Tag: ilimi

  • Laƙani Ta Hanyar Wuridi

    Laƙani Ta Hanyar Wuridi

    Da yawan ‘yan tsibbu kan yi wani adadi mai yawa na wuridi. Wanda a mafi yawan lokuta sunayen aljannu ake kira.

    Kuma koda an kira sunan Ubangiji Maɗaukaki, to kuwa za a sirka shi da waɗansu kalmomi ko haruffa da ba kasafai ake sanin ma’anarsu ba.

    Za ka iya gane wannan nau’i na wuridi, ya yin da aka ce sai an nemo turare kaza, ko sai an samo garwashin wuta a cikin ɗaki mai duhu. Shi ma wannan yana da tasiri a fagen laƙunƙuna haramtattu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Alamomin Gane Malami Mai Sihiri Ko Matsafi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Nema Wa Yara Samun Karatu Da Raba Su Da Abokanan Banza danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tsibbu Ta Hanyar Duba Ko Ilmin Taurari

    Tsibbu Ta Hanyar Duba Ko Ilmin Taurari

    Shi ma wannnan ba ya buƙatar wani dogon jawabi, domin kuwa duk Musulmin ƙwarai, ya san ba wanda ya san gaibu sai Ubangiji Maɗaukaki.

    Da’awar sanin gaibu kuwa, alama ce ta cuɗe-ni-in-cuɗe-ka da aljannu. Ko leƙen abin da Ubangiji Maɗaukaki ke tsoratarwa a kansa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Matsayin Tsibbu Da ‘Yan Tsibbu A Wurin Shehu Usman Bn Fodiyo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Aiki Kamar Yankan Wuƙa

    Aiki Kamar Yankan Wuƙa

    Irin wannan na faruwa ne a lokacin da matakan haɗa asiri; ko laƙani suka nemi a aikata wasu miyagun ayyukan saɓo.

    Kamar a ce sai ya taka Alƙur’ani ya shiga banɗaki da shi, ko ya rubuta ayoyin Alƙur’ani da wata ƙazanta; kamar rubuta shi da jinin haila ko rubuta Suratul Fatiha da baya da baya. Ko a ce ya yi Sallah babu alwala, ko a ce ya yi zina da ‘yarsa ko uwarsa ko mahaukaciya.

    Ko kuma ma, a rubuta wasu haruffa da zantuka da bai san ma’anar su ba; ko kuma ya nemo tufafi ko wani gashi ko farce ko wani abu daga mutumin da ake son yi wa asirin. To kai tsaye za mu gane sihiri ne, ma’ana tsafi ne.

    A irin wannan yanayi ne waɗansu malamai da rigima ta haɗa su a kan limanci; suka riƙa jifan junansu, da haka har suka halaka ‘ya’yansu da matayensu, daga ƙarshe ɗayan ya halaka gudan.

    Tambaya a nan ita ce, me yasa malaman da suke irin waɗannan laƙunƙuna ba sa iya yin tasiri kan manyan kafiran duniya da azzuluman Yahudawa?

    Amsa ita ce, saboda shaiɗan ba ya ruguza aikin sharri, sai dai ya ƙara masa ƙarfi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Laƙani Ta Hanyar Wuridi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Salati Ga Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Shin Mene Ne Tsafi Ko Sihiri?

    Shin Mene Ne Tsafi Ko Sihiri?

    Sihiri shi ne ƙulla yarjejeniya tsakanin matsafi da aljani, bisa sharaɗin matsafin zai aikata wasu ayyukan saɓo. Sannan aljanin ya taimaka masa ta hanyar yi masa biyayya cikin umarninsa.

    A duk lokacin da aikin saɓo ya fi muni da nesata daga Ubangiji Maɗaukaki, to kuwa aikin da aka sa aljanin ya fi saurin ci. Daga nan ne ake kiran irin waɗannan ‘yan tsibbu Malam Gobe-da-nisa.

    Amma idan matsafi ya taƙaita amsa umarnin shaiɗanin ko aljanin, to ba zai yi masa biyayya ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Aiki Kamar Yankan Wuƙa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan SHUGABANCI A WURIN HAUSAWA danna nan.

    Wan nan baya nin anciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya, Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr.Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Hausar Gardawa

    Hausar Gardawa

    Kasancewar tsarin tsangaya wani fage ne mai faɗi, kuma wata wayewa ce ga ma’abotanta mai zaman kanta; tsarin ya haifar da samuwar wasu lafuza ko ƙarin yare wanda ya keɓanci waɗanda ke cikin wannan da’ira ta gardawa.

    Kamar dai yadda sojoji ko wani rukuni na mutane ke da yaren da ya keɓance su, kuma ba mai gane shi, sai su ya su.

    Akwai Hausar gardawa mai alaƙa da Alƙur’ani, wata Hausar tasu na da alaƙa da shi kansa harshen Hausa, wata kuma mai Alaƙa da harshen Turanci ko kuma Larabci.

    Misalin mai Alaƙa da Alƙur’ani:-

    – Tilka: baƙar mace
    – tusuna: mummunar mace
    – Udda: gajeren mutum
    – Ƙala ƙato: malamin littafi
    – Na gaban innaka: maye
    – Wa hananan: an hana

    A wani lokaci kuwa, su kan ƙirƙiri wata sabuwar ma’ana a cikin shi kansa harshen na Hausa; misali:

    – Tashe:- tashi cikin dare don yin karatu maimakon tashe da ake yi da watan Azumi.
    – Sauka:- kammala karatun Alƙur’ani
    – Kasgi:- Jahili
    – Badawai:- ƙauye
    – Yankan baki:- raba kalma
    – Yanka Alamina:- yin ɓarna ko yin zina
    – Rani:- fita Neman karatu lokacin bazara
    – Banda:- kayan tafiya almajiri
    – Warat:- kiran gaggawa don cin abinci
    – Wanke:- baƙin ruwan da ake tawada da shi
    – Kwami:- karatu ko nacin karatu
    – Ɗan bajire:- guntun tuwo
    – Zaman sidi:- jiran abinci a wajen bara
    – Mako:- yin itacen sati
    – Gabza:- abincin maras daɗi
    – Malam Shehu:- talaka
    -Tsoma:- aljani a cikin gardawa
    – Kara:- kuskure ko tsallake
    – Buƙa:- gabatar da buƙata
    – Datsi:- rabo ko gutsiren abinci
    – Kantuga:- wasa ƙwaƙwalwa
    – Alif na gaban wau:- mutum marar ra’ayi
    – Shim mai ruwa Uku:- shashasha ko mara hankali
    – Miya ba gishiri:- makarantar islamiyya
    – Kaukau:- marowaci
    – Bakaddike/Kadikko:- almajirin da ya daɗe a gari
    – Kura:- matar gardi
    – Jargi:- busasshen nama
    – Bugu:- dafa tuwo
    – Gaga:- rashin ji
    – Bajancuri:- ba zato sai ya yi tilawa mai yawa
    – Curinbaje:- ana sa rai kuma sai ya kasa tilawa mai kyau

    Gardawa a tsarin tsangaya, ba su taƙaitu wajen ƙirƙiro sababbin ma’anoni cikin Alƙur’ani da harshen Hausa ba, har sai da suka kutsa cikin harshen Turanci. Misali:

    – Boko:- ilmin boko ko ilmin gangan
    – Ladan boko:- ƙaramar mota
    – Coca-Cola :- ko ka kula giya ce?
    -Chiyaman ko Shugaban cin amanar
    Ƙaramar Hukuma:-

    Tsokaci

    Canza salon kalmomin Alƙur’ani ya zuwa wata ma’ana, abu ne da bai halarta ba. Domin zancen Ubangiji Maɗaukaki ne da ɓace, ko wasa baya zuwa bayansa ko gaba gare shi. Don haka ya zama wajibi ‘yan uwa gardawa su kiyaye, domin hakan zai iya kai mutum ga yin ridda.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Asalin Tsibbu A Tsangayun Alƙur’ani danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Zubin Tsangaya Yake danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane

    Dabarun Zaman Lafiya Da Mutane

    A tasa gudunmawar a wannan fanni, shaihun malamı Abdullahi ibn Fodiyo (R.A) ya bayyana muhimman ƙa’i’doji waɗanda in mutum ya bi su, zai iya samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da kowane irin jinsi na mutane.

    Malamin ya yi wannan bayani ne a cikin littafinsa mai suna:

    “Aadaabu Mu’aasharat, Litaalibinnajaatı Fiddunya Wal Aakhirat”.

    Ga abin da malamin yake cewa:

    1. Ya ɗan uwa kada ka wulaƙanta kowa, domin kai ba ka san matsayin mutum ba a wurin Allah, wataƙila ya fi ka daraja

    2. Kada gafalallu ‘yan duniya masu sharholiya su ɗaɗa ka da ƙasa, har ka girmama su, saboda duniya ba a bakin komai take a ba wurin Allah.

    3. Ka kare mutuncinka, kada ka roƙi kowa sai Allah, sai dai bisa halin lalura. Kuma kada ka damu, ko ka zargi kowa in ka roƙa aka hana ka.

    4. Kada ka wahalar da kanka wajen yin wa’azi ga wanda ba ka ga wata alamar karɓar wa’azi daga gare shi ba. Kuma ka guji ambaton sunayen mutane (ko ƙungiyoyi) cikin wa’azinka.

    5. Idan ka ga mutane suna girmama ka, to ka gode wa Allah, ka roƙe shi ya tsare ka daga dogara ga mutane.

    6. Idan kuwa suka cutar da kai, to ka haɗa su da Allah, ka nemi kariyarsa daga sharrinsa, kada ka damu da ɗaukar fansa, har sai abin ya yı maka yawa, ka rasa da wanda za ka ji, ka ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba. Allah dai shi ne yake sanya a so mutum ko a ƙishi.

    7. Lokacin da kake cikin mutane, ka saurari maganganu na gaskiya, ka toshe kunnuwanka daga ƙaryace-ƙaryacensu. In za ka faɗi, faɗi gaskiya, ka zama bebe wajen faɗin zancen banza.

    8. Ka karanta abota da mutane, saboda yawancin mutane ba sa yin afuwa. ba sa rufa asiri, suna neman haƙƙinsu, amma su ba sa so su bawa mutane haƙƙinsu, sun fi yarda da ƙarya da kuma gulmace-gulmace. Kai zama da waɗansu mutanen ma dai ba shi da wata riba, farat-farat a fuska, amma a zuci ba sa sonka, kuraye ne su da fatun awaki, a kan zato suke yanke hukunci, ga su da yi da mutane, kuma ba sa da wani buri sai su ga bala’i ya same ka.

    9. Kada ka saki jiki da mutumin da ba ka san halinsa ba ta hanyar zama da shi a gida ɗaya, ko a kasuwa ko halin tafiya. Da kuma halayyarsa lokacin da yake cikin wadata da talauci, da murna da fushi. Sannan ka gwada mu’amala da shi ta kuɗi, ko ka bari sai lokacin da ka shiga cikin wani matsi, ka buƙaci taimakonsa ka gani zai taimake ka ko kuwa.

    Duk mutumin da ka gwada shi cikin waɗannan halaye ka ga ya haye to wannan shi ne mutum, in ya girme ka, ka ɗauke shi a matsayin uba, in ka girme shi ka mayar da shi ɗa, in kuma sa’anka ne, ka ɗauke shi a matsayin ɗan uwa.

    10. Ka karɓi aboki da maƙiyi cikin haba-haba amma ban da wulaƙantar da kai.

    11. Ka ja girman ka, amma ka guji girman kai.

    12. Ka ƙasƙantar da kanka, amma ka da ka wulaƙantar da kanka.

    13. Komai za ka yi, ka ɗauke shı (tsaka-tsaki).

    14. Ka guji yawan waiwaye lokacin da kake cikin jama’a.

    15. Kada ka rinƙa wasanni da sauran abubuwan ƙasƙanci a cikin mutane, kamar wasa da gemu, kwararrasa yatsu, sakace, gyaran hanci, yawan tofe-tofe da kaki, karairaya jiki, yin hamma ko atishawa a fuskar mutane.

    16. Ka zauna cikin nutsuwa, a yi magana cikiņ tsari.

    17. Ka saurari abokin hirarka lokacin da yake magana mai ma’ana. Kada ka zaƙe wajen nuna masa ya burge ka, kada ka nemi ya maimaita maganar.

    18. Ka daina yawan faɗar labaran ban dariya.

    19. Ka daina yawan faɗar nasarorinka da na iyalinka ko wakarka da sauransu.

    20. Ka guji ƙyale-ƙyale da caɓa ado kamar mace, amma kada ka zauna busu-busu kamar baiwa.

    21. Ka guji yawan sa kwalli.

    22. Ka guji naci.

    23. Kada ka goyi bayan kowa a kan zalunci.

    24. Kada ka bari ‘ya’yanka da iyalinka su san yawan kuɗinka, saboda in sun ga ba su da yawa, sai su raina ka, idan kuwa suna da yawa, sai su ci burin da ba za ka iya gamsar da su ba.

    25. Ka rinƙa yin barazana ga iyalinka lokaci-lokaci.

    26. Ka sassauta musu amma kar ya kai yadda za su raina ka.

    27. Kada ka rinƙa yawaita wasa da barorinka, sai su raina ka.

    28. Yayin da husuma ta haɗa ka da wani ka nutsu, ka guji wauta da gaggawa. Ka yi nazari sosai kan hujjojinka, kada ka yawaita waiwaye-waiwaye.

    29. Idan wani mai mulki ya ja ka a jiki, to ka yi taka tsantsan, kada ka saki jiki da shi, ka tausasa masa irin tausayin ka ga ƙaramin yaro, ka faɗi abin da zai faranta masa rai, in dai bai saɓawa shari’a ba. Kada ka yi karambanin shiga cikin harkokınsa da iyalinsa ko ‘ya’yansa ko mataimakansa.

    30. Ka guji abokin ta-faɗi-gasassa, wannan shi ne cikakken maƙiyi lokacin da duniya ta juya maka baya.

    31. Kada ka fifita kuɗi a kan mutunci.

    32. Idan ka shiga cikin mutane ka yi sallama, kada ka ƙetare mutane. ka zauna duk inda ya samu ya samu, ka yi wa na ƙasa da kai sallama.

    33. Ka guji zaman hira a gefen hanya; sai fa in za ka baiwa hanya haƙƙinta, shi ne kau da kai daga kallon haramun, taimakon wanda aka zalunta, agaza wa mabuƙaci, kwatance ga ɓatacce, amsa sallama, taimakon mabaraci, umarni da kyakkyawan aiki da hani ga mummunan aiki da kuma tanadin wuri na musamman domin yin kaki, ban da tofarwa a alƙibla, ko barin dama ko hagu sai dai a ƙarƙashin ƙafarka ta hagu.

    34. Kada ka zauna da masu mulki, in kuwa aka jarrabe ka da zama da su, to ka guji yi da mutane da ƙarya. Ka riƙe sirri, ka karanta buƙatu da kakaci, kai dai ka yi kaffa-kaffa da su. Ban da bankaɗa a irin su ko sukar mulkin su, ko ci musu mutunci, domin masu mulki ba sa yafe waɗannan laifuka.

    35. Kada ka yawaita zama da gama-garin mutane, in zama ya haɗa ka da su, kada ka sa baki a cikin hirarsu, ka kau kai daga munanan lafazuzzukansu, ka ƙaranta haɗuwa da su da yawan kakaci. Saboda yawan kakaci yana zubar da mutunci, da haifar da gaba, da mutuwar zuciya yana sanya rafkana yana janyo ƙasƙanci,, da kashe zuciya. ldan ka zauna a wuri aka yi kakaci yana da kyau kafin a tashi a karanta wannan addu’a:

    “Subhana kallaa humma wa bi hamdika ash hadu an laa ilaaha illaa anta astagfiruka wa a tuubu ilaika”.

    Domin karanta cikakken bayani akan Zaman Lafiya Da Iyali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Ziyarar Mara Lafiya danna nan.

    Wannan bayanin anciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

     

  • Abubuwan Da Suke Hana Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

    Abubuwan Da Suke Hana Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

    Wannan muhimmin abu wanda kowa yake buri, yana gamuwa da cikas da matsaloli daga ɓangarori daban-daban. A gaskiya ma dai mutane da dama masu begen zaman lafiya da kwanciyar hankali, su da kansu suke janyo hargitsi da tashin hankali ga kawunansu da sauran mutane.

    Wannan kuwa yana faruwa ta hanyar aikata abubuwan da suke hana zaman lafiya da kwanciyar hankali. Ga wasu daga cikin waɗannan abubuwa:

    Kafirci

    Kafirci shi ne babban abu da yake hana zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma wannan yana nufin kafirai su ne manyan maƙiya ga zaman lafiya da kwanciyar hankali. Allah Ta’ala ya ce “Kuma wanda Allah ya yi nufi ya ɓatar da shi, sai ya sanya ƙirjinsa a ƙuntace, kamar mai hauhawa cikin sama” (Suratul An’am: 125).

    Wannan aya tana siffanta irin damuwa da ƙunci da tsiya da kafiri yake ciki saboda kafircinsa. Ko da kuwa ya mallaki komai a duniyar nan. Dalilin wannan shi ne babu imanı tabbatacce a zuciyarsa, kuma ba shi da tabbatacciyar makomarsa.

    Ga rashin ƙa’idoji da ladabai na gaskiya masu tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Misalai a nan suna da yawan gaske, amma gajeren nazari kan rayuwar kafiran Amurka da sauran ƙasashen Turai na yaɗuwar kowace irin ɓarna, kamar fashi, fyaɗe, kisan kai da baƙin zalunci da ɗimuwa da madawwamiyar firgita, zai nuna mana yadda kafirci ke hana zaman lafiya da kwanciyar hankali. Ya Allah ka ƙara kiyaye mu. Amin.

    Saɓon Allah da aikata miyagun laifuffuka

    Saɓo da mugunta su ne abubuwa masu daraja ta biyu da suke fatattakar zaman lafiya da kwanciyar hankali. Wannan abu a fili yake, saboda duk wani mai saɓon Allah cike yake da ɓacin rai tsoro da rashin kwanciyar hankali. Misali mazinaci yana cike da tsoro da firgita don kada a gan shi, kuma yana gamawa sai wani irin mummunan ɓacin rai ya turniƙe shi. To ka auna halin da ɓarayi, ‘yan fashi, manema maza da sauran masu saɓo suke ciki. Su da kansu sun san babu zaman lafiya da kwanciyar hankali a tare da su.

    Ga abin da kafirin Bamaguje Wani mashahurin masanin falsala wato “Socrates yake cewa: “Haƙiƙa duk mai laifi ba ya rabuwa da tashin hankali da tsiya, musamman wanda ba a yi masa hukunci ba”. Ubangiji Ta’ala ya ce “Duk wanda ya kau da kai daga ambatona (Shari’ a ta) to haƙiƙa rayuwa mai ƙunci za ta tabbata a gare shi, kuma za mu tashe shi ranar Ƙiyama makaho” (Suratu Taha: 122) A wannan aya Allah Ta’ala ya tabbatar da rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali ga duk wanda ya keta hurumin shari’arsa, ya kama son zuciya ƙaunar nau’o’in saɓo da aiki da “kwance-tushe (constitution).”

    Hassada da ganin ƙyashi

    Hassada wani mummunan ciwo ne da yakan kama zukatan masu raunin imani da jayayya da ikon Allah. A duniyar nan babu wahalalle irin mahassadi. Saboda shi kullum baƙin ciki yake ga baiwar da Allah yake yi ga bayinsa, in tashi ne a kwace a ba shi, ko a fasa kowa ya rasa.

    Asara biyu ce ke afkuwa ga mahasadi, ta farko a duniya, domin a maimakon Allah ya kwace baiwarsa ga wanda yake yiwa hassadar, sai ma dai ya ƙara antayo masa ita, shi dai sai dai ya yi ta ci baya, haka zai ƙare a tsiya ce.

    A nan Bahaushe ya yi gaskiya, inda ya ce, “Hassada ga mai rabo taki ce”.

    Asara ta biyu ta shafi addini, da farko dai ga zunubin fushi da jayayya da hukuncin Allah, Ga zunubin gaba da musulmai, ga koyi da shugabannin mahassada wato Shaiɗan, Kabila da Arna, sannan kuma uwa-uba, hassada tana cinye lada kamar wuta da shiba. Ya ɗan uwa in dai kana son zaman lafiya da kwanciyar hankali, to ka wanke zuciyarka, ka saki ranka ka yarda da ikon Allah, in ka ga Allah ya yi ni’ima ga wani kada ka yi fushi, in kai ma kana so, ka roƙi Allah kuma ka bi halaltacciyar hanya domin neman abin. Sai ka huta da wahalar banza.

    Gaba da riƙo

    Gaba da mutane da matsanancin riƙo a cikin zuciya, su ma suna kandagarki ga samun zaman lafiya da kwanciyar hankali. Wannan shi ya sa kafin muminai su shiga aljanna sai an wanke zukatansu tas, an kawar da duk wani fushi da gaba daga zukatunsu, saboda ita aljanna gida ne na zaman lafiya da kwanciyar hankaii, mai gaba da riƙo kuwa ba shi da wani rabo a cikin wannan babbar ni’imá ta Allah. Saboda haka ɗan uwa ka so ‘yan uwanka musulmai, ka yi musu afuwa ka mance baya, domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Fushi

    Duk mutumin da ba shi da haƙuri, mai saurin fushi bini-bini ya tada jijiyar wuya yana huci, to haƙiƙa wannan mutum ba shi ba zaman lafiya ballantana kwanciyar hankali.

    Dalilin wannan kuwa a fili yake saboda ita wannan rayuwa cike take maƙil da abubuwan haushi a kewaye da ɗan Adam, dole ka ji ko ka gani ko ka shaƙa, a gida ko a hanya ko a kasuwa kai har a masallaci da makarantu, to in ba ka yi haƙuri ba yaya za ka yi? Sai dai in za ka iya zama kurma kuma makaho, in kuwa ba haka ba, to ka yi haƙuri, in duk ka ƙi wannan to ka yi sallama ke nan da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Zalunci

    Allah Ta’ala ya ce: “Haƙiƙa azzalumai ba za su rabauta ba (Suratu Yusif: 23). Wannan aya ta tabbalar ƙarara cewa ko a duniya ko a lahira da azzalumai ba su taba samun zaman lafiya da kwanciyar hankali ba.

    A halin yanzu babu buƙatar dogon bayani a kan wannan magana. Babbar shaida ita ce irin matsanancin tashin hankali da firgita da manyan azzalumai suke ciki a ko’ina a duniya. Duk inda za su za ka gansu a guje, suna kulli-kurciya da wasan ɓuya da jama’a. kai da dama daga cikinsu ba sa iya barci, sai sun sha ƙwaya, kuma duk inda za su, sai ka ga tsaro da muggan makamai kamar za a yaƙin duniya. Daga ƙarshe Allah yakan ƙarbi rayukan azzalumai cikin ƙasƙanci da wulaƙanci da tozarta. Kai Allah wadaran azzalumi. ɗan uwa a guji zalunci babba da ƙarami domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali

    Tsoron wanin Allah

    Duk mutumin da baya tsoron Allah, to lallai zuciyarsa za ta cika da tsoro da fargaba, mai dalili da mara dalili. Duk lokacin da mutum ya shiga cikin irin wannan hali to shi da zaman lafiya da kwanciyar hankali sai yadda ta yiwu.

    Imamu Malik (Radiyallahu Anhu) ya ce “Ka ji tsoron Allah sai komai ya ji tsoron ka, in kuwa ba haka ba sai ka yi ta jin tsoron komai har inuwarka”
    To ɗan uwa ina ka nutsuwa ga wannan mutum?

    Camfi

    Wani Shaihin malami mai nazari kan ɗabi’ar ɗan Adam Dokta Aziz Farid ya ce: “Mai imani da camfe-camfe yana faɗawa cikin musibu fiye da waɗanda yake tsoro”!

    Wato duk mutumin da ba zai yarda da tsarin Allah ba cikin rayuwarsa, a’a ya miƙa wuya ga camfe-camfe sai an yi kaza-kaza zai faru, in ba a yi kaza ba kaza ba zai faru ba, to wannan shi ma ya yi sallama da zaman lafiya da kwanciyar hankali. In kana so ka tabbatar da wannan magana, ka yi nazarin rayuwar mutumin da ya yi imani da camfi ka ga ruɗu da firgici, ɓacin rai, wahala, tashin hankali iri-iri rashin zaman lafiya da kowa. Ya Allah ka tsare mu.

    Mummunan zato

    Allah Ta’ala ya ce “Ya ku waɗanda suka yi imani, ku nisanci yawancin zato saboda wani sashi na zato zunubi ne” (Surat Al-Hujrat: 12). Kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: “Ku guji zato, saboda zato shi ne mafi ƙaryar zance” (Bukhari da Muslim ne suka rawaito).

    Idan mutum ya kasance kullum cikin mummunan zato ga kowa to zai rasa abokin zama, saboda da haka sai ya kasance cikin tsoro da tashin hankali, daga nan sai ya yi ban kwana da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Girman kai

    Mai girman kai yana rayuwa cikin tsiya, nunƙufurci da ɗacin rai, kafin kuma ya tunkuyi burjı (mutuwa) ya madawwamiya. Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: game da rayuwar ƙasƙanci “Wanda yake ɗauke da ƙwayar zarra na girman kai a zuciyarsa, ba zai shiga Aljannah ba” (Bukhari).

    Mutum mai girman kai, yakan take gaskiya, ya rinka wulaƙanta mutane, kuma duk da haka shi yana so a girmama shi, amma sai burinsa ya kasa cika, daga nan sai fushi da damuwa ya kama shi, sai zalunci shi ke nan shi ma sai ya nemi zaman lafiya da kwanciyar hankali ya rasa. Allah ya jiƙan Ɗan Maraya inda yake cewa “Girman kai rawanin tsiya”.

    Rataya zuciya da wanin Allah

    Wannan ya haɗa ka ƙwallafa rai, ka da wannan ya haɗa sakankancewa da samun wani abu daga wani mutum ko abu, ko makauniya kuma matsananciyar soyayya ga wanin Allah. Yin haka yana jawo ɗimbin wahala da ɓacin rai da tashin hankali. Ya ɗan uwa domin tabbatar da haka yi ƙoƙari ka karanta labarin nan na soyayya na Majnun Laila ka ga irin rayuwar wahala da tsiya da ya yi, kuma duk a banza. Ko kuma ka yi nazarin rayuwar wani wanda ya ƙwallafa ransa kan wani mutum ko albashi ko sana’a ya mance da Allah, ka ga yadda suka yi hannun riga da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    Shan abubuwa masu sa maye.

    Waɗansu ƙidahumai sokwaye sukan danƙarawa kansu ƙwayoyi da sauran abubuwa masu daɗin rai da nutsuwa, sa maye wai don su sami daɗin rai da nutsuwa, amma ina! Sai ka ga kamar mai ihun gobara ne, kuma ya tuttula fetur a cikin wutar. To yanzu mai karatu ka taɓa ganin wani ɗan ƙwaya cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali? A yi hattara.

    Waɗannan kaɗan ne daga cikin abubuwan da suke hana zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma.

    Wataƙila mai karatu ya ce, to shin waɗanne abubuwa ne suke tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali na gaskiya? To mai karatu ya gyara zama ka sha karatu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Suke Kawo Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Sakamakon Zalunci Yake danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Ruɗani Game Da Hanyoyin Samun Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali.

    Ruɗani Game Da Hanyoyin Samun Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali.

    1. Kuɗi

    Waɗansu mutanen gani suke yi, ba mai more rayuwa a duniyar nan da samun natsuwa sai mai kuɗi. Shi ne kawai yake iya huce haushin duniya, ai in ka sami kuɗi ka sami komai, ka haye ka wuce tsara, ka fi ƙarfin raini, haka suke gani.

    To amma shin kuwa abin haka yake mai kuɗi shi ne yake samun zaman lafiya da kwanciyar hankali?

    Bari mu ga waɗannan ‘yan misalai guda biyu:

    Ƙaruna biloniyan biloniyoyin duniya.

    Tun da Allah ya yi duniya ba a taɓa mutum mai mahaukaciyar dukiya ba irin Ƙaruna.

    Alƙur’ani ma da kansa ya jinjina irin tarin dukiyar da Allah ya mallaka masa. Ya zama tauraron duniya son kowa ƙin wanda ya rasa. Duk inda ya yi, sai sha’awarsa ake yi, ana haɗiyar yawu, ana ina ma ni ne Ɗanƙaruna. Yana takawa ɗaiɗai, yana hura hanci yana ganin ya fi kowa, babu wanda ya isa sai shi.

    Amma a ƙarshe kuɗinsa ne suka jawo masa halaka. Saboda irin girman kai da ɗagawa da ya rinƙa yi Allah ya halakar da shi da dukiyarsa. Karanta sura ta 28, suratul Ƙasas ka sha labari.

    Christina Aunasis

    Wata hamshaƙiyar biloniya ce yar ƙasar Jamus, wacce ta gaji dukiya ta fitar hankali daga iyayenta. Ubanta ya mutu ya bar mata tsabar kuɗi wuri na gugar wuri Dala miliyan dubu biyar da jiragen ruwa maka-maka, da na sama jibga-jibga, kai har tsibirai ubanta ya bar mata, ba a ma maganar gidaje gonaki da filaye. To shin wannan dukiya ta kawo mata zaman lafiya da kwanciyar hankali?

    Ga taƙaitaccen labarinta. Uwarta dai ta mutu cikin baƙin ciki da mummunan yanayi, bayan ubanta ya wulaƙanta ta ya sake ta. Yayanta kuma jirginsa na sama ya hau yana ta wasan asha-ruwan-tsintsaye a kai, sai kawai ya rikito da shi ya mutu. Shi Kuma ubanta neman suna ne ya kai shi ya auri tsohuwar matar tsohon shugaban Amurka “John Kennedy”. Duk da ta kafa masa sharaɗin ba za ta yarda ya kwanta da ita ba, kuma ba wani umarni nasa da za ta ɗauka ga kuma miliyoyin daloli da ya kashe-kashe, amma ka san mai jan kunne da neman suna….. duk da haka zaman bai yi daɗi ba ya sake ta. Haka dai ya mace cikin damuwa da alhini.

    Yanzu saura “Christina” ita kaɗai tare da ɗimbin dukiyarta. Da farko ta auri wani ɗan Amurka, amma ba a shekara ba ta sake shi. Sai ta tafi “Grecce” ta sake yin aure, shi ma abin bai yi daɗi ba, ta sallame shi.

    Daga nan sai ta nufi Rasha Kasar gurguzu, inda ba a yarda mutum ya zamo mai kuɗi ba, duk da haka ta yarda ta auri wani ɗan Rasha ta zauna ita kaɗai, ko yar aiki ba ta da ita, da ‘yan jarida suka tambaye ta yaya haka kuma? Sai ta ce, “Lalube nake ko na sami kwanciyar hankali”. Shekararta ɗaya a Rasha ta saki wannan miji. Sai ta nufi Faransa.

    A can ta auri wani Bafaranshe, aka yi gagarumin biki, ‘yan jarida suka tambaye ta game da dukiyarta sai ta ce: “Ni ce macen da ta fi kowa kuɗi a duniya, kuma ni ce macen da ta fi kowa hankali a duniya!”

    Bayan sun haifi ‘ya mace da wannan bafaranshe sai ta sake shi. Kai a ƙarshe dai tsintar gawar ta aka yi a Ajantana har yau ba a san dalilin mutuwarta ba.

    A gaskiya kuɗi dai shi kaɗai bai isa ya tabbatarwa da mutum zaman lafiya da kwanciyar hankali ba. Shi dai neman sa wahala, in an samu ba hutu, saboda tsoron kada su ƙare. Ga yawan tunani da damuwa. Ga tsoron ‘yan fashi ɓarayi da ‘yan ina-da- kisa, da zalunci a gwamnati, ba cikakken zama, ballantana isasshen barci, abinci ma ba shi da cikakken lokacinsa, ballantana iyali. Kai tashin hankalin yana da yawa. Allah ya kyauta, ya kuma ba mu na rufin asiri.

    2. Suna

    Waɗansu kuwa sukan ɗauka cewa kwanciyar hankali yana cikin yin suna. A ɓangaren wasan kwaikwayo da wasannin motsa jiki kamar ƙwallon ƙafa kokawa da sauransu. Masu irin wannan tunani za ka ga suna matuƙar sha’awar taurarin ‘yan wasa da shahararrun gwanaye a ɓangaren wasannin motsa jiki.

    To amma masu wannan tunani sun tafka kuskure, saboda babu waɗanda suka fi taurarin ‘yan wasa tashin hankali da rashin zaman lafiya. Ka ɗauki ƙwallon ƙafa, misali irin faman wahala da suke sha wajen gwaji (training) da wulaƙanta da suke kafin su cancanci zama zakaru, ga rashin zama wuri ɗaya, da dama daga cikinsu sukan salwantar da karatunsu saboda ƙwallo. Sukan shiga halin tsoro da faɗuwar gaba duk lokacin da za su kara da wani kulob. Idan kuwa ba su yi nasara ba, ai sun shiga uku a wajen magoya bayansu, za su sha la’ana da zagi, wani lokacin ma har da duka.

    Kuma ba wuya an mance da mutum, an koma kan wani gwarzon, shi kuma an jefa shi a kwandon shara. Daga nan sai ya shiga rayuwar takaici da ɓacin rai, musamman ganin ana yi babu shi. Haka dai zai ƙare ya mace a wulaƙance.

    To don Allah ɗan uwa ina abin sha’awa a nan.

    To in ka ɗauki ‘yan wasan kwaikwayo su ma haka suke, farkonsu shaye-shaye da lalata da rashin zama wuri ɗaya, rashin mutunci, rashin kunya ga zunubin ɓata tarbiyya, sannan kuma da tauraron mutum ya disashe, sai a tattara shi a koma wani. Ya mutu a banza ba addini ba adila. Shin yau ina su Pele James Brown, Amita, Dram, Danhaki, Gaso-rogo da sauransu?

    To haka ma kwanan nan za ka daina jin su wane da wance, an koma gefe ana nadama marar amfani. A gaskiya babu wata nutsuwa da kwanciyar hankali cikin waɗannan wasanni. Allah ya ganar da mu amin.

    3. Mulki

    To ko a cikin mulki da riƙon muƙamai sirrin zaman lafiya yake?

    Waɗansu da dama suna ganin zaman lafiya da kwanciyar hankali na ga mulki, haka suke gani. Amma ga mai lura ya san abin ba haka ba ne. Ɗauki masu riƙe da muƙamin siyasa a yau, ga dai kuɗin kamar na Ƙaruna, ga su ɓulɓul da manyan riguna, gidaje da motoci da sauran kayan alatu. Amma shin suna iya watayawa cikin ‘yanci kamar kowa?

    Ai ko wawa ya san wannan guje-guje da rundunar yaƙi da take biye da su, ba na lafiya ba ne. Kuma wace irin wahala ce ba a sha ba kafin a samu mulkin? Sannan in an samu, sai a kasa zaune a kasa tsaye ana tsoron sharrin ‘yan adawa da kuma gushewar mulkin. Daga nan sai cutar tazarce ta kama mai mulki.

    Sai hauma-hauma da danniya ko ta-zarce ko ta-kauce. In ta-zarce ƙarin matsala in kuwa ta-kauce to sai dai a lallaɓa “Chairman” domin har hauka ta-kauce kan haifar, komai zai iya faruwa.

    Akwai ɗimbin misalai a kan wannan batu nawa. Shin ina su Fir’auna da Hamana? Ina su Shah na Iran, Ferdinand Marcos na Filfin, da Mabutu na Zaire da Abacha na Nijeriya. To ai duk ba a nan take ba, in fa ba a shimfiɗa adalci ba, to tashin hankali sai an je lahira. Allah ya tsare mu. Amin.

    To kaga dai zaman lafiya da kwanciyar hankali na gaskiya babu shi a cikin mulki sai in a lahira ga shugaban da ya yi adalci.

    4. Wayewar kai da ci gaba

    In haka ne za mu iya cewa wayayyun mutane waɗanda suka ci gaba suke da fasahar ƙere-ƙere da ƙirƙire-ƙirƙire su ne masu zaman lafiya da kwanciyar hankali. Wato dai kamar irin su Amerika da ƙasashen Turai da ‘yan boko-addini. To amma bari mu yi nazarın su, su ma mu gani.

    A gaskiya duk ɗan boko da ya amsa sunansa ya san irin firgici da tashin hankali da Turawan yamma da na gabas suke ciki abin sai su. Tarbiyya ta daɗe da yin ƙaura daga wannan yanki har an mance da sunanta. Mutunci ba a yayin sa. Tuni mutanensa suka faku. Rayuwar ƙunci kuwa da fatara da rashin sanin inda aka dosa, sai wanda ya zauna da su ko yake karanta littattafai da mujallu da suke fitowa daga can.

    Wannan shi ne ya sanya a koda yaushe suke kashe kansu ta hanyar rataye kai, ko shan guba ko kuma bindige kai, to don Allah ɗan uwa ina zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin wannan rayuwa.

    Mai karatu ruɗani game da hanyoyin samun nutsuwa yana da yawa ta yadda waɗansu Wawayen ma gani suke yi ta hanyar shaye-shaye da aikata miyagun laifuka kamar zina, liwaɗi, fashi da sauransu, wai ta waɗannan hanyoyi za su iya cimma burinsu. Amma ina! Sai ka ga waɗannan mutane su suka fi kowa shiga tasku cikin rayuwarsu. Haka nan sukan rayu cikin tsiya da wahalar zuciya kuma su yi mummunar mutuwa, su je su tarar da mummunar makoma.

    Allah ya tsare mu.

    To mai karatu tun da dai mun ga babu ci cikin waɗannan abubuwa to mene ne haƙiƙar abin da ya ke hana samun zaman lafiya da kwanciyar hankali? Karanta waɗannan babi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Su Ke Hana Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Ziyarar Mara Lafiya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Domin Karanta Cikekken Littafin Danna nan

  • Zaman Lafiya Da Iyali

    Zaman Lafiya Da Iyali

    Allah Ta’ala ya ƙaddara rayuwar mace da namiji a tare cikin tsananin buƙatar juna; babu wanda zai iya rayuwa shi kaɗai a cikin su. Saboda haka ya zama wajibi mutum ya nemi hanyoyin zaman lafiya da abokin zamansa.

    A ɓangaren maza, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi umarni da juriya da haƙuri da kau da kai, da auna kirkin mace da rashin kirkinta, sai a dubi ɓangaren kirkin a kau da kai daga ɗaya ɓangaren. Kuma a aikace rayuwarsa (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) cike take da misalai kan haƙuri.

    Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam)ya ce; “Ku kyautata wa mata, saboda su an halicce su daga karkataccen ƙashin haƙarƙari, in ka ce za ka miƙar da shi, sai ya karye, karyewar sa shi ne saki”. (Bukhari da Muslim).

    Kuma (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “Kada mumini ya ƙi (matarsa) mumina, in tana ɓata masa da wasu halayen, ai tana faranta masa da waɗansu”. (Muslim).

    Wannan Hadısi ya nuna wa ma’aurata da su zama masu godiya da afuwa ga juna; kada a rinƙa kallon juna da ido ɗaya, ai idan rai ya ɓaci, to a yi amfani da hankali a duba amfanin juna ga juna, wannan sai ya shafe kowane irin laifi.

    Sannan kai miji duk abin da za ka yi wa matarka, ka yi mata shi saboda Allah kawai! kada ka ɗau don ba ta gode ba, ko ba ta yaba maka ba, mafi yawancin mata ba su san su yi godiya ga alherin mazajensu ba. In ka fahimci haka, sai ka zauna lafiya.
    lta kuma mace, babban abin da yake kanta shi ne, cikakkiyar biyayya da nuna ƙauna ta gaskiya ga mijinta. Tsaftar jiki da tufafi da mahalli da tattali da iya girki da sakin fuska da kuma magana mai daɗi; Sinadarai ne na zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin miji da mata.

    Wani masanin halin ɗan Adam a littafinsa mai suna: “Maganin Farir Jini Da Mallaka” wanda aka fassara shi da Larabci ya lissafa ƙa’i’dojin zaman Lafiya tsakanin miji da mata, ga su a dunƙule kamar haka:

    1. Ki guji saurin fushi da muskilanci da kuma nunƙufurci. Yawancin mata da zarar miji ya dawo sai su haɗe fuska, babu sauran walwala, sai kaushin magana da galatsi. Waɗansu mazan ma haka suke in sun shiga gida, sai fushi da ɓacin rai, kamar ‘yan wuta, amma da sun fita waje sai ka ga murna kamar suna aljanna. Domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a rayuwar aure, ya kamata kowa ya ajiye makamin a sakarwa juna fuska.

    2. Ku yi ƙoƙarin fahimtar halayen juna. In ka san halın mutum, shi ke nan ka ci maganin zama da shi, Ka da ka ce a dare ɗaya za ka canja halayen matarka, waɗanda ba ka so, ke ma ki ƙyale shi ya rayu yadda yake. Canjin hali sai a hankali. Kai a gaskiya mai wani halin zanen dutse ne, babu abin da zai iya kankare shi, to kuwa tun da haka ne, ai kowa sai dai a zauna da shi da halinsa.

    3. idan wani sabani ya faru tsakanin miji da mata, bai kamata a zargi juna ko faɗa ba a gaban yara, ko waɗansu baƙi. Wato bai kamata ka balbale matarka ko ki fada wa mijinki da mita ba, a gaban ‘ya’yanku ko waɗansu baki, ko da kuwa iyaye ne ko ‘yan uwa. A maimako haka, sai ku zauna bayan kowa ya huce ku sasanta da junanku.

    Wannan shi ma tushe ne babba na zaman lafiya.

    4. Duk mutum yana son in ya yi abin kirki a nuna ya yi, kuma a yaba masa, wannan sai ya ƙara masa ƙarfin gwuiwa, ya ninka abin da ya yi, ballantana mace, wacce take da ɗabi’ar son yabo da koɗa kai, koda kuwa kan ƙarya ne. saboda haka yayin da ka ga ta caɓa ado ko ta tsantsara girki to ya kamata ko yaya ka furta kalmomin yabo. Haka ke ma uwargida bai kamata ki mayar da mijinki kamar bawa ba, ko wanda kika baiwa ajiya, ko mai ya kawo ki karɓe ki yi shiru ba na gode, sai kuma in ba a yi ba ki ɗau fushi, yin haka ƙidahumanci ne da toshewar basira.

    5. Wani muhimmin abu mai tabbatar da zaman lafiya tsakanin ma’aurata shi ne, nuna farin ciki lokacin farin cikin abokin zama, kamar bikin ‘yar uwarta ko ƙawarta ko kuma na ‘yan uwan miji, kai ko bikinsa na ƙarin aure. Saboda idan ɗaya ya yi fushi yayin ɗayan yake farin ciki, lallai kam ba zaman lafiya. Saboda haka yana da kyau miji da mata su taya junansu murnar ko baƙin cikin abin da ya samu ɗayansu.

    6. Ya kai mai gida kasance mai hikima wajen nuna wa matarka kuskuranta. Misali idan ka ce ta kawo maka ruwa, sai ta tsaya wani wuni-wuni kuma ba wani aiki ne ya ɗauke ma ta hankali ba; to kawai ta gan ka a bakin rijiya ko famfo ka ɗebo ruwanka.

    Ko kuma ba ta shara da wuri, kai kuma ba ka son ganin wurin kaca-kaca, to tunda sanyin safiya ka ɗau tsintsiya ka kama shara, shi kenan, ka huta da ɓacin rai, ita kuma in dai mai hankali ce, sai ka ga ta gyara halinta. Ka daure ka gwada wannan maganin akwai huce haushi sosai a cikin sa.

    7. Akwai littattafai da dama da aka rubutu waɗanda suke bayanin rayuwar aure musamman ga waɗanda ba su taɓa yi ba. To me zai hana ka karanta ɗaya daga cikin waɗannan littattafan da kai da matarka domin kanku ya waye, ku fita daga duhun jahilci da ƙidahumanci. Saboda bincike ya nuna yawancin rigıngimu tsakanin ango da amarya jahilci ne yake haifar da su.

    Waɗannan ƙa’i’doji guda bakwai, suna da matuƙar amfani ga wanda ya yi aiki da su; wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin ma’aurata.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mene Ne Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Cin Mutuncin Mutane Da Sunan Hamayyar Siyasa. danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Hanyoyin Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali; wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Wasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya

    Wasu Birane Da Garuruwa Da Makarantu Da KumaTsangayu A Arewacin Najeriya

    Akwai wasu al’amura da ke jawo karkatar makaranta ko masu neman karatun Alƙur’ani zuwa wasu larduna ko biranen fiye da karkatarsu ga wasu lardunan ko biranen.

    Ƙaura daga wuri zuwu wani Wurin daban, abu ne da aka san makarantan tsangaya da shi, tun kaka da kakanni. Da yawa za ka ga Wata tsangaya cike da gardawa ko almajirai a lokacin rani; amma da zarar damina ta sauka sai ka neme su ka rasa. Irin wannan na faruwa ne saboda noma da aikin gona don samun ishasshen abinci.

    A wani lokaci kuma, makaranci kan yi ƙaura da almajiransa ko kuma gardi a karan kansa, idan ya sami labarin wata tsangaya mai tashen tara makaranta; ko kuma labarin wani mashahurin alaramma mai baiwa don ya fa’idanta daga baiwar da yake da ita. Yanayin wuri da ni’imarsa ko yalwar ruwa da wadatar ƙasar noma shi ma wani dalili ne da ke jawo taruwar makaranta.

    Irin wannan al’ada ita ake kira yawon bundi a wasu sassa na Arewacin Najeriya, musamman ma Sakkwato da kewayenta. Don ƙarin haske game da asalin wannan al’ada, sai a duba Babi na Huɗu cikin Sashe na Biyu kan ɗabi’un makaranta da halayensu cikin zamantakewar tsangaya.

    Wata tsohuwar al’ada tsakanin makarantan Arewacin Najeriya ita ce, tafiya Gabas, ma’ana ƙasar Barno don samun karatu. Don haka ne ma zai yi wuya ka sami wani makaranci a faɗin wannan nahiya ta Arewa; wanda bai dangana da Barno ko kewayenta ba ya yin neman karatu. Wannan na komawa ga irin rigayen da Kanem Barno ke da shi wajen karɓar Musulunci da tsohowar alaƙar wannan daula; da ƙasshen Larabawa, ƙarnuka masu yawa da suka shuɗe.

    Ƙasar Barno ta zamo tamkar wata Ka’aba ce ga manema Alƙur’ani. Makaranta, a bisa ɗabi’arsu, sun fi son wurin da za su keɓance kansu nesa da jama’a; kodayake buƙatun rayuwa na yau da kullum musamman buƙatar abinci ya jawo yawaitar almajirai da makaranta cikin birane da garuruwa masu cigaban kasuwanci da tashoshin mota da kasuwanni.

    Za mu iya ayyana wasu garuruwa da suka yi fice tuntuni da tara makaranata a Arewacin Najeriya kamar haka:

    – Ngazargamu
    – Gaidam
    – Gashuwa
    – Gubuci
    – NGuru
    – Damaturu
    – Takai
    – Bama
    – Ganjarma
    – Birniwa
    – Kebberi
    – Hadejiya
    – Kondiga
    – Paki
    – Kahutu
    – Hunƙuyi
    – Matazu
    – Tsakuwa
    – Maƙarfi
    – Kura
    – Zangon Daura
    – Ningi
    – Bunkure
    – Illela a Nijar
    – Kance a Nijar
    – Mutame a Nijar
    – Insharuwa da dai sauransu.

    Abu ne mai matuƙar muhimmanci sanin yawan tsangayunmu na Alƙur’ani, da yawan malamansu da almajiransu. Wannan ya sa tsohowar gwamnatin jihohin Arewa ƙarƙashin jagorancin Marigayi Sir Ahmadu Bello; Sardaunan Sakkwato ta aiwatar da wannan ƙididdiga a Makarantun Alƙur’ani Bisa ƙididdigar Gwamnatin Arewacin Najeriya (1960)

    Domin karanta cikakken bayani a kan Gudunmawar Tsangayun Alƙur’ani Wajen Cigaban Al’umma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.