Lokuta Da Yanayi Da Kuma Wuraren Da Ake Karɓar Addu’a

0
761

Yana cikin kamala da girman karamci da rahamar Allah ya sanya a kowanne lokaci dare da rana bawa ya fuskanci Allah yayi addu’a za’a amsa masa.

Tare da akwai wasu lokuta da gurare waɗanda Allah jalla wa’alaa ya albarkacesu da daraja ta musamman, wanda addu’a acikinsu keda tasiri na musamman. Ga wasu daga ciki:

1. Addu’a ranar Arafah.

2. Addu’a a Lailatul ƙadr.

3. Addu’a akashi daya cikin ukun karshen dare.

4. Addu’a bayan tahiyar karshe.

5. Addu’a a cikin sujjadah.

6. Addu’a tsakanin kiran Sallah da Iƙama.

7. Addu’a yayin saukar ruwan sama.

8. Addu’a ranar juma’a.

9. Addu’a yayin shan ruwan zam-zam.

10. Addu’a yayin da ake kiran sallah

11. Addu’a yayin tashi daga bacci.

12. Addu’a a kwanaki goman farko na Dhul-hijjah.

13 .Addu’a a cikin ka’abah.

14. Addu’a yayin gama karatu ko karantarwa.

15. Addu’a yayin da mayaƙa sukayi sahu.

16. Addu’a a majalissan da ake ambaton Allah.

17. Addu’a yayin da imani ya ƙaru a zuciya.

18. Addu’a bayan zare ran mamaci.

19. Addu’a yayin jifan jamraat.

20. Addu’a akan dutsen safa.

21. Addu’a akan dutsen marwa

22. Addu’a a mash’aril haram.

23. Addu’a yayin ziyarar marar lafiya.

24. Addu’a gabannin sallar azzahar.

25. Addu’a a watan Ramadhan.

26. Addu’a yayin sahur ga mai azumi.

27. Addu’a yayin buɗa-baki ga mai azumi.

28. Addu’a yayin shiga tsanani, matsi da ƙunci.

29. Addu’a da addu’ar zun-nun Alaihis salaam.

30. Addu’a da Istirja’i.

31. Addu’a a multazam.

32. Addu’a a Makam Ibrahim.

33. Addu’a yayin karatun suratul fatiha.

34. Addu’a yayin ƙarfafuwar Mahabbah da Ikhlasi a zuciya.

35. Addu’a yayin carar zakara.

Duba:

1. Du’aa na Dr. Yassir Qadhi

2. Addu’a wa Manzilatahu Minal Aqidatil Islamiyyah na Dr. Jilan Alarusiy wanda rubuntunsa ne, na Masters Degree kulliyatud da’awah, Qismul Aqidah a Jami’atul Islamiyyah Madinatul Munawwarah a shekarar 1410A.H.

3. Ahmiyyatud Du’a wa Kaifiyyatahu fis Sunnatin Nabawiyyah na Dr.Ibrahim al-Hamd.

Domin karanta cikakken bayani akan Alkunyar Da Ake Wa Manzon Allah (S.A.W) danna koren rubutun nan.

labarin da ya wuceHadisi Na Goma Sha Bakwai A Kan Haramcin Zalunci, Da Tasirin Addu’ar Wanda Aka Zalunta, Da Wajabcin Taimaka Masa
Labarin na GabaYadda Ake Noman Wake