Falalar Yin Aure

0
68

Aure shi ne ginshinƙin rayuwar mutane haɗi da yaɗuwar jinsin mutane, sannan  kuma dukkanin mutanan da basa yin aure ko gari ko jiha ko ƙasa za ka same su da  raunin tunani da hankali haɗi da rashin sanin ingantacciyar rayuwa. Aure yana da falaloli  masu girma ga waɗanda suka yi shi a matsayin sunnar ma’aiki (Sallallahu alaihi  wasallam) kuma suka kiyaye dokokin shi, ga kadan daga cikin su: 

Manzon Allah (sallallahu alaihi wasallam) ya ce “Wanda ya yi aure, haƙiƙa ya  kammala rabin addininsa, to ya ji tsoron Allah a sauran rabin” Wato ibadar  da aka halicce ka don ka yi ta, idan ka yi aure, Allah SWT ya ba ka rabin ta kyauta.

Mu’azu bn Jabalin (R.A)wani Sahabin Manzo (Sallallahu alaihi wasallam)  yace; “Sallar mai aure ta fi sallar marar aure sau arba’in”. Wato sai marar  aure ya yi sallah sau arba’in sannan za ya yi daidai da sallar mai aure guda ɗaya.

Ibn Abbas (R.A) sahabin Annabi SAW, yace; “Ku yi aure, domin kwana guda  da aure shi ne mafi alheri daga ibadar shekara dubu”. Waɗannan hadisan  akwai su cikin Buguyatul Muslimina. Waɗanda ba su da aure, su yi ƙoƙari su yi  aure kafin duniyar ta tashi.

Bukhari da Muslim su fitar da hadisi daga Ibn Mas’ud (R.A) ya ce: Manzon  Allah s.a.w ya ce “Ya ku taron samari! Duk wanda ya sami iko daga cikinku;  to ya yi aure, domin shi ya fi taimakawa wajen rintse gani, kuma shi ya fi  taimakawa wajen kare farji. Wanda bai sami iko ba, to ya yi Azumi, domin  Azumi garkuwa ne”.

Muslim ya fitar da wani hadisin daban daga Abu-Huraira (R.A) ya ce: Manzo  s.a.w ya ce “Idan ɗayanku ya ga wani abin da ya burge shi a jikin wata mace,  to ya koma zuwa ga iyalinsa, yin hakan zai mayar da abin da ke ransa na  sha’awa”. Waɗannan hadisai biyu sun nuna zahirin falalar da ke cikin aure da  kuma amfaninsa. Babbar falalar da ke cikin aure ita ce kare mutum daga  faɗawa cikin saɓon Allah ta hanyar kallon haramun ko aikata laifin zina.  Haka nan yana daga falalar yin aure akwai lada da Allah zai bai wa ma’aurata  a duk lokacin da suka biya buƙatarsu ta saduwa.

Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) yana faɗa a cikin wani hadisi  cewa “A cikin tsokar ɗayarku (wato, saduwa) akwai ladan sadaka”, sai wani  Sahabi ya ce “Yanzu ɗayanmu ya biya sha’awarsa, sannan ya samu lada” sai  Manzon Allah s.a.w ya ce “Shin idan ya sanya ta a haramun zai samu zunubi? (wato idan ya yi zina)? Sai ya ce “Ƙwarai!” Sai Manzon Allah s.a.w “To haka  idan ya sanya ta a halal zai samu lada”.

Na daga cikin falalar yin aure; samun ladan ciyarwa, Manzon Allah  (Sallallahu alaihi wasallam) ya ce “Ciyarwar ɗayanku ga iyalinsa ladan  sadaka ne”. To kun ga waɗannan falaloli ba wanda zai samu sai wanda ya yi  aure. Don haka na ke jan hankali samari da ‘yan mata da a zage damtse wajen  yin aure domin riskar waɗannan falaloli.

Ubangiji ka bai wa gwauraye cikin maza da mata damar yin aure. Ya kuma  sanya albarka cikin aurarrakin da aka yi da waɗanda za a yi. Ya Allah ka sa mu auri masu taƙawa da kwantar mana da hankali a duk lokacin da  muke cikin wani hali sannan su zamto hanyar shigarmu aljanna ameen. 

Don karanta alamomin  shigar so danna nan

Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

labarin da ya wuceJerin Abinci Da Suke Ƙarawa Mata Masu Shayarwa Ruwan Nono
Labarin na GabaFa’idojin Da Suke Cikin Yin Aure