ba so yake kawai ta bauta musu, ba ta jin za ta iya hakan kuwa.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Addu’ar wanda ya razana a cikin barci, da wanda ya kasa barci

    أَعُوْذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُون

    A’uzu bikalimaatil lahit tammati min gadabihi wa’iƙabihi, wa sharri ibadihi,wa min hamazaatish shayaɗeen wa’ayyahdurun

    Ina neman tsari da Kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da uƙubarsa, da sharrin bayinsa da kuma zungure-zunguren shaiɗanu, da su halarto ni (a cikin al’amurana).

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Edita @rumasau-kallamu

  • Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Wannan wani tsiro ne dakan fito a jikin mahaifar mace inda jariri ke zama ya rayu lokacin goyon ciki. Tsiron na iya kasancewa a kowanne sashi na cikin mahaifa.

    ME KE KAWO SHI?

    Babu takamaiman abinda aka san yana jawo hia domin ɓangaren da yaso ya fito kurum ake gani ya fara tsirowa yana girma a karan kansa, sai dai hakan bai faruwa sai jikin matan da jikinsu ke fitar da sinadarin Estrogen da Progesterone da yawa. Sannan yana kama matan da ke cikin lokacin hayayyafa wato bearing Age daga shekara 15 zuwa 49.

    ALAMOMIN FIBROIDS

    Alamomin sun ƙunshi;

    1- Ganin fitar jinin haila da yawa.

    2- Nauyin bayan gida wajen tsuguno ake yi da kyar.

    3- Yawan fitsari

    4- Ciwon baya ko ciwon ƙafafu

    5- Zafin fitsari a riƙa yin shi yana fita a wahalce.

    6- Ciwon ƙugu ko kwankwaso

    7- Aga jinin haila ya ci gaba da zuwa fiye da sati

    8- Ciwon mara a kai a kai tare da cewa an san ba lokacin zuwan jinin al’ada ba ne,

    9- Jinkirin haihuwa

    10- Yawan ɓari

    11- Jin zafi yayin saduwa.

    SHAWARA

    Haƙiƙa duba da duk waɗancan alamomin ya kamata a fahimci lallai akwai level ɗin da in ya kai matsalolin da macen za ta ke fuskata ba za ta iya jurewa ba. Don haka akan duba a asibiti a ga a wanne ɓangare ya fito da yanayinsa.

    Lallai duk macen da ke fuskantar da yawa daga alamun da na lissafa kar tai wasa da lafiya ta je a duba ta. Idan an taɓa duba ki an tabbatar kina da shi to zama haka bai dace ba domin da yawa ba ya barin ciki ya zauna jikin mace ko da an samu ya shiga, ga yawan ciwon ciki, sannan fitar jinin al’ada da yawa ka iya sawa ki rasa jini ki haɗu da anaemia wato ƙarancin jini.

    MAGANIN MATSALAR

    Akwai magani da ake bayarwa domin jiki ya rage fitar da sinadarin da ke sa girmansa wato estrogen da progesterone inda zai motse toh fa sai dai maganin ba ya ga yasa fibroids ɗin ya motse yakan haifarwa mace da complications na bushewar gaba domin sinadarin da jikin ya dena samarwa na da mahimmanci, yana kuma haddasa dena ganin jinin al’ada sam, yana kuma iya haddasa zagwanyewar ɓargon jiki ya zamto ta riƙa Jin ƙafafunta kamar ba nata ba kuma abu kaɗan na iya sa ta karye (osteoporosis).

    SURGERY

    Sannan in aiki ya kama ai shi ma ya bambanta akwai wanda in gefe fibroids ɗin yake ake iya yanka saman marar mace kaɗan a yi amfani da device a soki jikin fibroids ɗin domin sa shi ya motse, ko ta hanyar datse jijiyoyin jinin da ke zuwa ma fibroids ɗin, ko ta hanyar yin aiki cikin mahaifar a cire fibroids ɗin.

    Amma sahihiyar hanyar rabuwa da shi dungurungun shi ne ta hanyar cire mahaifar mace baki ɗaya to amma wannan in mace na da son haihuwa ta tara ‘ya’ya ko in ma ba ta taɓa haihuwa ba kin ga ba zaɓi ba ne. Sai dai a bi sauran hanyoyin.

    Sannan fibroids a karan kansa yake fitowa musamman in jikin mace na samar da sinadarin estrogen da progesterone sosai don haka being ne ba cancer ba ne amma kuma daga baya ka iya haifar da Mummunan illa wacce ka iya taimakawa cervix cancer samun damar kama mace.

    Karanta Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wanene Dele Giwa?

    Wanene Dele Giwa?

    (Ɗan jaridar da aka kashe ta hanyar aika masa wasiƙa mai ɗauke da bam a ciki)? Yau shekaru 37 ke nan da mutuwar ɗan jarida Dele Giwa, babban edita kuma jami’in kamfanin Newswatch, wanda aka kashe ta hanyar aika masa wasiƙa mai ɗauke da bam.

    An haifi shi a ranar 16 ga watan Maris na shekarar 1947 a garin Ile-Ife. Ya halarci Makarantar Local Authority Modern School da ke Lagere a garin Ile-lfe. Lokacin da mahaifinsa ya koma Kwalejin Oduduwa da ke Ile-Ife a matsayin mai wanki, Dele ya samu gurbin karatu a Kwalejin. Daga nan ya samu damar tafiya Amurka domin yin digiri inda ya yi digirinsa na farko a kan Turanci a Kwalejin Brooklyn a 1977.

    Ya samu damar yin digiri na biyu a Jami’ar Fordham duk dai a Amurkan. Ya yi aiki da jaridar The New York Times a matsayin mai taimaka wa ‘yan jaridu na tsawon shekara huɗu kafin ya dawo gida Najeriya ya kama aiki da jaridar Daily Times. Dele ya rasu a ranar 19 ga watan Oktoban 1986 ta hanyar wani bam da aka haɗa da ambulak wanda aka kai masa gida a zamanin mulkin soja na tsohon shugaban mulkin soja, Manjo Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

    An kashe shi a lokacin da yake karin kumallo tare da abokinsa Soyinka a gidansa da ke 25 a unguwar Talabi ta Ikeja da ke birnin Lagos. Ya rasu yana da shekaru 39 a duniya. Idan muka dubi yadda mutuwar tasa ta kasance, mutuwa ce a gidansa ta hanyar fashewar bam, wanda hakan shi ne abu mafi damuwa fiye da mutuwar. Wannan na iya zama dalilin da ya sa hatta bayan mutuwarsa ba a daina tambayar wanene ya kashe shi ba? Kuma me ya sa? Tambayar da har yau ba a daina yi ba.

    Abin takaici ne ƙwarai da gaske yadda ‘yan jaridar Afirka suka fuskantar keta haƙƙoƙi da ‘yanci saboda bayyana gaskiya ko ‘yancin faɗin albarkacin baki ta hanyar tsorata su ko tsangwamarsu ko barazana gare su da hare-hare da duka har tsarewa ba bisa ƙa’ida ba; da kuma kamawa ko ɗauri tare da ƙwace kayan aikinsu a wasu lokutan.

    Waɗannan suna cikin matsaloli da ‘yan jaridar Najeriya suke fuskata a lokacin da suke aikin tono wata gaskiya ko kuma almundahana. A Najeriya akwai wasu ‘yan jaridu da suka rasa rayukansu a yayin da suke tona asirin miyagu waɗanda suka aikata ba daidai ba.

    Dangane da kisan Dele kuwa, Janar Ajibola Kunle Togun (tsohon shugaban SSS na lokacin) ya ce, “Akan Dele Giwa aka fara amfani da bam ɗin takarda wajen kashe mutum a Najeriya.” Ya bayyana hakan a lokacin da ya yi hira da Ridwan Kolawole na Jairdar Legit.ng a Abuja.

    Ɗalibinku,
    Mohammed Bala Garba, Maiduguri.
    08098331260
    Marubuci/manazarci.
    10 Ogusta, 2023.

    Karanta Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Wasu sun san garuruwan da ake kira ‘Hausa Bakwai’ da ‘Banza Bakwai’ amma ba su san dalilin da ya sa ake kiransu da waɗannan sunayen ba. Wannan ne ya sa na ga dacewar yin wannan ɗan takaitaccen bayanin kamar yadda na taɓa karantawa a littafin ‘Kano Ta Dabo Cigari’ na Marigayi Wazirin Kano Alhaji Abubakar.

    Bayan Bayajidda ya gudo daga ƙasar Borno shi da matarsa mai suna Magaram saboda yunƙurin kashe shi da Sarkin (Shehu) Borno ya yi, sai suka zo wani gari da ake kira Garun Gabas a ƙasar Haɗeja. A nan ya bar matarsa saboda tsohon cikin da take ɗauke da shi ya wuce Daura.

    Bayan ya isa Daura cikin dare, ya sauka a gidan wata tsohuwa, sai ya nemi ruwa amma bai samu ba. Tsohuwar take faɗa masa dalilin da ya sa ba sa samun ruwa sai sau ɗaya a sati saboda wata macijiya da take hana ɗibar ruwan. Da Bayajidda ya ji haka, sai ya karɓi guga a wajen tsohuwar, ya nufi rijiyar Kusugu inda macijiyar take ciki, ya kashe ta ya ɗebi ruwa.

    Da gari ya waye, Sarauniya Kabara (wacce take mulkin Daura) ta ji labari, sai ta sa aka yi bincike aka gano Bayajidda ne ya kashe macijiyar. Ta kira shi ta ce za ta basa rabin mulkinta. Amma ya ƙi amincewa, ya ce mata sai dai a ɗaura musu aure da ita idan ta amince. Sarauniya ta yarda, aka ɗaura musu aure da Bayajidda.

    Sai jama’ar garin suka fara kiransa da ‘Makas-Sarki.’ Daga baya kuma suka koma ce masa ‘Sarki’ kawai. To daga nan ne aka samo kalmar Sarki da ake faɗawa wasu sarakuna a yau. Da Sarauniya Kabara ta haifi ɗa namiji, sai aka sanyawa yaron suna Bawo.

    A lokacin da Bawo yake mulkin Daura, an yi wata masifaffiyar yunwa a ƙasar Hausa, wacce ta zama babu inda ake samun abincin mai yalwa sai a wani wuri wanda shi ne Kano a yanzu. Don haka ƙabilu suka riƙa ƙaura zuwa wurare masu ɗan yalwan abinci domin su tsira da rayuwarsu.

    Bayan jama’a sun fita kowa ya samu in da ya fake, sai ya zamana babu shugabanci kowa zaman kansa yake. Daga nan sai zalunci ya yawaita a tsakanin jama’a. Masu ƙarfi su ƙwace kayan raunana. Wannan ne ya sa raunana suka fara kai kukansu Daura wajen Sarkin Bawo.

    Da ƙararraki suka yawaita, sai Sarki Bawo ya yi shawarar kafa shuwagabanci a dukan waɗannan wuraren da abin ya dama. Sai ya tura ɗansa Bagauda zuwa Kano, ya tura ɗansa Gunguma zuwa Zariya, ya tura ɗansa Duma zuwa Gobir, ya tura ɗansa Kumayo zuwa Katsina, ya ba wa ɗansa Gazori riƙon Daura, ya ba wa ɗansa Zamna Biram, ya tura ɗansa Kogo zuwa Rano. Waɗannan garuruwa da Sarki Bawa ya ba wa ‘ya’yansa ko ya tura su, su ake kiran Hausa Bakwai.

    Akwai kuma Banza Bakwai, wanda Sarki Bawo ya sake tura wasu ‘ya’yan nasa bakwai zuwa can. Sai dai kuma wasu masana sun ce ba ‘ya’yansa na cikinsa ba ne, ‘ya’yan ɗan uwansa mai suna Karaf-da-gari ne wanda Bayajidda ya haifa da wata baiwarsa mai suna Bagwariya. Waɗannan garuruwa bakwai da aka tura ‘ya’yan su ne: Zamfara da Gwari da Nupe da Yaruba (ilori) da Kwarrafa da Kebbi da Yawuri. Su ne ake kira Banza Bakwai.

    Wannan shi ne asalin yadda aka samo sunan ‘Hausa Bakwai’ da kuma ‘Banza Bakwai’.

    Mohammed Bala Garba, Maiduguri.
    08098331260.

    Karanta Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Ranar Juma’a suna gida da yake yara babu islamiyya; ranar ne kuma suke gyara gashin yaran mai kitso za ta zo. Tun da wuri Afaf ta tsefe nata kan, ita kuma Shukra da yake tun suna makaranta Khadeejan ta tsefe mata babu wanda ya ji kansu. Tun da suka gama cin abincin rana take faman lallaɓa Nasreen ta bari a tsefe mata amma har aka kusa kiran la’asar guda biyu suka tsefe. Bata  son a taɓa gashinta kwata-kwata don haka ta ƙi ma zama a tsefe.

    Khadeeja ta kamo hannunta tace ‘Zo kin ji Nas, kin ga fa Shukra za ta fi ki kwalliya tunda ta tsaya  an gyara mata nata. Ta zauna, har an fara tsifar ta zame kanta ta matsa tana zumɓura baki. Afaf tace ‘Anti wallahi  idan ba ki zare mata ido ba haka za ki yi ta fama da ita, sai a yi sati ana tsefe kanta a gidan Mama.’

    Ta cigaba da lallaɓata amma sam ta ƙi tsayawa; don haka ta kama hannunta ta zaunar da ita  tana cewa ‘Idan kika sake tashi sai na zane ki Nasreen, ko na sa almakashi na aske gashin kan  ya koma kamar na Yaya Habib.’ Ta dubi Afaf tace ‘Yaya Afaf ɗauko min slippers mai zafi idan  ba ta tsaya an tsefe ba zane ta zan yi.’

    Da sauri Afaf ta ɗauki slippers ta zo ta ajiye a gaba Nasreen wadda ta fara shessheƙar kuka tana  fizge-fizge. Khadeeja ta ɗan riƙe gashin tace zan dake ki fa Nasreen, ki rufe min baki bana son  jin kukanki.’

    Nan da nan ta haɗiye kukanta tana shessheka aka cigaba da tsifa Shukra tana mata dariya.

    Daga masallacin Juma’a ya wuce gida don ya gaida Hajia, da ya gaishe ta sai ya wuce gida don  Khadeeja tace idan ya dawo zai kai su saloon ita da yara a wanke musu kai da yamma kuma  akwai mai kitso a maƙota dama ita take musu.

    Yana shiga gidan ya sami Yaya Jidda da yaranta biyu ‘yan mata Naja da Farida, bayan sun gaisa  gaba ɗaya Yaya Jidda ta dube shi tace ‘Gidanka fa za mu tafi yanzu ni da yara, Hajia tace mu je  mu dubo su Afaf.’

    Yace ‘To ai sai ku tsaya mu tafi, don ni ma gaisawa kawai za mu yi na wuce.’  Kafin minti goma sun gama, suka shiga mota ya ja su suka kama hanya, suna tafe suna hira.  ‘To ya yaran? Ana kula da su dai ko?’ Ta tambaye shi.

    ‘Ah Alhamdulillah, gaskiya tana ƙoƙari.’ Ya faɗa cike da fara’a.To ai haka ake so, Allah ya sa ta ɗore.’ Tun a bakin gate ya yi hon, gaba ɗaya yaran suka fito ban da Nasreen. Habib ya taya shi buɗe  gate, bayan ya shigo da motar gaba ɗayansu suka yi masa sannu da zuwa.

    A nan suka fara gaida Yaya Jidda, bayan ta amsa tace ‘Ina Nasreena?’ Afaf tace ‘Tana ciki tsifa Anti Khadeeja take mata.’

    Suka wuce gaba ɗaya suka shiga gidan; kafin Khadeeja ta amsa sallamarsu Nasreen ta fizge  kanta wanda saura ɗaya a gama tsefe shi ta tashi tana share hawaye tace ‘Abbaaa.’ ta faɗa tana  zumɓura baki.

    Da sauri ya rungumeta ‘Ya haka na ganki wujiga-wujiga? Wa ya taɓa ki?’ Shukra ta tintsire ta dariya ta daga slippers ɗin da aka ajiye tace ‘Kukan tsifa take Abba shi ne  Anti za ta zane ta da slippers, ka ga nawa Anti yalash ɗin ko kuka ban yi ba har aka tsefe yanzu za  mu je saloon amma ban da ita. Anti tace tunda ba ta so a taɓa kanta aske shi za ta yi kamar na  Yaya Habib.’ Sannu da zuwa Yaya.’ Khadija ta faɗa tana karkaɗe jikinta. Yauwa.’ ya amsa ba yabo babu fallasa.

    Ta ƙare musu kallo tana ƙoƙarin zama tana cewa ‘To yanzu kuma tsifar ce sai an yi zaniya ni ‘ya  su?’ Kafin Khadeeja tace wani abu Afaf tace ‘Anti wallahi idan aka biye mata sai an yi sati ana wannan  tsifar, kullum haka ake fama da ita.’ Khadeeja tace ‘Ai ba a ma yi zaniyar ba ta bari an tsefe.’ Ta tsuguna ta gaida ita yayin da shi kuma ya ja hannun Nasreen ɗin suka shige ciki.

    Sai da ta kawowa Yaya Jidda ruwa sannan ta bi shi ɗakin. Tana shiga ta same shi a tsaye yana  cire kaya yayin da Nasreen take kwance a kan kujerar ɗakin, kafin tace wani abu yace ‘Wai me  yasa ne sai an yi duka sannan za a yi tsifar? Na ga tun tuni dama ana mata kitson ban taɓa ji an  doke ta ba.’ Tace ‘Yanzun ma ba a doke ta ba, ko Nasreen? Ta dai ƙi tsayawa a tsefe ne na takurata na tsefe  mata, amma ba a yi duka ba.’

    Ya kawar da kai ‘Ni dai bana son dukan yara, don Allah duk abinda yaro ya yi kada a dokar min shi. Uwarsu ma ba ta dukansu, ba na bari gaskiya.’ Ta sunkuyar da kai cikin ƙosawa tace ‘In sha Allah za a kiyaye.’

    Ta ajiye masa ruwan da ta kai masa tana cewa ‘Lunch ɗinka yana nan a table.’ sannan ta fito ta  bar shi a ɗakin.

    Bayan ta dawo parlor ɗin ta tarar Yaya Jidda tana ta yi wa Afaf tambayoyi, ta wuce su ta shige  kitchen. Ta tsaya a tsakiyar kitchen ɗin gaba ɗaya kanta ya kulle; daga shigowarsu suna nema suce ta  doki Nasreen, to yanzu haka suke so a bar Nasreen ɗin ta dinga yawo da kanta? Ga shi Afaf tace makarantarsu ana duba kitso duk ranar Monday. Ta jijjiga kai ta ƙarasa ta ɗauki saucer ta zuba  cake da cin-cin ta ɗebo lemo a fridge ta jera a tray ta kawo wa Yaya Jidda da yaranta, bayan ta  ajiye a gabanta tace ‘Ya wajen su Hajiya?’

    ‘Lafiya ƙalau.’ Ta amsa ba yabo babu fallasa. Suka yi shiru sai surutun Afaf da take ta bawa Naja labari. Shukra ta matso ta kwanta a jikin  Khadeeja tace ‘Anti ni ma lemon.’ Ta shafa kanta ta dubi Afaf tace ‘Yaya ki ɗauko mata lemon wanda babu sanyi.’ Ta miƙe, har ta kama hanyar kitchen ɗin Yaya Jidda tace ‘Ku ba za ku sha lemon ba?’ Afaf tace ‘Ai da shi muka je school.’

    Shukra tace ‘Anti tace idan an kawo wa baƙi abinci mutum ya daina cewa zai ci, ni ma dai kawai  lemon zan sha.’ Khadeeja tace ‘Ki ɗauko muku lemon idan kuna so.’

    Jimawa kaɗan Abbansu ya fito daga ɗakin ya wuce dining ya zauna ya fara cin abinci; yana cikin cin abincin ya juyo yace ‘Kai Habib kun ci abinci ne?’ Yace ‘Tun ɗazu Abba, acici har ta yi round 2.’ Ya faɗa yana zungurar Nasreen.

    Khadeeja ta miƙe ta shige ɗaki, don gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi. Ta kula ƙiri-ƙiri neman laifinta ake yi; kamar ma Yaya Jiddan zuwa ta yi ta bincike ta. Ta ƙarasa ta zauna a kan gadonta ta zuba  tagumi. Bayan ya gama cin abincin ya shiga ɗaki ya fito da mukullin motarsa, ya dubi Khadijan yace ‘Idan  kun shirya muje na kai ku saloon ɗin.’

    Gaba ɗaya suka fice har da su Yaya Jidda, ya ajiye su a hanya sannan ya wuce. Tun daga wannan lokacin kuma sai Yaya Jidda ta mayar da shi ɗabi’a, duk Juma’a sai ta zo gidan.  Haka za ta zauna a parlor ta yi ta ƙare musu kallo tana kula da duk wani motsinsu, ga tambayoyi  waɗanda idan ta gama yi wa yaran za ta bi Khadeeja da neman ƙarin bayani. Sai dai ba ta taɓa  samun wani abu na zargi ba kuma Khadeejan ba ta taɓa ba ta dama ta yi wata fitna ba don duk abinda ta tambaya tana daure zuciyarta ta ba ta amsa gwargwadon iko, kuma cikin girmamawa.

    Ranar Talata ce kuma a ranar Khadeeja take sa ran za ta koma makaranta, tun dare ta sanarwa Mustapha. Ya amsa mata ba tare da wata matsala ba.

    Haka ta tashi tun kafin asuba ta shirya yaran tsaf, suna tafiya makaranta ta yi maza ta yi wanka sannan ta ɗan rage aiki don tana da lecture 9am. Bayan sun gama breakfast ta miƙe daga dining table tana tattara plates ɗin tana cewa ‘Babe bari na saka hijabi na sai ka yi dropping ɗina a school.’

    Yace ‘Ok, but kada ki ɓata lokaci don kada ki makarar da ni.’ Kusan a lokaci guda suka fito daga ɗakin kowa a shirye, sun kawo tsakiyar parlor ta dube shi tace ‘Yau kai za ka ɗauko yara ko? Don ni ina da lectures 9am to 4pm.’

    Ya ɗan ɓata rai cikin nuna damuwa yana cewa ‘I thought za ki dawo ki ɗaukosu, kin san ni sai 5pm nake tashi daga wajen aiki.’ ‘To ai ka ga ni ma sai 4pm zan tashi, kuma I can’t miss these lectures don last week ma ka ga ban je ba. Gara dai ka sami wani ya ɗauko su kawai.’

    Ya buɗe motar ya zauna yayin da ita ma ta zauna a kujerar gaba, yace ‘To ai ko an ɗaukosu ma wajen wa za a kawo su tunda ba kya gidan?’ ‘Haka ne fa, most days ma lectures ɗina har 4pm ne.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci; gaba ɗaya ma shi ya manta tana wata makaranta. Yanzu ya take so ya yi da yaran? Wa zai ɗauko su kuma wa zai zauna da su? Wannan ai shi ne an gudu ba a tsira ba. Muryarta ce ta katse masa tunani tana cewa ‘Babe ka ga da muna da mai aiki sai ta ɗaukosu ta shirya su su tafi islamiyya kafin na dawo; musamman idan Babba ce.’

    Cikin jin daɗi yace ‘Ƙwarai kuwa, zan yi wa Yaya Jidda magana sai a sami mai aikin kafin next week.’ ‘No, ka bari idan na yi wa Mommy magana za ta sa a samo mana a garinsu, mutanen suna da amana sosai ga aiki.’ Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki bari tukunna idan aka rasa a wajen Yaya Jidda sai a gayawa Mommy ɗin.’ Ba ta ji daɗin wannan maganar ba kuma ta san da ya kalle ta da zai gane sai dai son zuciyarsa ne a gabansa; don haka sai kawai ta yi shiru. Ba ta son abinda zai haɗa ta da Yaya Jidda don gaba ɗaya matar ta fice daga ranta, ta kula kamar tana neman laifinta ne ido rufe.

    A bakin department ƙawayenta Maryam da Jamila suka tare ta, ana ta ihu ana murna ga amaryar Babe. 9am to 11am suka fito daga lecture, wanda zai yi musu 12pm to 2pm ya aiko aka gaya musu ba zai zo ba. Don haka suka wuce hostel ɗakin su Maryam. Suna shiga Khadeeja ta nemi waje ta kwanta, Jamila ta taɓata tace ‘Ke da za ki bamu labarin amarci kuma sai ki kama wani bacci.’

    Ta bige hannunta tana cewa ‘Bar ni wallahi baccin da yake kaina ya fi na wata guda.’ Maryam ta yi dariya tace ‘Bar ta Jamila, kin san kwanan ibada take yi.’ Haka suka yi ta hirarrakinsu a kanta tana ta faman bacci. Har suka gama hirarrakinsu tana bacci, don haka ba su tashe ta ba suka fice sayen abinci. Basu daɗe da fita ba ta farka, bayan ta wanke fuska ta yi alwala ta yi Sallah. Ta zauna a kan dadduma tana tunani; tun ba a yi nisa ba ta gaji da auren Mustapha. To amma tana son shi, matsalarta kawai yaransa kuma da yanda ba zai bari ta yi musu tarbiyya ba. Kusan tun da ya kawo mata yaransa ba ta huta ba, wannan baccin da ta yi ji ta yi kamar an ɗauke wani dutse da ta daɗe tana dakonsa. Ko ina a jikinta ciwo yake, fatan ta kawai a samo mai aikin nan ko za ta huta. Duk da tana tsoron a kawo mai aiki daga gidan Yaya Jidda; gani take kamar CCTV camera ce kawai za a kawo mata.

    Tana zaune tana wannan lissafin wayar Yaya Mama ta shigo; bayan sun gaisa tace ‘Ya na ji ki haka ne amarya? Ko bacci kike yi ne?’

    ‘Wallahi ina hostel Yaya, kin ganni gyangyaɗi na gama.’ ‘To ya maganar mai aikin, tunda dai gaskiya aikin gidan nan ya fi ƙarfinki ga yara huɗu.’

    ‘Ya ce yayarsa za ta kawo mai aikin.’ ‘To ai shikenan, duk ɗaya ne. Kawai dai idan ta zo sai ki sa ido, kada ki bari ta shisshige miki; ke ko a cikin gidan ki kula kada ki kuskura ki dinga barinta tana shigar miki ɗaki, kitchen da store ma duk ki kula da motsinta. Yaran ma ki dinga kula da alaƙarta da su idan ba haka ba sai ta zame muku fitna.’ Yaya Mama ta faɗa.

    Cikin sanyin murya tace ‘To Yaya.’ Yanda ta ji muryarta bai gamsar da ita ba tace ‘Ko da wata matsala ne?’ No, ba wani problem. Ni ga ni ma a school na dawo sai yamma zan koma gidan.’’Ok, Mommy ma tace min kun je weekend ke da yaran naki.’ ‘Eh.’ Suka dan taɓa hira daga baya suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Khadeeja ta bi wayarta da kallo kawai sai ji ta yi tana hawaye; ta yi kewar gida sosai, gaba ɗaya a yanzu ma ba ta san me take so ba, kawai dai ta gaji. Motsin su Maryam ya sa ta share hawayenta ta basar.

    Kwana biyu da yin maganar kuwa sai ga mai aiki; dattijuwa ce Baba Habi. Yaya Jidda da kanta ta kawo ta. Sai da ta tafi sannan Khadeeja ta nuna mata ɗakin yara inda a nan za ta dinga kwana.

    Ta nunnuna mata ayyukan kafin yaran su dawo daga islamiyya. Nan da nan ta fara ba tare da nuna wata kyuya ba, ga shi tana da hanzari wajen yin aikin.

    Yan kwanakin nan gaba ɗaya ba ta jin daɗin jikinta, gaba ɗaya ba ta san me yake damunta ba. Ranar Laraba ce, tana jin Mustapha yana tashinta daga bacci kafin asuba yana cewa ‘Ki tashi yara za su makara fa.’ Ta juyo tana yamutsa fuska tace ‘Babe bana jin daɗi wallahi, daga kwancen nan ma ni jiri nake ji ga headache. Bana jin zan iya tashi yau.’

    Ya miƙa hannu ya taɓa jikinta yana cewa ‘Subhanallah, me yake damunki?’ Ni ma ban sani ba, ta amsa muryarta na rawa. Ya matsa ya leƙa fuskarta, sai kuma ya sauka daga kan gadon yana cewa ‘Bari na gama da yara sai na kai ki asibiti, amma ki daure ki tashi ki shirya.’

    ‘To, ka bari gobe ma je asibitin mana.’ No, yau za mu je kin ga ana maganar za a saka lockdown saboda COVID 19 idan aka rufe ban san lokacin da za a buɗe garin ba. Gara mu je mu gama komai a siyo miki magani yanzu haka malaria ce.’ Ya faɗa sannan ya fice daga dakin.

    Baba Habi ce ta shirya yaran, duka da kasancewar ita ba ta iya girki ba haka suka haƙura Afaf ta nuna mata ta dafa musu indomie. Bayan sun sha shayi da burodi ta zuba musu indomie a lunchbox. Duk yanda ya so ya koma baccin bayan asuba ranar haka ya hakura ya zauna a parlor ɗin yana taya su shiryawa. Bayan ya kai su makaranta ya dawo ya shirya, ya taimakawa Khadeeja ita ma ta shirya suka wuce asibiti suka bar Habi a gidan.

    Suna zuwa likita ya tabbatar musu da cewa ciki ne da ita, aka ba ta magungunan suka taho. Kafin su isa gida sai da ya siyo magungunan, suna dawowa ya miƙawa Baba Habi magungunan ya yi mata bayani. Ya shiga ɗakini inda Khadeeja take kwance ya tsaya a kanta yace ‘Ki daure Habi ta haɗa miki abinci ki ci ki sha magani, shi ne za ki ji daɗin jikinki. Kin ga waɗannan magungunan ita Ma’u idan tana sha ko laulayin kirki ba ta yi, haka take ci gaba da harkokinta har ta haihu.’

    ‘Yanzu zan fito ai.’ Ya yi mata sallama ya tafi office. Indomie ɗin dai Baba Habi ta dafa mata sannan ta shiga ɗakin ta taso ta, ta sha maganin ta ɗan ci abinci sannan ta koma ta sake kwanciya. Kafin Habi ta ɗauko yara daga makaranta ta ɗan ji ƙwari, zuwa dare rashin ƙwarin jikin ya ragu don da kanta ta lallaɓa ta yi musu tuwo miyar kuka. Kwana biyu laulayin ya yi wa Khadeeja sauƙi don tana dagewa tana shirya yara makaranta kuma tana shiga kitchen ta yi abinci da taimakon Baba Habi.

    Ranar laraba suna zaune a parlor da magriba ita da yara da Abbansu; tana zaune a tsakiyarsu tana yi musu homework yayin da shi kuma Abbansu yake zaune a kan kujera yana ta faman danna waya yana kuma kallon labarai a BBC. Baba Habi ta fito daga dakin yara da sallama, bayan Khadeeja ta amsa sallamarta ta tsuguna daga gefe ta dubi Khadeeja tace ‘Uwar dakina ina so zuwa gida gobe, na ji an ce za a kulle garin. Zan je na dubo yarana idan na kwana ɗaya sai na dawo kafin a rufe garin.’

    Abbansu ya ɗago kansa daga kallon wayar yace ‘Baba ai da kin bari mu ga abinda hali zai yi tunda kin ga ita ma Khadeejan ba ta da lafiya.’ Ta juya Kai ‘To ai Yallaɓai kafin a kulle garin, na baro yara gara na je na dubo tunda ana maganar idan an rufe garin za a yi watanni kafin a buɗe.’

    Kafin ya yi magana Khadeeja ta dube shi tace ‘Ka bari ta je ai na ɗan ji sauƙi, gara ta je ta dawo kafin a rufe garin ga azumi ma yana tahowa.’ ‘Haka ne.’ Ya amsa ya cigaba da abinda yake yi.

    Gari yana wayewa bayan ya dawo daga kai yara makaranta ya ba wa Baba Habi kuɗin mota Khadeeja kuma ta haɗa mata abin da za ta ba ta ta kama hanya a kan jibi za ta dawo.A ranar da daddare aka sanar da total lockdown a Nigeria, an hana duk wata zirga zirga sai dai kowa ya zauna a gida a ga abinda hali zai yi.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    1. Rabbana Sarki Ilahu,
    Rabbi mai tayar da ruhu,
    Rabbi ga baiwarka Hauwa.

    2. Babu mai tsarki ya naka,
    Babu mai rahama kamarka,
    Rabbi kai rahama ga Hauwa.

    3. Babu mai jin ƙai kamarka,
    Babu mai tausai irin ka,
    Don Rasulu ka dubi Hauwa.

    4. Duk Karamci na wurinka,
    Ragwame ita ce sifarka,
    Rabbi rangwantawa Hauwa.

    5. Yadda duk ka yi babu mita,
    Ba mu jayayya da yin ka,
    Rabbi kai rahama ga Hauwa.

    6. Hauwa Ƙamshi jaruma ce,
    Babu shakka malama ce,
    Mai rubuce-rubuce Hauwa.

    7. Rabbi duk an mata shaida,
    Kamila ce mai ibada,
    Sayyada laƙabi na Hauwa.

    8. Rabbi ta yabi mai Madina,
    Kuma ta yi riƙon amana,
    Sa Rasulu ya san da Hauwa.

    9. Rabbi kai rahama gare ta,
    Rabbi kai jin ƙai wurin ta,
    Rabbi don kakarmu Hauwa.

    10. Rabbi sanyaya kabarinta,
    Rabbi kyautata kwanciyarta,
    Faɗaɗa shi saboda Hauwa.

    11. Sa Rasulu ya zo gare ta,
    Sa ya yo murnar zuwanta,
    Har ya ce “sannunki Hauwa.”

    12. Hauwa sai mun zo gare ki,
    Wataran za mu biyo ki,
    Za mu sadu ki ji ni Hauwa.

    13. ‘Yan uwa nai ta’azziya,
    Marubuta ga marsiyya,
    Na ta’aziyya ta Hauwa.

    14. Rabbana ka daɗo salati,
    Gun Habibu da yai wafati,
    Shi masoyi ne ga Hauwa.

    15. Ɗanbala suna Mohammed,
    In ka so ka kirani Ahmed,
    Ke ta’azziya ta Hauwa.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    12:03pm
    2 October, 2025.

    Karanta Gyara Kayanka

    Edita@rumasau-kallamu

  • Gyara Kayanka

    Gyara Kayanka

    Rabbana tuba nake yi,
    Nayi saɓo ba kaɗan ba.

    Na yi alƙawari gare ka,
    Zan yi bauta ba da ɗar ba.

    Dana zo shaiɗan ya ja ni,
    Ban yi bautar ko kaɗan ba.

    Ya raba ni da kai masoyi,
    Bai bari na zaunu lau ba.

    Ya hana ni saninka Allah,
    Bai bari nai ilimi ba.

    Shi yake ta zuga gare ni,
    Ko zumunta ban idar ba.

    Ka hana ya sa ni nayi,
    Ban tunanin zunubai ba.

    Ka umarta ya hana ni,
    Bai bari na aikata ba.

    Ya haɗa ni Walidaina,
    Ba su yo fahari da ni ba.

    Nai wulakanci ga bayi,
    Ban ragwantawa na jini ba.

    Kuma na yayyaɗa karya,
    Ban ko binciki gaskiya ba.

    Na yi sata na yi karce,
    Ban ji tausan ‘yan uwa ba.

    Na yi zunɗe na yi gulma,
    Nai harara ba kaɗan ba.

    Na yi zamba cikin amince,
    Duk da dai ba ka fallasa ba.

    Na yi shaidar zur a fili,
    Ban tunanin mutuwa ba.

    Kana na ha’inci bayi,
    Har maƙwabta ban bari ba.

    Rabbi nai wasa Sallah,
    Ban yi san da kace a yo ba.

    Ka haramta na halarta,
    Ban zaton haɗuwa da kai ba.

    Babu mai ikon hana ni,
    Ko ya ce nayi ba da ni ba.

    Duka na’u’o’in kaba’ir,
    Ɗanbala bai bar guda ba.

    Duniya ita ce ƙawata,
    Ko da ɗai ba ta kunyatan ba.

    Ban tunanin za na ƙaura,
    Gunka wai domin na tuba.

    Ba shiri mutuwa ta zo min,
    Ba ta yo sallama da ni ba.

    ‘Yan uwana nata kuka,
    Ba su so mutuwa a nan ba.

    Suka min suturar Musulmi,
    Ba su ce Allah tir da ni ba.

    Har waɗanda na yi wa cuta,
    Suka zo mini ba kaɗan ba.

    Suka min sallah da roƙon,
    Gafara ba su gajiya ba.

    Suka kai ni cikin kushewa,
    Addu’a ba su daina yi ba.

    Suka juya za su koma,
    Nai kiran ba su waiwayo ba.

    Daga nan na gano bala’i,
    Ban zaton haka a ciki ba.

    Ga duhu zafi macizai,
    Ko kaɗan ba su tausayan ba.

    Sai Mala’iku sukka zo,
    Ba su yo sallama da ni ba.

    Suka min wasu tambayoyi,
    Ban ko amsa guda ciki ba.

    Daga nan na shige masifa,
    Wanda ban yi zaton gani ba.

    ‘Yan uwana sai mu farga,
    Duniya ba gun zama ba.

    Za mu girbi abin da mukkai,
    Walla ba maganar wasa ba.

    Rabbana shirye mu Allah,
    Rabbi ba don nai batu ba.

    Har iyayye da ‘yan uwana,
    Da Musulmai ban baro ba.

    Rabbana ninko salati,
    Ga Rasulu ba ka ƙi ya ba.

    Ɗanbala daga Borno yai ta,
    Ɗan Bahaushe ba Ibo ba.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    8:27pm
    13 August, 2024

    Karanta Duka A Murɗe

    Edita@rumasau-kallamu