Fa’idojin Da Suke Cikin Yin Aure

0
50

Fa’idojin da suke cikin aure ba za su ƙididdigu ba. Amma ga wasu kaɗan daga ciki  za mu lissafo kamar haka:- 

  1. Yin aure biyayya ne ga Umarnin Allah da Manzonsa. 
  2. Yin aure yana sanya Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) farin ciki a ranar  lahira. Yace : “Ku yi aure ku hayayyafa. Domin ni zan yi ma sauran al’ummomi  alfahari da ku a ranar Alkiyama”. 
  3. Ta dalilin aure za a samu wanda zai fito ya furta kalmar Shahada!! “la ilaha illal  lahu Muhammadur rasulullahi”
  4. Ta dalilin aure ne za ka samu zuriyar da za su yi maka addu’a bayan rasuwarka.  Wannan yana daga cikin ayyukan da ladansu ba zai yanke ba har abada. 
  5. Yin aure ya kan zama dalilin runtsewar idanun mutum daga kale-kallen haramun,  sannan ya kare masa al’aurarsa daga zina. 
  6. Ta dalilin aure ne za ka samu damar taimaka ma ‘yar uwarka musulma, ka aure ta, ku kiyaye kan ku daga zina. 
  7. Ta dalilin aure ne za ka samu cikar addininka, da ninkawar ladanka fiye da wanda  ba su da aure. 
  8. Ta dalilin aure ne za ka samu ladan ciyar da matarka, da ɗaukar nauyinta, da ladan  samar mata da mazaunin da za ta rayu.
  9. Ta dalilin aure ne za ka samu damar ƙara yawan musulman duniya ta hanyar  haihuwar da za ka samu. 
  10. Ta dalilin aure ne za ka samu damar karkatar da himmarka daga kan neman biyan  buƙatarka ta hanyar haram izuwa ga hanyar halal. Da kuma samun ladan saduwa da  iyalanka. 
  11. Za ka samu lada mai girma sosai idan har Allah ya azurtaka da ‘ya’ya mata guda  biyu, kuma ka yi haƙuri da su ka kyautata musu, ka kyautata tarbiyyarsu, su za su  zama garkuwarka daga shiga wuta. 
  12. Idan har ‘ya’yanka guda biyu suka rasu, kuma ka yi hakuri, to Allah zai shigar  da kai Aljanna saboda wannan. 
  13. Ta dalilin aure za ka samu karuwar mutuncinka da darajarka a cikin al’umma. Ka shiga sahun mutanen da za su iya jagorantar lamuran rayuwar al’umma.
  14. 14. Ta dalilin aure ne za ka samu taimakon Allah cikin lamarinka. Kamar yadda  Manzon Allah (s.a.w) yake cewa: “Mutum Uku, hakki ne akan Allah ya  taimakesu. Wanda zai yi aure don nufin kame mutuncinsa da bawa wanda yake  neman ‘yancinsa saboda ya samu daidaituwa (A cikin Addini) da kuma Mujahidi  (mai yaƙin ɗaukaka addinin Allah)

Danna nan domin karanta alamomin shigar so 3

Domin karanta falalar yin aure danna nan

Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

labarin da ya wuceFalalar Yin Aure
Labarin na GabaTarihin Hakimin Kudan Marigayi Alhaji Ishaƙ Muhd Ashir Kudan