Yadda Ake Aikin Hajji A Sauƙaƙe

0
3637

Hajji wajibi ne a kan kowanne musulmi sau ɗaya a cikin rayuwar mutum. Matuƙar akwai hali, saboda umarni ne na  Allah (SWT) “….Allah na da haƙƙi a kan mutane na ziyarar ɗakin ( ka’aba) ga wanda ya samu ikon zuwa gare shi… “. ( Aali Imraan :197).

“Kuma ku cika Hajji da Umra domin Allah… ( Baqara:196).
Waɗanda suke da damar yin aikin Hajji, amma kuma suka ƙi yi, haƙiƙa sun yi babban saɓo, hakan na nuna kafurci. Ga wanda ya sauke aikin Hajjinsa na farko, to lalle ya sauke farali, ƙara yin aikin Hajji bayan sauke farali, to wannan ƙarin ya zama nafila.

“Karɓaɓɓan aikin Hajji na wanke dukkanin zunubai”

MIKATI: Annabi (SAW) ya ce :”Waɗannan keɓantattun wurare ne da ake ce musu “Mawaqit” ko miƙati. Bai halatta ga maniyyaci ya wuce waɗannan wurare ba tare da ya yi harama ( niyya, sa ihrami) ba.

Mafi yawan mutanen Afirka na tafiya ne ta jirgin sama, waɗanda ke sauka a garin Madina ko Jidda, saboda haka miƙatinsu ɗaya ne da mutanen Madina, idan a Madina suka sauka, haka kuma idan a Jidda suka sauka, to miƙatinsu shi ne ake kiran Shi da Aljuhfa. Shi wannan wuri hamada ce ana kiran Garin  Juhfa, kamar yadda yake a hoto na kasa.

Miƙatinka ya danganta daga inda ka taso ko inda za ka sauka, don haka, duk inda ka sauka sai ka tambayi miƙatinsu.

HARAMA (IHRAAM ): Kowanne maniyyaci ya shiga ihrami daga miƙatin da yake kan hanyar sa. Ga maza za su cire tufafinsu, su sa Ihrami guda biyu. Wato gyauto da za su rufe ƙasan jikinsu, mayafin kuma a rufe ragowar saman jikinsu.

Mata kuwa, za su sa suturarsu ta al’ada su rufe ko’ina ban da fuska da hannayensu. Kuma ba za su sa liqabi ba da safar hannu.

NIYYA : Ana yin niyya ne a miƙati yayin sanya ihrami, Annabi (S. A. W) ya ce :”Kowanne aiki sai da niyya ..”.
Mutum zai yi niyya a zuciya sannan ya faɗi :”Labayk Allahumma Labayk. ”
Da wannan mutum ya fara rukunan Umra kenan. Kamar yadda ake buɗe sallah da fadin Allahu Akbar.

Ka ga mai harama zai ce :”Labayk Allahumma bi-umrah ” . Ko “Labayk Allaahumma bi-hajj ” Ga mai yin Tammattu’i wato haɗa Umra da Hajji.
Wanda duk yai harama da Umra,  dole ya kammala Umararsa, sannan ya cire Ihraminsa. Ya zauna ya jira a Makka har sai Takwas ga Dhul-Hijjah . Sai ya sake sa Ihraminsa a nan Makka.
Mai yin Tammattu’i akwai bukatar yai yanka. Wato yanka dabbarsa (hadaya)  a wajen aikin Hajji ranar Goma ga watan Dhul-Hajj.
“…To, idan kuna cikin aminci, to, wanda ya ji daɗi da Umra zuwa Hajj, sai ya biya abin ya da sauƙaƙa daga hadaya… “.(Baqara :196).
Rukunan farko na Umra su ne: sanya ihrami. Sai Niyya a zuciya, sai kuma harshe ya furta “Labbayk Allaahumma bi-Umra ” ko ” Labbayk Umrah “.
Wanda duk ya shiga ihraminsa to ba zai yi waɗannan  abubuwan ba,  su ne :
Saduwa da iyali.

Sanya Tufafi ɗinkakke ga maza.
Ba sa wando,  riga, takalmi,  safa…
Ma’aurata ba za su yi Sumba,  runguma  da ire-iren waɗannan ba.
Saboda faɗin Allah :
“…To,  wanda ya yi niyyar Hajji a cikinsu, to,  babu jima’i,  kuma babu fasiƙanci, kuma Babu jayayya a cikin Hajji… “.
(Baqara:197).Ka na gama harama sai kuma Talbiyya. Wato faɗin :
Labbayk Allaahumma Labayk, Labbayk laa sharika laka Labbayk, Innal Hamda Wa ni’imata laka wal mulk laa sharika lak.  Na amsa maka Ya Ubangiji! Na amsa maka. Na amsa maka,  ba Ka da abokin tarayya. Na amsa maka. Haƙiƙa Godiya da Ni’ima duk naka ne,  da mulki. Ba Ka da abokin tarayya.
Za ka ci gaba da talbiyya tun daga miƙati har zuwa Makka. Za ka Ɗaukaka murya ka yi ta faɗa. Har ka isa Makka cikin masallacin harami, ka fuskanci ka’aba. Sai Rukuni na biyu na Umra.

Ɗawafin ɗakin Allah na nufin yin zagaye bakwai. Za ka fara ɗawafin da ga bakin dutse. Kana mai faɗin kabbara “Allahu Akbar ” . Sai ka ci gaba da zikiri da addu’a. Idan ka zo tsakanin kusurwar Rukunul Yamani da Hajarul Aswad. Sai a kowanne kewaye na ɗawafinka, ka dinga faɗin wannan addu’ar :
” Yaa Ubangijinmu!  Ka ba mu mai kyau a duniya da Kuma mai kyau a lahira, kuma ka kiyashe mu azabar wuta “. (Baqara:201).
Idan maniyyaci ya samu dama, sai ya sumbaci bakin Dutse. Ko kuma ya shafa shi da hannunsa. Ko da wani abu sai ya sumbaci abin. Ko Idan akwai taron mutane sosai. Kawai idan ya yi nuni da hannunsa  ma ya isa. Ba a buƙatar ka cutar da su. A wajen ƙoƙarin sai ka sumbaci baƙin Dutsen.
Wannan ɗawafin Qudum shi ne ake kira ɗawafin isowa. Zagayen ukun farko na ɗawafin ana yinsa cikin hanzari, amma fa ba gudu ba. Sunnonin wannan ɗawafi ga namiji ya kwaye kafaɗarsa ta dama. Wato ya sa tsakiyar mayafinsa ƙarƙashin hamatarsa ta dama. Gefen mayafi biyo kuma ya sa su a kan kafaɗarsa ta hagu.
Bayan ka gama ɗawafi sau bakwai. Sai ka yi sallah raka’a biyu a bayan Maƙami Ibrahim. Idan ba Ka samu dama ba, to a ko’ina ka sami fili a cikin masallacin sai ka yi sallarka.
Daga nan ya je ya sha Zam-zam har ya cika cikinsa. Kuma ya zuba shi a jikinsa. Zam-zam ruwa ne mai albarka da ya ke maganin cututtuka.

Mai harama zai tafi zuwa ga wani ƙaramin dutse ana ce masa Safa. Sai ka karanta wannan : “Lalle dutsen Safa da na Marwa suna daga cikin Alamomin addinin Allah… ” ( Baqara:158).
Sai kuma ka ce : “Na fara da abin da Allah Ya fara da shi”.
Sai ka hau kan dutsen safa ka fuskanci ka’aba ka ce :
Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar.
La’ilaha illal lah, wahdahu laa sharika lah,  lahul mulku wa lahul hamd,  wa huwa ala kulli shai’in qadeer. La’ilaha illal lah wahdah,  anjaza Wa’adah, wa nasara abdah,  wa hazamal ahzaba wahdah.
Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, wanda ba shi da abokin tarayya. Mulki na gare shi, kuma godiya ta tabbata a gare shi. Kuma shi mai iko ne a kan komai. Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah , shi kadai din sa,  Allah Ya zartar da alkawarinsa,  kuma ya taimaki bawansa, kuma ya kayar da rundunonin kafirci shi kaɗai dinsa.
Sai ka yi Addu’a ko da wane irin yare ne ko da Hausa ne kuwa.
Kuma ka ƙara addu’ar can ta sama. Ka sake wasu addu’o’inka a karo na biyu. Ka kara maimaita addu’ar can a karo na uku. Kuma ka kara wa kanka addu’o’i.
Sai ka sakko ka wuce zuwa Marwa. Idan ka zo ga alamomin nan guda biyu. Sai ka ƙara daga ƙafa ( gudu)  a tsakaninsu. Amma fa kafin ka zo gare su. Bayan ka wuce su, sai ka yi tafiyarka ta al’ada.
Wannan gudun yana tuno mana yadda Mahaifiyar Annabi Isma’il Wato Hajara ta yi ta fama. haƙurinta da juriyarta domin yardar Allah.
Haka mutum zai ta maimaitawa tsakanin Safa zuwa Marwa . Lalle ne mutum ya yi ƙoƙarin kaucewa  addu’o’in da ba su inganta ba.

Wannan shi ne rukuni na huɗu. Kuma na ƙarshe a cikin aikin Umra. Wato aski ko saisaye. Kammala shi ne zai sa mutum ya fita daga Ihraminsa.
Aske kai gaba ɗaya shi ne ya fi akan saisaye. Sai dai ga wanda niyyarsa Tammattu’i ce. To wannan saisaye ya fi masa. Ragowar gashinsa zai bar shi, har sai ya kammala rukunan aikin Hajjinsa. To sai ya sake gaba ɗaya.
Kana gama wannan,  to za ka aika ta dukkanin abubuwan da ba za ka yi su ba. Kamar su saduwa da iyali,  da sanya tufafi na al’ada,  da sa safa,  da hula da dai sauransu.
( Baqara:196).
A zamanka na jiran lokacin fita aikin Hajji. Za ka yawaita karatun Qur’ani , da ziyarar malamai,  da sallah a harami. Za ka yi dukkan abin da kake so. Amma fa ban da asarar Lokaci, wajen hira da abokanai ko musu da su . Ka dage sosai wajen yawan ambaton Allah har zuwa takwas ga wata ya zo. To sai ka sake shiga ihraminka,  harama amma a wannan karan da Hajji ne.

RUKUNAN AIKIN HAJJI .

-Zaman Minna
-Tsayuwar Arfa
-Zaman muzdalifa
Takwas ga wata ake fita domin gabatar da aikin Hajji. Tambayar ita ce , shin akwai buƙatar mutum ya dawo miƙati domin yin harama? A’a mutum zai yi haramarsa a ko’ina daga inda yake zaune a Makka. Za ka iya yi daga masaukinka (hotel )  ko daga masallacin Harami.
Za ka yi Niyya a zuciyarka, sai kuma fadar : “Labbayk Allaahumma bi-hajj “. Ko labbayk Hajjatan “.
Wannan ya Kawo mu wata muhimmiyar tunatarwa a kan Niyya. Wasu kan yi rashin Lafiya a lokacin da suke aikin Hajji. Har ya zama ba za su iya kammala rukunan aikin Hajjinsu ba. Idan haka ta kasance, to fa dole mutum ya dawo a shekara mai zuwa. Zai sake Hajjinsa, Kuma yai yanka.
Sunna ce mutum ya yi niyya tare da faɗar wannan addu’ar. Ita Wannan addu’a za ta zama kariya daga abubuwan da za su faru, ba tare da sani ba.
Addu’ar ita ce : Labbayk Allaahumma bi-hajj “.
Kuma ka ƙara wannan :
“Allaahumma Muhalli haisu habastani “.
Wanda duk ya yi wannan, to ko da ya kasa cikatawa, saboda rashin Lafiya. To babu yanka a kansa. Wato haka Allah Ya ƙaddara wa bawansa ba zai cikata ba.

ZAMAN MINNA :Zaman Mina na farawa ne daga takwas ga watan Dhul-Hajj. Maniyyaci zai fita ya zuwa Mina. Ana son ya zauna ya yi sallar azahar, da la’asar, da Magriba,  da isha,  da kuma asuba. Washegari Wato tara ga wata kuma da safe zai fita zuwa filin Arfa.

TSAYUWAR ARFA :Za ka zauna a Arfa ka yi ta yin talbiyya :”Labbayk Allaahumma Labayk “. Za ka iya yin karatun Qur’ani da yawaita addu’o’i, ko da kuwa da irin harshenka ne  Hausa ko Turanci .
Ka yawaita kabbara “Allaahu Akbar ” . Tasbihi, da Hamdala “Alhamdulillah “. Ba za ka bar filin Arfa ba, har sai rana ta faɗi. Duk wanda bai samu damar halarta Arfa ba. To kuwa ba shi da Hajji saboda Annabi (S. A. W) ya ce : Tsayuwar Arfa ita ce Hajji “.
Abin tambayar a nan shi ne,  ko dole ne mutum sai ya hau kan dutsen Arfa ne? Amsar ita ce, a’a.  Saboda Annabi (SAW)  bai yi ba. Shi ya tsaya ne a kan dabbarsa ( Rakumi) a gindin dutsen Arfa.

ZAMAN MUZDALIFA : Idan rana ta faɗi,  sai ka taho Muzdalifa. A nan za ka yi sallar magariba da isha gaba ɗaya . Magariba yadda take, amma isha ƙasaru ( Wato raka’a biyu). A nan Muzdalifa za ka zauna har sai asuba ta yi, sai ka yi sallar asuba. Kwana a Muzdalifa wajibi ne saboda Allah Ya ce :” …Sa’anan idan kun taho daga Arafat, sai ku yi ta ambaton Allah a Wurin Mash’aril Harami,.. (Baqara :198).
Mash’aril harami na nufin Muzdalifa.
Za ka yi ta Hailala “La ilaha IllAllah ” Tasbihi :”SubhaanAllah ” kabbara da su talbiyya.

GOMAN ZULHAJJ: Goma ga watan Zulhajj babbar rana ce. Kuma rukunanta su ne :
Jifan Shedan
Yanka ( hadaya)
Aski
awafi

JIFA: Za ka tsinci tsakwankwani guda bakwai. Ka yi jifa da su, kowanne jifa kana faɗar “Allahu Akbar “. Ɗaya bayan ɗaya. Ba a jefa duka tsakwankwani bakwai lokaci guda.
Za ka matso kusa sosai da jamra, a lokacin da za ka yi jifa. Domin ka da ka cutar da mutane dake gabanka.
Wannan ginin Jamra da ake jifa,  ba ita ce shaiɗan ba. Za ka ga wasu na zagi, da tsinuwa,  har da jifa da takalmi, wannan duk bai dace ba. Ana yin jifa ne domin biyayya ga umarni Allah. Ko da kuwa mutum bai san hikimar aikata hakan ba.

YANKAN HADAYA : Bayan gama jifa, sai ka taho Mina wajen yanka hadayarka. An fi so a ce kai ka yanka da kanka. Amma babu laifi ka sa wani yai maka yanka. Har ma za ka iya biyan kudin hadaya,  ta bankin Rajhu Bank dake nan Mina.
Za ka iya yanka dabba ta kowacce irin shekara saboda Allah Ya ce : …To, Idan an kange ku, to, ku bayar da abin da ya sauƙaƙa na hadaya… “(Baqara :196)
Kun ga ashe ba a tantance shekarun ba. Haka kuma za ka iya ci daga cikin hadayarka.
ASKI : Bayan gama hadayarka sai kuma ka yi aski.

DAWAFI :Za ka koma Makka ka yi ɗawafi guda bakwai, kamar yadda ka yi farkon zuwanka. Sai dai wannan sunansa ɗawafin Ifadah. Shi ba a hanzari a zagayen ukun farko. Haka kuma babu fito da kafaɗa. Za ka yi dukkan Zagayen ɗawafin ne,  kana tafiya kawai. Za ka iya yinsa cikin tufafinka na al’ada.
Mutum na fita daga Ihraminsa ne lokacin da ya gama jifa. Haka ma za yi komai da aka hana ka yinsu. Amma ban da saduwa da iyali.

RUKUNAN DA AKE GABATARWA A RANAR GOMA GA WATAN ZUL-HAJJI:

Jifa jamra Karama
Yanka hadaya
Aski
Ɗawafi
An tambayi Annabi (SAW)  a kan yin su a jere. Ko fara wani kafin wani. Sai ya ce :”Ku yi su ba komai, Ku yi su ba komai “.
Saboda haka ma ake samun waɗanda suke cikin aikin Hajji ƙungiya guda. Amma fa wannan na ɗawafinsa da safe, wannan da rana.

RANAKUN SALLAH: Abin da ya rage ma yanzu shi ne ka zauna kwanaki uku a Mina. Mene ne abin yi a wannan zaman na Mina.?
A lokacin zaman Mina za ka ci ka sha. Kuma za ka yawaita ambaton Allah. Kuma za ka iya ci daga yankan hadayarka. Idan kuwa kuɗin ka bayar,  to ba za ka gan shi ba. Za a yi ma sadaka da shi ne.
Waɗannan ranaku, su ne ranakun farin ciki da jin daɗi .Wato ranakun Idin sallah.
A rana ta uku kamar azahar. Za ka fita domin yin jifa Jamra ukun gaba ɗaya. Za ka fara jifa daga ƙaramar Jamra. Sai ta tsakiya,  sai kuma babbar Jamra. A kowacce ka yi jifa da duwatsu guda bakwai . Kuma aN kowacce kana faɗin :”Allaahu Akbar”.

JAMRA TA FARKO: Bayan ka gama jifa, za ka tsaya ka roƙi duk abin da kake so.
JAMRA TA BIYU : Ka ɗan dakata sai ka yi ta addu’a.
JAMRA TA UKU :Za ka bar wajen ba tare da yin addu’a ba.
Za ka gabatar da wannan jifa ne,  a kwanaki ukun nan. Wato 11, da 12, da 13 ga Zul-Hajj . Ana kiran waɗannan ranakun :”Ayaam Tashriq “. Wato ranakun bushewa. Saboda yadda  a da can alhazai ke shanya nama ya bushe. Suna ajiye shi, har su kammala aikin Hajjinsu,  su tafi gida da Namansu. Kasancewar a lokacin da can babu na’urar sanyi ta adana nama.
Kana gama wannan jifa, to ka kammala aikin Hajji. Za ka iya dawowa gida wajen iyalanka. Har ma ana samun wasu su dawo gida washegarin da su ka kammala Hajjinsu.
Allah Ya ce :”
( Baqara: 203).
Za ka iya barin Mina tun a ranar 12 ga wata. Sai ka haɗa duka jifa. Wato da na 12, da 13, a rana guda ( Duka a 12 ga wata kenan).
Ka ga a kowacce Jamra za ka yi jifa da duwatsu bakwai na ranar 12 . Sai kuma ka ƙara wasu bakwai na ranar 13. Haka za ka yi a ƙarama, da ta biyu,  da jamra ta uku.
Za ka yi hakan ne idan ba ka son zaman Mina. Wato za ka koma gida. Allah Ya ce :”(Baqara:203)
Haka ma dai ana so ( Mustahabbi ne ) ka yi ɗawafin bankwana ( ɗawafin wadaa) kafin ka tafi garinku.
Annabi (SAW) ya ce :Ka da mutum ya bar Makka,  a tafiyarsa ta ƙarshe har sai ya yi ɗawafin ƙarshe a ɗaki mai tsarki “.

MATA DA JININ HAILA A LOKACIN AIKIN HAJJI: Idan Mace ta fara jini a farkon lokacin da take gabatar da rukunan aikin hajjinta. Ko kuma yayin da ta kusa gama aikin Hajji. To fa za ta ci gaba har ta kammala dukkanin rukunai. Sai dai kawai ban da ɗawafi. Shi za ta jinkirta shi, har sai ta yi tsarki tukunna. Sai ta je ta yi ɗawafi.
Haka kuma, ko da ta fara jini ne, da ta fara zagayen farko na ɗawafin  isowa (ɗawafin Qudumi). To,  za ta cigaba da dukkanin rukunan aikin Hajji. Sai ta kammala su,  ta jira ta yi tsarki. Sannan ta yi ɗawafin tana bankwana ( dawafin Ifada).
Hajji da Umararta ba su ɓaci ba. Saboda haka jinin haila ba matsala ba ne ga mata a lokacin aikin hajjinsu.
FIFIKON HAJJIN TAMATTU’I: Mafificin aikin Hajji shi ne tamattu’i. Wato wanda aka haɗa Umra da Hajji. A shi ne ake samun lokaci a tsakaninsu. A lokacin Umra ka sanya ihraminka. Da ga ka kammala, ka ajiye har sai lokacin Hajji ka ƙara sawa.
Wasu za su ce, Annabi (SAW) ya yi hajjin Qirani. To kuma yaya za a yi mu ce kuma tamattu’i ta fi fifiko?
Annabi(SAW) ya ce :” Da a ce ban taho da hadayata tare da ni ba, da na cire ihramina,  sai in mayar da ita Umra”.
Wato wanda ba zai cire Ihraminsa ba,  shi ne wanda ya taho tare da hadayarsa tun kafin miƙati. Allah Ya ce : “..Wala tahliku…. Mahilla.. “(Baqara:196).
Annabi (SAW) bai bar sahabbansa sun yi Ƙirani ba.
Ga wanda ya yi Tamattu’i, sai ya yi hadaya a 10 ga watan  Zul-hajji. Wanda kuɗinsa bai isa yai hadaya ba. Ko ya nemi dabbar saya, ya rasa. To sai ya yi azumi guda uku. Sannan Idan ya dawo gida ya yi guda 7.
Allah Ya ce : “Faman lam yajid… Hadiril masjid haraami “(Baqara:196)
Ga masu fama da talaucin da ba za su iya sayen hadaya ba. Za su azumci kwanaki uku  11, da 12, da 13 ga Zul-Hajj . Sauran ragowar azumi 7 sai  sun koma kasarsu.
Allah yai daɗin tsira da aminci ga fiyayyen halitta. Annabi (SAW)  da alayensa da sahabbansa.

Ku kasance a wannan gida mai albarka don cigaba da samu ingantattun shirye-shiryemmu.

labarin da ya wuceYadda Ake Cire Auto Download A WhatsApp
Labarin na GabaYadda Ake Rage Zafin Kishi
Amin Yusuf Gwamna
Sunana Amina Yusuf Gwamna Shugaba Kungiya Mace ta Musamman da ke kokari inganta rayuwar Mata da kanana Yara. Marubuciya litattafai hausa. Kuma Shugaba Makarantu Abu-Nusaiba Da ke Ring road, kano.