Tatsuniyar Arɗo Da Ndoffiwa

0
11

Ga ta nan, ga ta nanku.

An yi wani makiyayi wai shi Arɗo a can kusa da wani baƙin daji da ake kira Dajin Gafiya. Yana zaune da matarsa ɗaya, wai ita Hodanego. Shi Arɗo kullum yakan yini a daji ne wurin kiwo, amma ita matarsa ta ha’ince shi, domin tana da kwarto mai suna Ndoffiwa.

Kullum idan mijinta ya tafi kiwo, sai ta kama kaza daga cikin kajin gidan ta yanka wa kwartonta, ta shirya abinci mai daɗi su ci tare. Ana nan, wannan abu yana tafiya, har dai wata rana wata maƙwabciyar Arɗo ta kira shi ta ce da shi: “A gaskiya Arɗo duk lokacin da ka tafi kiwo sai matarka ta kira kwartonta, ta kama kajinka ta ɗebi hatsinka ta yi abinci, su ci tare.

Idan kana son ka kama su, ka yi kamar ka tafi kiwo, sai ka dawo jim kaɗan ka gani.” Sai Arɗo ya amince da shawarar. Rannan sai ya yi yadda ya saba, ya fita kamar ya tafi kiwo, amma sai ya laɓe a gidan maƙwabciyar nan tasa, ya shiga fako. Can sai ya ga matarsa ta kama kazarsa ɗaya ta yanka ta gyara ta kuma ɗora girki sai ƙamshin daɗi ke tashi.

Da ta gama abinci, ta zuba a akusa, ta rufe da faifai ta ɗauka ta fita, ta kama hanyar gidan kwarton nan tiryan-tiryan, ba tsoro, ba shakka. Sai da ta ɗan yi nisa, sai ya bi ta a baya. Ba ta tsaya ko’ina ba sai gidan kwartonta; amma ta tarar ba ya gida. Arɗo kuma yana daga inda ya raɓe ya ga ta shiga, ta ajiye abincin ta fita daga gidan, amma shi Arɗo sai ya laɓe, har sai da ta yi nisa.

Sai ya je ya shiga gidan, ya zarce har ɗakin da ta ajiye abincin, ya zauna ya cinye shi kakaf. Daga nan sai ya ɗauki akushin tuwon, ya yi kashi a ciki ya kuma ɗauki akushin miya ya yi fitsari a ciki, shi ma ya rufe, ya sai kai ya yi tafiyarsa.Shi kuwa Ndoffiwa ashe wurin hirarsa ya je.

Da suka gama hira, sai ya gayyaci abokansa su je cin abinci a gidansa. Duk da cewa ba shi da mace, ya tabbatar kwartuwarsa za ta kai abinci. Suka shiga gida, ya ɗauko akusa. Yana buɗe akushin tuwo, sai ya ga tsibin kashi. Da ya buɗe akushin miya kuma, sai ya ga fitsari; zarnin fitsarin da ɗoyin kashin suka buge shi tare da abokansa.

Kamar sun haɗa baki, sai suka ce: “Ka gayyato mu gidanka domin ka wulaƙanta mu shi ya sa ka ba mu kashi ko? Lallai ka cika mara kunya.” Haka a fusace suka fice, suka bar shi. Shi kuma kwarto sai ya shirya a zuciyarsa zai kawo wata kwartuwar, domin ya ɓata wa Hodanego rai saboda ta kai masa kashi da fitsari a madadin abinci.

Sai ya tafi wajen wata kwartuwar. Bai jima da fita ba, Hodanego ta koma gidansa ɗibar akusa. Da ta ɗaga, sai ta ji da ɗan nauyi sai ta ɗaga faifan da ke kai domin ta ga ko bai ci abincin ba ne. Tana buɗewa sai ga wani gandareren kashi, wanda ya kume ɗakin da ɗoyi. Wannan abu ya baƙanta mata rai.

Sai ta fusata, baƙin ciki ya kama ta. A cikin zuciyarta ta ce: “Amma Ndoffiwa ba shi da mutunci. Na kawo masa abinci a mutunce, amma kuma ya saka mini da kashi da fitsari a akusa? Bari zan yi maganinsa.” Nan take ta juye kashin nan da fitsari a kan gadonsa. Ta sa kai ta yi tafiyarta.

Ba da daɗewa ba, Ndoffiwa ya koma gidansa tare da sabuwar kwartuwarsa. Da suka shiga ɗaki ta zauna a kan gado, sai ta ji alamar laima, sai ta taɓa da hannunta, ta ji. Nan da nan ta gane ashe kashi ne. Nan take ta miƙe a fusace, ta shiga ƙwala wa Ndoffiwa ashariya, ta ce ashe shi ƙazami ne.

Ta zazzage shi ta more, sai ta kaɗe zanenta, ta fita daga ɗakin, ta bar gidan. Da fitarta, sai ya kwashe kayan ɗakinsa ya wanke. A cikin daren nan kuma Arɗo ya zagaya inda ya yi shanya, ya kwashe kayan. Sai ya kai su rafi ya zuba, suka bi ruwa. Da gari ya waye Ndoffiwa ya je kwaso shanya, amma bai ga ko bante ba.

Baƙin ciki ya cika shi, sai ya yanke shawarar ya bunƙa wa ɗakinsa wuta; gobara ta tashi ya yi kururuwa, mutane suka taru aka kashe gobara. Wani ya kawo wani tsumman riga ya ba shi. Da ya sa rigar, kuma ya lura hankalin mutane na wajen kashe gobara sai kawai ya sulale, ya bar garin. Kurunkus.

Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

  • Aure ba wasa ba ne; dole a kiyaye ƙa’idojinsa ko kuma a yi da-na-sani.
  • Abin kunya kan sa mutum garinsu ya gagare shi zama.
  • Rama cuta ga macuci ibada ne.

Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

Danna nan don karanta Tatsuniyar Marainiya Mai Turmi

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTatsuniyar Marainiya Mai Turmi
Labarin na GabaTatsuniyar Biri Da Kare
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.