Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Mijin Marigayiya Babi Na Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Biyu

    Kamar yanda aka yi alƙawari ranar Asabar 18th February, 2020 waliyyan Mustapha suka sami  karɓa ta girmamawa a gidan kakan Khadija. Bayan sun gaisa an musu maraba suka gabatar da  sadaki N100,000 da kuma kuɗin aure N50,000. Baba Sani ƙanin mahaifin Khadija ya sa hannu ya karɓi kuɗin ya matsa ya ajiyesu a gaban mahaifinsu Alhaji Baba. Cike da fara’a da murmushi Alhaji yace ‘Ma sha Allah, Allah ya sa albarka Allah ya nuna mana.’

    Gaba ɗaya mutanen da ke wajen suka amsa da Amin. Baba Safiyanu wanda Yaya ne a wajen mahaifin Khadija ya yi gyaran murya yace ‘Alhaji ni ina ga tunda ga sadaki an kawo kuma ga waliyyan ango ai sai kawai a ɗaura auren nan yanzu. Yanda  abubuwa suke tafiya rufe garin nan fa za ayi, tunda ka ga ƙasashen duniya suna ta rufewa fa.  COVID 19 ɗin nan ana maganar ta shigo ƙasar nan sosai, ko da wanne lokaci za a iya shiga lockdown.’

    Alhaji yace ‘Ikon Allah, kace abun ya zo mana kenan. To Allah ya tsare mu da zuri’ar mu.’ Ya dubi  waliyyan Mustapha yace ‘To idan a shirye kuke sai a ɗaura auren ai, nan da sati mata sai su yi bikinsu su kai amarya kafin a ce an kulle ƙasar.’

    Cike da murna Alhaji Muhammad wanda shi ne Babba a waliyyan ango yace ‘Ah ai mu a shirye muke, hakan ai ya fi sauƙi Alhaji, Alhamdulillah Alhamdulillah. Shi Mustapha ai a shirye yake, lefe  ma da sauran kaya duk gobe sai mata su zo su kawo.’

    Nan da nan suka gyara zama, Baba Sani ya kirawo mahaifin Khadija ya sanar da shi wanda shi ma a take ya amince, sannan ya kirawo maƙota da wasu daga cikin dangi. Su ma ‘yan uwan Mustapha suka sanar da shi ya taho shi da abokansa mutum biyu. Kafin minti talatin guest room ɗin Alhaji ya cika da mutane ana ta murna. Ba tare da ɓata lokaci ba aka ɗaura auren Khadija da Mustapha.

    Tana kwance a parlor ɗinsu a kan doguwar kujera tana chatting a waya yayin da ƙanwarta Nabila take zaune tana kallon TV; ƙaninsu Ahmad ya shigo parlor ɗin da gudu yana ihu ‘Ta zama matar aure, Ya Khadija ta zama matar aure…’ Zumbur ta miƙe daga kujerar yayin da ita ma Nabila ta miƙe tana cewa ‘Kai fa kana da matsala, don Allah ji yanda ka firgita ni.’

    Khadija tace ‘Wai me kake cewa ne?’ Yana dariya yace ‘Wallahi an ɗaura miki aure da Mustapha yanzu a gidan Alhaji.’ Ta buɗe baki tana kallonsa cike da tsananin mamaki. Nusaiba ta daki kafadarsa tace ‘Kai Ahmad  ka ji tsoron Allah.’ Yace ‘Wallahi da gaske nake, kirawo Baffa a waya ki tambaye shi.’

    A take Mommy ta fito daga ɗaki riƙe da waya jiki a sanyaye, Ahmad ya kalle ta yace ‘Mommy ai an ɗaura auren Yaya Khadija ko?’ Ta ɗaga kai tana cewa ‘Eh, yanzu Baffanku yake gaya min an ɗaura auren.’ a juya ta dubi Khadija  tace ‘Khadija kin zama matar aure.’

    Ta faɗa kan kujera kamar wadda aka tura, to murna za ta yi ko me? Bata taɓa zata za a ɗaura aure yau ba, ta zata za a yi yanda aka saba; a kawo kuɗin aure a zo a sa rana sannan a shirya biki a nutse. Shikenan yanzu ta zama matar Mustapha? Ikon Allah. Ta kai hannu ta shafa kwarmin idonta inda ta ji danshi; ƙwalla ce ta faɗo. To kukan me take yi?  Murna take yi ko kuwa tsabar mamaki ne?

    Nabila ta zauna ta doro hannunta a kafaɗarta tana kallon Mommy tana cewa ‘To Mommy sai mu fara shirin bikin kenan ko kai ta kawai za a yi haka?’ Ta banka mata harara tana cewa ‘Sai kace wata kaza?’ Mommy tace ‘Uhm, sai dai mu jira Baffanku ya dawo mu ji.’ Ta koma daki ta bar su a nan.

    Gaba ɗaya tunanin Khadija ya tsaya, wannan ɗaura auren da aka ce an yi mata yana nufin nan  da ‘yan kwanakin za ta tare a gidan Mustapha. Fatanta ɗaya Daddy ya bari a yi biki don gaskiya tana son biki. Ƙarar wayarta ne ya katse mata tunani, tana kallon wayar ta yi murmushi “My love” shi ne sunan da ta yi saving lambar Mustapha da shi.

    ‘Hello.’ ta amsa murya ƙasa-ƙasa. Muryarsa zaƙwai cike da farin ciki yace ‘Ya na ji ki haka? Ko ba kya farin ciki ne? Alhaji ya hutar da mu, kin ga next weekend kawai sai a kawo min amarya ta.’ Ta yi dariya ‘I was just not expecting it to happen today, but Alhamdulillah. Ai babu abinda ya fi zama da masoyi daɗi.’

    ‘Haka ne. So me kike buƙata na bikin, ki sami Yaya Mama ku yi lissafi zuwa an jima sai ki gaya min na turo miki ta account ɗinki. In sha Allah ranar Tuesday za a kawo lefe.’ ‘Ok, hakan ya yi.’ ‘Common, ni ina so na ji muryarki ta yi zaƙi zaƙwai kamar tawan nan.’

    Tayi dariya ‘Ka kirawo ni in an jima kafin nan na sha zuma za ka ji zaƙin da muryar za ta yi.’ Suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta a kan gadon cikin sanyin jiki. Dab da azahar Yaya Mama ta ƙaraso tare da yaranta Anisa da Jawad. Ita ce Babba a ‘ya’yan  gidan su Khadija. Bayan ta gama tsokanar Khadija ta shige ɗaki inda ta tarar da Mommy tare da  ƙanwarta Anti Naja’atu suna ta tattauna bikin; don Baffa ya sanar da su a shirya a yi biki ranar Asabar da Lahadi idan an gama sai a kai amarya.

    Bayan ta gaishesu ta zauna suka cigaba da tattaunawa a kan bikin. Jimawa kaɗan Yaya Mama tace ‘Ni wallahi Mommy tausayi ma Khadija take ba ni, Allah ya sa dai da gaske yake sonta kuma ya cigaba da kula da ita. Ga yara har huɗu yana shirin haɗa mata da  su, ai sai a hankali.’

    Anti Naja tace ‘Kada ki damu ai mace komai ƙanƙantarta raino ba ya gagararta.’ Mommy tace ‘Yaran ma fa yana kawosu nan wajenta, kamar suna da tarbiyya da sauƙin hali ma.’ ‘To kin ji ma. Kada ki yi mata magana ma ki sa ta zata wani tashin hankali ne don na ganta tun da  aka ce an ɗaura auren nan jikinta ya yi sanyi.’ Haka suka gama tattaunawarsu suka tashi.

    Ranar Lahadi bayan Magriba aka shirya Khadija a ka kai ta gidan Mustapha. Bai zo da abokansa ba sai mutum ɗaya wato Badaru, ba tare da ɓata lokaci ba suka sallami  ƙawayen amarya Badaru ya kwashe su. Bayan ya rufe gidan ya dawo ya same ta tana ta faman share hawaye. Ya zauna ya lallasheta har tayi shiru sannan suka yi Sallah ya buɗe musu abincin da ya zo da shi suka ci. Da kansa ya kwashe kayan da suka gama cin abincin sannan ya dawo ya same ta a zaune a inda ya bar ta.

    ‘Yauwa, tunda mun ƙoshi taso na nuna miki gidan naki kafin mu kwanta.’ ya faɗa yana murmushi. Ta miƙe a kunyace, har sun kama hanyar fita daga ɗakin ya juyo ya dube ta yana murmushi yace  ‘Bari mu fara daga nan, nan ne ɗakinki.’ Ta yi murmushi murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ok.’

    Ya wuce ta bi shi a baya ya nuna mata ragowar gidan; bayan ɗakinta sai ɗakinsa sai kuma ɗakin yara inda nan ne kuma ɗakin baƙi. Sai kuma parlor guda ɗaya da dining area a dai-dai kofar  kitchen. Bayan sun gama zagayawa ya kashe fitulun sannan suka wuce ɗakinsa inda za su kwana.

    Ranar da Khadija ta cika kwana uku da tarewa a ranar bakin danginsa da suke ta zuwa ganin amarya sun lafa, don tunda gari ya waye babu wanda ya zo har azahar ta yi. Suna zaune a parlor suna hirarrakinsu aka fara kiran Sallah, ya miƙe yana cewa ‘Bari na je masallaci na dawo.’

    ‘Ok, by then ni ma na yi sallar na yi serving lunch.’ ta amsa ita ma tana miƙewa. Ta yi masa a dawo lafiya ya fice ita kuma ta shige kitchen. Kafin ya dawo ta yi Sallah ta gyara kwalliyarta sanna ta jera abincin a kan dininga table. Yana  dawowa ta yi masa sannu da zuwa sannan ya zauna a dining table ta zuba abinci suka fara ci.  Fried rice ne tare da sauce ɗin hanta da salad, daga gefe kuma ga haɗaɗɗen zobo.

    Shiru suka yi kowa yana ta kai loma, sai da Mustapha ya kusa cinye abincin nasa sannan ya ajiye cokalinsa ya ɗauki zobon da ta zuba masa a kofin tangaran ya kora. Yana ajiye kofin ya ɗauki cokalinsa yana gyara abincin ya dube ta yana cewa ‘Umm! Kin iya girki fa.’ Ta yi dariya tace ‘Ai da na zaci santin kurma kake da ka kasa magana.’

    ‘Au ashe ma sa min ido kika yi.’ ya faɗa yana sake cika baki da abincin. Ta yi dariya ita ma ta cigaba da cin abincin. Bayan ya haɗiye na bakinsa yace ‘Ina ga ai ya kamata in an jima mu je mu ɗebo su Afaf ko? Tun da suka ji an kawo ki suke ta zumuɗi.’

    Ta kalle shi tana wasa da cokalinta a kan abincin saboda ta riga ta ƙoshi, tace ‘Babe ai na zata za a bar su sai mun ɗan huta, ka ga shekaran jiya fa na tare. Ko gajiyar biki ma ai ban gama hucewa ba.’ ‘Haba, ai sai ku huta tare, kin san su ma fa they missed home don tunda mahaifiyarsu ta rasu rabonsu da gida.’

    ‘Allah sarki, ni kaina ina ɗokin dawowarsu nan but babe please ka bari koda zuwa next week ne na ɗan gama kwance kayana.’ ta faɗa da muryar magiya da lallashi. Ya ture farantin gabansa ya sake cika kofinsa na zobo, ya ɗan gatsina fuska yace ‘Ok, amma dai  ba za su ji dadi ba. Ɗazu muka gama waya da su suna ta ɗokin dawowa wajenki.’

    Ya miƙe ya nufi wajen TV yayinda ita ma ta miƙe ta fara tattara kwanukan tana cewa ‘Allah sarki,  in sha Allah next week da ni za mu je mu ɗaukosu ka ga daga nan ma sai mu biya gaba ɗaya mu gaida Mommy mu gaida su Hajiya sai mu dawo gida.’

    ‘Umm!’ ya amsa yana canza channel ɗin TV. Ta cigaba da kwashe kwanukan tunani kala-kala yana yawo a ƙwaƙwalwarta; ta yi zaton yana ɗokin kasancewa da ita, ta yanda zai bari su ɗan ƙara fahimtar juna kuma su more amarcinsu kafin ya ɗauko yaran amma shi yana maganar yau. Babu ƙananan yara a gidansu amma kusan  kullum suna tare da yaran Yaya Mama, ta san yara ba za su bari ta mori amarcinta ba tunda su rayuwarsu suna buƙatar kulawa ne kullum.

    Musamman tunda ga Shukra mai shekaru uku kacal.  Sati ɗayan ma da tace a ƙara kawai dai daurewa ta yi don ita da a tunaninta ta sami kamar wata uku a gidan kafin ya kawo mata yara tunda a can ma inda suke ana kula da su. To amma bata da wani zaɓi, zuwa next week ɗin sai ta bi shi su je su ɗauko yaran.

    Ana fara kiran magriba ya yi alwala ya ɗauki mukullin motarsa, ya same ta a kitchen tana tsugune a tsakiyar kitchen ɗin tana tuka tuwon shinkafa. Motsinsa ya sa ta saurara da tuƙin tuwon ta juyo, ta dube shi tace ‘Fita za ka yi? Ko masallaci za ka je?’

    ‘Eh, daga masallacin zan wuce na dubo yara sai kuma na wuce wajen Hajiya.’  Ta ɗan langabe kai ‘Babe ai da ka dawo, ni ma sai na shirya mu je na gaida Hajiyan.’ ‘No ki bari next week za mu je tare.’ Ya amsa yana duba wayarsa.

    Ta saki tuƙin tuwon ta miƙe ta nufeshi da niyyar ya rungume shi, sai dai ya ɗan kauce don haka ta gefe ta rungumo shi. Jikinta ya ɗan yi sanyi ta sumbaci kumatunsa tace ‘A dawo lafiya Babe, I  will wait for you idan ka dawo sai mu yi dinner tare. Ka gaida su Hajiya.’ ‘Ok.’ ya amsa sannan ya fice.

    A parlor ya sami Alhaji, bayan sun gaisa suka ɗan taɓa hira. Alhaji yace ‘Wai ka ɗebo yaranka  kuwa?’ ‘Ban ɗebo su ba, tace a bari sai zuwa next week idan ta gama hutawa.’ Yana wani kau da kai. ‘To babu laifi; amma fa idan ka ɗaukosu to ka saka ido, ka san mata yanzu ba sa son riƙo. Idan  ba ka yi wasa ba haka za a mayar maka da yara kamar almajirai a gidanka.’

    ‘In sha Allah zan kula, duk da ma na kula kamar ba ta da muguntar.’ ‘A a, basu fa da tabbas, kai dai ka sa ido. Kuma ka dinga bincikar duk motsinsu.’ Ya faɗa yana nuna shi da yatsa. Suka ɗan sake hira sannan ya shiga wajen Hajiya inda ya same su ita da Yaya Jidda suna hira; da yake ita gidanta kusa da gidan ne wataran ma sai an yi sallar Magriba take zuwa.

    Bayan sun gaisa suka cigaba da hirarsu gaba ɗaya. Jimawa kaɗan Yaya Jidda tace ‘Musty ina amarya? Tsohuwar sirikar taka ta baka yaran ko har yanzun ba za ta bayar ba?’ Ya gyara zama yace ‘Haba, sai kace ita ta haifa min su ai dole ta ba ni su.’ Hajiya tace ‘Sai yaushe za ka ɗauko su?’

    ‘Tace wai a bari ta huta zuwa next week, don ni da yau ma na so a ɗaukosu. Yanzu ma idan na fita zan je na kai musu biscuits ɗin da na saya musu.’ Yaya Jidda tace ‘Wai wacece tace a bari ta huta? Khadeejan?’ Yace ‘Eh, tace wai a bari ta huta ta gama ware kayanta kafin a kawo su.’ ‘Kai Musty! Yanzu kai har ka ba ta dama su da gidan ubansu sai ta ga dama za a kawosu, to me  ta yi ya gajiyar da ita har take buƙatar hutu.’

    ‘To ni ma dai haka na gani, amma dai zan ga yanda za mu yi.’ Ya faɗa yana kauda kai. Hajiya tace ‘To ka dai dinga kula sosai don kada ta dinga cutar da su, ka sa ido sosai don yanzu  mata ba tausayi ne da su ba.’ Yaya Jidda tace ‘Musamman gashi tun yanzu ta fara iyayi da kafa dokoki, a jira ta huta kafin a kawosu gidan ubansu.’

    Haka suka gama hirarrakinsu suna jaddada masa ya sa ido sosai kada Khadeeja ta cutar da yaransa; ya yi musu sallama ya wuce gidan iyayen Ma’u wajen yara. Sai da ya tsaya a hanya ya saya musu yoghurt da gasasshiyar kaza sannan ya wuce.

    Yana shiga bayan sun gaisa da Mama ta turo masa yaran suka same shi a guest room. Suka karɓi kajin da yoghurt suka kai wa Mama; wadda ta riga ta saba idan ya kawowa yaran abu to ba zai ba ta ba sai dai ya ba wa yaran a hannunsu su su kai mata; sannan suka dawo wajensa suna ta murna don su sun shirya kayansu tsaf yau za su tafi wajen Anti Khadeeja.

    Hakan ya yi masa daɗi don dama hakan yaso. Nan da nan suka sheƙa cikin gida suka fara fitowa da kayansu, Anti Nihla kanwar Ma’u ta taya su duk suka fito da akwatunansu. Mama ta fito ta same shi, bayan ta zauna tace ‘Ga mutanena nan tunda suka ji uwarsu ta tare sun kasa zaune sun kasa tsaye fa, ni da muka yi da su sai an kwana biyu amma ka ga suna ganinka sun fara fito da kaya. Kayan nasu ma fa wasu suna wajen wanki.’

    ‘Wallahi kuwa, ai babu komai daga baya sai na zo na karɓar musu sauran, kuma ma ai za su dinga zuwa in Sha Allah.’ Ya ba ta amsa. Haka aka gama fitar da kayan aka zuba masa a mota ya kwashe su suka kama hanya, suna ta murna za su je wajen Anti Khadija.

    Tunda ta gama tuwo ta yi Sallah sai ta yi wanka ta shirya cikin bum short ɗinta da wata figalalliyar riga, ta sha turare sai ƙamshi take yi ga gidan ma ta yi fes da ko ina ta kunna turaren wuta ƙamshi sai tashi yake a hankali.

    Tana kwance a kan three-seater tana danna waya ta jiyo motarsa ya buɗe gate yana shigowa, ta tashi zaune ta ɗan gyaggyara tana jiran ya shigo ta taro shi daga bakin kofa. Mintuna kaɗan ta fara jiyo motsinsu a kofar shigowa parlor, ya zura mukullin yana ƙoƙarin buɗewa yana cewa ‘Afaf riƙe hannun Shukra na buɗe kofar.’

    Ta ɗan yamutsa fuska tana ƙoƙarin ta gane shi da su waye; tas ta jiyo muryarsu gaba ɗaya. Ta ɗan rikice kaɗan tana mamakin dalilin da yasa ya taho da su bayan ya amince sai next week. Ta  jiyoshi yana zare mukullin daga jikin kofar; ta kalli jikinta yanda take kusan tsirara. Ta yi wuf ta zaga bayan kujera daidai lokacin da yake sako kai cikin parlor ɗin, ta ɗauki jilbab ɗinta wanda yake ajiye a saman kujera ta saka.

    Tana ƙarasa saka jilbab ɗin suka shigo da gudu bayan ya shigo, suka haɗa baki gaba ɗaya ‘Anti  Khadeeja, Anti Khadeeja.’ Suka karasa da gudu suka rungume ta suna murna. Haka ta yashe baki tana amsa gaisuwarsu, ta ɗauki Shukra tana cewa ‘Shukra baby, ya Mama?  Kin baro ta tana kuka ko?’

    Cikin muryarta ta gwaranci tace ‘Ba kuka take ba, ta ce ma na gaisheki.’ ‘Ina amsawa.’ Ta ajiyeta ta kama hannun Habib tace ‘Ya Habib, welcome.’ Ta kalli Mustapha suka haɗa ido, ya yi sauri yace ‘Sun ƙi bari na na taho sai da suka biyo ni, ga  kayansu nan sai ku shigar.’ ‘Uhm, bari mu gani.’ Ta amsa murya ƙasa-ƙasa.

    Ta ɗauki babban akwatin nasu ta ja ta nufi ɗakin yaran tana cewa ‘Afaf ɗauko wannan jakar mu kai ɗaki.’ Afaf ta kama jakar tana ƙoƙarin ɗagawa Abbansu yace ‘Ke ajiye jakar nan ba za ki iya ɗauka ba.’ Suna tsaye a ɗakin a gaban wardrobe tana tambayar Afaf ina jakar Abbansu ya shiga ɗakin ɗauke da jakar, yace ‘Ga ta nan, gani na yi ba za ta iya ɗaukowa ba na ɗauko mata.’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, Yaya Afaf ai ba raguwa ba ce, jakar ma da babu nauyi.’ Suka yi dariya gaba ɗaya, ya ja yaran suka fice daga ɗakin suka bar ta ita kaɗai tana ƙoƙarin samarwa akwatin kayansu waje. Bayan ta ajiye akwatin a kusa da mudubi ta ɗan ja baya ta ƙare  wa ɗakin kallo; komai tsaf yake tunda an share lokacin da ana kafi sai dai ba a shimfiɗa zanin gado ba a kan babban gadon nasu. Bata san a ya suke kwana ba kafin a aurota amma dai tana  jin a kan gadon suke kwana duka. Ta fito ta same su a parlor sun baje suna kallo suna ta yi wa  Abbansu surutu.

    Ta dube su tace ‘Bari na ciro hijabin nan Afaf sai ki tayani mu gyara ɗakin. Abbansu yace ‘Wannan ce za ta yi wani gyaran ɗaki? Babu abinda ta iya fa.’ Ta yi ‘yar dariya tace ‘Bari ka gani.’ Ta shige ɗakinta; tana shiga ta cire hijabin ta jefa kan gado, ta ƙarasa gaban wardrobe ta buɗe tana duban babban rigar da za ta saka. Wani malolo ya tokare mata maƙogoro saboda takaici; to ta ina za ta soma? Haka kawai ya kwaso mata yara a wannan daren. Da ya gaya mata ma ai da tuni ta gyara ɗakin. Ta ja gajeren tsaki a Fili.

    Motsin shigowarsa ne ya katse mata tunanin, ya nufota yana cewa ‘Na zata a nan ɗakinki za su kwana ai.’ Ta ɗan goge idonta ta juyo tana cewa ‘No, gara kawai na gyara musu ɗakinsu tunda babu wata ƙura da yawa a ɗakin sai su kwanta a can.’ Ya ɗan taɓe baki ‘Ok, amma dai za ki dinga zuwa kina duba su ko?’

    ‘Eh mana wannan ai dole ne.’ Ta amsa tana ɗan juya jikinta. Ya juya ya fita ba tare da ya ko kalli jikin nata ba. Ta kalle jikinta ta ɗan murguɗe baki; yau dai  kwalliyarta ta tashi a aikin banza kenan. Ta janyo babbar riga a wardrobe ɗin ta saka, ta sa hula ta rufe gashinta sannan ta fito. Kai tsaye  ta wuce kitchen ta ɗauki tsintsiya da parker, ta fito parlor ɗin ta dube su tace ‘Taso Afaf, maza mu gyara ɗakinku ku sami wajen kwanciya.’

    Ta wuce ta barsu, a tunaninta yarinyar za ta biyo bayanta. Sai dai har ta shiga ɗakin ta fara ƙoƙarin sharewa babu motsin tahowarta, ta ɗan dakata da sharar da take yi ta kwala mata kira. A maimakon yarinyar ta amsa sai Abbansu yace ‘Abinci muke ci.’

    Ba tare da ta amsa ba ta sunkuya ta cigaba da sharar, har ta ɗan yi nisa a sharar sai kuma ta tuna cewa ya yi abinci suke ci fa; to wanne abincin? Tuwon da ta tuƙa da shinkafa gwangwani 1 da Rabi ɗin ya tasa yaransa a gaba suke cinyewa? Bayan ta gaya masa za ta jira shi ya dawo su ci abincin dare tare? Tuwon ma da gaba ɗayansa malmala uku ne ta tuƙa saboda ta san miyar ba za ta isa su ci ɗumame ba.

    Har ta ajiye sharar ta nufo parlor ɗin sai kuma ta tuna idan ta zo me za ta yi a kai, don haka sai  kawai ta cigaba da sharar ta tana fatan Allah ya sa su rage mata tuwon. Ta share ɗakin ta karkaɗe ko ina sannan ta shimfiɗa zanin gadon da ta ɗauko daga ɗakinta. Ta kalli ɗakin ta ga ko ina ya yi tsaf, sannan ta ɗauko sharar da ta kwashe ta fito.

    Suna zaune a kan dining table suna ta cin tuwo shi da ‘yayansa, kafin ta yi magana Abbansu ya dubeta yace ‘Yauwa ɗan ƙaro mana tuwon nan Habib bai ƙoshi ba, ga Shukra ma kamar za ta ƙara.’ Ta ɗan zaro ido tace ‘Wai kun ciye na flask ɗin?’ ‘To nawa yake, ai ba shi da yawa.’ Kafin ta ba da amsa Nasreen tace ‘Kuma miyar ta yi daɗi Anti.’ Ta yi murmushin yake tace ‘Shikenan dama na dafa, ko ni ma ban ci ba.’

    Habib yace ‘Abba ni fa ban ƙoshi ba, dama bamu ci abincin dare ba lokacin da muka taho gashi mun manta ba mu karɓo kazar mu ba a wajen Mama.’ Abbansu ya dube ta yace ‘Yanzu ya za ki yi da Habib? Yunwa yake ji.’ ‘Akwai ragowar bread sai mu raba ni da shi mu sha da tea, don gaskiya yanzu ba zan so ɗora tukunya ba.’ ba tare da ta saurari amsarsu ba ta wuce kitchen da sharar a hannunta.

    So take ta sami waje ta yi kuka ko ta ji sanyi a ranta, don haka ba tare da ta kalli wajen ba ta jefa sharar ta juya sink ta fara wanke hannunta. Abbansu ta jiyo a bayanta yace ‘Khadeeja, daurewa fa za ki yi ki dafa wa Habib Indomie don shi ba ya cin bread kuma kin ga ai ba ya kwana da yunwa  ba.’

    Ta kalle shi suka haɗa ido tace ‘Babe na gaji ne wallahi, ni ma ina son tuwon amma na haƙura zan ci bread.’ Ta ɗan saurara tana kallon yanda yake ƙara haɗe rai, sai kuma cikin sanyin murya tace ‘Amma Afaf ta zo na kunna mata cooker ta dafa musu Indomie ɗin.’

    Ya kalle ta sheƙeƙe yace ‘Wai ke me kika ɗauki Afaf ne she’s only eleven babu abinda ta iya na aikin gida. Idan ta girma dai ta koya but ki daure kawai ki dafa masa.’ Ta juya ta ba shi baya saboda hawaye ne yake shirin ƙwace mata, ya juya ya fice ya bar mata  kitchen ɗin.

    Ta share hawayenta ta sauko da tukunya ƙarama ta zuba Indomie ɗin da ruwa da komai ta kunna wuta ta ɗora. Ta koma ta jingina da sink ta tsaya ta kafa tagumi; yanzu shikenan har ta gama amarcin, ko awa biyu yaran nan ba su yi da zuwa ba amma sun gundire ta, anya kuwa za ta iya wannan rayuwar. Ko da yake dai yanzu suka zo ta san ba su fahimce ta ba ita ma kuma ba ta fahimcesu ba; amma dai za ta ɗora su a saiti kwanan nan.

    Tana cikin juye Indomie ɗin suka shigo kitchen ɗin suka wanke hannuwansu, sai dai abinda ya b ata mamaki babu wanda ya ɗauko plate ɗin da ya ci abincin ya kawo kitchen ɗin; duk a dining table ɗin suka baro mata. Ta gama juye Indomie ɗin ta miƙawa Habib bayan ya gama wanke hannu; haka ta fito ta kwashe kwanukan daga dining su kuma suna zaune suna kallon TV. Ta  haɗo shayi ta ɗauki guntun bread ɗinta ta wuce ɗaki.

    Bayan ta gama shan shayin ta ɗauko kofin ta fito, tana isa gaban sink ɗin za ta ajiye kofin ta ga Indomie ɗin da ta dafawa Habib ko rabi bai ci ba kuma ga dukkan alamu ya ƙoshi kenan. ‘Mtsewww’ ta ja tsaki a Fili. Ta wanke hannunta ta fito daga kitchen ɗin. Har za ta wuce ɗaki Abbansu yace ‘Ki zo ki shirya su sun fara jin bacci kin ga goma har ta gota.’

    Ta juyo ta dawo, ta ɗauki Shukra wadda ta riga ta fara gyangyaɗi Afaf, Habib da Nasreen suka bi bayanta. Sune suka nuna mata kayan baccinsu ta taimaka musu duk suka yi brush sannan suka shirya, ‘yan matan gaba ɗaya suka haye gadon. Ta kalli gadon ta ga ma ba zai ishesu ba don haka ta koma dakinta ta dauko katifar da aka kawo mata saboda baƙi ta shimfiɗawa Habib a ƙasa. Ta gama tsaf za ta kashe musu fitula Nasreen yace ‘Anti ba a kashe mana fitila sai mun yi barci.’

    Ta mayar da fitilar ta kunna musu sannan ta fice daga ɗakin, ta wuce Abbansu a parlor ta shige ɗakinta. Ta riga ta gaji sosai don haka ita ma kayan bacci kawai ta saka ta rufe ɗakin nata ta wuce ɗakinsa, ta kwanta ta rufe idonta.

    Lokacin da Khadeeja ta fito daga ɗakinsa ya zata ɗakinsu Afaf za ta koma don su kwana tare, amma sai ya ga ta shige ɗakinsa. Ya tashi ya shiga ɗakin yaran inda ya tarar dukansu sun yi  bacci, don haka ya kashe musu fitilar ya fito daga ɗakin. Ya kashe fitilun falon ya shige ɗaki.

    Tana kwance a kan gado kamar ma bacci take yi, don haka ya ƙyaleta. Bayan ya gama shirinsa ya kwanta, ya miƙa hannu ya taɓa ta, ta juyo ta buɗe ido tace ‘Babe, ka shigo?’ ‘Um.’ Ya amsa a gajarce. Ta fara ƙoƙarin matsowa jikinsa, ya tashi zaune yana cewa ‘Kin baro yara su kaɗai, kin ga daga nan ma ai ba lallai ki jiyo motsinsu ba. Ni da na zata ma tare za ki kwana da Shukra a ɗakinki fa,  she’s just 3 ba ta saba kwana ita kaɗai ba.’

    Ta ɗan matsa ta koma inda ta baro tana cewa ‘No, they will be fine fa, ba ka ga a tsakiyar yayunta na sata ba kuma duk fa sun yi bacci. Ka ga na ma saka alarm wajen biyun dare zan je na dubasu sai kuma da asuba.’ ‘Uhm, amma dai da kin daure kin kwana da su ɗin.’

    ‘Kada ka damu ina jinsu.’ Ta faɗa sannan ta gyara kwanciyarta ta juya masa baya ta rufe ido.  Haka kawai zai ce ta je ta kwana a cikin yara; to ai ko ‘yar da ta haifa ce shekara uku ai raba wajen kwana za su yi. Ba zama ta fara wannan aikin ba balle ya sallamawa yaran ita.

    Har barci ya fara ɗaukanta suka ji an murɗa ƙofar, ya riga ya murɗa mukullin da ya shiga don haka sai ƙofar ba ta buɗe ba. Aka ƙwanƙwasa a hankali, suka tashi zaune tare shi da Khadeejan. Kafin suce wani abu Nasreen tace ‘Abba Shukra ce ta tashi za ta sha shayi.’ Ya kalli Khadeeja yace ‘Oh, na manta ban gaya miki ba tana farkawa shan tea da daddare, tunda  aka yaye ta ta saba. Ki je ki haɗa mata shayi, daga ta sha za ta koma bacci.’

    ‘Shayi? A wannan daren? Ko fa 4 hours ba su yi ba da cin tuwo, ikon Allah.’ ‘Idan ba ki ba ta ba haka za ta yi ta yi wa mutane kuka har sai an ba ta, kije ki haɗo mata gobe sai  ki haɗa ki sa a flask kafin ta kwanta.’ Ya faɗa yana sake ɓata rai. Ta ɗaura zaninta a ƙirji ta sauka daga kan gadon ta fice daga ɗakin cike da takaici.

    A tsakiyar gadon ta sami Shukra tana kuka, duk yanda zuciyarta ta kai ga ƙuna a wannan lokacin dole ta danne fushinta. Ta miƙa mata hannu tana ɗan murmushi tana cewa ‘Ahh! Sorry Shukra, ya aka yi? Kukan me kike yi? Cikin shessheƙar kuka da gwarancinta tace ‘Tea.’

    Ta zauna a gefen gadon ta rungume ta tana shafa bayanta tana mata magana cikin lallashi ‘Ya  isa, ya isa. Da safe ke zan fara haɗawa shayi kin ji Baby Shukra, kin ga dare ya yi ko? Mu yi bacci da safe sai mu sha tea ko, har da bread ma da ƙwai ko?’

    Ta gyaɗa kai alamar eh, amma fa hawayenta ya ƙi daina zuba har da shesshekar. Ta cigaba da shafa bayana tana lallaɓa ta yayin da Nasreen ta koma ta kwanta har bacci ya fara ɗaukanta. Abbansu ya ya turo ƙofa ya shigo ɗakin, Shukra ta leƙo ta kafaɗar Khadija cikin shessheƙa tace  ‘Abba tea zan sha.’

    Ta ƙwace daga jikin Khadijan ta sauko ta taho wajensa, ya rage tsawo ya ɗauke ta ya rungumeta yana cewa ‘Ya isa, Anti ba ta ba ki shayin ba?’ ‘Tace sai da safe.’ ta faɗa tana shessheƙa. Ta mike ta rungume hannuwanta a ƙirjinta ta kalle shi da fuskar tausayi tace ‘Babe, ka bar ni da ita za ta koma bacci kuma a hankali za ka ga ta ma daina farkawan shan shayi da daddaren. Ka barni na lallaba ta idan ta yi bacci zan taho.’

    Kallonta yake da mamaki a fuskarsa, sai da ta gama sannan yace ‘Yunwa fa take ji, haka za ta kwana da yunwa. She’s only 3, idan ta girma da kanta za ta daina duk yayyenta ma haka babarsu take rainonsu.’ Cikin ƙosawa tace ‘Kai dai ka bar ni da ita mana, I promise you she will be just fine.’

    Ta ƙaraso kusa da shi, ta miƙa hannu ya dafa kafaɗarta yana cewa ‘Kin ga, ki yi haƙuri ki haɗo mata shayi kada ki saka ta kwana da yunwa tunda ba ta saba ba. A hankali za ki ga da kanta za ta daina.’ Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ohkk!’

    Ta wuce ta bar shi a nan ta nufi kitchen; tea at 1pm, wannan wane irin tashin hankali ne? Idan da ya kyale su ta san tabbas za ta raba ta da wannan shan tea ɗin amma har wani cewa yake yi kada ta barta da yunwa. Ta ƙarasa kitchen ɗin ta haɗo mata tea a kofi ta ɗauko ta fito. Tana zuwa ta same shi zaune a gefen gadon ragowar yaran duk suna ta baccinsu yayin da yake zaune rungume da Shukra; har bacci ya fara ɗibanta amma tana shiga ya ɗagata yace ‘Yauwa  Baby tashi ga shayinki.’

    Ta tashi tana muttsike ido, ya miƙe tsaye ya nunawa Khadijan wajen ta yana cewa ‘Zauna sai na ajiye miki ita idan kin gama ba ta tayi bacci kya taho.’ Ya ajiye mata ita a kan cinyarta ta fara ba ta shayin sannan ya fice ya bar su.

    Bayan ta gama ba ta shayin ta saka ta ta yi fitsari sannan ta kwantar da ita ta ɗan jijjigata bacci ya  fara kwasarta sannan ta wuce ɗakin. Ko da ta shiga ɗakin ya riga ya yi bacci, don haka ba tare da  ta kunna fitila ba ta lalubi waje ta kwanta a gefen gadon. Motsin kwanciyarta ne ya farkar da shi, ya ɗan matso ya rungumota ta baya yana sumbatar bayan wuyanta. Ta ɗan motsa tace ‘Mmmm!’

    Yace ‘Kin san gobe yara za su school ko? Sai ki tashi da wuri don ki shirya su.’ A take jikinta ya yi sanyi; gaba ɗaya ma ta manta da wannan tunda ita ta riga ta sanar da ƙawarta su yi mata attendance ba zata koma ba sai ta yi sati. Ya cigaba da lalubenta tana ƙoƙarin zamewa, saboda ita gaba ɗaya ma komai ya fita daga ranta;  a halin yanzu ma kuka take son yi. Sai dai haka ta haƙura ta bar shi ya yi yanda ya so sannan ta  kwanta tana fargabar yanda za ta tashi nan da awowi kaɗan ta cigaba da hidima.

    Ana fara kiran assalatu ya tasheta daga bacci, sai da ta yi da gaske sannan ta iya saukowa daga kan gadon. Ta yi alwala ta wuce kitchen tunda da ɗan sauran lokaci kafin a tada Sallah. Ta tsaya a tsakiyar kitchen ɗin tana tunanin inda za ta fara; a hankali dabara ta faɗo mata; macaroni da sauce za ta dafa musu in ya so sai ta dafa indomie da kwai su yi breakfast. Nan da nan ta ɗora  sannan ta ɗebo tsofaffin flasks ɗinsu da ta gani a store ta wanke sannan ta je ta yi Sallah.

    Ta zata idan ya dawo daga masallaci zai tsaya ya taya ta shirya su amma ga mamakinta sai ya wuce su a parlor ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da baccinsa. 7:15 am ta gama komai duk ta yi musu wanka sun shirya, suka zauna a dining table ta kawo musu abinci ta zubawa kowa Indomie da dafaffen ƙwai guda ɗaya. Daga fuskokinsu ta san ba  indomie suka so ci ba, suna cikin cin abincin yayin da ita kuma take zaune a table ɗin tana ba wa Shukra a baki Nasreen ta kalle ta tace ‘Anti da ma dankali da ƙwai kika soya mana.’

    Ta kalle ta tana murmushi tace ‘Saboda kar ku makara shi yasa na yi sauri na dafa Indomie, but insha Allah weekend idan babu makaranta sai a soya muku dankali kin ji. Yanzu maza ki cinye kafin Abba ya fito ya kai ku school.’

    Suka cigaba da cin abincinsu. Jimawa kaɗan Abbansu ya fito yana riƙe da mukullin mota, suka haɗa baki gaba ɗaya suka gaishe shi. Bayan ya amsa yace ‘Maza ku gama mu wuce school kada ku makara.’ Ya kula da ragowar ƙwai a plate ɗin kowa banda Habib, ya dube shi yace ‘Kai ina naka ƙwan?’ Yace ‘Shi na fara cinyewa Abba.’ Nasreen tace ‘Abba ni ina son dankali, Anti tace ba za a dinga soya dankali ba sai weekend.’ Ta  langabe kai kamar abun tausayi.

    Ba tare da ya kalli Khadeejan ba yace ‘No, za a dinga soyawa kada ki damu, maza ki ci abinci mu tafi.’ Tana jinsu ta kawar da kanta, don sai dai idan shi zai dinga tashi ya soya ita ba za ta iya soya dankali da sassafe ba. Nan da nan suka gama; Habib ne ya fara miƙewa har ya juya tace ‘Ɗauke plate ɗinka da cup ɗin ka kai kitchen.’

    Ya ɗauke plate ɗin ya tafi da shi, suma ‘yan uwan da suka ga haka kowa idan ta miƙe sai ta ɗauke plate ɗinta ta wuce da shi. Suka ƙarasa shiryawa suka fice tare da Abbansu. Kafin ya dawo ta soya dankali da ƙwai ta jera a dining table sannan ta wuce ɗaki; wanka za ta shiga sai kuma ta tuna ko da ta yi wankan dai kitchen za ta shiga ta yi wanke-wanke ga shara, don haka ta ga gara ta bari idan ta gama aikin ta yi wankan.

    Sai da ya yi wanka ya shirya sannan ya fito a shirye, kai tsaye ta riga ta shirya abincin a dining  table don haka suka zauna. Yana buɗe kwanon yace ‘Sai da suka tafi kuma kika soya dankali?  Sun fi son soyayyen abinci idan za su tafi school.’ Ta ɗan langabe kai ‘To ai Babe ba zan iya soya wani abu before 7am ba, da a ce ma dai ina da mai aiki ne. Amma hakan ma weekend zan soya musu in sha Allah.’

    ‘To ai da kin bari sai weekend ɗin ma ci gaba ɗaya, yanzu idan sun dawo ai za su ga ɓawon ba daɗi ai kuma ma Shukra za ta gaya musu tunda ita ta ci. Mai aikin ma kuma za a ɗauka.’’Uhm.’ Suka cigaba da cin abincin ba tare da kowa ya ce komai ba.

    Gaba ɗaya ma abincin sai ya fice daga ranta; kenan duk abinda ba za ta ba wa yaransa ba baya so ita ta ci. Haka tunani kala-kala suka yi ta yawo a kanta. Ya gama cin abincin ya fice ya bar su ita da Shukra. Sai wajen 10am ya kirawo ta a waya, bayan ta ɗauka yace ‘Mantawa na yi ban gaya miki ba idan 1pm ta yi sai ki je ki ɗauko yara daga school.’

    Ta ɗan yi shiru don ta zata shi zai ɗaukosu, tace ‘Ohk, but zan iya zuwa a ƙasa?’ ‘No, kin san school ɗin ai ba nisa sosai amma dai ku hau a dai-daita sahu sai ki tafi da Shukra.’ ‘Ok.’ Suna gama wayar ta miƙe ta ɗora abincin rana don ta gama da wuri. Lokaci yana yi ta ɗauki  Shukra suka tafi suka ɗauko ‘yan makarantar. Suna dawowa bayan sun huta ta shirya su suka tafi  islamiyya.

    Dab da magriba ya dawo. Bayan ya huta yana zaune a parlor shi da yaran tana jiyo shi yana  tambayar Afaf abinda aka yi da baya nan, an ɗauko su da wuri daga school? Sun ci abincin rana?  Me suka ci? Sun makara a islamiyya? Haka dai ya cigaba da tambayoyinsa tana kitchen tana jiyo su, kamar ta fito ta yi magana sai kuma ta share ta cigaba da abinda take yi; tunda dai ta san  ba ta yi musu komai ba. A haka suka ƙarasa satin nan tana bakin ƙoƙarinta wajen kula da yaran nan gaba dayansu.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    بِسْمِ الله.

    Bismillah

    Da sunan Allah.

    Addu’ar Sanya Tufa

    .الْحَمْدُ لِلّهِ الذِي كَسَانِي هَذَا الثَّوْبَوَرَزَقَنِيهِ مِنْ غَيْر حَوْل مِني وَلاَ قُوَّةٍ
    Alhamdulillahil lazi kasani hazas sauba warzuƙnihi min gairi haulin minna wala ƙuwwa

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya tufatar da ni wannan tufa, kuma ya arzurta ni da ita, ba tare da wata dabara daga gare ni ba ko wani ƙarfi.

    Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayin Harshen Hausa A Ƙarni Na 21 Da Tagomashinsa

    Matsayin Harshen Hausa A Ƙarni Na 21 Da Tagomashinsa

    sahalaliyu@gmail.com
    Kira: 059 671 4064
    WhatsApp: +2347065994177
    SASHEN NAZARIN HARSUNAN NIJERIYA DA KIMIYYAR HARSHE, JAMI’AR JIHAR KADUNA, NIJERIYA.

    Maƙalar Da Aka Gabatar A Taron Ranar Hausa Ta Duniya a Ƙasar Ghana (Kumasi) Don ƙara Wa Juna Sani. Mai Taken: Zango: Ƙaura Daga Keɓancewa Zuwa Fahimta: Rawar Da Gwamnati Ke Takawa Wajen Aiwatar Da Manufofi. Wanda Ƙungiyar Matasan Zongo-Hausa Ta Ghana Suka Shirya A Ƙarqashin Jagorancin Masarautar Sarkin Zango.

    AGUSTA, 2025.

    Tsakure
    Manufar wannan takarda ita ce bayyana tunanin da Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) don keɓe wannan rana ta Talata 26 ga watan Ogosta, don ta kasance muhimmiyar rana ga harshen Hausa don ƙara nuni matsayinsa da kuma tagomashinsa a idon duniya baki ɗaya.

    Akwai wani ƙiyasi da aka fitar, wanda yake nuna cewa akwai kimanin adadin harsuna a duniya wanda yawansu ya kai kusan dubu bakwai da ɗari shida (7,600), amman kuma harshen Hausa shi ne wanda zakaransa ya yi cara har ya kai matsayin harshe na goma sha ɗaya a duniya(11) (Bunza, A.M 2023). Kuma wani abin lura shi ne, harshen Hausa ya kai shekaru ɗari da ashirin (120) a matsayin karatun boko musamman a ƙasar Nijeriya.

    Sannan kuma akwai wata nasara da shi wannan harshen na Hausa ya samu wannan nasara kuwa ita ce: yadda ake samun kafafen yaɗa labarai cikin gida Afirka da ma ƙasashen Turawa. Alal misali: akwai gidajen rediyo kamar irin su: BBC da VOA da RFI da DW ƙasar China da Ghana dai sauran su. Baya ga wannan kuma, takardar ta fito da yadda ake samun ƙara yaɗuwar harshen a wasu kafafen sada zumunta na zamani kamar irin su: Facebook da WhatsApp da Instagram da Twitter har ma da shafukan yanar-gizo.

    Gabatarwa

    Babu wata wayewa da mutum zai yi tunƙaho da ita face sanin wanene shi? Kuma daga ina yake? Sannan da me yake magana?. A sanadiyyar mulkin mallaka da kuma sakaci da harshenmu da al’adunmu ne ya janyo cewa wasu daga cikinmu suke ganin cewa wai har akwai wani harshe da ya fi harshensu na gado (harshen uwa). Duk wani wanda ya rasa harshensa na asali, to ya rasa wani babban jigo na rayuwarsa, domin kuwa da harshen ne zai iya ɗaga hannunsa ya bugi ƙirji ya nuna kansa.

    Muddin aka ce an yi watsi da harshen uwa (Hausa), to haƙiƙa an yi watsi da al’adunmu da tarbiyyarmu da kyawawan ɗabi’unmu. Babu wata waye da ta wuce mutum ya san harshensa da kuma abin da harshen ya ƙunsa. Bayanai sun nuna cewa wannan rana ita ce karo na goma sha ɗaya (11) da ake gudanar da wannan taron na Ranar Hausa ta Duniya.

    Haƙiƙa Majalisar Ɗinkin Duniya (United Nation) sun yi la’akari ne da wasu abubuwa da suka shafi harshen Hausa har suka ware wannan rana ta musamman don harshen Hausa, waɗannan abubuwan kuwa sun haɗa da:

    • Yawan yaɗuwar harshen
    • Yawan masu magana da harshen
    • Yawan aikace-aikace (rubutu) da harshen
    • Yawan samun kafofin yaɗa labarai da harshen
    • Yawan amfani da shi a kafofin sada zumunta na zamani
    • Yawan amfani da shi a harkokin siyasa
    • Yawan amfani da shi a gidajen jaridu

    HARSHEN HAUSA DA ƘASAR HAUSA

    A wannan ɓangaren kuma, batutuwa biyu ne za a warware su: wato mecece Hausar ita kanta? Da kuma ina da ina ne ƙasashen Hausa? Bari mu fara da batun Mecece Hausa?
    A ma’anar da ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero Kano ya bayar, ya ce:

    “Hausa shi ne harshe da ake magana da shi.”
    Sannan kuma ya ce: “Hausa harshe ne.”
    Ya ƙara da cewa: “Hausa na nufin azanci ko hikima.”
    Shi kuwa Hornby, A.S (2015) cewa ya yi:

    “Harshen Hausa shi ne harshen da Hausawan Afirka ta Yamma suke amfani da shi musamman a Nijeriya da Nijar sannan kuma ake amfani da shi a wasu sassa na Yammacin Afirka a matsayin harshen sadarwa a tsakanin al’umma mabambanta.”

    WANENE BAHAUSHE?

    A nan kuma za mu yi magana ne a kan shin wai wane ne Bahaushe?
    Bunza, A.M (2019) ya ba da wannan amsa da cewa: Bahaushe shi ne:

    • Wanda yake bugun gaba da zama Bahaushe.
    • Wanda ba shi da wasu al’adu da harshe sai na Hausa.
    • Wanda iyayensa da kakanninsa Hausawa ne.
    • Wanda yake da dangantaka da tushe daga tussan karuruwan Hausa kamar su: Zazzaganci ko Katsinanci ko Kananci ko Gobiranci ko Katsinanci ko kuma Sakkwatanci.
    • Wanda yake da tsaga (shasshawa) ta fuska daga cikin tsagetsagen Hausawa na zuriya.

    HAUSA A IDON MAJALISAR ƊINKIN DUNIYA (UNITED NATION)

    Wannan gaɓar ita ta haifar da wannan takarda, domin kuwa Majalisar ɗinkin Duniya ta yi amfani da irin kallon da ta yi ma harshen Hausa ne a matsayin na 11 a faɗin duniya, inda ta kawo cewa:

    • Mandarin (China) mutane 1,009,000,000 masu magana da shi
    • English mutane 983,000,000 masu magana da shi
    • Hindustani mutane 544,000,000 masu magana da shi
    • Spanish mutane 527,000,000 masu magana da shi
    • Arabic mutane 422,000,000 masu magana da shi
    • Malay mutane 281,000,000 masu magana da shi
    • Russian mutane 267,000,000 masu magana da shi
    • Bengali mutane 261,000,000 masu magana da shi
    • Portugues mutane 229,000,000 masu magana da shi
    • French 229,000,000
    • Hausa mutane 150,000,00 (https://www.gistmania.com/talk/.353020.0html)

    Daga wannan ƙididdiga da suka gabatar, hakan ya tabbatar mana da cewa lallai harshen Hausa karansa ya kai tsaiko kuma wuyansa ya isa yanka, keɓe rana ta musamman da Majalisar ɗinkin Duniya ta yi don ƙara raya wannan harshen namu, abin a yaba ne kuma yin hakan zai ƙara kima da tagomashi ga harshen har ma da masu harshen.

    HAUSA A ƘASASHEN ƘETARE

    Shin me ya kai harshen Hausa zuwa wasu ƙasashen da ba na Hausawa ba? Ba tare da tsawaita magana ba, daga cikin dalilan da suka kai Hausa da Hausawa wata duniyar da ba ta Hausa sun haɗa da:

    • Fatauci
    • Neman ilimin addini
    • Yaɗa Addinin Musulunci
    • Cinikin bayi
    • Aikin hajji
    • Aikata wani abin kunya
    • Neman ilimin book
    • Aikin gwamnati (www.amsoshi.com)

    Waɗannan da ma wasu dalilai masu yawa da suka kai harshen Hausa da Hausawa wasu ƙashen da ba nasu ba.

    KAMMALAWA

    Daga bayanai da suka gaba, mun fahimci cewa lallai harshen Hausa ba ƙyalle ba ne kuma ba ƙashin yarwa ba ne. Sannan kuma mun ga irin yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta kalli harshen Hausa wanda ake ganin wannan daraja da martaba da harshen yake da shi ya sa ta ware rana ta musamman don gudanar da taro da yin bita a kan wasu al’amura da suka shafi harshen Hausa da kuma irin gudunmawar da harshen yake bayarwa a rayuwarmu ta yau da kullum.

    Mun ga yadda aka samu wasu gidajen rediyo da kafafen sadarwa na zama suke mu’amala da harshen Hausa. Sannan mun fahimci wanene Bahaushe da kuma inda harshen Hausa yake matsayinsa a duniya tare da masu Magana da shi. Sannan mun ga wasu dalilai da suka kai harshen da ma masu harshen wasu ƙasashen da ba ƙasar Hausa ba.

    Manazarta

    Bunza, A.M (2013), “Don Me Ake Karatun Hausa?” Harsunan Nijeriya Volume XXIII. 2011-2013. Center for the Study of Nigerian Languages, Bayero University: Kano.
    Hornby, A.S (2015), Oxford Advanced Learner’s Dictionary of Current English 9th Edition. Oxford University Press: United Kingdom.
    Ƙamusun Hausa Na Jami’ar Bayero (2006). Cibiyar Nazarin Harsuna Nijeriya: Kano.
    www.amsoshi.com
    A Wata Hira da Aka Yi da Bunza, A.M a Shekarar (2023)
    https://www.gistmania.com/talk/topic.353020.0html

    Domin karanta Gudunmawar Ali Gumzak Wajen Samarwa Da Kuma Haɓaka Finafinan Hausa danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    لاَ إِلَهَ إلا اللهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إلا الله رَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمُ .

    La’ilaha illallahul azeemul haleem, la’ilaha illallahu rabbil arshil azeem, la’ilaha ilallahu rabbus samawati warabbul ardi wa rabbul arshil kareem.

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare Shi), Mai haƙuri (Mai jinkirin azaba tare da cikakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Alarshi, Mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai, Ubangijin ƙasa, Ubangijin Al’arshi, Mai yawan baiwa.

    اللّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو فَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِيطَرْفَةَ عَيْنٍ وَأَصْلِحْ لي شأني كلهلا إله إلاأَنتَ.

    Allahumma rahmataka arju fala takilni ila nafsee ɗarfata aini wa’aslih lee sha’ani kullah, la’ilaha illa anta.

    Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka Kar Ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma Ka kyautata mini sha’anina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

    لاَ إِلَهَ إلا أنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظالمين

    La’ilaha illa’anta subhanaka inni kuntu minaz zalimeen

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka, lalle ni na kasance daga cikin azzalumai.

    الله الله رَبِّى لاَ أُشْركُ بِهِ شَيْئاً
    Allah Allah rabbi la ushrika bihi shai’an

    Allah! Allah ne Ubangijina, ba na yin tarayya da Shi da wani abu a cikin bauta.

    Karanta Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    اللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتابِ ، سَرِيعَ الْحِسابِ ، اهْزِمِ الأَحْزَابَ ، اللّهُمَّ اهْزِمُهُمْ وَزَلْزِلْهُمْ .

    Allahumma munzilal khitabi, sari’al hisabi, ihzimil ahzaaba, allahumma ihzimuhum wazalzilhum.

    Ya Allah! Mai saukar da Littafi, Mai gaggawan sakamakoKa karya kungiyoyin abokan gaba. Ka karya su, Ka girgiza su.

    Karanta Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    ‘Hey Babe.’ Ta faɗa tana wani rangwaɗa kai tare da juya ƙwayar idonta kamar dai ga Babe ɗin a gabanta tana kallonsa. ‘Mai kyau, ya kike?’ Ya faɗa daga ɗaya ɓangaren. ‘Lafiya. Yanzu nake dawowa daga school gashi nan na kusa shiga gida.’

    ‘Oh, ni ma yanzu na mayar da su Afaf gida wajen Hajiya. Mun je shopping ne and I bought a few  things for you nake so na kawo miki later. Is that ok? ‘Yes Babe, kai ma ka san ina nan idan dai kai ne kake son ganina. Ya yarana? Hope suna lafiya?’

    ‘Alhamdulillah ga su nan. I just can’t wait to have you so we can all live in one place na huta da  visiting yarana.’ ‘Aww! Kada ka damu, very soon in sha Allah. We will talk more about it idan ka zo in sha Allah  don yanzu zan shiga gida ka san Mommy ta hanani waya a kan hanya.’

    Ya yi ‘yar dariya yace ‘Kuma fa haka ne, to sai mun haɗu.’ Suka yi sallama suka ajiye wayar. Da sallama ta shiga gidan tana ta fara’a kamar wadda aka yi wa wani babban albishir. Babu kowa  a parlor ɗin sai Mommy tana shirin tashi ta shiga sallar Magriba. Bayan ta amsa sallamarta tace  ‘Yau kuma haka kike tafe kina tallan macleans?’

    ‘Kai Mommy! I’m just Happy.’ Ta faɗa tana dariya. Ta wuce ɗakinsu yayin da Mommy ta shige nata ɗakin. Tana sane da yanda take tafiya tana murmushi ɗin kuma tana jin daɗin hakan. Idan dai a kan  Mustapha ne fiye da haka ma za ta yi. Muryarsa kawai take buƙatar ji ta shiga farin cikin da ba ya  misaltuwa. Wata bakwai da suka wuce suka haɗu, amma saboda yanda ya iya soyayya da  tarairaya ya shiga zuciyarta kamar wanda suka yi shekaru a tare.

    Da ya sami yanda yake so ma da tuni an ɗaura musu aure don shi a shirye ya zo, ita ce take ɗan dakatar da shi don tana so ta gama level 1 kafin a yi mata auren. Sai dai a daren jiya Baffanta ya sanar da ita cewa ta gaya  masa ya turo maganar aurensu. Ta jefa Jakarta a kan gadonsu wadda ta faɗa kan ƙanwarta Nabila. Nabila ta make jakar ta ja  tsaki tace ‘A a, must you be stubborn?’

    Tayi dariya tana cewa ‘A tashi dai a yi sallah.’ Ta matsa gaban wardrobe ta fara kokarin cire kayan jikinta.

    Kamar yanda ya yi mata alƙawari ana idar da sallar isha’i ya iso gidan nasu. A tsakar gida suka  zauna inda ta saka musu kujerun roba a rumfar mota, ta ajiye ƙaramin tebur a tsakanin kujerun  wanda ta ɗora ruwa da lemon roba masu sanyi a kai.

    Bayan sun gaisa suka ɗan taɓa hira, hirar da a mafi yawancin lokuta ita ce take yi shi bin ta kawai yake da kallo yana murmushi yana ba ta gajerun amsoshi. Mustapha kenan; haka yake kamar wani basarake, komai nasa a hankali sannan kuma bisa tsari.  Wannan ya sa yake ƙara burge ta.

    Ta ɗauki ruwan robar da ta ajiye ta buɗe ta miƙa masa tana cewa ‘Ko ruwan ba ka sha ba Yallabai.’ Ya yi murmushi yayin da ya karɓi ruwan yana cewa ‘Kuma kin san ƙishirwan nake ji ba, don tun  daga gida muke waya da su Afaf har na zo nan suna ta surutu duk sun gajiyar da ni.’

    ‘Kai haba, surutun na su nawa yake?’ Ta faɗa tana dariya. Suka cigaba da hirarsu har zuwa lokacin da ya tashi tafiya wajen ƙarfe tara. Sai da ta raka shi bakin motarsa kafin ta yi masa sallama sannan tace ‘Baffana yace na gaya maka mutanen  gidanku za su iya zuwa maganar aurenmu ranar Asabar mai zuwa.’

    Take fara’ar sa ta ƙara faɗi, ya dube ta kamar ya rungume ta yana ta murmushin da ita ma yake saka ta murmushi. Yace ‘Allah Khadeeja! Kai amma na ji daɗi wallahi, in sha Allah ranar Asabar ɗin kuwa za su zo da kuɗin aure da sadaki gaba ɗaya.’ Ta yi dariya ‘Kai garaje, saurin me kake?’

    ‘To ai na kula ba kya tausayina, so kike ki yi ta ja min rai kina bari na sauro yana cinye ni saboda  zance.’ ya faɗa da murya kamar ta mai shagwaɓa. Ta yi dariya ‘To kwanan nan za ka huta in sha Allah.’ Suka yi sallama cike da farin ciki bayan ta sanar da shi gidan kakanta inda nan ne za su je maganar  auren nata.

    Cikin walwala yake tuƙin lokaci zuwa lokaci yana yi wa kansa murmushin jin daɗi saboda wannan labarin da Khadeeja ta sanar da shi. Watansu bakwai kacal da haɗuwa amma ya nutsu da hankalin yarinyar kuma ya yaba da tarbiyyar gidansu, ya tabbatar za ta kular masa da su Afaf kuma za ta tsaya a kan tarbiyyarsu ba tare da wata mugunta ba.

    Wata takwas kenan da rasuwar matarsa Asma’u, wadda ita ce ta haifa masa yara huɗu; Afaf mai  shekaru goma sha ɗaya, Habib mai shekaru tara, Nasreen mai shekaru shida sai Shukra mai shekaru uku. Ba wani rashin lafiya ta yi ba, haka kawai da daddare tace kanta yana ciwo don haka a gaba ya saka ta sai da ta sha ƙwayar Panadol sannan ta kwanta; sai dai da yake kwananta sun ƙare haka aka wayi gari sai gawarta. Ya yi matuƙar baƙin cikin rasuwar Ma’u kuma ya ji tausayin  kansa da yaransa, gaba ɗaya rayuwarsa ta tsaya saboda rashin Ma’u.

    Tunda aka kwana uku da rasuwar Asma’u mahaifiyarta ta tattara yaran ta tafi da su gida aka cigaba da kula da su. Can yake zuwa kullum ya ɗauke su ya kai su makaranta idan an tashi ya mayar da su. Ana kula da su sosai kuma suma suna jin daɗin zaman gidan sai dai shi ya fi so ya  rayu tare da yaransa.

    Da farko ya so ya kwashe su ya kai su gidan yayarsa; tunda mahaifiyarsa ta tsufa da yawa ba za su sami kulawa ba a wajenta. Amma sai mahaifiyar Ma’u tace ba za ta bayar  da yaran ba. Sun so su sami matsala domin da kwashe su ya yi ba tare da izininta ba ya mayar da  su gidan Yayar tasa, sai da manya suka shiga cikin maganar aka yi yarjejeniya a kan idan ya yi  aure zai je ya ɗebi yaransa. Don haka ba ƙaramin daɗi ya ji ba da Khadija tace an ba shi izini ya turo.

    Ya riga ya sanarwa Khadija idan ta tare zai dawo da yaransa kuma tayi na’am da hakan. Shi yasa ma wasu lokutan yake kwaso su ya kai mata su har suka saba sosai. Ya yi mata bayanin irin ƙaunar da yake musu da kuma yanda yake so ta dinga kula da su kamar ita ta haife su; kuma ta yi na’am  da hakan. Don ko a yanzun ma tana ƙoƙari wajen hidimarsu da jansu a jiki ga kyaututtuka, gashi  wata ran da kanta take masa waya ya kawo mata su.

    Duk da ya riga ya je gidan mahaifinsa da safe amma a daren ma haka ya koma cike da farin ciki  ya sanar da mahaifinsa cewa iyayen Khadija sun ba shi damar ya turo. Mahaifinsa yana zaune a  kan kafet a dakinsa ya dube shi bayan ya gama sanar da shi inda za a kai kuɗin yace ‘Shikenan  rigimar yara ta ƙare ko, ga amarya ga yaranka sai ka sami natsuwa.’

    Ya yi dariya ya sunkuyar da kai. Daga baya ya yi musu sallama ya wuce gidansa cike da farin ciki.

    Karanta Yadda Ake Lefe A Auren Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Kafuwar Ƙasar Qatar

    Tarihin Kafuwar Ƙasar Qatar

    Daga Ottoman Empire zuwa Mulkin Mallaka da Bayan ’Yancin Kai

    Gabatarwa

    Qatar ƙasa ce da ke Tekun Farisa (Persian Gulf), wadda ta samo kanta daga ƙarƙashin mulkin dauloli daban-daban har zuwa samun cikakken ’yancin kai a shekarar 1971. Tarihinta ya haɗa da tasirin Ottoman Empire, mulkin mallakar Birtaniya, da kuma gwagwarmayar da ta yi wajen bunƙasa tattalin arzikinta ta hanyar mai da iskar gas na halitta.

    1. Qatar a Zamanin Daular Ottoman

    Tun daga ƙarni na 16, yankin Qatar ya kasance a ƙarƙashin tasirin Daular Ottoman, bayan sun ƙwace ikon Tekun Farisa daga Mamluks a 1517. Duk da haka, ikon Ottoman bai yi ƙarfi sosai a yankin ba, musamman saboda nisan ƙasa da kuma tsananin tasirin ƙabilu na cikin gida.

    A ƙarni na 19, Sheikh Mohammed bin Thani, wanda daga baya ya zama uba ga gidan Al Thani, ya nemi tallafin Ottoman domin kare Qatar daga mamayar Bahrain da sauran makwabta.

    2. Mulkin Mallaka da Tasirin Birtaniya

    Bayan raunin da Daular Ottoman ta shiga a farkon ƙarni na 20, Qatar ta shiga ƙarƙashin tasirin Birtaniya. Yarjejeniyar Anglo-Ottoman ta 1913 ta tabbatar da janyewar Ottoman daga yankin.

    A 1916, Sheikh Abdullah bin Jassim Al Thani ya rattaba hannu kan yarjejeniyar da Birtaniya, wadda ta sanya Qatar ƙarƙashin kariya (protectorate). Wannan ya ba Birtaniya ikon kula da tsaro da hulɗar ƙasashen waje, yayin da gidan Al Thani ya ci gaba da sarauta a cikin gida.

    3. Durƙushewar Tattalin Arziki da Gano Mai

    Qatar ta dogara da kamun kifi da nemo lu’u-lu’u (pearling industry) har zuwa shekarun 1930. Rushewar kasuwar lu’u-lu’u saboda synthetic pearls daga Japan da kuma bala’in tattalin arziki na duniya ya jefa ƙasar cikin fatara.

    Sheikh Abdullah ya rattaba hannu da Anglo-Persian Oil Company a 1935, amma haƙar mai ta fara ne a hukumance a 1949 saboda Yaƙin Duniya na II. Wannan ya fara sauya tattalin arzikin Qatar daga talauci zuwa samun kuɗaɗen shiga.

    4. Hanyar Samun ’Yancin Kai

    A shekarun 1950–1960, kuɗaɗen mai sun fara canza tsarin rayuwa a Qatar. Bayan Birtaniya ta sanar da janyewarta daga yankin Gulf a 1968, Qatar ta fara tunanin shiga cikin United Arab Emirates, amma ta janye saboda sabani da Bahrain.

    A ƙarshe, a 3rd September 1971, Qatar ta ayyana ’yancin kanta kuma Sheikh Khalifa bin Hamad Al Thani ya zama Amir na farko a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta.

    5. Bunƙasar Tattalin Arziki Bayan ’Yancin Kai

    Bayan samun ’yancin kai, Qatar ta ci gaba da dogaro da mai. A shekarun 1980s zuwa 1990s, gwamnatin ƙasar ta karkata ga isakar gas na halitta (LNG) daga babban filin North Field, wanda shi ne ɗaya daga cikin manyan ajiyar gas a duniya.

    Wannan mataki ya bai wa Qatar damar zama ɗaya daga cikin ƙasashe mafiya arziki, tare da zuba jari a fannoni kamar:

    • Ilimi (Qatar Foundation, Education City).
    • Wasanni (FIFA World Cup 2022).
    • Jiragen sama (Qatar Airways).

    Kammalawa

    Tarihin Qatar ya nuna yadda ƙasar daga ƙaramin tsibiri da ke dogaro da kamun kifi da lu’u-lu’u ta koma cikin manyan ƙasashe masu arziki da tasiri a duniya. Hakan ya samu ne ta hanyar gwagwarmaya daga ƙarƙashin mulkin Ottoman zuwa Birtaniya, sannan ta yi amfani da albarkatun mai da gas wajen bunƙasa tattalin arzikin ta.

    Manazarta (References)

    [^1]: Rosemarie Said Zahlan, The Creation of Qatar (London: Routledge, 1979), shafi na 12–25.

    [^2]: Habibur Rahman, The Emergence of Qatar: The Turbulent Years, 1627–1971 (Kegan Paul International, 2005), shafi na 40–52.

    [^3]: Allen J. Fromherz, Qatar: A Modern History (Georgetown University Press, 2012), shafi na 64–70.

    [^4]: J.E. Peterson, Historical Dictionary of Saudi Arabia and the Gulf States (Scarecrow Press, 2003), shafi na 122–130.

    [^5]: Jill Crystal, Oil and Politics in the Gulf: Rulers and Merchants in Kuwait and Qatar (Cambridge University Press, 1995), shafi na 89–92.

    [^6]: Zahlan, The Creation of Qatar, shafi na 130–145.

    [^7]: Rahman, The Emergence of Qatar, shafi na 200–212.

    [^8]: Fromherz, Qatar: A Modern History, shafi na 150–160.

    [^9]: International Monetary Fund (IMF), Qatar: Economic Outlook Report (Doha, 2020).

    Karanta Gudunmawar King Abdulazeez Da Birtaniya Wajen Kafa Ƙasar Saudi Arabia

    Edita@rumasau-kallamu

  • Lissafi Akwai Zaƙi

    Lissafi Akwai Zaƙi

    Assalamu alaikum yara.

    Shin ko kun san cewa lissafi, wato Mathematics,  wani abu ne mai daɗin gaske?  Kuma idan ka iya za ka gane cewa yana da sauƙi. Kawai dai ɗan lokaci za ka ba da ka yi ya bita, sai ka ɗanƊani zumar lissafi.

    Daɗin daɗawa lissafi ilimi ne na yau da kullum. Misali- kullum sai an raba muku abu a gida. Wannan sai da lissafi. Idan kin je yawin sallah kin dawo za ki zo ki ƙirga kuɗin da kika samu. Wannan sai da lissafi. Baban ku zai ce tela ya gwada ku domin ɗinkin kayan salla. Wannan ma sai da lissafi. Idan Abban ki zai gina muku sabon gida sai an yi gwaje-gwaje da yawa. Duka wannan sai da lissafi. Ashe ko yara kun ga ilimin Math yana da matuƙar anfani. Ba abun mu guje shi ba ne. Kawai za mu ba da ɗan lokaci ne sannan kuma mu daina tsoro.

    Sai mun haɗu a gaba

    Domin karanta Yunƙurin Hausantar Da Kimiyya Da fasaha danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    اللهُمَّ رَبَّ السَّمَاوَاتِ السَّبْعِ ، وَرَبَّ الْعَرْشِ الْعَظِيمِ، كُنْ لِي جَاراً مِنْ (فُلَانِ بنِ فُلان) وَأَحْزَابِهِ مِنْ خَلَائِقِكَ ، أَنْ يَفْرُطَ عَلَيَّ أَحَدٌ مِنْهُمْ أَوْ يَطْغَى عَرَّ جَارُكوَجَلَّ ثَنَاؤُكَ ، وَلَا إِلَهَ إِلاأنت

    Allahumma rabbas samawatis sab’i wa rabbal arshil azeem, kun lee jaran min (fulan bin fulan) wa’ahzabihi min khala’iƙika, an yafruda alayya ahadun minhum au yadga, azza jaruka, wajalla sana’uka, wala’ila ha illa anta

    Ya Allah! Ubangijin sammai bakwai, kuma Ubangijin Al’arshi mai girma, Ka kasance Mai tsari gare ni daga (wane ɗan wane), da dukkan rundunarsa daga cikin halittunka kar wani daga cikinsu ya yi gaggawar azaba a gare ni, ko ya ƙetare haddi. Kariyarka ta buwaya, kuma Yabonka ya girma, kuma babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

    اللَّهُ أَكْبَرُ، الله أعَزُّ مِنْ خَلْقِهِ جَمِيعاً ، اللهُ أَعَزُّ
    مِمَّا أَخَافُ وَأَحْذَرُ ، أَعُوذُ بِاللهِ الذي لا إلَهَ إلاّ هُوَ ، الْمُمْسِكِ السَّمَاوَاتِ السَّبْعِ أَنْ يَقَعْنَ عَلَى الأَرْضِ إِلا بِإِذْنِهِ ، مِنْ شَرِّ عَبْدِكَ (فَلان ، )وَجُنُودِهوَأَتْبَاعِهِ وَأَشْيَاعِهِ مِنَ الْجِنِّ وَالإِنسِ. اللهُمَّ كُنْلِي جَاراً مِنْ شَرِّهِمْ ، جَلَّ ثَنَاؤُكَ وَعَزَّ حَاَرُكَوَتَبَارَكَ اسْمُكَ ، وَلاَ إِلَهَ غَيْرُكَ (ثلاث مرات)

    Allahu akbar Allahu a’azzu min khalƙihi jami’an,Allahu a’azzu mimma akhafu wa ahzar, a’uzu billahil lazee la’ilaha illahu, almumsikis samawatis sab’i an yaƙa’ana alal ardi illa bi’iznih min sharri abdika (fulan)wajunudihi wa’atba’ihi wa’ashya’ihi minal jinni wal’ins. Allahumma kun lee jaran min sharrihim, jalla sana’uka wa’azza jaruka, watabarakas muka, wala’ilaha gairuka.(salasa marraat)

    Allah Shi ne Mafi girma. Allah Shi ne Mafi buwaya daga dukkanin halittarsa. Allah Shi ne Mafi buwaya daga abin da nake jin tsoronsa kuma nake shayinsa. Ina neman tsarin Allah, Wanda babu abin bautawa da gaskiya sai Shi, Mai rike sammai daga su ruguzo a kan kasa sai da Izininsa, daga sharrin bawanka wane (ya ambaci sunansa), da rundunarsa, da mabiyansa, da kungiyoyinsa na aljanu da mutane.

    Ya Allah! Ka zamo Mai tsari gare ni daga sharrinsu. Yabonka ya girma, kuma Kariyarka ta buwaya, kuma alherin Sunanka ya yawaita, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba Kai ba. (Sau uku)

    Domin karanta Yadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take danna nan 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Maganin Damuwa Da Baƙin Ciki

    Addu’ar Maganin Damuwa Da Baƙin Ciki

    اللّهُمَّ إِنِّي عَبْدُكَ ابْنُ عَبْدِكَ ابْنُ أَمَتِكَ، نَاصِيَتِيبيَدِكَ ، مَاضٍ فِيَّ حُكْمُكَ، عَدْلٌ فِيَّ قَضَاءُكَ أسْأَلُكَ بِكُلِّ اسْمٍ هُوَ لَكَ سَمَّيْتَ بِهِ نَفْسَكَ أَوأَنْزَلْتَهُ فِي كِتَابِكَ ، أَوْ عَلَّمْتَهُ أَحَداً مِنْ خَلْقِكَ أَوْ اسْتَأْثَرْتَ بِهِ فِي عِلْمِ الْغَيْبِ عِنْدَكَ أَنْ تَجْعَلَ
    الْقُرْآنَ رَبيعَ قَلْبِي ، وَنُورَ صَدْرِي ، وَحَلاءَحُزْنِي وَذَهَابَ هَمِّيَْ

    Allahumma inni abduka inbnu abdika ibnu amatika,nasiyatee biyadika,madin fiyya hukmuka, adlun fiyya ƙada’uka, as’aluka bi kulli ismin huwa laka sammaita bihi nafsaka au anzaltahu fee khitabika, au allamtahu ahadan min khal’ƙika awistaasarta bihi fee ilmil gaibi indaka an taj’alal ƙur’ana rabee’a ƙalbee,wa nura sadree wajala’a huznee wazahaba hammee.

    Ya Allah! Ni bawanka ne, kuma ɗan bawanka, kuma ɗan baiwarka. Makwarkwaɗata a Hannunka take, hukuncinka zartacce ne a kai na, kuma ƙaddararka gare ni mai adalci ce. Ina roƙon Ka da kowane Suna naka, Wanda Ka ambaci Kanka da Shi, ko Ka saukar da Shi a cikin Littafinka, ko Ka sanar da Shi ga wani daga cikin halittarka, ko Ka keɓance Kanka da saninsa a cikin ilimin da ke da ke wurin Ka, da Ka sanya Alkur’ani ya zama kaka ga zuciyata, da haske ga ƙirjina, da kwaranyewa ga baƙin cikina, da kuma mai tafiyar da damuwata.

    اللّهُم إنِّي أَعُوْذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحُزْن، وَالْعَجْز وَالْكَسَلِ وَالْبَحْلِ وَالْجُبْنِ ، وَضَلْعِ الدَّيْنِ وَغَلَبَةِالرِّجَال

    Allahumma inni a’uzu bika minal hammi walhuzin, wal’ajzi walkasal walbukli waljubni, wadal’il deeni wagalabatir rijaal.

    Ya Allah! Ina neman tsarinka daga damuwa, da baƙin ciki, da gajiyawa, da lalaci, da rowa, da ragwantaka, da nauyin bashi, da rinjayen mazaje.

    Karanta Addu’ar Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari

    Edita@rumasau-kallamu