Alamomin Tsufa.

0
573

Da zarar tsufa ya cimma mutum, alamominsa za su bayyana a tare da shi, kamar:

a. Yanƙwanewar fata da tattarewa.
b. Tsanantar cututtukan gado kamar hawan jini, ciwon shuga, olsa mai riƙe baya da ƙirji (basir).
c. Raunin ƙwayoyin dake ba wa jiki garkuwa.
d. Ciwon gaɓoɓi. Da dai sauransu.

Saboda haka, babu wanda zai tsufa wani mai ba da magani ko likita ya ba shi maganin da zai tafiyar masa da tsufansa ko gajiyawar da ya yi.

Bayan haka, an karɓo Hadisi daga Abu Hurairi Allah ya yarda da shi ya ce: “Haƙiƙa ya ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana cewa “Tabbas a habbatus sauda (baƙin algaru) akwai waraka daga kowane ciwo sai dai mutuwa.” Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.
Wato babu wani magani da yake hana mutuwar bawa idan lokacin mutuwarsa ya yi, kuma yadda tsufa ba shi da magani, to haka ma mutuwa ba ta da  magani.
Bayan haka, malaman Hadisi suna fuskantar da maganar da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya yi ta cewa akwai waraka daga kowane ciwo a tattare da habbatus-sauda cewa, wannan bayani ba Manzon Allah ya shafi cututtukan da sanyi yake sabbabawa ne, ba kowane irin ciwo ba.

Domin karanta cikakken bayani a kan Amfanin Kaho danna nan.

Wannan bayanin an ciro Shi ne daga littafin Akula Da Lafiya Wanda Abubakar Abbas Ibrahim ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceMuhimman Abubuwan Da Suke Inganta Lafiya.
Labarin na GabaSunayen Manzon Allah ( Sallallahu alaihi wassallam)