Tatsuniyar Sandar Arziƙi

0
6

Ga ta nan, ga ta nanku.

A can wani gari da ya yi iyaka da ƙasar Aljanu, akwai wani mutum mara sukuni da matarsa, da ɗansu ɗaya. Suna zaune a cikin wannan hali, sai ɗan ya isa aure. Iyayen nasa sai suka ce da shi: “Yanzu ga shi ka isa aure, amma ba mu da abin da za mu aura maka mata da shi.”

Amma mahaifinsa yana da wata sanda; sai ya ba shi ita yace: “Ka kama hanyar duk garin da ka zaɓa a zuciyarka; sandar za ta zama sanadin yin aurenka.” To, da yake yaron mai biyayya ne, sai ya karɓi sandar ya cewa mahaifansa: “Na gode, kuma na tafi. Allah ya ba ni sa’a.”

Baki ɗaya suka ce: “Amin.” Yaro yana cikin tafiya a daji, sai ya tarar da wasu mutane suna jifan tsuntsaye. Sai ɗaya daga cikinsu yace: “Kai yaro, ka taimake mu da aron sandar nan taka mu jeho tsuntsu mana.” Ba tare da wani musu ba, sai kawai ya ce: “Ga ta.” Suka karɓa, suka jeho tsuntsaye da yawa da ita.

Amma kuma sai sandar ta maƙale a jikin rassan bishiyar. Da ya ga sandarsa ta maƙale, sai ya fara waƙa yana cewa: “Tam, tam, Sai kun biya ni sanda ta. Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni. Takan cishe ni, Tai min aure.” Sai suka ce: “Kash, ga shi kuwa ba mu da komai sai dai mu ba ka tsuntsu ɗaya.”

Sai ya ce: “To, ku ba ni.” Suka ba shi tsuntsu, ya karɓa ya kama hanya. Yana cikin tafiya sai ya tarar da wata mace ta girka abinci. Sai ta ce da shi: “Kai yaro, ba ni tsuntsun nan naka in gani.” Da ta karɓa, sai kawai ta gyara shi, ta yi miya da shi. Yana ganin haka sai ya ce: “

Tam, tam, Sai kin biya ni tsuntsuna, Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai ta ce: “Wayyo samari, ai ban san haka abin yake ba, sai dai ba ni da komai sai tuwon nan da ka gani.”

Da ya ji haka sai ya karɓi tuwon mara biyar, ya kama hanya riƙe da abinsa. Yana cikin tafiya, sai ya tarar da wasu manoma, sun yi aiki sun gaji; yunwa ta sa sun galabaita. Da suka ga tuwo a wurin yaro, sai suka ce: “Ɗanyaro mu ga tuwon nan mana.” Da suka karɓa sai suka cinye. Da ya ga sun cinye masa tuwo, sai ya fara waƙar da ya saba

“Tam, tam, Sai kun biya ni tuwona, Tuwona da mai girki ta ba ni, Da ta karɓi tsuntsuna,
Tsuntsuna da maharba suka ba ni, Maharban da suka ɓatar da sandata, Sandata da uwata ta ba ni, Ubana ya ba ni, Yakan cishe ni, Ya yi min aure.” Sai suka ce: “To ga shi ba mu da komai. Amma in kana son fartanya ko magirbi, sai mu ba ka ɗaya.”

Da ya ji hakasai ya ce: “Ba komai, ku ba ni magirbi, ya wadatar.” Nan take suka ba shi magirbi ɗaya, ya kama hanya. Yana cikin tafiya, ya kusa isa wani babban birni, sai ya tarar da wasu mutane sun fara haƙa ƙabari za su yi jana’izar wata gawa. Da suka ga magirbi a hannunsa, sai babbansu ya ce: “Yaro ba mu aron magirbin nan mana mu haƙa ƙabari.

”Ba wani musu, sai ya ba su. Suna cikin tonon rami, sai magirbin ya kare da ganin haka sai ya fara wakarsa: “Tam, tam, > Sai ka biya ni gawata, > Gawata da masu haƙar ƙabari suka ba ni, > Masu tonon ƙabari da suka karya magirbina, > Magirbina da manoma suka ba ni, > Manoma da suka cinye tuwona, > Tuwona da mai abinci ta ba ni, > Mai abinci da ta karɓi tsuntsuna, > Tsuntsuna da maharba suka ba ni, > Maharba da suka ɓatar da sandata, Sandata dauwatataba ni, > Ubana ya ba ni, > Yakan cishe ni,
> Ya yi min aure.” >

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Yin biyayya ga magabata tare da jure wahalhalun rayuwa sukan kawo nasara a rayuwa.
  • Mai arziki ko a ƙwara ya sayar da ruwa.
  • Arziki a ƙasa ake tako shi.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Karanta Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo
Labarin na GabaTatsuniyar Makauniya Da Ɗanta
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.