Category: Al’adu

Wannan shafin yana koyar da yadda al’adun Hausawa suke wanda ya ƙunshi tarbiya da addinin su, da ma sauran al’adu  da ba na Hausawa ba, a cikin harshen Hausa kuma a sauƙaƙe.

WikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara. Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa.

  • Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa

    Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa

    Waƙoƙi : Masana sun yi ƙoƙarin bayyana asalin samuwar waƙoƙi baka a ƙasar Hausa.

    Daga ciki akwai ra’ayin Satatima (1999:30) inda ya bayyana cewa: “Al’ummar ƙasar Hausa sun sami basirar kiɗa..

    Harda waƙa daga tsofaffin daulolin Ghana da Mali da Songhai wanda wasu sassa na ƙasar Hausa suka kasance ƙarƙashin mulkinsu

    kafin ƙarni na sha tara.

    Masu wannan ra’ayi har sun kai ga cewa daga waɗannan tsofaffin dauloli Hausawa suka samu kayan kiɗa irinsu kakaki, wanda aka samu daga Songhai cikin ƙarni na sha shida. Algaita kuwa an samo ta ne daga Songhai da Mali”.

    A wurin Gusau (2003:5-6) kuwa, ya kawo hasashe guda uku waɗanda yake ganin su ne asalin waƙar baka.

    Waɗannan hasashe kuwa su ne:

    Ra’ayi na farko, suna ganin ana jin ɗan’adam ya ƙagi waƙa ne tun lokacin da ya fara neman abinci ta hanyar farauta, daga nan ya gano noma sai waƙa ta ƙara haɓaka.

    Ra’ayi na biyu kuwa, an nuna cewa, ana ganin waƙa ta samo asali ne daga wani maroƙi ‘Sasana’.

    Domin haka, a wannan ra’ayi ana jin makaɗan Hausa jikokin wannan mutum ne.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Kiɗa da Makaɗi danna nan

  • Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa

    Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa

    Wannan bincike dai ya yi ƙoƙarin binciko wasu muhimman al’amura; game da wasu matsaloli da suka addabi gidajen mafi yawan Hausawa; inda binciken ya gano musabbabinsu ta amfani da wasu waƙoƙin Hausa na Situdiyo.

    Matsalolin Aure -Daga cikin abin da binciken ya gano, ya bayyana lalle akwai matsaloli a tsakanin ma’aurata a Ƙasar Hausa, sannan ya fayyace matsalolin ta hanyar amfani da zantukan mawaƙan baka na Situdiyo.

    Binciken dai ya gano yadda mawaƙan baka na Situdiyo suke taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma ta hanyar lalubo matsalolin da suka addabe su, da kuma bayyana su cikin hikimar zance irin tasu.

    Har wa yau, binciken ya nuna waƙa yalwatacciyar hanya ce ta isar da saƙo ba jefa nishaɗi kurum a tsakanin al’umma; ta yadda da ita za a iya gano matsalolin da suka dabaibaye al’umma; har ma a yi kirdadon hanyoyin magance matsalolin.

    Binciken dai ya ƙara tabbatar da cewa aikin waƙa; aiki ne na fasaha da bincike ta yadda ba haka kawai da ka ake yin waƙa ba; har sai an yi bincike yayin da ake son isar da wani saƙo; ko kuma yin ishara ko hannunka mai sanda ko kuma faɗakarwa a cikin waƙoƙin baka na Situdiyo.

    Wani babban abu kuma muhimmi da wannan binciken ya gano shi ne muhimmancin mawaƙa da kuma; ƙoƙarin taƙaituwa zuwa ga abin da suka faɗa a matsayin ita ce matsala ga wani rukuni na al’umma; ko wani abu da yake faruwa a tsakanin al’umma.

    To mawaƙa ma na iya tsinkayowa da kuma ayyana basirarsu wajen sanar da jama’a a waƙe.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta bayani a kan Ma’anar Aure danna nan

    Domin karanta bayani akan Abin da Bincike Ya Gano Game Da Matsalolin Aure A Ƙasar Hausa danna nan

  • Muhallan Da Ake Waƙoƙin Fiyano Na Hausa

    Muhallan Da Ake Waƙoƙin Fiyano Na Hausa

    Muhallan da ake waƙoƙin Fiyano na Hausa su ne wuraren da mawaƙan Hausa masu amfani da fiyano suke rera waƙoƙinsu.

    Muhallan Fiyano su ne kamar haka:

    1. Fina-finan Hausa

    Wato irin fina-finan da ake yi a ƙasar Hausa, ko kuma Hausawa suke yi, ko kuma ake yi da harshen Hausa; To a cikinsu akan samu kaɗe-kaɗe na fiyano; da kuma waƙoƙin da aka yi amfani da fiyano wajen aiwatar da su.

    2. Tarukan Siyasa

    A nan ya shafi dukkanin wani dandazon mutane da za a tara a dalilin siyasa, wanda a wannan wuri akan samu waƙoƙin da aka rera da kiɗan fiyano, a wasu lokutan ma akan samu makaɗan fiyano a wurin.

    3. Bukukuwa

    Dukkanin wani nau’i na biki, sawa’un bikin suna ne ko aure ko wanin waɗannan. A nan, za a iske waƙoƙi da dama da aka rera su ta hanyar amfani da fiyano. A wani lokaci kuma, akan samu makaɗan fiyano a wuraren bukukuwa domin yin kiɗan fiyano.

    4. Majalisi

    Wannan kuwa ya shafi wuraren yabon Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) da halifofinsa da sauran mutanen kirki. A wannan muhalli ma, akan yi amfani da fiyano wajen yin kiɗa ga waƙar da aka yi ta yabo.

    5. Tallace-Tallace

    Dukkanin wani nau’i na tallace-tallace, sawa’un tallar magunguna ne ko wasu abubuwa ne, kamar robobi da kayan abinci da yaduna da sauransu. To a nan, su ma akan yi musu waƙoƙi ta hanyar amfani da kiɗan fiyano

    6. Kafofin Yaɗa Labarai

    Wannan ya shafi kafofin sadarwa kamar gidajen radiyo da talabijin, domin sukan yi amfani da kiɗan fiyano a yayin da wani shiri ya ƙare kuma suna son sanya wani. Haka zalika, sukan yi amfani da shi domin tallata wani abu da wani kamfani zai ba su.

    7. Yabon Masoya

    Ma’abota soyayya tsakanin maza da mata sukan yi amfani da fiyano wajen yabon junansu, wato za a iske budurwa ta yi wa saurayinta waƙa, kuma ta je an yi mata kiɗan fiyano, ko kuma shi ya mata waƙa, kuma ya je an masa kiɗa da fiyano.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Kiɗan Fiyano A Wajen Hausawa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta bayani a kan Asalin Kiɗan Fiyano danna nan

    Domin karanta bayani akan Misalan Waƙoƙin Hausa Na Fiyano danna nan

  • Misalan Waƙoƙin Hausa Na Fiyano

    Misalan Waƙoƙin Hausa Na Fiyano

    Zainab (2009:84) ta ce “Waƙoƙin fiyano na Hausa su ne waƙoƙin da suka samu canje-canje; daga kayan kiɗa na gargajiya zuwa kayan kiɗa na zamani; kamar fiyano da jita da sauransu”.

    Kamar yadda aka ambata a sama, yawancin mawaƙan wannan zamani suna amfani da fiyano ne wajen kaɗe-kaɗen waƙoƙinsu, don haka kenan waƙoƙin da suka samar na kiɗan fiyano ne.

    Cikin irin waɗannan waƙoƙin akwai:

    • Sakarkari ta Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa)
    • Rayuwa tana faruwa ta Fati Musa Ƙofar Wambai
    • Gatana ta Malam Nafi’u Nguru
    • Ku Ɗinka Hijabi ta Malam Ibrahim Lalula Nguru
    • Bulaliya ta Abubakar Sadiq Suwa’ilu
    • Rawa-rawa ta Naziru M. Ahmad
    • Almajiri ta Muhammad Sani Aliyu
    • Ƙarshen Tika-tika Tik ta Aliyu Auta Masani, Nguru
    • Ku Yi Haƙuri ta Jibrin Muhammad Jalatu
    • Waƙar Rigar ‘Yanci ta AbdulAziz Abdullahi Ningi

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Kiɗan Fiyano A Wajen Hausawa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Muhallan da Ake Waƙoƙin Fiyano na Hausa danna nan

    Domin karanta bayani akan Ire-iren Kiɗan Fiyano danna nan

  • Masu Yin Kiɗan Fiyano A Ƙasar Hausa

    Masu Yin Kiɗan Fiyano A Ƙasar Hausa

    Bayan samun fiyano a ƙasar Hausa, an samu makaɗa da dama da suka sayo ta; kuma suka buɗe shaguna a wurare daban-daban domin yin kaɗe-kaɗe na fiyano.

    Daga cikin masu kiɗan fiyano a ƙasar Hausa akwai:

    1. Ahmad Mahmud Gusau

    2. Basiru Bala Maigoro, Sokoto

    3. Dauda Adamu Kahuta (Rarara)

    4. Faruq Nagudu

    5. Rabi’u Dalle

    6. Firdausi Yar Dubai

    7. Aminu Garba Maidawayya

    8. Usaini Kaɗo Ƙofar Na’isa

    9. Zainab A Baba

    10. Adamu Hassan Nagudu

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Kiɗan Fiyano A Wajen Hausawa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mawaƙan Da Ake Yi Wa Kiɗan Fiyano danna nan.

    Domin karanta bayani akan Muhallan Da Ake Waƙoƙin Fiyano Na Hausa danna nan

  • Samuwar Fiyano A Ƙasar Hausa

    Samuwar Fiyano A Ƙasar Hausa

    Gusau (2008:6) ya bayyana fiyano wani abin kiɗa ne baƙo ga Hausawa da suka samu ta hanyar hulɗa ta Turawa”.

    Samuwar waƙoƙin fiyano na Hausa ya kawo wani sabon al’amari ga manazarta waƙoƙin Hausa. Hakan kuwa ya faru ta yadda waƙoƙin suka zo da wata siga. Ga su kamar rubutattun waƙoƙi, amma sun yi kama da waƙoƙin baka.

    Binta (2011:77)

    Ta bayyana cewa, “Shigowar kiɗan fiyano zuwa ga Hausawa; yana da dangantaka da sha’awar kallo da sauraron kaɗe-kaɗen fina-finan Indiya da Hausawa suka tsinci kansu a ciki.

    Domin kuwa waɗannan fina-finai na Indiya su ne suka zamanto fitilu masu haske ga yawancin masu shirya fina-finan Hausa.

    Ƙoƙarin kwaikwayon kaɗe-kaɗen waɗannan finafinai ne yasa Hausawa suka dinga amfani da kiɗan fiyano suna rera waƙoƙin Hausa, suna sakawa a cikin fina-finai da ake kira na Hausa.

    Ado Ahmad Gidan Dabino ya fito da fim ɗinsa mai suna ‘In Da So Da Ƙauna’; wanda aka yi kiɗan fiyano na farko a fim”.

    Gusau (2011:8)

    Ya bayyana cewa, “Daga bisani, bayan Hausawa sun iya karatu da rubutu na Ajami da kuma na Boko, sai aka samu wasu mutane suna rubuta waƙoƙi, amma sai su ɗora musu rauji na karin murya, sa’an nan su rera su tare da amon kiɗa (sauti na kiɗa)…

    Har wayau, kayan kiɗan da ake amfani da su wajen rera waɗannan waƙoƙi sun ƙunshi kayan kiɗa na zamani ne kamar: Mandiri da fiyano da jita da gangunan Turawa da makamantan su”. 

    Har akan jinjina kafin a iya rarrabewa tsakanin waƙoƙin na baka ko rubutattu. Wanda ya zama wani ƙalubale ga manazarta waƙoƙin Hausa. Domin kowa da yadda yake kallon su. Wasu na yi musu kallon waƙoƙin baka, wasu na cewa rubutattun waƙoƙi ne. Wasu kuwa sun kira su da waƙoƙin zamani.

    Waƙoƙin fiyano na Hausa sun samu karɓuwa sosai da sosai wajen mutane, don kuwa waƙoƙin kullum sai ƙara bazuwa da karɓuwa suke yi. Kuma suna samun masu saurare, musamman matasa maza da mata. Haka kuma, kullum manazarta suna sauraren su, suna aiki a kansu.

    Yaɗuwar Waƙoƙin Fiyano

    Yaɗuwar waɗannan waƙoƙi na fiyano ta nuna cewa, sun samu karɓuwa, kuma sun yi tasiri. Saboda duk abin da ba ka da sha’awa a kansa, ba za ka mayar da hankali a kai ba. Don haka, yawan jin su a ko’ina, a wayoyin hannu da motoci da kantuna da gidajen rediyo na gida da na waje, ya nuna cewa sun samu karɓuwa.

    Daɗin daɗawa, waƙoƙin a kullum ƙara yawaita suke yi, mawaƙan na ta ƙara samun basirar rera waƙoƙin. Har ta kai sukan yi irin waɗannan waƙoƙi a ƙungiyance.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Kiɗan Fiyano A Wajen Hausawa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wuraren Da Ake Kiɗan Fiyano (Situdiyo) danna nan

  • Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa

    Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa

    Auren Hausawa – Auren nan na da ma’anoni da dama daga masana; domin sun yi ƙoƙarin faɗaɗa ma’anar zuwa ga ɓangarori da dama; amma a nan za mu kalli ma’ana guda ɗaya wadda ta dace da batunmu.

    Auren Hausawa – CNHN (2006:22) ya bayyana shi da cewa, “Dangantaka tsakanin namiji da mace ta hanyar shari’a”.

    Domin ƙarin bayani a kan aure danna nan https://wikihausa.com.ng/maanar-aure/

    A nan, za mu iya cewa, aure nufin haɗuwar mutane biyu (namiji da mace) bisa wasu sharuɗa da shari’a ta gindaya domin tabbatar da zaman tare na har abada.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahim Baba(Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Muhimmancin Aure a Ƙasar Hausa danna nan

    Domin karanta bayani akan Manufar Rayuwar Aure A Addini Da Wayewar Zamani danna nan

  • Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa

    Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa

    Alhassan (1981:1) ya bayyana Ƙasar Hausa ta asali tana Afirka ta Yamma; a farfajiyar dake tsakanin hamadar sahara da dazuzzukan da suka doshi gaɓar tekun Atilantika daga kudu.

    Kuma ana kiran Ƙasar da suna Sudan ta Yamma, wato tsakanin Tafkin Chadi da gwuiwar Kogin Kwara daga yamma

    A bayanin Ibrahim (1982:1); ya nuna cewa Ƙasar Hausa tana shimfiɗe ne a can Arewacin Nijeriya da kuma Kudancin Jamhuriyar Nijar a cikin Afirka ta Yamma. Daga gabas ta yi iyaka da ƙasashen Borno;

    Haka ma daga yamma ta yi iyaka da ƙasashen Dahomey a gaɓar Kogin Kwara. Daga arewa ta yi iyaka da Ƙasar Adar a cikin Jamhuriyar Nijar; Daga wajen kudu kuma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari da kuma ƙabilun kudancin Zariya da na kudancin Bauchi.

    A wannan zamani a iya cewa Ƙasar Hausa yanki ne wanda ya mamaye dukkan Jihar Kano da Katsina da Arewaci Jihar Kaduna da wasu ɓangarorin Bauci da Gwambe da Neja da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar.

    Idan aka tayar da saiti daga Arewa zuwa Kudu; Ƙasar Hausa tana farawa daga Azbin har ya zuwa kusurwar Arewa maso Gabas da tsaunukan Jos. 

    Daga nan sai ta shararo ta yi arewa maso yamma ta yi mahaɗa da ƙaton rafi na kogin Kabi. Daga wannan wuri ta karkata ta nufi arewa maso gabas har Azbin. (Birnin-Kudu, 2002:11-12 a cikin Sallau, 2013:481).

    Ƙasar Hausa wadda take shimfiɗe a shiyyar Sudan ta Tsakiya, a tsari na gargajiya a iya cewa ta haɗa da ƙasashen sarakunan Katsina, Kano, Daura, Zazzau, Kabin Argungu, Gwandu, Gumel, Haɗejiya, Ƙwanni, Maraɗi da Tassawa.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo Wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Bahaushe? danna nan

    Domin karanta bayani akan AL’ADAR BAHAUSHE danna nan

  • Wane Ne Bahaushe?

    Wane Ne Bahaushe?

    Idan muka juya kan sanin wane ne Bahaushe kuwa? A iya cewa mafi yawancin mazauna Ƙasar Hausa su ne al’ummar Hausawa.

    Amma akwai wasu ƙabilu waɗanda suka yi kaka-gida a wannan Ƙasa ta Hausa; har hakan ya sanya suka koma Hausawa a harshe da al’adu da kuma adabi.

    Waɗannan ƙabilu kuwa sun haɗa da Fulani, Buzaye, Barebari, Nufawa, Yarbawa da sauransu. Amma Ibrahim (1981:1) ya bayyana cewa Hausawa su ne mutanen dake zaune a Ƙasar Hausa tuntuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa.

    A ra’ayin Adamu (1983:3) kuwa, na ganin Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabantansu suka yi daga Ƙasar Hausa; zuwa wasu sassa dake maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da Ƙasar Hausa; koda kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adun Hausawa, sun ɗauka su Hausawa ne.

    Misali, Abakwariga dake zaune a Jihar Taraba ta Nijeriya da kuma wasu dake ikirarin cewa su Hausawa ne; waɗanda ke zaune a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Faso da Mali.

    Magaji (1986:3), ya nuna Hausawa dai su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa. Haka kuma dukkanin al’adunsu da ta’adunsu na Hausa.

    Haka kuma addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu.

    A ra’ayin Sallau (2000:71) kuwa, na ganin waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi zuwa Ƙasar Hausa sun manta da harshensu da adabinsu da al’adunsu na asali sun ɗauki na Hausawa. A taƙaice sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’ada. Misalin ire-iren waɗannan mutane sun haɗa da Barebari, Kambarin Barebari, Barebarin Katsina da Buzaye da wasu Fulani.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ladubban Addu’a A Musulunci danna nan

  • Yadda Siffofin Masu Ba Da Tarbiya Suke

    Yadda Siffofin Masu Ba Da Tarbiya Suke

    Masu hikima suna cewa: In mutum ya ce zai ba ka riga to ka dubi ta jikinsa kuma “wanda ba shi da abu ba zai iya bayar da shi ba.”

    A kan haka ya wajaba a kan duk wani wanda nauyin tarbiyya ya hau kansa iyaye, malamai da shugabanni ya kasance mai tarbiyya ne shi a kan kansa.

    Wani mutum ya tambayi malamansa cewa ya koya masa yadda ake yin tarbiyyar ‘ya’ya a lokacin ‘yarsa ta fari tana wata ɗaya da haihuwa, sai malamin ya ce da shi ai kuwa ka makara. Saboda ita tarbiyya tun kafin a yi aure ake fara yin ta ba sai an haifi ɗan ba.

    Malamai sun yi bayanin siffofin da ya wajaba mai ba da tarbiyya ya siftantu da su in dai yana son ya sami nasarar aikin tarbiyya kuma ya yi tasiri.

    A Taƙaice Ga Waɗannan Siffofin

    Ya kasance mai haƙuri da juriya da naci, kada ya ɗauka cewa tarbiyya aiki ne na sha yanzu magani yanzu.

    1. Ya yarda cewa haƙƙi ne wajibi a kansa. Ya rinƙa jin haka a ransa a kowane lokaci. wannan zai hana shi yin watsi da tarbiyyar iyalinsa.
    2. Ya rinƙa sa ido da lura da bibiya, saboda tarbiyya kamar dashe ne in ba a bibiyarsa da kula da shi sai ya bushe ya lalace ko dabbobi da ƙwari su kashe shi.
    3. Yi dan Allah (Ikhlasi) kada mutum ya nemi wani lada ko yabo a kan tarbiyyar ‘ya’yansa da iyalınsa sai a wurin Allah kawai. Saboda haka ban da alfahari ban da fariya ban da gorantawa ‘ya’ya da iyali ban da raina ‘ya’yan wasu.
    4. Tarbiyya tana buƙatar tausasawa da bin al amura sannu-sannu daki- daki, tsanani da gallazawa kawai ba sa kawo gyara, dole sai ana cizawa ana hurawa.
    5. Mai ba da tarbiyya shugaba ne, saboda haka ya kamata ya siffantu da siffofi na shugabanci ya kasance jarumi, mai adalci, mai kwarjini, mai iya ɗaukar nauyin waɗanda yake jagoranta, mai kyauta, sauƙin kai da saussauci a inda ya dace, mai tsanani a inda ya dace, da dai sauran siftofi na jagora ko shugaba na gari.
    6. Harkar tarbiyya ba abu ne da ake yinsa da ka ba, lallai sai an yi karatun tarbiyyar saboda tana farowa, tun kafin a auri uwar da har ta haife shi ya balaga, za a yi masa tarbiyyar jiki, Imani, halaye, ladabai, haƙƙoƙi, siyasa da sha’awa. To in ba ilimi ta yaya wannan aiki zai yiwu.
    7. Wajibi ne mai tarbiyya ya kasance mai adalci.
    8. Ya kasance yana ɗaukar matakai na gasakiya a komai ya daidai ta tsakanin tsanani da sassauci da sakin hannu da rowa, ya kasance tsaka-tsaki a komai.

    9 Wanda yake da tsananin rowa da ƙanƙamo da masifar son abin duniya ba zai iya tarbiyya ba. Dole ya kasance mai sakin hannu da sakin fuska. Kada ya ɗauka asarar kuɗi yake yi in ya biya kuɗin makaranta ko ya sai abinci da sauran buƙatun ‘ya yansa.

    10 Ya kasance mai nuna ƙauna ta gaskiya ga’ ya’yansa maza da mata ‘ya’yan uwar gida da na amarya.

    11 Dole ne mai tarbiyya ya kasance nutsattse mai hankali da tsari a rayuwarsa.

    12 Wajibi ne mai tarbiyya ya kasance ya siffantu da kyawawan halayen da yake umarni da a aikata su, yana nisantar munanan ayyukan da yake hanawa. Kada ya zama fitina ga waɗanda suke a ƙarkashinsa.

    13 Ya kasance mai kyakkyawan fata da sakakkiyar zuciya kada ya rinƙa camfa abubuwa ko saurin siƙewa da fidda rai kan samun nasara.

    14 Ya kasance mai jin ƙai da tausayi.

    15 Ya kasance mai tsoron Allah (Taƙawa) wannan sharuɗɗa muhimmancinsa ya gawurta.

    Karanta Masu Rera Waƙa

    Edita@rumasau-kallamu