Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

    Addu’ar Sanya Sababbin Tufafi

     

    اللّهُمَّ لَكَ الْحَمْدُ أَنتَ كَسَوْتَنِيهِ، أَسْأَلُكَ خَيْرَهُوَخَيْرَ مَا صُنِعَ لَهُ وَأَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّهِ وَشَرِّ مَا صُنِعَ لَهُ

    Allahumma lakal hamdu anta kasautanihi ,as’aluka khairahu wa khaira ma suni’a lahu, wa a’uzu bika min sharrihi wa sharri ma suni’a lahu

    Ya Allah! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne Ka tufatar da ni shi (wannan tufar). Ina roƙonka alherinsa da alherin abin da aka yi shi dominsa, kuma ina neman tsarinka daga sharrinsa da sharrin abin da aka yi shi dominsa.

    Karanta Yadda Ake Adduar Razana A Cikin Barci

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Nau’in Zazzaɓin Cizon Sauron Da Ke Shafar  Ƙwaƙwalwa Yake

    Yadda Nau’in Zazzaɓin Cizon Sauron Da Ke Shafar Ƙwaƙwalwa Yake

    A WANNAN LOKACIN NA ZAZZAƁIN MALARIA MUSAMMAN GA YARA YANA DA KYAU MUSAN YADDA ZA MU MAGANCE “CEREBRAL MALARIA” TA HANYAR HAƊAKAR MAGUNGUNAN ANTIMALARIAL DRUGS DA KUMA ANTIBIOTICS DRUGS

    Cerebral malaria wani nau’in zazzaɓin cizon sauro ne mai zafi wanda yake shafar ƙwaƙwalwar mutum. Yana kama yara da manya. Ƙwayar cutar “Plasmodium falciparum parasite” ce take haddasa shi, kuma tana shiga jikin mutum ne idan sauro mai ɗauke da ƙwayar cutar ya ciji mutum.

    Idan ƙwayar cutar ta shiga cikin jikin mutum, tana kai hari ne a kan jajayen ƙwayoyin jininsa (red blood cells), kuma ta toshe masa ƙananan jijiyoyin jini na cikin ƙwaƙwalwarsa. Hakan zai haifar da kumburin jijiyoyin da kuma rashin gudanar jini a cikinsu. Daga nan sai tsokokin ƙwaƙwalwa su lalace.

    Alamomin kamuwa da cutar cerebral malaria sun haɗa da:

    • Ɗaukewar numfashi (seizure),
    • Rikicewa (confusion),
    • Suma (coma),
    • Da lalacewar jijiyoyin jini na laka (neurological vessels damage).

    Idan aka tabbatar da kamuwa da cutar, to, ya zamo dole a ɗauki matakin gaugawa wajen magance ta domin a kaucewa rasa rayuwar maras lafiyan.

    Ƙwayar cutar cerebral malaria ta bambanta da sauran nau’ukan malaria, waɗanda mabambantan plasmodium parasites suke haddasawa. Sauran nau’ukan malaria ɗin sun ƙunshi:

    1. Plasmodium falciparum wanda yake haifar da zazzaɓi mai zafi, kuma shi ne yake haddasa yawancin mace-macen da malaria take kawowa a faɗin duniya.

    2. Plasmodium vivax wanda yake haifar da zazzaɓi mai yawan dawowa bayan an sha magani. Ƙwayar cutar takan zauna a cikin hantar mutum ne na lokaci mai tsawon, kuma hakan shi ne ya sanya take yawan dawowar.

    3. Plasmodium ovale wanda ba a cika samunsa a cikin al’ummarmu ba. Shi ma yana yawan dawowa.

    4. Plasmodium malariae wanda yake haifar da zazzaɓi maras tsanani. Sai dai zai iya zama a cikin jinin mutum na lokaci mai tsawo, ya riƙa sanyawa mutum rashin jin daɗi. Ma’ana, shi bai warke ba, kuma shi bai kwanta saboda rashin lafiyar ba.

    5. Plasmodium knowlesi, wanda yake kama dabbobi, musamman birai (macaque monkeys), amma zai iya kama mutum.

    Magance cerebral malaria yana buƙatar ɗaukar matakai na haɗakar magunguna saboda hatsarin cutar. Yin amfani da alluran jijiyoyi na antibiotics, kamar IV gentamicin da IV ceftriaxone, tare da magungunan malaria (antimalarial drugs), yana da manufa kamar haka:

    1. Kare maras lafiya daga kamuwa da cututtukan bacteria idan baya da su, ko kuma magance su idan yana da su (prevention or treatment of bacterial infections): wanda ya kamu da cuta mai tsanani irin cerebral malaria, garkuwar jininsa takan yi rauni sosai, kuma hakan yana iya bayar da dama ga cututtukan bacteria su shiga jikinsa su haɗu da na malaria ɗin su ƙara rikita jikinsa. Antibiotics kamar gentamicin da ceftriaxone za su taimaka wajen magance cututtukan bacteria ɗin.

    2. Ƙoƙarin kare maras lafiya daga kamuwa da haɗakar cututtuka (covering for potential coinfections): a yankunan da cutar malaria ta yi ƙamari (malaria endemic regions), akwai yiwuwar maras lafiya ya haɗu da wasu cututtukan bacteria. Saboda haka, yin amfani da waɗannan antibiotics ɗin ga maras lafiyan zai samar masa da kariya mai yawa (broad-spectrum coverage) daga cututtukan bacteria da suke cikin muhallin.

    3. Cututtukan da ake iya ɗauka daga asibiti (hospital-acquired infections): maras lafiyan da aka kwantar a asibiti, yana iya fuskantar hatsarin kamuwa da wasu cututtukan daban, na wasu marasa lafiya da suke cikin asibitin. Allurai na antibiotics za su taimaka wajen bayar da kariya daga kamuwa da waɗannan cututtukan.

    Don haka, a rinƙa yin haɗakar magungunan malaria da kuma magungunan antibiotics ga maras lafiyan da yake fama da cutar cerebral malaria, abu ne wanda yake dai-dai.

    Karanta Hanyoyin Shayar Da Jaririn Da Mahaifiyarsa Ta Rasu
    Edita@rumasau-kallamu

  • Nazari A Kan Tasirin Watsi Da Littattafan Hadisi A Cikin Addini Da Al’umma

    Nazari A Kan Tasirin Watsi Da Littattafan Hadisi A Cikin Addini Da Al’umma

    Gabatarwa

    A zamanin nan, wani sabon rikicin addini ya taso a wasu sassan Arewancin Najeriya game da asalin Aƙida da kuma tushen ilimin addini. Wasu mutane waɗanda ba su da zurfin ilimi a fannin ʿUlūm al-Ḥadith (ilimin hadisi) ko ʿUlum al-Din (ilimin addini) — suna kiran Musulmi da cewa su dogara da Alƙur’ani kaɗai, su watsar da Hadisi saboda suna ganin wasu hadisai “sun taɓa mutuncin Annabi ﷺ.

    ” Wannan ra’ayi, duk da cewa yana iya kama da tsoron Allah a zahiri, yana da matuƙar hatsari ta fuskar aƙida, ɗabi’a, da zamantakewa. Addinin Musulunci ya ginu ne a kan Alƙur’ani da Sunnah, waɗanda ba za a iya raba su ba. Watsi da Hadisi yana lalata asalin Musulunci kuma zai haifar da ruɗani da rarrabuwar kawuna a cikin al’umma.

    Alƙur’ani kansa ya umarci Musulmai da su bi Annabi ﷺ: ‘Kuma abin da Manzon Allah ya ba ku ku karɓa, abin da kuma ya hana ku ku guje masa.’ (Surat al-Ḥashr 59:7). Wannan aya ta tabbatar da cewa Sunnah ita ce tushe na shari’a da imani bayan Alƙur’ani. Annabi ﷺ ya ce: ‘An ba ni Alƙur’ani da wani abu makamancin sa tare da shi.’ (Sunan Abu Dawud, 4604). Wanda ya ƙi Hadisi, tamkar ya ƙi wani ɓangare na wahayi ne, yana kuma rushe tsarin Shari’a, ɗabi’a, da aƙida gaba ɗaya.

    A tarihi, ƙungiyoyin da ke ƙin Hadisi (Qur’aniyyah) sun taɓa fitowa a lokuta daban-daban. Dalilansu yawanci jahilci ne game da hanyoyin binciken hadisi, ko tasirin ra’ayoyin Turawa masu son lalata Musulunci. A yankin Arewacin Najeriya, wannan aƙida tana samun gindin zama musamman a wajen masu jahilci, ko masu son farin jini a idon jama’a. Suna ɗauka cewa ƙin Hadisi na kare mutuncin Annabi ﷺ, alhali kuwa hakan yana goge tarihin koyarwarsa da kyawawan halayensa.

    Mummunan Tasiri da Illolin Ra’ayin Watsi da Hadisi

    1.1 Lalata Imani da Shari’a — Ba tare da Hadisi ba, ba za a iya fahimtar Musulunci daidai ba. Hanyoyin Sallah, Zakka, Azumi, da Hajji duk daga Hadisi ake koyonsu. Rashin bin Hadisi yana kaiwa ga lalacewar ibada da rushewar addini.

    1.2 Rage Darajar Annabi ﷺ — Wanda ya ƙi Hadisi yana rage matsayin Annabi ﷺ a matsayin Manzo. Wannan yana saɓawa kalmar Allah da ta ce: ‘Bai yi magana daga son zuciyarsa ba, abin da yake furtawa wahayi ne da aka yi masa.’ (Surat an-Najm 53:3–4). Saboda haka, ƙin Hadisi yana nufin shakku cikin wahayi, wanda yana iya kai wa ga kufr al-juhūd.

    1.3 Rarrabuwar Kawuna da Ƙungiyoyi — Idan aka watsar da Hadisi, kowa zai fassara Alƙur’ani yadda ransa yake so. Wannan zai haifar da rarrabuwar ra’ayi da ƙungiyoyi masu saɓa wa juna. (Surat al-An‘ām 6:159)

    1.4 Raguwar Hankali da Ɗabi’a — Hadisi na ƙunshe da koyarwar ɗabi’a da halayen Annabi ﷺ. Idan aka watsar da shi, al’umma za ta rasa shugabancin ɗabi’a, za a samu ruɗani da raunin ruhi.

    1.5 Wulaƙanta Malaman Addini — Wa’azin irin wannan yana sa mutane su raina manyan malamai kamar Imam al-Bukhari, Muslim, da Ahmad ibn Hanbal. Wannan yana haifar da girman kai da rashin girmama ilimi.

    1.6 Tasirin Ra’ayoyin Yammacin Duniya — Yawancin masu ƙin Hadisi a yau suna bin hujjojin Turawa masu son cire Musulunci daga ikon Annabi ﷺ.

    A yankin Arewacin Najeriya, irin wannan ra’ayi yana jawo: ruɗani ga matasa; rashin haɗin kai a al’umma; rage girmamawa ga malamai; lalacewar tsarin karatun addini; da kuma rikicewar shugabanci.

    Gargadin Annabi ﷺ

    Annabi ﷺ ya yi gargaɗi da cewa: ‘Wani lokaci zai zo inda mutum zai zauna a kan gadonsa yana cewa: “Mu bi Alƙur’ani kaɗai; abin da muka samu halal a cikinsa, za mu ɗauka halal; abin da muka samu haram, za mu ɗauka haram.

    ” Lallai abin da Manzon Allah ya hana, kamar abin da Allah Ya hana ne.’ (Sunan Abu Dawud, 4604). Wannan Hadisi yana bayanin halin da ake ciki a yau kuma yana nuna cewa wannan tunani alama ce ta karkacewa daga hanyar gaskiya.

    Watsi da Hadisi ba ƙaramin kuskure ba ne hatsari ne ga asalin Musulunci. Yana rushe ginshiƙin Shari’a, yana wulaƙanta ikon Annabi ﷺ, kuma yana buɗe ƙofa ga ruɗani, sekularizm, da rarrabuwar kai.

    Don haka wajibi ne a ƙarfafa ilimi da fahimta mai kyau game da Hadisi, gina girmamawa ga malamai, da yin da’wah mai ilmantarwa don gyara wannan kuskuren. Wanda ya watsar da Hadisi, ya watsar da Annabi ﷺ. Alƙur’ani saƙo ne daga Allah, Sunnah kuma ita ce aikace-aikacen sa. Addinin Musulunci ba zai rayu sai da biyunsu tare.

    Rubutu da nazari: Huzaifa Mukhtar Muhammad

    Dalibin ilimi

    Karanta Manufar Rayuwar Duniya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Hanyoyin Shayar Da Jaririn Da Mahaifiyarsa Ta Rasu

    Hanyoyin Shayar Da Jaririn Da Mahaifiyarsa Ta Rasu

    IDAN MAHAIFIYAR JARIRI TA RASU KUMA BABU HALI NA SIYAN MADARA TA GWANGWANI (FORMULA MILK) ZA KU IYA BIN WAƊANNAN HANYOYIN DOMIN SHAYAR DA JARIRIN:

    1. Samun uwa mai shayarwa: A nemi wata uwa da take shayarwa domin ta taimaka ta shayar da jaririn. Wannan ɗabi’a ce da ta dace da shari’ar Musulunci da al’ada.

    2. Madarar dabbobi: Idan babu uwa mai shayarwa, ana iya yin amfani da madarar shanu ko akuya, wacce aka tafasa ta domin kashe ƙwayoyin cutar da suke cikinta, sa’annan a gauraya ta da ruwa mai tsabta (dilution) domin samun sauƙin narkewarta a cikin jaririn.

    3. Yin dabarun zuwan ruwan nono: Mace tana iya neman izinin mijinta domin ta yi amfani da dabarun da ruwan nononta zai zo (induced lactation), domin ta shayar da jaririn.

    Karanta Dalilan Da Ke Sa Zubar Ruwan Nono Alhalin Babu Ciki Ko Goyo
    Edita@rumasau-kallamu

  • Dalilan Da Ke Sa Zubar Ruwan Nono Alhalin Babu Ciki Ko Goyo

    Dalilan Da Ke Sa Zubar Ruwan Nono Alhalin Babu Ciki Ko Goyo

    Abin da yasa na sake yin wannan rubutun shi ne ganin yawan tambayoyin da ‘yan-uwa mata suke ta yi a kan matsalar a kullum.

    Zubar ruwan nono babu ciki ko goyo yana faruwa ne saboda hauhawar sinadarin prolactin a cikin jikin mace. Akwai wata ƙaramar jaka (gland) wacce take maƙale a jikin ƙasan ƙwaƙwalwa, wacce ake kira “pituitary gland’, ita ce take samar da sinadarin prolactin ɗin.

    Idan jakar tana samar da sinadarin prolactin fiye da yadda jikin mace yake buƙata, to, shi ne hauhawar sinadarin prolactin wanda ake kira “hyperprolactinemia” a likitance. Idan kuma jakar tana samar da sinadarin prolactin ƙasa da abinda jiki yake buƙata, to, shi ne “hypoprolactinemia”.

    Idan kuwa prolactin yana zubowa daidai da halin da jikin mace yake buƙata, to, shi ne “normal physiological prolactin level”. Magana ta gama-gari ita ce, adadin yawan sinadarin prolactin da ake buƙata a jikin mace, bisa ma’aunin ɗakin binciken kimiyya (laboratory), shi ne:

    1. Macen da ba ta da ciki (non-pregnant woman): 25 micrograms per litre (mcg/L).

    2. Macen da take da ciki (pregnant woman): daga 80 zuwa 400 mcg/L.

    3. Macen da take shayarwa: daga 200 zuwa 400 mcg/L.

    NAU’IN RUWAN NONON DA YAKE ZUBO WA MACE SAKAMAKON HAUHAWAR SINADARIN PROLACTIN

    Idan mace tana da matsalar hauhawar sinadarin prolactin, to, ruwan nonon da zai riƙa zubo mata zai kasance kamar haka:

    1. Launi (colour): launinsa zai iya zamowa fari (whitish), ko garai-garai (clear), ko ɗorowa (yellowish).

    2. Kauri (texture): zai iya zamowa maras kauri (watery), ko mai danƙo (sticky).

    3. Yawan zuba (discharge frequency): zai iya zamowa yana zuba a kai-a kai (continuously), ko lokaci-lokaci (intermittently), ko sai an matsa (when nipple is squeezed).

    4. Ɗanɗano (taste): zai iya zamowa mai ɗanɗanon zaƙi-zaƙi (sweetened), ko gishiri-gishiri (salty), ko maras ɗanɗano (tasteless).

    YADDA HAUHAWAR SINADARIN PROLACTIN YAKE HANA MACE ƊAUKAR JUNA BIYU

    Yawanci mace mai hauhawar sinadarin prolactin takan kasa ɗaukar juna biyu. Dalili shi ne sinadarin yana haifar da abubuwa kamar haka:

    1. Hana mace iya saka ƙwan haihuwa (suppression of ovulation): hauhawar sinadarin prolactin yana hana jikin mace zubo da ruwan gonadotropin releasing hormones (GnRH) daga jakar thalamus wacce take cikin ƙwaƙwalwa (hypothalamus).

    Shi kuma GnRH dole sai ya zubo sa’annan jakar sinadarin pituitary wacce take cikin ƙwaƙwalwa za ta zubo da sinadarin luteinizing hormone (LH), wanda yake da matuƙar muhimmanci wajen bai wa mace damar saka ƙwan haihuwa (ovulation) da kuma yin al’ada yadda ya kamata (normal menstrual cycle).

    2. Rikicewar al’ada (irregular menstruation): hauhawar sinadarin prolactin yana haifar da rikicewar al’ada ko kuma ɗaukewarta gaba ɗaya. Hakan zai iya sanya ɗaukar juna biyu ya yi wahala.

    3. Rikita ayyukan jakar ƙwan haihuwa (interference with ovarian function): hauhawar sinadarin prolactin yana hana jakar kwan haihuwa ta yi aiki yadda ya kamata ta fuskar samar da ƙwan haihuwa da kuma yin girmansa.

    4. Rashin samar da yanayi mai kyau a mahaifa (impaired corpus luteum function): koda juna biyu ya samu, kuma ƙyanƙyasasshen ƙwan haihuwa ya shige cikin mahaifa, to, akwai buƙatar kyakkyawan yanayi domin rayuwar ɗan-tayi. Hakan zai yiwu ne idan jikin mace yana samar da sinadarin progesterone isasshe. Shi kuma progesterone ba zai samu ba sai idan halittar corpus luteum tana da kyau.

    A taƙaice, idan mace ta ga ruwan nono yana zubo mata alhalin babu ciki ko goyo, kuma ta daɗe sosai da yin yaye, to, ta je asibiti domin a yi bincike a tabbatar da daidaiton zubar ruwan sinadarin prolactin ɗinta. Amma akan samu matan da ruwan nononsu ba ya ɗaukewa kwata-kwata, kuma hakan ba ya hana musu ɗaukar juna biyu, sai dai ba su da yawa a cikin mata.

    ABUBUWAN DA SUKE HAIFAR DA HAUHAWAR SINADARIN PROLACTIN

    Su ne:

    1. Tsirowar ƙari a jikin jakar sinadarin pituitary (prolactinomas): wannan ƙari ne amma ba na cancer ba (noncancerous tumour) wanda yake sanya zubar ruwan sinadarin prolactin. Abubuwan da suke haddasa fitowar ƙarin prolactinomas su ne gado, hauhawar sinadarin estrogen, juna biyu, wahalhalun bayan haihuwa, cututtukan jakar sinadarin pituitary.

    2. Laulayin amfani da magunguna (medication side effects): yin amfani da magungunan cututtukan ƙwaƙwalwa (antipsychotics), ko magungunan rage damuwa (antidepressants) ko magungunan hawan jini (antihypertensives), ko magungunan hana tashin zuciya da amai (antinausea), duk suna iya haifar da hauhawar sinadarin prolactin.

    3. Rashin yin aikin jakar sinadarin thyroid yadda ya kamata (hypothyroidism): wannan yana faruwa ne sakamakon yin tiyata a jakar thyroid, ko ƙarancin sinadarin iodine, ko gado, ko laulayin hasken na’urar hoton x-ray, ko nisan shekaru.

    4. Daɗaɗɗen ciwon ƙoda (chronic kidney disease): idan ƙoda ba ta yin aikinta yadda ya kamata na sarrafa sinadarin prolactin, to, akwai yiwuwar ya hauhawa ya haddasa zubar ruwan nono.

    5. Ɗaukar juna biyu da shayarwa (pregnancy and breastfeeding): samun juna biyu da shayarwa suna sanya hauhawar sinadarin prolactin domin samun isasshen ruwan nono ga jariri. Wasu matan sukan yi tazarce kamar yadda na faɗa a sama. Ma’ana, ko da sun yi yaye, to, sinadarin prolactin ɗin ba zai sauka ba. Don haka za su cigaba da ganin zubar ruwan nono har su sake samun wani cikin. Wannan ba matsala ba ne Insha Allah.

    6. Damuwa da kuma ayyukan motsa jiki mai tsanani (stress and excessive physical exercise): idan mace tana yawan shiga cikin yanayin damuwa, to, akwai yiwuwar sinadarin prolactin ɗinta ya hauhawa. Haka nan idan tana yin ayyukan motsa jiki mai yawa.

    7. Hauhawar sinadarin prolactin wanda aka kasa gane asalinsa (idiopathic hyperprolactinemia): akwai lokacin da mace za ta sami hauhawar sinadarin prolactin, kuma duk binciken da za a yi, amma daga ƙarshe sai a kasa gane abinda ya haddasa shi.

    DALILIN DA YASA HAUHAWAR SINADARIN PROLACTIN YAKE DA WUYAR MAGANI

    Mata masu yawa suna yin ƙorafin cewa sun yi amfani da magunguna da yawa har sun gaji, amma matsalar zubar ruwan nono ba ta sake su ba. Lallai warkar da matsalar yana da wahala saboda dalilai kamar haka:

    1. Rashin iya gano ainihin abinda ya haifar da matsar (inability to diagnose the root cause): matuƙar likita bai yi binciken ƙwaƙwaf wajen gano abinda ya haifar da hauhawar sinadarin prolactin ba, to, zai yi wahala a magance ta cikin sauƙi. Za a yi ta magani daban kuma ciwo daban. Ma’ana, ya kamata a bibiyi dukkan abubuwan da na faɗa a sama ɗaya-bayan-ɗaya har a gano tushen matsalar.

    2. Girman ƙarin prolactinomas (tumour size): Idan fitowar ƙarin prolactinomas ne ya haifar da matsalar, to, girman ƙarin zai iya shafar saurin warkewa ko rashin warkewar matsalar. Ma’ana, idan ƙarin ƙarami ne, to, zai fi sauƙin warkarwa. Idan kuwa ya girma, to, sai an dage da shan magani. Ƙila ma sai an yi aikin tiyata.

    3. Amsar da jikin mace yake yi wa magani (medication tolerance): halittar jikin mutane ta bambanta, wani yana da saurin amsar magani, wani kuwa akwai wahalar amsar magani. Magungunan da aka fi yin amfani da su wajen magance zubar ruwan nono su ne bromocriptine ko cabergoline. Jikin mace ya bambanta wajen saurin amsa ko rashin amsarsu.

    Karanta Abubuwan Da Ke Haddasa Rashin Zuwan Al’ada (AMENORRHEA)
    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Haka Khadeeja ta kwana a asibitin ƙarƙashin kulawar Anti Iyami. Tun dare likita ya gama da ita aka ba ta duk wasu magungunanta, ya sanar da Anti Iyami za a iya tafiya da ita gida. Don haka gari yana wayewa ƙarfe takwas na safe Anti Iyami ta gama aiki za ta tafi gida ta shiga ɗakin da Khadeejan take.

    Bayan sun gaisa tace ‘Yanzu akwai inda yake miki ciwo Khadeeja.’ Ta jijjiga kai tace ‘A a, ko ina ya warware, yanzu ma na gama breakfast ɗin da kika aiko min da shi.’ ‘Ok, so ki kirawo Mustapha kice masa zan wuce da ke gida sai mu tafi na kai ki gidan Mommy ɗin.’

    Ba ta son ta yi magana da shi sai ta je gidansu don haka cikin sauri tace ‘Ai yanzu na kirawo shi bai ɗauka ba, ina jin yana bacci ko baya kusa da wayar amma na san da ya gani zai kira. Mu wuce kawai tunda tun jiya na gaya masa za mu wuce gidan.’

    ‘Ohk, to tashi mu tattara kayan mu wuce. Ni ma tun dare na kirawo Mommyn naki na sanar da ita, da safe ma mun yi waya. Na dai ce mata kada ta kirawo ki ne don duk lokacin da na shigo sai na same ki kina bacci, shi yasa nace ta bari idan kin tashi zan kirawo ta ku yi magana.

    But ba komai idan mun je za ta ganki tunda mun shirya.’ Nan suka haɗa kayan Khadeejan waɗanda daman ba yawa ne da su ba suka shiga motar Anti Iyami suka kama hanya.

    Khadeeja tana zama a mota ta lalubo wayarta ta saka ta a silent ta jefa a jaka don ba ta so Mustapha ya kirawo ta a gaban Anti Iyami domin ba ta san me zai ce ba idan ya ji ta wuce gidan Mommy. Duk inda suka je checkpoint aka tsayar da su da an ga uniform ɗin Anti Iyami kuma ta nuna ID card sai a bar su su wuce, haka har suka isa gidan Mommy.

    Tun suna asibitin Anti Iyami ta sanar da Mommy za su taho don haka kafin su isa an ɗorawa Khadeeja ruwan wanka, suna shiga ta wuce ɗakin Mommy inda Azumi mai aikinsu ta sirka mata ruwan a banɗaki. Ba tare da ɓata lokaci ba ta faɗa wanka.

    A parlor Mommy suka zauna da Anty Iyami; bayan sun gaisa sun jajantawa juna Mommy tace ‘Ina Mustaphan? Ai na zata tare kuke da shi.’ Ta gyara zama tace ‘Bai zo ba ma yau da safen duk da dai tace ta gaya masa nan za mu huto, amma don Allah ƙawata a duba yarinyar nan.’

    Cike da kulawa Mommy tace ‘In sha Allahu kuwa, ke ma kin san ba zan barta haka ba ko akwai wata matsala ne da ta samu ko rashin lafiya.’Ta jijjiga kai ‘Babu fa, kawai dai tace min tana son dawowa gida. Duk dai wasu tambayoyi da zan yi mata na yi ta nuna min babu komai, to amma kin ga akwai yaransa guda huɗu.

    Wataƙila hidimar gida da ta yaran ce take mata yawa ga ciki shi yasa ta sume masa. Baccin da ta dinga yi kawai ya tabbatar min da cewa ba ta samun isasshen bacci wallahi, don shi yasa ma na ƙi tashinta ku yi waya. Gaskiya ku bincika, ya nema mata mai aiki ko ya san yanda zai yi da yaransa.’

    ‘Umm! To kin ga dai idan ma da wata matsala ba ta faɗa ba, koda yake kwanaki tace mai aikinsu ba ta nan a bata aron Nabila amma Baffansu ya ƙi amincewa. Wataƙila saboda babu mai aikin ne abun ya yi mata yawa ga laulayi.’

    ‘Gaskiya dai ku duba, ko da za ta koma ku bar ta ta huta ta sami natsuwa sannan kuma a ɗaukar mata mai aiki.’ Suka ƙarasa hirarrakinsu daga baya suka yi sallama Anti Iyami ta kama hanya.

    Bayan ta fito daga ta tarar da farfesun kaza mai rai da lafiya wanda Mommy ta dafa mata sannan ga shayi mai kauri Azumi ta haɗa mata da burodi a gefe, cikin sauri ta gyara jikinta ta sa kaya sannan ta shimfiɗa dadduma a gaban gado ta miƙe ƙafafu ta zauna ta fara cin abinci.

    A nan Mommy ta shigo ta same ta ita ma ta zauna, sai da ta gama cin abinci sanna ta fara yi mata tambayoyi. Ba ta ɓoyewa Mommy komai ba ta sanar da ita halin da ake ciki, ta tabbatar mata cewa idan dai da mai aiki musamman babba wadda ba za ta sa ta surutu ba.

    Sai dai ta kasa gaya wa Mommy cewa gaba ɗaya ma ko da da mai aikin ita ji take kamar ma Mustaphan baya ƙaunarta, gani take kamar yanda take zama kullum cikin hidima ya sa ba ta gane kulawarsa a gareta. Don haka ta bar wannan a ranta tana fatan idan an sami mai aiki ya zama suna samun lokaci a tare to za ta fuskanceshi.

    Muryar Mommy ce ta katse ta tana cewa ‘To yanzu yaushe zai zo ya ɗaukeki?’ Ta kalle ta suka haɗa ido ta sunkuyar da kai sanna cikin muryar shagwaɓa tace ‘Mommy kin ga yanzu mai aikin ba ta dawo ba, kuma na gaya miki shi ba zai taya ni komai ba kuma ba zai bari yaransa su tayani ba.

    Kawai ki bar ni sai bayan sallah ko kuma duk lokacin da mai aikin ta dawo ko aka sami wata.’ Mommy ta jijjiga kai tace ‘Na fahimce ki, amma me kike so na gayawa Baffanku? Shi kuma Mustaphan wane dalili za a ba shi na riƙe ki a nan ɗin. Tunda dai ciki ya fice an riga an wake; kuma ga ki nan kowa yana ganinki ras.’

    Ta karyar da kai kamar abin tausayi tace ‘Umma ni dai don Allah ki san yanda za ki yi a bar ni na huta. To bari mu gani. Idan kuma akwai wani abun da Mustaphan yake yi miki wanda kike so a yi masa magan to ki gaya min.’

    ‘Babu komai tunda ma bai hana a ɗauki mai aikin ba, in sha Allahu da ta dawo ko kika samo min wata zan koma.’ Ta gyara zama ta kafa tagumi ‘Hmm! bari mu ga yanda za mu yi da Baffan naki tukunna.’

    Sai da suka gama wannan hirar sanna ta tuna tunda suka shigo ba ta ma nemi wayarta ba, ta san yanzu haka Mustapha yana ta faman kiranta. Cikin sauri ta miƙe ta ɗauko wayarta daga jakarta, ai kuwa tana dubawa taga missed calls ɗinsa har guda goma sha ɗaya.

    Tana gani danna masa kira, ko ringing ba ta yi ba ya ɗauka ‘Hello, wai ina kika shiga ne naje asibiti ina ta nemanki? Na rasa mai ba ni tsayayyiyar amsa, sai ce min kawai ake kin tafi da Anti Iyami, na za ta gida za ta kawo ki na dawo gidan kuma baku zo ba. Kin sa ina neman haukacewa na rasa wanda zan kira don ban san me zan ce musu ba.’

    ‘Subhanallah! Ka yi hakuri Babe, wallahi ka ganni nan ai gidan Mommy ta kawo ni. Na kirawo ka ba ta shiga ba kuma shi ne na jefe wayar a jaka na manta sai yanzu da na fito daga wanka na tuna. Amma shi ne ba ki gaya min ba? Kin san wulaƙancin da aka dinga yi min a checkpoint kuwa?’

    Ta tausasa murya ‘Sorry Babe, wallahi laifi na ne don tun a asibitin Anti Iyami tace na kirawo ka sai wayar ta ƙi shiga.’ Ya ɗan saki numfashi ‘To me yasa ba ku taho nan ba ko kuma a jirani na zo? Me ya sa za a kai ki gidan Mommy?’

    Ta ɗan yi shiru, shi ma bai yi magana ba yana sauraronta; ta murguɗe baki kamar yana kallonta tace ‘Ai ka san dai idan an haihu ana zuwa wanka gida, may be shi yasa da suka yi waya Mommy tace a kawo ni gida.’

    ‘To kuma shi ne aka rasa wanda zai gaya min.’ Cikin ƙosawa tace ‘To ba ga shi na gaya maka ba, kuma ai nace maka mantawa na yi.’ Ya ɗan ja numfashi ‘Uhm! To ya jikin naki? Shike nan an gama yi miki alluran?’

    ‘Na sami sauƙi, ga ragowar magungunana na taho da su daman yawanci na kwana bakwai ne, amma na sami sauƙi. To idan an buɗe gari sai na zo na ɗauke ki, ina ga ranar Saturday za su ɗan buɗe mu, nan da kwana uku kenan.’

    ‘Uhm, to ka dai zo amma gaskiya sai bayan sallah zan dawo kafin nan na dan huta na gama arba’in tunda ka san shi ma ɓarin ai sai an yi wanka. Ɓarin, gaskiya ban taba ji ba. Ma’u ma fa su biyu tana yin ɓarin amma na biyun babu wanda ma muka gaya wa a nan ta yi zamanta ta cigaba da hidimarta.

    Hutawa kawai ta yi na kwana biyu. Idan ka zo dai ma yi maganar.’ Ta tamabye shi yaran ya ba ta su suka gaisa sannan suka yi sallama suka ajiye waya.

    Tunda yake bai taɓa ganin son zuciya irin wannan ba, ya za a yi a ɗauke masa mata kuma a ce sai bayan sallah za ta dawo? Kawai saboda ta yi ɓari. Asma’u ma ai ta yi ɓari har sau biyu ma; na farkon shi ne bayan haihuwar Habib, bayan an yi mata wankin ciki a ranar suka dawo gida.

    Ko maganar ta je gidansu ma ba a yi ba kawai dai an kawo mata ƙanwarta tunda dama tana da mai aiki. Na biyun kuwa ma bayan haihuwar Nasreen babu wanda suka gaya wa, suna zuwa asibiti aka ce musu ya fice gaba ɗaya ba sai an yi wankin ciki ba aka ba su magunguna suka dawo gida.

    Kawai dai ya san ba za ta koma ɗakinsa ba sai bayan kwana arba’in, kuma ba shi da matsala da wannan. Amma su iyayen Khadeeja saboda son zuciya sai akwai su ɗauke ‘yarsu? Kuma ko gaya masa ba za ayi ba.

    Haka ya gaji da saƙe-saƙensa ya sake daga wayar ya kirawo Alhaji ya gaya masa, don bai gaya musu cewar a asibiti ma ta kwana ba yana so ya je da safen ya gani tukunna. Shi ma Abban ya nuna rashin jin daɗinsa da aka tafi da ita, musamman da ya gaya masa ba su ma tambaye shi ba suka tafi da ita.

    Bayan sun gama waya da Alhaji ya kirawo Ummansu ita ma ya sanar da ita. Suma su Afaf sai da ya yi musu bayani don tunda ya dawo ba su ganshi tare da Khadeeja ba suke ta faman yi masa tambayoyi. Babu yanda za a yi ya iya ɓarin Khadeeja ta zauna a gidansu, ya suke so ya yi?

    Ga lockdown an hana mutane fita sannan kuma su ɗauke masa mata. Kwana ukun nan ma da zai yi da yaran bai san ta ina zai fara ba don yana tuna yanda a kwana ɗayan nan suka gama firgita shi; ga gari a kulle balle ya kai su gidan Umma. Gaskiya da an buɗe gari ranar Asabar zai je ya ɗauko ta tunda dai ko shi ya tambaye ta jiki ta ce da sauƙi.

    Sai can da yamma dabara ta faɗo masa; ya ɗauki waya ya kirawo Baffan Khadija, bayan sun gaisa ya jajanta masa jikin Khadeejan sannan ya sanar da shi cewa ranar Asabar idan aka buɗe gari zai zo ya ɗauki Khadeejan.

    Ba tare da matsala ba kuma Baffan ya amsa masa da hakan ya yi, don haka cikin walwala ya ƙarasa wuninsa. Bayan Ummi ta gama haɗa musu kayan shan ruwa shi da yara ta wuce ta tafi gidansu ta bar su.

    Tun bayan dawowar Khadeeja gidan sau ɗaya Baffanta ya shiga ɗakin Mommy ya same ta ya yi mata sannu. Yana zaune a parlor bayan ya dawo daga sallar tarawih Mommy ta shiga ta same shi, ta zauna a gefensa suna kallon labarai a tashar Aljazeera tare. Bayan sun ɗan taɓa hira yace ‘Ɗazu Mustapha ya kirawo ni yana duba Khadeeja, ya ma ce min idan an buɗe gari ranar Asabar zai zo su tafi.’

    Ta ɗan gyara zama ‘Ranar Asabar fa kwana uku kenan, haba ai sai ta kwana arba’in. A ah to ai ni na za ta sun gama magana da ita ne a kan hakan.’ Ta jijjiga kai tace ‘Gaskiya dai ba su yi wata magana ba don da kanta tace min tana so ta yi arba’in ɗin. Suna zuwa da na sa ruwan zafi nayi mata wanka ta ji dadin jikinta da kanta tace a bar ta ta yi arba’in ɗin.

    Haba, kuma haka za a mayar da ita haihuwar fari babu wani gyara? Sai kace ‘yar tsana.’ ‘To ai na ga ɓari ne ba haihuwa ba.’ ‘To ai Baffan Nabila ɓari ya fi haihuwa wahala sosai ma, sannan kuma na fari ne haka za a ba shi matar ya ma kasa ɗaga mata ƙafa a kwana arba’in ɗin.’

    ‘To na ga dai ai matarsa ce ko? Ina laifi, kuma ma ai shi ma ba zai ce bai san waɗannan hukunce-hukuncen ba tunda ga yara nan har huɗu an haifa masa.’ Ta sake gyara zama ‘Ku dai yi haƙuri Baffa a bar ta ta yi kwana arba’in ko a ƙalla talatin, kafin nan ta ji daidai a jikinta sai ta koma.’

    Ya ɗaga wayarsa ya cigaba da dubawa yana cewa ‘To ai shikenan idan ya zo sai ku yi masa bayani, ni bani da matsala da hakan.’ ‘Yauwa, ai lalacewar zamanin ba ta kai an daina wanka da gyara a haihuwar fari ba. Amma dai idan ya zo sai ka yi masa bayanin idan kana nan tunda ka ga kai ya nema, gara ku cigaba da magana man to man.’

    Ya yi dariya yace ‘To babu laifi.’ Ya san halin matarsa da kishi, yanzu haka haushi ta ji shi Mustaphan bai kirawo ta ya duba Khadeejan ba ko a ƙalla ya gaya mata zai tafi da Khadeeja ranar Asabar tunda ya san ita ce za ta shirya Khadeejan amman ya kirawo Baffa. Jimawa kaɗan kuma ta fice ta ba shi waje.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    A gajiye ya shiga gidan wajen ƙarfe tara na dare, yana shiga yaran suka taso da gudu gaba ɗaya tun kafin ya gama rufe ƙofar motar suba cewa ‘Abba ina Anti Khadeeja?’ Ya ɗauki shukura ya kama hannun Nasreen yana cewa ‘Tana asibita, likita ya kwantar da ita, amma gobe in sha Allahu zan je na taho da ita.’

    Ya tattara su suka shige cikin gidan. Yana shiga bayan Ummi ta yi masa sannu da zuwa ya sallame ta ya fito ya raka ta sai da ta shiga gida ta kirawo masa babanta ya yi godiya sannan ya koma gida. Sai da ya biya sallar Magriba da Isha’I duk da yunwar da yake ji sannan ya zo ya zauna a parlor a gajiye, ya dubi Afaf wadda take kwance tana yin game a tab ɗinta yace ‘Afaf ɗauko min flask da kayan shayi.’

    Ta miƙe ta shiga kitchen ɗin, jimawa kaɗan ta fito ɗauke da kayan shayin bayan ta ajiye tace Abba babu ruwan zafi a flask ka jira na dafa maka, wanda Anti ta zuba mun sha shayi da shi mu da Ummi.’

    ‘No, bar shi kawai. Ɗauko min zoɓo ki kawo min ragowar abincin da kuka ajiye na ci, yunwa nake ji.’ Kafin ta ba shi amsa Habib yace ‘Abba ai tun kafin ku fita zoɓon ya ƙare a nan, ka manta? Kuma dama shi kenan wanda Anti ta zuba ragowar na jiya ne.’

    Kafin yace wani abu Afaf tace ‘Abba babu fa abincin ma sai dai ragowar rice and stew, gaba ɗaya dankalin muka cinye kuma da peppersoup ɗin, amma akwai ragowar watermelon a fridge. Ko na dafa maka indomie?’

    Ya kalle ta yana shafa kai na ɗan lokaci, ya ma rasa me zai ce mata saboda yanda gaba ɗaya ya jigata saboda yunwa, coke kawai ya samu a asibiti da wani guntun burodi ya ci. Ya zata za su rage abincin amma wai duk sun ciye. Muryar Afaf ce ta katse shi tana cewa ‘Bari kawai na dafa maka indomie ɗin Abba.’

    ‘No, bari na shiga kitchen ɗin na gani.’ Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Ya ɗan ɗauki yana kallon kitchen ɗin bai ma san ta inda zai fara ba; har ya ɗauki tukunya zai dafa indomie sai kuma ya tuna ai akwai cereal, don haka ya mayar da tukunyar ya ajiyeta a muhallinta.

    Ya zuba ruwan zafi a kettle ya tafasa ya haɗa cereal, ya ajiye ya fiddo kankana daga fridge ya yanka sannan ya ɗauko ya dawo parlor ɗin. Yana zama Shukra ta matso tana dariya ‘Abba zan sha golden morn ɗin.’Ya bi ta da kallo da cokali a hannunsa; ba ta taɓa ba shi takaici ba kamar a wannan lokacin don ya tabbatar sun ƙoshi tunda gashi sun cinye duk wannan uban abincin da Khadeeja ta dafa.

    Ya dubi Afaf yace ‘Tashi ki ɗauko cereal, ki haɗo min da tea flask da komai na haɗa mata.’ Kafin Afaf ta dawo Nasreen tace ‘Abba ni ma zan sha.’ Don haka tana kawowa ya sa ta koma ta ƙaro kofi, ya haɗa musu cereal ɗin su biyun.

    Babu wadda ta sha cokali uku a cikinsu, suka tashi suka bar masa a nan. Kafin ya gama cinye nasa abincin duk sun fara gyangyaɗi don haka ya sa Afaf ta ɗauko musu kayan baccinsu ya shirya su bayan ya raka su sun yi brush sun yi fitsari. Bayan sun kwanta sannan Afaf da Habib su ma suka shirya, Afaf ta zauna a gefen gado ta yi tsuru-tsuru shi ma Habib sai ya hau katifarsa ya kwanta yana zare ido.

    Yana tsaye daga bakin kofa yace ‘Yaya dai Afaf? Ki kwanta mana, ko akwai wata damuwa ne?’ Ta jijjiga kai tace ‘Kawai tunawa na yi da Mommy, ita ma muna bacci ta mutu.’ Ya gaji sosai ga kansa yana sarawa, babu abinda zai iya yi musu na lallashi, ya buɗe baki a gajiye yace ‘In sha Allahu babu abinda zai sami Anti, ku yi addu’a ku kwanta ku yi bacci kawai.’

    Habib shi ma ya tashi zaune yana share ƙwalla ‘Wallahi Abba ni ba zan ma iya baccin ba, Allah ya sa dai kada Anti Khadeejan ma ta mutu ta bar mu. Har yanzu idan na tuna Mommynmu sai na yi kuka.’ Kafin ya yi magana ita ma Afafa ɗin hawaye ya fara bin fuskarta, ta sunkuyar da kai ta sa masa kuka har da shassheƙa.

    Ji ya yi kamar ya ɗora hannu a ka ya sa ihu; ina ma yaran nan za su bar shi ya huta, yanzu ya zai yi da su? Manyan cikinsu da yake ganin su ne ba za su bashi matsala ba su ne suke so su hana shi bacci. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da Afaf ya rungumota yana cewa ‘In sha Allahu babu abinda zai sameta, ku daina kuka ku yi mata addu’a Allah ya ba ta lafiya. Goben nan ma zaku ga an sallamota.’

    Ta fara share hawayenta, Habib wanda shi ma ya taso ya dawo kusa da ita yace ‘Abba to ka kirawo mana ita a waya mu yi mata sannu.’ Ya zaro wayarsa daga aljihu yana cewa ‘To ai da bana son kiranta saboda kar na dame ta don an yi mata allurai, ban sani ba ko har da ta bacci a ciki. Amma bari na kirawo ta sau ɗaya idan ta ɗaga shikenan idan kuma ba ta ɗaga ba sai mu haƙura da safe ma sake kira.’

    Ya lalubo lambarta ya danna mata kira, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta ɗaga. Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Hello.’Yace ‘Hello, Khadeeja ba ki yi bacci ba?’ ‘Na ɗan yi, farkawa dai na yi kuma na ji wayar tana ringing. Ai tun ɗazu aka gama wankin cikin har na ɗan ci abinci.’ ‘Sannu. Wankin cikin ba wahala kenan?’

    ‘Hmmm! Akwai wahala ba kaɗan ba, kawai dai da an gama aka ba wa mutum maguguna sai ya sami relief.’ ‘Sannu. Afaf ce dama ita da Habib wai ba za su iya barci ba sai sun yi miki sannu.’ Ta yi murmushi mai sauti domin ta ji daɗi har cikin ranta, ta tabbatar cewa yaran nan suna ƙaunarta kuma da zai barta da su komai nasu zai zo da sauƙi amma shi komai gani yake kamar za ta cuce su.

    Muryar Afaf ce ta katse ta bayan da Abbanta ya ba ta wayar ‘Anti.’ ‘Na’am Afaf, ya aka yi ba ki yi bacci ba.’ ‘Babu komai Anti, ya jikin naki? Ke ya aka yi ba ki yi baccin ba? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Yanzu zan yi Afaf, kuma na sami lafiya don likitan ma ya ce gobe za a sallame ni.’ Suka ɗan taɓa hira sannan ta yi mata sallama ta miƙawa Habib wayar. Bayan sun gama gaba ɗaya ya karɓi wayar ya katse ya yi mata sai da safe. Ya yi musu sai da safe suka kwanta, har zai kashe fitilar Afaf tace ‘Abba kada ka kashe mana fitilar, in an jima ka zo ka kashe.’

    Haka ya bar musu fitilar ya fice. Can bayan awa ɗaya ya gama abinda yake yana so ya kwanta saboda ya gaji ya zo zai kashe musu fitilar, yana kashewa Afaf da Habib suka haɗa baki a lokaci guda suka ce ‘Abba kada ka kashe fitilar.’ Da mamaki yace ‘Kai! Me kuke ba ku yi barci ba?’

    Afaf tace ‘Abba to ni dai na kasa bacci, da ma za ka taya mu kwana.’ Habib yace ‘Eh wallahi Abba don ni wallahi tsoro nake ji.’ Takaici ya kama shi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka suna zare ido ya je ya kwanta? Wannan wacce irin fitna ce a daren nan ga shi ya gaji.

    Baya son barinsu su kaɗai don haka ya wuce ɗakinsa yaje ya shirya ya rufo gidan sannan ya dawo nan ɗakin; katifar Habib ƙarama ce ya san ba za ta ishe su ba don haka kawai ya gyarawa Nasreen da Shukra kwanciya ya ɗan sami waje a gefen gadon ya kwanta bayan Afaf ta kwanta a ɗaya gefen. Ya yi addu’a ya tofa musu sannan yace kowa ya rufe idonsa kada ya sake jin motsinsu.

    Tunda ya kwanta yake jin wani ɗan ɗoyi haka, idan iska ta busa sai ya ji kamar ɗoyin ya buso cikin ɗaki idan iskar ta wuce kuma sai ya daina ji. A haka bai san lokacin da bacci ya ɗauke shi ba. ‘Subhanallahi!’ ya faɗa bayan ya yi firgigit ya tashi, ya kai hannunsa ya taɓa inda yake kwance daidai ɗuwawunsa ya ji shi a cikin ruwa sosai. Ya ɗaga hannun yana kallo da tsananan mamaki ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.’ Ya sake fada a fili.

    To fitsarin kwance ya yi ko me? Gashi yaran duk sun yi bacci balle yace wani ne ya zuba masa ruwa; tunda shi dai ya san ba ya fitsarin kwance. Motsin Shukra da ya ji a kusa da shi ne ya tabbatar masa da cewa ita ce ta yi fitsarin, ya miƙa hannu ya taɓata ya ji ta a jiƙe amma tana ta baccinta hankali kwance.

    Ya kai hannu zai janye Nasreen daga kusa da ita ya jita itama a jiƙe ‘Tab!’ ya faɗa a fili. Kenan duka su biyun suke fitsarin kwance ko kuwa yau suka fara? Don shi tunda Khadeeja ta tare a gidan nan sau ɗaya ya taɓa ji an ce Shukra ta yi fitsari. Ya kalli Afaf wadda ita tana can ta takure a ƙarshen gadon tana baccinta, ya danna wayarsa ya kalli lokaci ya ga ƙarfe biyun dare.

    Ba zai iya tashin yaran nan ba don haka ya lallaɓa ya sauka daga kan gadon ya fice ya shiga ɗakin Khadeeja ya samo zanin gado ya zo ya rufe su saboda kar sanyi ya dinga kaɗa su ga danshi. Bayan ya gama rufe su ya zo ficewa daga ɗakin ɗoyin da yake ta ji ya sake dukan hancinsa; wannan ɗoyin ai sai ya kumburawa mutum ciki.

    Kamar daga banɗaki ɗoyin yake fitowa don haka ya koma ya buɗe ƙofar banɗakin ya shiga, ya karasa ya leka toilet din ya tarar babu komai a ciki duk da haka dai ya danna flushing ya juya zai fita. A daidai bakin kofa daga jikin bango ya ci karo da fo ɗin Shukra wanda ɗazu Afaf ta cire wandon Shukra mai ɗauke da kashi ta jefa a ciki. Pant ɗin yana nan da kashin a yanda ta ajiye har ya fara bushewa amma duk ya ɗumame bandaki da ɗoyi.

    Ya ɗan ja baya kamar a firgice, to wa Afaf ta ajiyewa wannan kashin? Yanzu ya zai yi da shi ga shi duk ya ɗumame gidan da wari. Ya ɗaga hannuwansa ya zuba a aljihu, danshin da ya ji ya tuna masa cewa wandon a jiƙe yake da fitsrin Shukra ce ko Nasreen shi ma bai sani ba. Ya yi tsaki ya fito daga banɗakin ya wuce ɗakinsa yana tunanin yanda zai yi da kashin, ga shi a jikin pant yake balle ya sa a toilet ya yi flushing.

    Sai da ya yi wanka ya canza kaya sannan ya fito daga ɗakin, yana fitowa ya ji warin kashin nan har parlor ɗin saboda ya bar kofar a buɗe. A fusace ya wuce kitchen ya ɗauko ƙatuwar baƙar leda ya zo ya ɗauki fo ɗin ya ƙulle a ledar, ya sake ɗauko wata ledar ya ƙara ƙullewa sannan ya ɗauki mukulli ya buɗe ƙofa ya fice ya jefa a shara; gari yana wayewa zai sami yaro ya fitar masa da sharar.

    Ya san dai Shukra ta iya hawa toilet yanzu, duk da idan ta so rigima sai tace sai ta hau fo amma shi dai ya zubar don ba zai iya wankin kashi ba kuma ba zai iya bari Afaf ta yi ba ta zo ta yi musu jagwalgwalo da kashi. Yana dawowa cikin parlor ɗin ya kalli agogon bango ya ga ƙarfe uku har ta wuce, abinda ya yi masa saura bai fi awa ɗaya da rabi ba a yi assalatu.

    Sai a lokacin ya tuna ba shi ma da abincin sahur, ga shi kuma ko a lokacin ma yunwa yake ji balle yace zai yi ɗore. Kai tsaye ya wuce kitchen ya ɗora indomie sannan ya tafasa ruwan shayi; nan da nan ya juye indomie ɗin a plate ya ɗumama stew ya zuba sannan ya haɗa shayi, ya kwaso ya dawo dining table ya fara ci.

    Tun kafin ya haɗiye lomar farko ya fara jiyo hayaniyar Shukra a ɗakinsu, yana zuba loma ta biyu ta buɗo ƙofar ɗakin ta fito tana kuka tana ‘Antiiii..’ Ya ajiye cokalin yace ‘Menene Shukra?’ ‘Shayi zan sha Abba’ Har cikin zuciyarsa takaicinta ya kama shi, to amma ya zai yi da ita? Haka ya kirawo ta ya zaunar da ita a kan kujera, tun kafin ya gama gyara mata zamanta zarni ya cika masa hanci; sannan ma ya tuna ta yi fitsarin kwance.

    Ya gyara mata zama yace ‘Bari na gama sahur sai na haɗa miki shayin.’ Ya ɗauki cokali ya zuba loma a bakinsa yayin da ita kuma ta fara mutssike ido tana kuka. ‘Menene kuma?’ ya tambayeta ‘Yunwa nake ji, shaaayiii.’ Ya duba agogon wayarsa, saura bai fi minti goma sha biyar ba a yi assalatu ga shi ba ya jin zai kai azumin nan idan bai yi sahur ba, ya kalle ta yanda take ta kuka kamar wadad aka ciza.

    Bai taba jin haushin Shukra kamar yau ba, amma babu yanda zai yi. Haka ya juye mata rabin shayin da ya haɗa zai sha ya saka mata madara da milo ya miƙa mata sannan ya cigaba da cin abincin. Yana yi yana kallon lokaci saboda kar a kirawo assalatu. Haka ya ci abincin nan ya yi sauri ya kwankwaɗe shayinsa rabin kofi sannan ya ɗora da ruwan sanyi duk a lokaci guda.

    Yana ajiye kofin aka fara kiran assalatu, ya kwantar da kansa a jikin kujerar yana mayar da numfashi. Shukra da take kan kujera tana gyangyaɗi bayan ta shanye shayinta ta taɓo shi tana cewa ‘Abba kashi zan yi.’ A ɗan zabure ya dube ta yace ‘Kashi Shukra?’ Cikin halin ko in kula tana murje idonta tace ‘Um.’ Ta fara ƙoƙarin sauka daga kujerar da take zaune.

    Ya jijjiga kai cike da takaici; su wai yara ba a hutawa da hidimarsu ne? Tunda ya dawo daga asibiti ake abu ɗaya ga shi duk yana neman fita daga hayyacinsa amma babu alamar sauƙi. So yake ma ya sami natsuwa ya turawa Khadeeja message ta whatsapp ya ga ko tana online amma ba su ba shi time ba, a halin yanzu ma kansa ciwo yake ga bacci duk kansa ya cushe bai ma san ta ina zai fara ba.

    Haka ya bi bayanta har banɗaki, Allah ya taimake shi ba ta ma nemi fo ba ya taimaka mata ta hau toilet ta yi kashinta. Yana zaune a gefen gadonsu ya jiyo ta daga banɗakin tana cewa ‘Abba na gama. Gaban shi ya faɗi da ya tuna wai shi take sa rai ya yi mata tsarki; ya juya ya kalli Afaf wadda take baccinta hankali kwance.

    Ya san idan ya tashe ta za ta yi mata tsarkin to amma fa ita ma bata kwanta da wuri ba. Ya jijjiga kai ya mike bayan da ta sake maimaita masa ta gama a karo na uku. Haka ya tashi ya shiga banɗakin ya wanke mata kashin ya wanko hannunsa ya fito ya canza mata kaya ya mayar da ita ya kwantar da ita a kusa da Habib saboda katifar kan gadon ta jiƙe; zuwa lokacin masallatai duk sun riga sun tayar da sallah.

    Yana fitowa daga ɗakin yayi alwala ya ta-da sallah a ɗakinsa, yana zaune a kan dadduma yana azkar Nasreen ta turo ƙofa ta shigo ɗakin, ta ƙaraso ta faɗa jikinsa tana cewa ‘Abba na tashi, ba ka dawo mana da Anti Khadeeja ba?’ ‘Eh, sai an jima.’ Ya faɗa yana ture ta. ‘Ki je ki ce Ant….’ Sai kuma ya tuna Antin ba ta nan don haka ya gyara zance yana ƙoƙarin miƙewa ‘Mu je na wanke miki jiki ki canza kaya sai ki yi sallah.”

    ‘Abba ni yunwa nake ji.’ Ya ɓata rai yace ‘Sai an canza kaya kuma kin yi sallah.’ Haka ya yi ta fama da yaran nan, ga shi ita Afaf ma fushi take da shi saboda bai tashe ta sahur ba tunda Anti tana tashinta tana yin azuminta. Sai wajen ƙarfe takwas na safe sannan ya tashi ya koma ya roƙo Baban Ummi ta shigo ta karɓi yaran don yana son ya tafi asibiti wajen Khadeeja. Yana shiga ɗakinsa ya zauna a gefen gado ya danna mata kira.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Ke Haddasa Rashin Zuwan Al’ada (AMENORRHEA)

    Abubuwan Da Ke Haddasa Rashin Zuwan Al’ada (AMENORRHEA)

    Idan al’ada tana daɗewa ba ta zo ba sai bayan watanni 3 zuwa 6, wannan shi likitoci suke kira “amenorrhea”. A gaskiya wannan yanayin bai kamata a ce mace tana fama da shi ba. Idan kuma ya auku, to, yana nufin cewa mace tana da matsala kenan.

    Amenorrhea ya kasu gida biyu kamar haka:

    1. Primary amenorrhea: Wannan yana nufin daɗewa na farko ko kuma daɗewa na asali wanda al’ada take yi ba ta zo ma mace ba. Abinda yasa ake kiransa daɗewa na farko ko na asali shi ne yana faruwa ne ga mace budurwa wacce ba ta taɓa yin al’ada ba a rayuwarta, sai ya kasance ta kai munzalin da ya kamata a ce ta fara al’adar, to, amma sai ba ta zo mata ba.

    Mafi yawanci budurwa tana fara al’ada ne tsakanin shekaru 9 zuwa 13. Don haka idan budurwa ta kai shekaru 16 zuwa 18 ba ta fara al’ada ba, to, wannan shi ne primary amenorrhea.

    2. Secondary amenorrhea: Shi kuma wannan yana nufin daɗewar da al’ada take yi ba ta zo ba har na tsawon watanni 3 zuwa 6 ga babbar mace, watau ba budurwa ba.

    Da primary amenorrhea da secondary amenorrhea suna faruwa ne saboda dalilai masu yawa, waɗanda suka haɗa da:

    1. Yanayin da Allah ya halicci tsarin jiki kamar ɗaukar ciki, shayarwa, nisan shekaru (menopause) da sauransu. Idan mace tana cikin ɗaya daga cikin waɗannan yanayin, to, za ta fuskanci ɗaukewar al’ada.

    2. Shaye-shayen magunguna kamar na family planning ko kuma domin warkar da wata cuta da take damun mace.

    3. Lahani wanda ya sami tsarin jikin mace na haihuwa (reproductive system defects) kamar jakar da take ɗauke da ƙwaya-ƙwayan haihuwa (ovary) ko mahaifa (uterus) idan suka sami matsala.

    4. Rashin daidaiton zubar sinadarai a cikin jiki (hormonal imbalance).

    5. Yin ayyuka na wahala.

    6. Damuwa (stress).

    7. Kasancewar mace ta zamo mai tsananin ƙiba ko tsananin sirantaka.

    Hanyar kaɗai da za a iya magance amenorrhea ita ce idan aka tuntuɓi likita ya yi bincike mai zurfi domin gano wasu daga cikin dalilan da suke haifar da shi, daga nan sai a bayar da maganin da ya dace.
    Karanta Yadda Tsiron Mahaifa Yake

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Haƙuri

    Amfanin Haƙuri

    Haƙuri: Shi ne danne zuciya a kan wani abu mara kyau, wanda ya baƙantawa mutum zuciya.

    Haƙuri yana da matuƙar amfani ga mutane, kamar yadda ya zo a cikin littafin Sheikh Abdulrahim bin Ahmad Alkadhi mai suna “Daƙa’ikul khabar” shafi na 17 babi na goma sha biyu yace, labari ya gangaro cewa wanda aka jarabce shi da wata masifa, sai ya yaga tufafin sa ko ya bugi ƙirjin sa (to hukuncin wanda ya aikata haka) kamar (wanda) ya riƙi makami ne zai yi yaƙi da Allah (Subhanahu wata’ala).

    Sannan kuma an ruwaito daga Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace wanda ya ɓalle ƙofa ko ya yaga tufafin sa ya yi da wata masifa ta same shi ko ya bugu wajan zaman sa ko ya sare bishiya ko ya yanke gashin kan sa (saboda tsanani masifar da ta same shi), to za a gina masa gida na wuta a kan kowane gashi (wanda ya cire), sa’annan kuma Allah ba zai karɓi aikin sa na farilla ba ko na nafila matuƙar yana kan wannan hali.

    Har ila yau, Allah zai ƙuntata ƙabarinsa, kuma zai tsananta yi masa hisabi, sannan kuma dukkanin mala’ikun da suke sama da ƙasa za su dunga tsine masa, haka kuma za a rubutawa laifuffuka guda dubu a gare shi, sannan zai tashi a cikin ƙabarin sa tsirara.

    Haka kuma, wanda ya karya gefan jikin sa, saboda wata masifa, to Allah zai karya addinin sa, idan kuma ya bugi ko ya mari kumatun sa ko ya azabtar da fuskar sa, to Allah (Subhanahu wata’ala) ba zai kalle shi ba da rahmar sa ba ranar alƙiyama.

    Bugu da ƙari, kuma ya zo a cikin shafi na 18, babi na goma sha huɗu a cikin wannan littafin yace Sayyadina Aliyu bin Abu-ɗalib (karramallahu wajhahu) yace “haƙuri ana yin sa ne ta hanyoyin guda uku; na farko yin haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, na biyu yin haƙuri a kan saɓawa Allah, na uku haƙuri a kan wata masifa wacce ta samu mutum.

    Saboda haka, duk wanda ya yi haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari, sa’annan kuma ko wace daraja yawanta ta kai tsakanin sama da ƙasa.

    Wanda kuma ya yi haƙuri a kan saɓawa Allah, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari shida ranar lahira, haka kuma kowace dajara yawan ta ta kai faɗin sama da ƙasa, wanda kuma ya yi haƙuri a kan wata masifa wacce ta same shi, to Allah zai ba shi lada ba tare yi masa hisabi ba (ranar lahira).

    Karanta Tarihin Farfesa Abdallah Uba Adamu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Ko da gari ya waye Khadeeja ba ta ma san lokacin da Ummi ta zo ba don tun daga bakin gate ya tare ta yace ta koma kada ta sake zuwa sai bayan Sallah. Sai wajen sha ɗaya sannan ta fito ta ɗan gayggyara gidan, wanke-wanke ne ma ya ɓata mata lokaci don yana da yawa sosai. Haka ta wanke su gaba ɗaya a famfon waje sai da shigo kifewa sannan Afaf ta taya ta.

    Tana gamawa ta shige ɗakinta ta kwanta; ba ta taɓa jin gajiya irin wannan ba a rayuwarta, ga shi duk wata gaɓa da take jikinta ciwo take yi. Tun 3pm ta shiga kitchen ta fara ƙoƙarin haɗa kayan shan ruwa; dankali da ƙwai za ta soya sai jollof sphagetti sannan ga peppersoup ɗin nama. Da akwai ragowar zoɓo na jiya don haka ba za ta sake haɗa wani ba.

    Yaran suna zaune a parlor ta zo ta wuce ta shiga kitchen, tana wucewa Afaf ta bi bayanta. Ta so ta koro Afaf ɗin daga kitchen amma dai ta haƙura ta bar ta, suna yin aikin. Ba su daɗe da farawa ba Habib ya shigo kitchen ɗin, ya kalli dankalin da aka ajiye a tsakiyar kitchen ɗin yace ‘Anti wannan ferayewa za a yi?’

    Tace ‘Eh, so nake na ɗora kifin nan sai na zauna na feraye shi.’ ‘Kawo wuƙa na feraye Anti.’ Ya faɗa yana buɗe cabinet, ya zaro roba ya tara ya ɗebu ruwa. Tace ‘Ka bar shi Habib zan feraye. Ya sa hannu ya ɗauki wuƙa a kan sink yana cewa ‘Na iya feraye dankali fa Anti, idan na feraye miki sai ki yanka.’

    Bai saurari amsarta ba ya tsuguna ya fara feraye dankalin. Afaf ta ajiye kayan miyan da ta gama wankewa a kusa da Khadeejan tace ‘Anti na wanke kayan miyan.’ ‘To ki yanka mana albasar nan, rabi slicing za ki yi rabi kuma ki yanka ƙanana sai a saka a soup da fried egg.’ Ta ɗauki albasar ta wanke ta zuba a chopping board ta fara yankawa.

    Ba su ji lokacin da Mustapha ya ƙaraso bakin ƙofar kitchen ɗin ba; a dai-dai lokacin nan wuƙar da Afaf take yanka albasa ta goce ta yanke mata hannu. Ta dire albasar ta make murya tana cewa ‘Waiyo Anti na yake.’ Da sauri ta saki abinda yake hannunta ta nufi wajen Afaf ɗin tana murmushi cike da kulawa tana cewa ‘Sorry, garin yaya Afaf. Ki…’Da sauri ya ƙarasa ya kama hannun Afaf ɗin yana cewa ‘Garin Yaya kika yanke, me ya sa kika dauki wuka?’

    Ya juya ya dubi Khadijan yana cewa ‘Na gaya miki sai kin san aikin da za ki dinga sa yaran nan amma ke gani kike kamar kawai bana son su taya ki aiki ne. Yaushe Afaf za ta iya wani yanka albasa.’ Afaf ta zare hannunta daga nashi hannun ta juya ta wanke a sink, ta dube shi tace ‘Ya ma daina jinin Abba bari na je na daure.’

    Yana juyawa ya dubi Habib wanda yake ta ferayar dankali ya daka masa tsawa ‘Ka ajiye wuƙar nan ka tashi, namiji da kai kana wani feraye dankali. Tashi ka ba ni waje.’ Ya juya kan Khadeeja wadda ta riga ta cigaba da aikinta kamar ba da ita yake magana ba, yace ‘Na gaya miki ki daina sa yaran nan aikin da ya fi ƙarfinsu, bana so. Shi Habib ma da yake namiji me ya haɗa shi da wani harkar girki? Bana so.’

    Bai ga alamar za ta ba shi amsa ba don haka ya juya shi ma ya fice suka barta ita kaɗai a kitchen ɗin. Ta rasa me ma za ta yi, ta goge fuskarta ta cigaba da aikinta. Haka ta lallaɓa ta gama komai, zuwa magriba ta zubawa kowa aka sha ruwa. Ta gaji iya gajiya don haka ba ta ma da kuzarin da zata iya wani musu da shi, ta dai riga ta gama yanke wa kanta hukunci da zarar an buɗe gari za ta tafi gidansu ba za ta dawo ba sai ta haihu ko kuma ya ɗauki mai aiki.

    A haka aka cigaba da azumi, kullum cikin wannan yanayin Khadeeja take haɗawa da hidimar gidan da ta yaran ta yi ta fama. Kullum sai ta yi wa Shukra da Nasreen wanka, tsarkin kashi tsarkin fitsari duk ita take musu. Duk wata fitinarsu ita ce me kulawa. Ga shi tana fama da Shukra wadda sai yanzu ne da suka kwana biyu ta fara hana ta kashin wando.

    Yanzu idan dai ba wasa take yi ba ba ta kashin wandon ta iya zuwa ta gayawa Anti za ta yi kashi. Amma idan tana wasa haka za ta tsuguna a wajen wasan sai ta gama kashinta sai dai a ji wari. Haka dai take ta fama.

    Juma’a ce yau ɗin, gaba ɗaya a jigace take jin ta saboda azumi na sha ɗaya kenan za a kai kuma kullum ita kaɗai take hidimar gidan da ta yara. Gashi kuma ta ƙi ta ajiye azumin saboda ko ba ta yi azumin ba ma ba iya cin abincin kirki take ba. Haka dai ta tashi jikinta duk babu ƙwari, ta ɗan yi iya abinda za ta iya ta koma ta kwanta.Tun wajen 2pm ta taso ta fara aikin abincin shan ruwa don tana so ta gama da wuri, tunda zuwa yanzu yaran ma sun hakura sun daina yunkurin tayata.

    Sai dai ita ɗin ma ta rage aiyukan da yawa don duk abinda ta kasa rabuwa take da shi. Dankali da ƙwai kawai ta soya ta dafa shinkafa ta ɗumama ragowar stew ta juye a flask, ta kawo ruwan shayi ta zuba a flask. Saura wajen rabin awa a sha ruwa ta gama ta kawo komai ta jera, ta wuce ɗaki ta kwanta bayan ta gayawa Afaf ta kula kada kannenta su yi ɓarna.

    Ba ta yi minti goma da kwanciya ba Nasreen ta shigo ɗakin da gudu tana taɓa ta tana cewa ‘Anti Shukra ta yi kashi, Abba ya ce ki zo ki wanke mata.’ Ta tashi zaune tace ‘A toilet ɗinku ta yi kashin?’ ‘A wandonta ta yi Anti.’ ‘Je ki ina zuwa.’ Ta ja tsaki ta koma ta kwanta bayan Nasreen ta fice daga ɗakin. Jiri take ji sannan a wani ce ta zo ta wanke kashi, kashin da tace a daina yi mata a wando.

    Ta yi zaton ma a toilet ta yi kashin ta je ta yi mata tsarki. Kafin ta gama yanke hukuncin da za ta ɗauka Abbansu ya shigo, bayan ta amsa sallamarsa yace ‘Ki zo ki wankewa Shukra ta yi kashi.’ Ta dafe kanta ta tashi tana cewa ‘Ba lallai na iya ba ne don wallahi jiri nake ji gashi yau tun safe marata take ciwo.’

    ‘To na ce ki ajiye azumin kin ƙi, ki bar shi haka ki huta. Ki taso ki gyara mata alwala zan je na yi an kusa kiran sallah.’ Ta miƙe a hankali ta biyo bayansa suka fito daga ɗakin. Tana shigowa parlor ɗin Shukra ta sunkuyar da kai, ta harare ta tace ‘Kin sani ai mara kunya, nace ki daina yin kashi a wando amma kin ƙi ko? Yau gidansu ƙyanƙyaso za ki kwana a can ake kashi wando.’

    ‘Don Allah ki yi mata a hankali, komai lokaci ne ai za ta daina ne a yi mata haƙuri.’ Ya faɗa yana shirin komawa ɗakin ya yiwo alwala. Ta tsuguna za ta ɗauke ta ta ji kanta ya biyo ta kamar zai faɗo, ta dafe goshi ta koma ta tsaye tace ‘Kai! Ba zan iya ba fa.’ Ya juyo ya tsaya ‘Menene?’

    ‘Ba zan iya tsugunawa ba fa, jiri kwasa ta yake.’ ta ƙarasa kan kujera ta zauna ta dafe goshi. Ta dubi Afaf tace ‘Ba ni ruwa na sha Afaf, ga kiran Sallah nan an fara. ’Nan da nan ta cika Kofi da ruwa ta miƙa mata, ta sha kaɗan ta jingine kanta tana riƙe da ruwan. Kukan Yusra ne ya katse su tana cewa ‘Anti na daina ba zan kuma ba, mantawa na yi daman.’

    Ta yunkura za ta miƙe Afaf ta yi sauri ta dafe ta. Abbansu ya dubi Khadija yace ‘Don Allah ki lallaɓa ki wanke mata kashin nan, Wannan wane irin abu ne? Yanzu wa kike so ya wanke mata kashin?’ Afaf ta aika Nasreen ta ɗauko fo a toilet ta cire wandon da yake cike da kashi ta jefe a fo ɗin sannan ta ɗauke Shukran ta nufi banɗaki. Ta wanke mata sannan ta dawo ta gyara wajen, zuwa lokacin Abbansu ya fito daga alwala.

    Ya zauna ya sha ruwa sannan ya miƙe zai tafi masallaci. A daidai lokacin ita ma Khadeeja ta ɗago kanta tace ‘A dawo lafiya.’ Yana jin ta ya yi banza da ita saboda yanda yake jin haushinta, kuma tabbas sai ya kora mata bayani in an sha ruwa. Daga yau ma ba za ta sake yin azumin ba tunda dama mai ciki tana da damar ajiyewa. Ta miƙe tana gatsina fuska, kawai sai gani ya yi ta sulale za ta faɗi.

    Ya zabura zai tare ta ya yi fatali da casserole ɗin dankali, a lokaci guda Habib ya saki jug ɗin zobon da ya fito da shi daga kitchen ya tarwatse a wajen ya ƙarasa kanta. Duka su biyun kafin su ƙaraso ta zube. Abbansu ya ɗago kanta yana jijjigawa ‘Khadeeja, Khadeeja, Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun, Khadeeja.’ Ko motsawa ba ta yi.

    Ya sunkuce ta ya kwantar da ita a kan three seater, ya ƙara gudun fanka sannan ya kunna AC. Ya cire mata ɗankwalin da yake kanta ya fara yi mata fifita. Yaran gaba ɗaya suka jeru a kanta suka yi tsuru-tsuru; Afaf ta leƙa fuskarta ta kafaɗar Abbansu tace ‘Abban ita ma mutuwa za ta yi ta bar mu ko?’

    ‘Ke bana son rashin hankali, ba mutuwa za ta yi ba.’ A take yaran suka saka masa kuka mai ban tausayi. Afaf ta rungume Nasreen da Shukra suka haɗa kai suna kuka. Habib ya taɓa shi yace ‘Abba ka kai ta asibiti kada ta mutu ta bar mu.’ ‘Kai rufe mana baki.’ Gaba ɗaya shi ma ya ruɗe, jikinsa har rawa yake yi. Ya janyo jug ɗin ruwan sanyi ya jiƙa hannunsa ya shafa mata a fuska. Ta ja numfashi ta buɗe idonta, sai kuma ta mayar ta rufe.’Khadeeja.’

    Ya kirawo sunanta da ƙarfi yana jijjiga ta. Da gudu su Afaf suka ƙarasa kanta suna kira ‘Anti, Anti.’ ‘Khadeeja.’ Ya kara kiran sunanta a firgice. Ta buɗe ido ta sake rufewa. Ya miƙe tsaye ya ɗan tura yaran yana cewa ‘Ku zauna na ɗauko mukullin mota, asibiti zan kai ta yanzu, babu abinda zai same ta in sha Allahu.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗauko mukulli ya fito, ya je ya buɗe kofar motar ya dawo ya ɗauke ta bayan ya yafa mata mayafi ya wuce yaran suna biye da shi ya kwantar da ita a bayan motar. Bayan ya rufe ƙofar motar ya juyo ya kalli yaran yana tunani; to yanzu ya zai yi da su? Wa zai bar wa su? Ya san shi kansa ma sai ya amsa tambayoyi a checkpoints ga shi ma’aikatan asibitin ma kamar tsoron mutane suke balle ya kwashi yara su tafi.

    Ya shafa kai sannan ya sake kallonsu cike da damuwa; da a ce gari a buɗe yake da sai ya wuce da su ya ajiyesu gidan Hajiya to amma ya san ba zai yiwu don zai yi ta ɓata lokaci a checkpoint. A take dabara ta faɗo masa. ‘Ku tsaya a nan ina zuwa.’ Ya ba su umarni sannan ya fice daga gidan ya turo gate ɗin.

    Yana fitowa ya ƙarasa gidan su Ummi, ya yi sa’a yana tsayawa maigidan yana dawowa daga masallaci. Bayan sun gaisa ya sanar da shi so yake Ummi ta zo ta zauna masa da yara ya je ya kai Khadeeja asibiti. Ya janjanta masa sannan ya shige gidan ya turo masa Ummin. Haka ya sako ta a gaba ya dawo gidan ya bar mata yaran ya ja motar ya nufi Aminu Kano Teaching Hospital da ke Kano.

    Yana zuwa asibitin aka nuna masa gynae emergency inda nan ne ake karɓar masu ciki waɗanda suke buƙatar taimako na gaggawa, nan da nan suka karɓe ta aka fara duba ta; duk da dai su kansu ma’aikatan za ka gane cewa suna cikin yanayi na tsoro saboda Covid19. A nan wajen aka nuna masa benchi ya zauna yayin da ita kuma aka tura ta a kan gadon marasa lafiya aka shige da itaɗdakin bincike.

    Tana kwance a kan gadon yayin da take amsa tambayoyin ma’aikaciyar jinya sai wata ma’aikaciyar wadda ta ji suna kira matron ta shigo, ma’aiakaciyar ta juya tana kallon matron tana cewa ‘Matron wannan fa sai an yi mata scaning, cikin nan na jikinta kamar ficewa zai yi duk da dai tace ba ta fara bleeding ba amma dai tana jin alamunsa.’

    Matron ɗin ta ƙaraso ta tsaya a kanta, tace ‘Ah! Wannan ai Khadeeja ce, wa ya kawo ta?’Jin an ambaci sunanta ya sa ta buɗe idonta a hankali, ta yi murmushi a gajiye lokacin da suka haɗa ido ta gane wadda ta ambaci sunan nata. Cikin sanyin murya tace ‘Anti Iyami.’ ‘Na’am, Khadeeja. Wa ya kawo ki?’ ‘Mustapha ne.’

    Ta juya ta kalli abokiyar aikin nata tace ‘’Yata ce ai, ita ce wadda muka yi biki kwanaki fa yarinyar Habiba wadda nace miki childhood friend ɗina ce.’ Da fara’a tace ‘Aaah! Allah sarki, to abun ya zo kenan haihuwa yaƙin mata.’ ‘Ai kuwa. Bari na kirawo Dr. Jamil ya zo ya duba min ita sai mu je na kai ta scanning ɗin mu ga ko za a iya sallamarta a daren nan.’

    Har ta juya za ta fice Khadeeja ta riƙo hannunta, ta juyo tana cewa ‘Akwai wani abu ne Khadeeja?’ Ta yi murmushin yaƙe ta goge ƙwallar da ta gangaro daga gefen idonta tace ‘Kada ki sallame ni Anti Iyami, ki yi wa Mommy waya ta zo ta ɗauke ni gida zan tafi.’ Ta ɗan ranƙwafo tana shafa kanta tana duban fuskarta tace ‘Ok, kada ki damu, ki samu ki huta tukunna likita ya duba ki. In sha Allahu yanzu zan kirawo ta ko ba ta zo ba da safe idan na tashi daga aiki sai na tafi da ke gidan Mommy ɗin. Kada ki damu.’

    Ta juya ta fice yayin da Khadijan ta mayar da idonta ta rufe. Tare da likitan suka dawo, bayan ya duba Khadeeja aka je aka yiwo scanning tare da Mustaphan aka dawo. Bayan likita ya duba scanning ɗin yace cikin jikinta ya lalace fita zai yi, don haka za a yi mata wankin ciki sannan akwai allurai da ruwa da za a saka mata.

    Da kansa ya je ya siyo komai ya kawo sannan suka koma wajen Khadeeja tare da matron; a nan Khadeejan take sanar da shi cewa martron kawar Mommy ce. Ya sake gaisheta cike da girmamawa, bayan ta amsa ta dubi Khadeejan tace ‘Likita ya ce cikin jikinki ya lalace don haka za a yi miki wankin ciki, ga magunguna kuma ya rubuta miki sannan ga drip idan an gama wankin cikin zan saka miki kin ga yau a nan zamu kwana da ni da ke.’

    Ta yi murmushin yake, ta dubi Mustapha tace ‘Ka tafi, ka bar yara a gida. Anti Iyami za ta kirawo ka  idan akwai wani abu tunda ka ga tare zamu kwana ma, zuwa da safe za mu yi waya in sha Allah. Matron ta fice ta ba su waje. Bayan ta fice ya matsa kan Khadeejan yana shafa fuskarta yace ‘Sannu, kin ba ni tsoro fa.’

    Ta yi murmushi.Ya cigaba ‘Kafin safiyar ta yi sai ki samu ki yi min message ɗin duk abinda kike so na taho miki da shi, idan kuma Allah ya sa da safen za su sallame ki ma shikenan sai kawai na zo mu tafi. Na yi maganar abinci ma Anti Iyami tace na bari za ta kawo miki, but in ana son wani abu kiyi min magana sai na saka miki kuɗi a account ɗinki ko transfer ne sai ki yi musu.’

    Ya sa hannu a aljihunsa ya zaro wayarta ya miƙa mata yana cewa ‘Ga wayarki, ba zan kirawo ki ba don kada na dame ki ko na tashe daga bacci, but please da kin farka ki kirawo ni.’ Ta karɓa tana murmushi tana cewa ‘Ok, ka gaishe min da su Yaya Afaf.’ Ya fice ya bar ta a kwance. Yana fitowa ya sami Anti Iyami da abokan aikinta a station ɗinsu, ya yi mata sallama bayan ta ƙarbi lambar wayarsa sannan ya wuce.

    Tun a daren Anti Iyami ta kirawo Mommy ta sanar da ita halin da ake ciki, sai dai ba ta gaya mata cewa Khadeejan tace gida zata taho ba. Ta dai sanar da ita cewa tana hannunta idan akwai wani abu za su ji zuwa wayewar gari. Tana tsaye aka yi wa Khadeeja wankin ciki sannan aka ba ta ɗaki, ta saka mata drip da alluranta sannan ta haɗa mata shayi mai kauri.

    Ta sakata a gaba bayan ta shanye sannan ta zuba mata shayi da kwai ta cinye sannan ta ajiye mata saucer da kankana da lemon ɓawo tace ta shanye kafin a jima. Ta sha tambayoyi a wajen Anti Iyami wadda take ƙoƙarin gane dalilin da yasa Khadeejan take son tafiya gida; sai dai ba ta sami komai ba don da a tunaninta ko Mustaphan yana abusing ɗinta ne. Ita kuma ta sanar da ita kawai ba ta da lafiya ne sannan kuma ga aikin gida da raino wanda ya yi mata yawa shi yasa take son ta je gida ta huta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu