Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Tatsuniyar Mai Haƙan Ɓera

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum da ba ya aikin komai sai ya fita farauta, yana haƙar ramukan Ɓera. Idan ya kamo ɓeraye yakan yanka ya yi bandar naman ya kai kasuwa ya sayar. Wani lokaci yakan fita wannan farauta tare da wani maƙwabcinsa, har ma sun yi suna ƙwarai wajen wannan sana’a tasu.

    Wata rana shi da maƙwabcinsa sun fita farauta, sai suka ga wani babban rami. Da suka tsaya za su haƙa sai maƙwabcin ya ce: “Wannan fa ramin Kura ne bana Ɓera ba. Kada mu tono abin da zai cuce mu.” Sai ya ce da shi: “Kai dai ka cika tsoro, idan dai kai ba za ka haƙa ba, ka tafi ka ba ni wuri.” Da maƙwabcin nasa ya ji haka sai ya tafi abinsa, ya bar shi yana tona ramin.

    Da ramin ya yi zurfi sosai, sai yasa ƙwaryarsa domin ya kama ɓerayen da yake zato suna cikin ramin. Sai ya ji an buge ƙwaryar. Da ya duba sai ya ga ashe Kura ce, har ma ta miƙo ƙafarta waje. Nan da nan ya jefar da kayan haƙan ya kama gudu. Yana cikin gudu ne ya tarar da wasu manoma a gona, sai ya ce da su: “Ku taimake ni ku ɓoye ni mana, ga Kura nan ta biyo ni za ta cinye.”

    Da suka ji haka sai suka ce: “A a, ka yi gaba, ba za mu iyaba.” Haka ya ci gaba da gudu, har ya tarar da wasu mutane masu noma da hanci, ya roƙe su da su ɓoye shi; su ma suka ce ya yi gaba. Ya sake yin gaba da gudu, har ya tarar da masu noma da duwawu, sai ya tsaya ya ce su taimake shi, amma su ma suka ƙi.

    Sai ya ci gaba da gudu, har ya hango wata ’yar bukka sai ya matsa kusa ya leƙa; amma
    ba komai a ciki sai Kunkuru yana zaune. Sai ya dubi Kunkuru ya tambaye shi: “Ina mai bukkar nan? Ina so ya taimake ni ya ɓoye ni.” Sai Kunkuru ya ce: “Ai ni ne mai bukkar, shigo zan ɓoye ka.”Sai mutumin ya ce da Kunkuru: “Manya ma ba su ɓoye ni ba sai kai da karambani za ka ce ka ɓoye ni?”

    Kunkuru ya ce da shi: “Kai dai shigo mana ka gani.” Mai neman Ɓera dai ya tsaya da gardama, har ma ya juya zai tafi, amma kafin ya fara tafiya sai ya hango Kura ta doso bukkar, kuma ya san idan ya fita za ta kama shi. Ai bai san sanda ya kutsa bukkar Kunkuru ba, kuma ya ɓoye shi. Da Kura ta ƙaraso sai ta ce da Kunkuru:

    “Da namana a ɗakin nan.” Kunkuru ya ce: “Babu namanki a ɗakin nan.” A nan Kunkuru da Kura suka kama faɗa, kafin wani ɗan lokaci Kunkuru ya kashe Kura. Da mutumin nan ya ga haka, abin ka da halin ɗan Adam sai kawai ya ce da Kunkuru: “Ni kuma ai nama ya samu a araha; bari ma in feɗe shi, kuma ina son ƙwaryar.”

    Da Kunkuru ya ji haka sai ya ce da shi: “Ka haƙura da fatar Kurar nan mana, ta fi maka amfani. Ka ma kwashe naman nata ga baki ɗaya.” Mutumin nan dai ya ƙi, ya dage shi dai ƙwaryar Kunkuru yake so. Kunkuru dai ya yarda, ya kuma ce da shi: “To, zan haɗa ka da karnuka su raka ka garinku, domin duk sanda fatar Kurar nan za ta cinye ka sai su kama ta da ci.”

    Da ƙyar dai mutumin ya yarda ya tafi da karnukan. Mutumin nan shi da karnuka sun kama hanya sun yi nisa, sai ya ji ya gaji, ya ajiye fata a gindin wata bishiya zai huta. Ajiye ta ke da wuya sai ta fara motsi tana kukan Kura. Da karnuka suka ga haka sai suka rufar mata, suka murƙushe ta, ta daina kukan, kuma ta daina motsi, ya tashi ya ɗauka suka ci gaba da tafiya.

    Bayan wani lokaci kuma, sai ya tsaya zai yi fitsari, fata kuma ta fara motsi. Karnuka kuma suka fara haushi fiye da irin wanda suka yi a baya. Sai mutumin wai ya ji haushi, ya daka musu tsawa, har suka tsorata suka gudu. Kafin ka ƙifta ido, ai fatar nan ta rufe mutumin nan ta cinye shi, kowa ya huta da taurin kansa. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Taurin kai da rashin ɗaukar nasiha babu abinda yake jawo wa mai shi sai cutarwa da faɗawa halaka.
    • Wanda bai ji bari ba, ya ji hoho.
    • Kowa ya ɗebo da zafi, bakinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Makauniya Da Ɗanta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Tatsuniyar Sarkin Maƙera Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku. A wani ɗan ƙauye, an yi wata mata mai ’ya’ya biyu, mace da namiji. Sunan namijin Fugo shi ne wa; ita kuma macen sunanta Awa, ita ce ƙanwa. Shi Fugo maƙeri ne. Ana nan, sai wata rana wani mutum daga wani gari mai nisa ya zo ya ce yana son ya auri Awa, sai aka yarda, aka ba shi ita.

    Bayan an gama biki, sai ya ɗauki matarsa suka tafi garinsu, wanda ba a bin hanyar zuwansa da rani saboda akwai wani dodo da kan tsare hanyar, ya cinye matafiya duk lokacin rani. Amma kuma da damina ba ya taɓa kowa. Ana nan, ana nan sai a wata damina Fugo ya je garin mijin ƙanwarsa Awa don ya gaishe su.

    Bayan ya dawo da rani sai mahaifiyarsu ta rasu, kuma ana so a aikawa Awa garin da take aure, to amma ba hali saboda a cikin rani ne; kowa yana tsoro kada ya bi hanyar dodon nan ya cinye shi. Ana cikin neman mai zuwa, sai kurciya ta ce za ta je ta gaya wa Awa saƙon. Sai ko aka ba ta saƙo, ta tashi sama, ba ta sauka ba sai a kan ɗakin Awa.

    Awa na kwance a ɗaki, sai ta ji kurciya tana waƙa, tana cewa:

    “Awa, Awa kina barci,

    Ga uwarki can,

    Tana barci tun shekaran jiya,

    Tun shekaran jiya ba ta tashi ba,

    Ki shirya, za ki dakan gero.”

    Sai ta fito ta saurara da kyau, ta fahimci lafazin waƙar kurciya, sai ta fashe da kuka, har da kururuwa. Da mijinta ya ji, sai ya shigo ya tambaye ta abin da ya faru. Sai tace an aiko mata da rasuwar uwarta ne. Da ya ji haka sai yace: “To, ga shi hanya ba za ta biyu ba. Yanzu yaya za a yi?”

    Duk da cewa Awa ta san dodo yana hanya kuma tabbas idan ta bi hanyar zai cinye ta, sai ta ce ita kam lallai sai ta je ta gano kushewar mahaifiyarta tun ba ta daɗe da rasuwa ba. Da mijin Awa ya lura lallai ta tsaya kai da fata sai taje, sai ya ce: “To, shi ke nan, sai mu yi wata dabara, mu yanka miki shanu, mu raba su gida bakwai, idan dodo ya taso zai
    cinye ki, sai ki jefa masa kashi ɗaya.

    Da haka har ya ƙoshi, ke kuma ki isa gida.” Sai Awa ta ce: “To na gode, mai gida.” Aka kama shanu, ya yanka, ya sa aka kasa nama gida bakwai, aka zuba wa Awa a cikin masaki. Da ranar da aka sa ta zo, sai ta kama hanya, ɗauke da masakin nama. Tana cikin tafiya a daji, sai dodon nan kwatsam ya ɓullo, yana tafiya yana waƙa, yana cewa:

    “Maraba, lale, lale,

    Wannan mata, lale,

    Ina za ki je?

    Gaya mini, ina za ki je?”

    Dodon nan baƙi ne ƙirin, ga gashi duguzunzun; abin gwanin ban tsoro. Idan ya buɗe baki sai turiri ke fita. Amma Awa ba ta tsorata ba, sai kawai ma ta mayar masa da waƙa:

    “Ni Awa, ni Awa,

    Zan je makokin mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan je kai kayan mutuwa,

    Mutuwar uwata,

    Zan kai kayan miya,

    Kayan miyar mutuwar uwata.”

    Sai dodo ya matso kusa da ita ya ce: “Buɗe in gani; menene a ciki?” Da ta buɗe masaki ya ga naman sa ne, sai ya ce: “Ko dai ki ba ni ko in haɗiye ki.” Sai ta ce: “Idan ka haɗiye ni zan yi maka kuka.” Sai dodon ya ce: “Yi kukan mu ji.” Sai ta ce:

    “Wai, wai, wai, Gari ya yi zafi,

    Uwata ba ta nan,

    Uwata ta tafi lahira.”

    Tana gama waƙar, sai ta ɗauki yankan nama ɗaya ta jefa masa. Da ya tsaya yana ci, sai ta kama hanya tana sauri. Kafin ya cinye ta yi nisa. Da ya cinye, sai ya sake bin ta, ya sha gabanta ya kama waƙa, ita kuma sai ta mayar masa. Duk sanda ta jefa masa naman, sai ta fara gudu, shi kuma ya ɗauki naman ya tsaya ya cinye.

    Da ya cinye sai ya sake bin ta. Haka suka rinƙa yi, har naman ya ƙare. Ba ta yi
    nisa ba sai ta yar da masakin, ta kama gudu. Shi kuma da ya cinye nama, sai ya bi ta. Da ta ga dai ya kusa kamo ta, sai ta hau bishiya, shi kuma ba zai iya hawa ba; sai ya tsaya a gindin bishiyar.

    Can sai ya ɗaga kai ya ce da Awa: “Ki sauko in cinye ki”. Ita kuma ta rasa yadda za ta yi, sai kwatsam ga kurciya ta sauka a kan bishiyar. Sai Awa tace da ita: “Idan na aike ki wurin yayana me za ki ce da shi?” Sai kurciya ta ce: “Zan ce da shi Fugo kana maƙera kana ƙira, amma ƙanwarka tana can a kan bishiya dodo zai cinye ta a dokar daji.”

    Sai Awa ta ce da kurciya: “Yawwa, haka za ki je ki faɗa masa.” Nan take kurciya ta tashi sama, ba ta tsaya a ko’ina ba sai kan bishiyar da ke kusa da maƙerar Fugo. Da saukarta ta fara waƙa tana maimaita saƙon da aka aiko ta sanar wa Fugo. Da ya ji waƙa, sai ya ɗaga kansa sama, ya ga kurciya, ya kuma fahimci abin da ta faɗa.

    Sai ya shiga shiri, domin bai ga ta zama ba, saboda dodo zai kashe masa ƙanwa. Ya ɗebi makamai irin waɗanda yake ƙerawa, kamar masu da kwari da baka da takubba da sauransu, ya kwance karnukan farautarsa guda goma, sai ya ce da kurciya ta tashi sama, zai bi inuwarta har gindin bishiyar da dodo ya tsare masa ƙanwa.

    Haka Fugo ya kama hanya, kurciya na yi masa jagora. Idan ya saki hanya, sai ta yi waƙa, shi kuma ya bi inda ya ji muryarta, har dai suka isa. Suna zuwa, sai suka tarar da dodon a inuwar bishiyar yana barci. Ba tare da jinkiri ba, sai Fugo ya zaro kibiya ya ɗirka wa dodon nan. Kafin ya farka, sai da Fugo ya yi masa ruwan kibau kamar ashirin.

    Da ya farka, kafin ya wartsake Fugo ya jefa masa masu kamar guda tara. Amma duk da haka da ya wartsake sai aka ji yana cewa: “Kai wane cinnaka ne yake damuna?” Shi kuma Fugo sai ya zaro wasu kibau masu dafi, ya dinga ɗana su yana sakar wa dodo ɗaya bayan ɗaya a idonsa na dama, nan take idonsa ya tsiyaye.

    Kafin ya san abinda ake ciki, Fugo ya sake auna ɗaya idon, kuma ba kuskure ya same shi. Shi ma nan take ya tsiyaye, dodo ya zama ba ya iya gani. Tuni dafin kibiyar ya bi jikin dodo, har ya zamanto ba zai iya tashi ba. Sai Fugo ya ce da Awa ta sauko. Sai dodo ya ce: “Ki sauko in cinye ki.” Da Fugo ya ji haka, sai ya zare takobi ya sassare dodo, ya yi masa gunduwa-gunduwa.

    Awa tana gani, amma da ta yunkura za ta sauko, sai guntayen naman dodo suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Da Fugo ya ga haka sai yasa karnukansa suka cinye naman dodon gaba ɗaya, sannan ya ce ƙanwarsa ta sauko. Da ta miƙo ƙafarta za ta sauko, sai ƙasusuwan suka ce, idan ta sauko za su cinye ta. Sai ya sake sa karnukansa suka cinye ƙasusuwan.

    Daga nan kuma ta sake miƙo ƙafarta za ta sauko, sai busasshen jinin dodon da ke ƙasa ya ce, ta sauko ya cinye ta. Daga nan dai sai Fugo ya sa karnukansa suka gwaguye jinin da ya yi kasko a ƙasa, har dai suka tabbatar babu kome a wurin, sai ya ce to ta sauko. A nan ne fa ta sauko lafiya, yasa ta a gaba, suka kama hanyar gida.

    Nan da nan labari ya bazu cewa Fugo Sarkin Maƙera ya kashe dodo, kuma hanya ta yi lafiya, rani da damina, babu sauran fargaba. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Haƙuri da juriya da nuna jarumta sukan sa a shawo kan matsala komai tsaurinta.
    • Farar aniya laya.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha-maza-ha-mata sai ya gani.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Tatsuniyar Umbagila Da Dodo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani ƙaramin ƙauye da yake kusa da wani daji ai cike da dodanni. Ɗaya daga cikin dodannin ya matsawa mutanen wannan ƙauyen, yana kama su ya bautar da su. Yakan fita ɗibar kayan miya duk ranar Asabar. Saboda haka mutanen ƙauyen suka daina fita ɗibar kayan miya a ranar da Dodon yake fita domin kada ya kama su ya mayar da su bayi.

    Mutanen da ya kama ne sukan dafa masa abinci da sauran wahalhalun gida na yau da kullum. Ana nan cikin haka shekara da shekaru, sai wata rana wata yarinya wai
    ita Umbagila ta ƙudurce a zuciyarta cewa za ta je ɗebo kayan miya ranar da Dodo yakan je, watau ranar Asabar.

    Sai ta gaya wa uwarta. Da uwar ta ji abin da tace sai ta dube ta ta ce: “Kada ki je domin ranar Asabar Dodo yakan je ɗibar kayan miya, idan kin je zai kama ki.” Umbagila ta ce da uwarta: “Ni dai ki yi min addu’a lallai kam zan je.” Haka dai ta haƙura ta ƙyale ta ta ɗauki ƙwarya ta shiga dajin da mutanen ƙauyen kan je neman kayan miya.

    Tana cikin cirar ganyen lalo da ayayo da karkashi da barkono da sauran kayan miya, kwatsam sai ta ji motsi a bayanta, kafin ta juya sai ta ji Dodo ya cafke ta. Tana ganinta a hannun Dodo sai ta fashe da kuka. Da ya ga ta fara kuka, sai ya ce mata ta daina kuka, idan ta yarda za ta aure shi ba zai cinye ta ba.

    Ba tare da gardama ba Umbagila ta ce da Dodo: “Na yarda in aure ka.” Shi ke nan Dodo ya kai ta gidansa ya ajiye ta, kuma ya ce daga wannan rana ba zai ci abincin da bayi suka dafa ba sai wanda ta dafa. Duk sanda Dodo ya je farauta, ko yawace-yawacensa ya dawo, da ya iso kusa da gida sai ya fara waƙa yana cewa:

    “Umbagila matata,

    Umbagila amaryata,

    Umbagila ina tuwona?”

    Ita kuma da ta ji sai ta amsa masa da cewa:
    “Dodo mijina,

    Ga tuwonka can a bakin randa,

    Ga furarka can a bakin randa,

    Ga ruwan sha nan a bakin randa.”

    Haka dai suka ci gaba da zama da Dodo. To dama Dodo yana da wata hatsabibiyar kaza a gidansa. Wata rana ya tafi yawo, sai Umbagila ta haɗa kayanta za ta gudu. Da kaza ta ga alamar za ta gudu, sai ta kira Dodo tace: “Dodo, Dodo za ta gudu.” Nan da nan ya dawo gida yace: “Na ji labari za ki gudu.”

    Sai ta yi masa murmushi tace: “A a, na shanya kayana ne, kuma yaya zan gudu in bar mijina?” Da ya ji haka sai ya ce: “Yawwa matata, na san ba za ki gudu ba.” Sai ya fita harkokinsa. Kullum idan Umbagilatayi ƙoƙarin gudu, sai kazar nan ta fallasa ta. Rannan dai sai ta zauna ta kama kuka a daidai lokacin da ta san Dodo ya kusa dawowa.

    Da ya shigo gida ya tarar tana kuka sai yace: “Me ya sa ki kuka, matata?” Sai ta ce: “Ina so in ci kaza ne, kuma na san ba ni da wanda zai ba ni ita.” Sai ya ce da ita: “Yanzu  saboda wannan ne kawai kike kuka?” Ta ce: “E, saboda haka ne.”Ya ce: “To, daina kukan haka, zan yanka miki kaza.” Sai ko ya kama kazar nan mai fallasa ya yanka suka cinye.

    Bayan sun cinye, sai Dodo ya fita farauta. Ita kuma ta shiga haɗa kayanta za ta gudu. Sai gashin kazar nan ya kira Dodo yace: “Dodo, Dodo, dawo gida matarka za ta gudu.” Tana jin haka sai ta shiga ɗaki ta ɓarke da kuka. Can Dodo ya iso gida ya tarar da matarsa tana sharar kuka, sai ya nemi jin abin da ke damun ta.

    Ta ce masa: “Bana son ganin gashin kazar nan a gidan nan.” Da jin haka sai ya tattara gashin kazar ya ƙone, ya sa bayinsa suka kwashe tokar suka kuma ƙanƙare jininta daga wurin da aka yanka ta. Washegari da Dodo ya tafi yawonsa, sai Umbagila ta kwashe ’yan komatsenta, ta gudu gidansu, ta kuɓuta daga sharrin wannan Dodo. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ƙin bin umarnin iyaye yakan janyo wa ɗan ya fuskanci matsaloli masu yawa a rayuwarsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Tatsuniyar ‘Yan Goma Sha Ɗaya

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kusa da dajin Ƙanzon Kurege, akwai wani mutum da ke zaune da matarsa. Mace ce mai haƙuri da son taimakon mijinta a hidimar da yake yi ta kula da gida. Suna nan, sai Allah ya ba matar ciki. Sannu a hankali, ciki ya girma, sai mijinta ya ce tunda cikinta ya girma, ta daina zuwa rafi ɗaukar ruwa, amma sai tace ai babu mai taimaka mata.

    Ta ci gaba da zuwa ɗaukar ruwan. Ana nan, wata rana matar nan ta je ɗaukar ruwa sai ta fara naƙuda a bakin rafi. Da sauran matan da suka je ɗaukar ruwa tare suka ga halin da ta shiga, sai suka kai ta gida. Da haihuwa ta zo, sai ta haifi jarirai goma sha ɗaya. Goma daga ciki ba su da jiki; guda ɗaya ne kaɗai cikakken mutum.

    Bayan kwana bakwai aka raɗa wa kowannensu suna. Karamin cikinsu, watau mai jiki, sai aka sa masa suna Kurma. Yaran nan suna nan yau da gobe har suka girma. To amma sai
    aka lura sauran goman duk miyagu ne, har ma sun fara ƙoƙarin cinye ƙanen nan nasu. Da iyayensu suka ga haka, sai suka kira Kurma suka ce: “Tun da ‘yan’uwanka ba za su bar ka ba, gara ka sulale cikin dare ka yi tafiyarka wani gari.”

    Can cikin dare sai babansu ya ta da Kurma daga barci ya ba shi wata sanda ya ce ya kama hanya ya tafi kawai. Kurma ya karɓi sandar da ubansa ya ba shi, ya kama hanya a cikin daren ya fice daga garin. Da gari ya waye, ‘yan’uwan suka leƙa ɗakinsa, ba su ganshi ba, sai suka tambayi uwarsu inda yake; ta ce ba ta sani ba.

    Da suka tambayi ubansu, sai ya ce da su: “Kurma ya ce in ba shi sanda zai
    je wani gari, kuma na ba shi ya tafi.” Da suka ji jawabin ubansu sai suka rasa yadda za su yi. Bayan Kurma ya koma wani gari da zama, sai ya haɗu da matar da yake so ya aura. Saboda ba shi da dukiyar da zai yi auren, sai ya sayar da sandar nan da ubansa ya ba shi lokacin da zai baro garinsu, ya biya sadaki aka ɗaura musu aure.

    Kurma yana nan zaune da matarsa cikin jin daɗi. Bayan wani lokaci sai matar ta ce: “Mai gida ya kamata mu je garinku ganin gida domin in san garinku da danginka da mahaifanka.” Da ya ji abin da ta faɗa sai ya ce: “Mhm, watau ba ki sani ba ne, ai ‘yan uwana duk ba su da gangar jiki, kuma mayu ne, idan mun je za su cinye mu.” Sai ta ce a a, ita dai sai sun je tun da mahaifansa suna nan ba wani mugun abu da zai faru.

    Da ya ga ta matsa sai sun je, sai ya ce: “To kada ki ce na hana ki zuwa, ki shirya mu tafi.” Bayan sun kammala shirye-shirye, sai suka kama hanyar garinsu Kurma. Da suka isa ƙauyen, suna shiga gidan sai suka ci karo da ɗaya yana mirginawa a ƙasa. Da matar Kurma ta ga kai ne yake mirginawa babu gangar jiki, sai tsoro ya kama ta, ta fashe da kuka.

    Su kuwa ‘yan’uwan Kurma da suka ji shi ne ya zo har da matarsa, sai suka kama waƙa suna cewa: “Lale, lale, Maraba da Kurma, Kurma lale, Kurma sannu da zuwa, Kurma lale, Kurma ina sandarka ne?” Da Kurma ya ji sun nemi sanin inda sandar da mahaifinsa ya ba shi, sai ya ce: “Na sayar da sandar.” Sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “Me ka yi da kuɗin?” Sai ya ce: “Na yi aure da su.” Suka ce: “Ina matar?”

    Sai Kurma ya amsa wa mai tambayar: “Ga ta nan a bayana, tana kuka.” Wani kuma ya tambaye shi: “Me ya sa take yin kuka?” Haka dai suka rinƙa yi masa tambayoyi, har suka shiga cikin gidan. Da uwarsu ta ga ɗanta, sai ta zo ta tarye su shi da matarsa a cikin murna a tsakar gida, ta ce su shiga ɗaki, suka shiga. Suka ƙara hutawa, har zuwa faduwar rana.

    Da dare ya yi sai uwar ta kira Kurma ta ce: “Ka san ‘yan uwanka mayu ne, me ya sa ka kawo ‘yar mutane a cinye ta?” Sai ya amsa da cewa: “Tana so ta gaishe ku ne da baba.” Sai uwar ta ce: “To shi ke nan, idan an ɗauke ƙafa zan ɓoye ku a rumbu, in sun tambaye ni in ce kun tafi; idan sun kwantasai kugudu.” Da dare ya tsala, sai ta ɓoye su a rumbu.

    Can cikin dare sai ɗaya daga cikin ‘yan’uwan Kurma ya tambayi uwarsu inda Kurma da matarsa suke. Sai ta ce: “Ai sun tafi.” Sai ya ce: “To amma yaya nake jin ƙanshin mutum a gidan nan?” Sai ta ce: “Ai ni ma mutum ce, in kuma za ku cinye ni to.” Sai baki ɗayansu suka ce: “A a, ba za mu cinye wadda ta haife mu ba.”

    Don uwar ta kwantar musu da maitar da ta motsa, sai ta ce musu: “Ai ba su tafi ba; sun je gai da ƙawayena ne; da zarar sun dawo zan dafa su.” Can cikin dare sai uwar ta taso Kurma da matarsa da ke barci a rumbu ta ce musu: “Ba ku ga babanka ba saboda ya yi bulagiro. Ga shi kuma lokacin gudu ya yi, sai ku kama hanya kafin su gane.”

    Ashe da ma ‘yan’uwan tuni suka zaci za a yi musu dabara ne, suka fice daga gidan suka tafi jiran Kurma da matarsa a bayan gari. Kurma da matarsa sun kama hanya za su gudu, sai wani da ya sanshi ya gaya masa cewa ‘yan’uwansa suna can a kan hanya suna jiran sa shi da matar su cinye su. Yana cikin wannan tsoro da damuwa, sai ga wata tsuntsuwa ta zo.

    Sai Kurma ya roƙe ta, ta ɗauki matarsa ta tsallakar da ita can gaba da inda ‘yan’uwansa suke fakonsu shi da matarsa. Nan take tsuntsuwa ta yarda, matarsa ta hau suka tashi sama. Shi kuma Kurma sai ya ɗauki ganga yana kiɗa har ya isa inda ‘yan’uwansa suke. Da ya isa sai ya fara waƙa.

    Su kuma sai suka tambaye shi matarsa; sai ya ce ya bar ta a gida. Da jin haka sai suka kama hanyar gida da gudu. Shi kuma da ya ga sun yi nisa, sai ya kama hanya ya yi ta gudu, har ya je ya sami matarsa suka yi tafiyarsu. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Bin iyaye bin Allah.
    • Tarbiya ce garkuwar kowane yaro.
    • Ceto daga Ubangiji yakan zo ne ta kowane hali.
    • Makusancinka na iya zama makashinka.
    • Zumunci maganin bala’i.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mata Da ’Ya’yanta

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Tatsuniyar ‘Yan Bakwai Da Aljana

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can kusa da dajin aljannu wanda aka ce ya yi iyaka da bangon duniya, akwai wata mata mai ’ya’ya maza su bakwai. Ana nan, ana nan sai yaran suka girma, har dai suka isa aure. Da gyatumarsu ta ga sun isa aure, sai ta tara su ta ce: “Ya kamata a ce yanzu kun yi aure, tunda ga shi Allah ya sa duk kun girma, kowa ya mallaki hankalinsa.”

    Da suka ji haka, sai babban cikinsu ya ce wa uwar: “Za mu yi aure, amma muna so a sama mana ’yan mata bakwai waɗanda suke uwarsu ɗaya.” Sai babarsu ta ce: “Kash, amma ai duk garin nan babu irin ’yanmatan da kuke so, sai dai ku tlafi nema wani garin.”

    Sai suka bi maganar mahaifiyarsu, suka shirya suka kama hanya za su neman matan aure. Bayan ’yan bakwai sun bar gari sun kama hanya, sun yi tafiya mai nisa, sai suka haɗu da wata mata da ’yarta ɗaya suna noma. Da ta ga samari bakwai rigis, sai ta ɗaga kai ta dube su tace: “Sannunku samari.” Su kuwa suka amsa gaisuwarta a cikin ladabi.

    Sai ta tambaye su inda za su. Sai babbansu ya ce mata: “Za mu je neman matan aure ne.” Da ta ji haka sai ta ce: “To ga ’yata idan za ku aura.” Tare da ban girma sai ɗaya daga cikinsu ya ce: “A a, muna neman ’yan mata bakwai ne waɗanda suke uwarsu ɗaya kamar mu.” Wannan bayani ya rufe mata baki, sai ta ce: “To, shi ke nan; ni dai
    ’yata ɗaya ce idan za ku karɓe ta.”

    Sai suka ce: “A a, mun gode.” To ashe wannan mata aljana ce ba su sani ba. Da suka yi nisa daga inda take, sai ta yi irin saurin aljannu ta je can gabansu a wata gonar da ’ya’ya mata biyu. Saboda suna da ladabi da girmama manya, a nan ma suka gaishe ta, ba tare da sun san ita ce ba, saboda ta sauya kama. Matar nan ta tambaye su labarinsu, suka faɗa mata tare da bayani a kan abin da suka fito nema.

    Sai ta nuna za ta ba su ’yanmatan nan biyu idan sun amince. A nan ma dai a cikin hikima suka yi mata bayanin cewa ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya suke nema. Suka wuce suka bar ta a wannan gonar. Da matar nan ta ga sun wuce, sai ta ɓata, ta je gaba ta ƙara sake kamanni. Ta shiga wata gonar tare da ’yan mata uku.

    Haka dai ta dinga yi musu har sai da suka kai biyar. Sai suka ce su fasai sun sami ’yan matan da su ma bakwai ne kamar su. Sai aljana ta sake ɓata, ta rikiɗa ta zama wata mata kyakkyawa mai ’ya’ya mata bakwai suna taya ta noma. Da samari bakwai suka zo za su wuce sai matar ta yi musu sallama. Da suka gaisa sai ta tambaye su inda za su.

    Kamar yadda suka saba yin bayani a baya, sai suka ce za su neman aure ne, to amma sai ’yan matan da zasu aura ɗin sun kai bakwai, kuma ’yan ciki ɗaya kamar su. Da jin haka sai ta ce wa babban cikinsu: “To tun da mun haɗu ni ma ina da ’yan mata bakwai ’yan ciki ɗaya kamar ku, in kun yarda sai in haɗa ku.” Sai baki ɗaya suka amsa mata: “Yawwa; yanzu muka sami matan da za mu aura.”

    Daga nan sai matar nan ta kai su gidanta, ta sa ’yan matan suka yi wa samarin nan ruwa. Da suka ɗebo ruwa suka kawo, sai kowacce ta ba wanda za ta aura; amma fa ruwan ba ruwa ne na gaske ba, duk jini ne, in ban da na ɗan’auta; shi yarinyarsa ba ta kawo masa ruwan jini ba.

    Da ’yan matan suka tafi sai ɗan’autansu ya ce kada su sha ruwan da aka ba su saboda jini ne, ba ruwa ba. Da sauran suka ji haka, sai suka zubar, ya ba su nasa suka sha suka ƙoshi. Can kuma sai ’yan matan suka shiga dafa wa baƙinsu abinci. ’Yan mata shiɗa suka ɗebo naman mutane da uwar ta yi tanadi, suka shiga dafa wa samarinsu; amma ƙaramar cikinsu ta ɗan’auta, sai ta ɗebo naman shanu ta girka wa masoyinta ɗan’auta.

    Da suka dafa abinci suka kawo wa mazajensu, sai da aka zo cin abinci, ɗan’autansu ya ce su zubar da abincin domin da naman mutane a ciki. Da suka zubar sai ya kawo musu nasa suka ci, har suka ƙoshi. Da dare ya yi, sai aka nuna wa kowannensu ɗakinsa shi kaɗai. Amma ɗan’auta da amaryarsa sai suka shiga wata bukka.

    Can bayan duk sauran sun yi barci, sai surukarsu, watau aljana ta fara wasa wuƙarta domin ta riga ta yanke shawara idan dare ya yi za ta yanka su duka. Saboda ɗan’auta ya san abin da matar take son yi, sai ya zagaya ya shiga kowane ɗaki, yana cire wa mazan kayansu yana sa musu na mata, su kuma matan yana sanya musu kayan mazan.

    Da ya gama, ya koma ɗakinsa ya shirya ya kama tona rami har zuwa garinsu. Da ya gama sai ya kwanta yana sauraron matar nan ta dinga shiga ɗaki-ɗaki tana yanka ’ya’yanta ba tare da ta sani ba. Da ɗan’auta ya tabbatar matar ta gama yanke-yanken ta koma, sai ya fita ya tashi duk ’yan’uwansa don su gudu.

    Sai suka shiga ramin da ya tona suka tafi gida. Ita kuwa aljana da gari ya waye sai ta fara buga ƙofofin ’ya’yanta don su tashi, amma shiru. Da ta karairaya ƙofofin ta shiga ɗakunan, sai ta tarar ashe ’ya’yanta ne ta yanka gaba ɗaya. A nan take ta fara kuka. Da ta ɗan huce, sai ta ce sai ta yi maganin yaran nan.

    Sai ta rikiɗa ta zama goɗiya ta shiga garin ’yan bakwai. Da ta je daidai gidansu sai suka gan ta. Sai ɗan’auta ya ce a bar shi ya kama ta, sai babbansu ya ce: “Ai kai ne ƙarami don haka bai kamata ka kama goɗiyar nan ba.” Sai ya bari babbansu ya kama ta ya ɗaure ta cikin gidansu yana kiwonta, har ta yi ƙiba, ta yi kyau.

    Bayan wasu kwanaki sai ɗan’auta ya ce da yayansa: “Yau zan kai maka goɗiyarka rafi.” Sai ya ce: “To, na gode.” Sai ya kwance goɗiya ya kai rafi ya ɗaure a jikin bishiya; sai ya samo wata babbar sanda ya fara jibgar goɗiyar nan yana waƙa yana cewa: “Ba goɗiya ba ce, aljana ce.”

    Ya doke ta sosai har ta rame. Da ya koma gida da goɗiyar sai yayansa ya ga duk jikinta jina-jina, kuma ta rame. Ganin haka sai yayan nasa ya kama shi da faɗa. Sai ɗan’auta ya ce: “To shi ke nan, muna nan da kai za ka zo ka yi da-na-sani.” Washe-gari sai babban wan su ɗan’auta ya hau goɗiyar domin ya kai ta rafi shan ruwa.

    Amma da goɗiyar ta ga sun fita daga cikin gari, sai ta kama sukuwa kamar za ta tashi, ba ta tsaya ba sai a gidan aljanar da ta so yanka su. Tana isa ta zame, ya faɗo ƙasa, kuma ta rikiɗa ta koma siffarta ta aljana. Sai ta dube shi tace: “’Yan banza; ni kuka kashe wa ’ya’ya, to duk sai na cinye ku. Tashi ka jiƙa waccan tokar miyar don zan dafa ka da ita in an jima da daddare.”

    Sai ya tashi ya jiƙa tokar miya; sai aljana ta ce: “Zauna kusa da tokar don da ita zan dafa ka.” A can gida ba a ga yayan ɗan’auta ya dawo ba, sai ɗan’auta ya rikiɗa ya koma ɗan maraƙi ya je gidan aljana. Daga shiga sai ya nufi inda ɗan’uwansa yake zaune, ya ture tokar da ke gabansa.

    Da babban ya ga haka sai ya ce wa aljana: “Kin ga ɗan maraƙi ya zo ya zubar da ruwan tokar.” Sai aljana ta ce: “Maza ka kwashe ka kai can waje, ka dawo ka sake jiƙa wata.” Shi kuwa sai ya bi umarninta. Ya kori ɗan maraƙi waje, sai ya sake jiƙa toka ya zauna a gefe. Yana zaune sai ɗan maraƙi ya sake zuwaya zubar da ruwan tokar.

    Sai ya tashi ya kirawo aljana ya gaya mata cewa ɗan maraƙin nan ya sake zubar da ruwan tokar. Sai aljana ta ce: “To ka kora shi ka kai shi bakin gangaren can mai
    nisa.” Da ya kora ɗan maraƙi har suka yi nisa da gidan aljana, sai ga ɗan maraƙi ya koma ɗan’auta. Sai ya dubi yayansa ya ce: “Ai dama na gaya maka ka yi hankali da goɗiyar nan.”

    Ba dai tare da ɓata lokaci ba sai ya ce da yayansa su tafi gida. Nan da nan suka kama hanya. Can da aljana ta ga shiru, sai ta bi sawu, sai ta ga alama lallai sun gudu. Sai ta ce: “Zan yi maganin ɗan’auta.”A nan take aljana ta rikiɗa, ta zama kyakkyawar budurwa ta shiga garin su ’yan bakwai, tana tafiya har ta kai ƙofar gidansu. Da suka gan ta sai suka ce dukkansu kowa yana son ta, amma daga ƙarshe suka amince a bar wa yayansu ita.

    Suka bar masa, aka ɗaura musu aure. Da dare ya yi suna ɗaki da matarsa sai ya ga ta rikiɗa ta zama aljana; sai ta ce: “Kun ɗauka za ku tsira daga sharri na ne?” Kafin ya ma gane abin da yake ciki, sai ta yi farat ta ƙwaƙwale masa ido, ta tafi da shi. Da gari ya waye aka buga ƙofa, sai aka ji shiru. Ɗan’auta ne ya kira yayansu ya amsa, sai ya gayawa ƙannensa amarya ta ƙwaƙwale masa idanu.

    Ɗan’auta ya ce shi kenan, ya san abin da zai yi; ya kama hanya ya je bakin rafi ya cika cikinsa da ruwa, ya rikiɗa ya zama tsohuwa, ya yafa mayafi ya tafi gidan aljana. Da ya isa ya yi sallama, sai ta amsa. ’Yar tsohuwa ta shiga ta ce wa aljana ta ji an yi mata rasuwa shi ya sa ta zo yi mata gaisuwa, kuma ta ƙara ba ta haƙuri da rashin da ta yi.

    Da aljana ta ji jawabin tsohuwa, sai ta yi mata godiya, kuma tace: “To me zan ba ki ne tsaraba tun da kin zo yi mini ta’aziyya daga nesa?” Sai tsohuwa ta ce: “Haba babu komai, sai dai ina da wata matsala da ta dame ni.” Da aljana ta ji haka sai ta ce: “Wace irin matsala ce?” Sai tsohuwa ta shiga marairaita ta ce wai yau mijinta ya yi shekara da shekaru ba shi da ido, da yana gani ma da tare za su zo gaishe ta.

    Da ta ji wannan sai ta ce wa tsohuwa: “Haba ai babu komai; ina da wasu idanu da na ƙwaƙwalo na zo da su jiya. Sai ki ɗauka, idan kin je gida ki jiƙa su a rama ki sa masa su.”
    ’Yar tsohuwa ta yi godiya, ta ɗebi idanu ta kama hanya. Da ta fita waje sai ta rikiɗa, Ɗan’auta ya koma kamanninsa na farko ya ƙyalkyace da dariya.

    Ashe aljana ta gane shi ne ya zo; sai ta ji haushi ta ce: “Na san yadda zan yi da shi da ’yan’uwansa.” Da ɗan’auta ya je gida, sai ya samo rama ya jiƙa idanun, ya sanyawa yayansa, nan da nan ya fara gani. Ana nan sai wata rana ’yan bakwai suka tafi daji su yanko ciyawa. Da suka yanka, sai kowa ya ɗaure tasa, amma sai ɗan’auta ya ga wani babban maciji ya shiga ta yayansu.

    Sai kawai yace: “Yaya ka bar mini taka zan ɗauka, kai ka ɗauki tawa.” Sai yayan ya amince da maganar ɗan’auta. Sai ɗan’auta ya sami igiya ya ɗaure ciyawar yayan nan tamau, yadda macijin nan ba zai iya motsi ba. Ya yi haka ne domin ya san aljana ce ta zama maciji.

    Da kowa ya ɗauki ciyawarsa suka kama hanyar gida, can sun kusa da gari sai suka tarar an hura wuta tana ci ganga-ganga, abin ban tsoro. Sai ɗan’auta ya jefa ciyawarsa a cikin wutar. Da suka ga haka, sai ’yan’uwansa suka ce: “Me ya sa ka jefa ciyawar ka a cikin wuta?” Sai ya ce: “Ku tsaya za ku gani.” Can da wutar ta lafa, sai ya ɗauki kara ya tona ciyawarsa, sai suka ga macijin nan ya ƙone ƙurmus.

    Mamakin baiwar ɗan’auta ya kama ’yan’uwansa. Shi kuwa ba abin da ya dame shi; sai yace musu: “Mu tafi gida, daga yanzu ƙaryar aljanar nan ta ƙare.” Wannan ne ya sa a ko ina ake tsoron ’yan bakwai. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba kullum akan kwana a kan gado ba.
    • Yawan shekaru ba shi ne wayo ba, Allah na yin baiwarsa ga wanda ya so yaro ne shi ko babba.
    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Wata Mayya Da Danta

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Tatsuniyar Maye Da ’Ya’yansa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum a wani gari da ke gabas da garin nan. Yana da mace ɗaya da ’ya’ya biyu mata. Da suka isa aure Allah ya ba su masoya, aka yi musu aure aka kai kowacce ɗakinta. Bayan ’yan shekaru kowacce ta haifi ’ya’ya. Ana nan, sai aka aika musu uwarsu ta rasu; sai dai su ba su san cewa ubansu maye ne ba, kuma shi ne ma ya cinye uwar tasu.

    Shi ke nan yaran nan suka je gidan ubansu saboda zaman makoki, amma sai suka tarar uban nasu ya cinye gawar uwar tasu, domin yunwar maita ta kama shi, kuma babu wanda zai ci sai gawar. Da ya ji muryar ’ya’yansa, sai ya kulle kansa a cikin ɗaki don kada su gani, su gane.

    Duk sanda suka kai masa abinci, sai yace su ajiye a ƙofar ɗaki. Bayan sun yi kwana biyu a gidan, sai a dare na uku ya tara su, ya fara zaro harshe yana haɗiyar yawu. Sai suka gane cewa shi ya cinye babarsu, kuma yana so su ma ya cinye su. Da man sunan ɗaya Nkwa, ɗaya kuma Sektiraye.

    Sai ya fara kiran su yana cewa: “Nkwa da Sektiraye duk da ’ya’yanku, Ku jira ni ina zuwa, Zan cinye ku, Da man ina jin yunwa.” Da suka ji haka sai suka kama ’ya’yansu suka ɓuya, kuma suka ajiye kabewa a kan gado suka lulluɓe ta. Da dare ya yi tsaka, sai
    kawai ya tashi ya kama cin kabewar da ke kan gado.

    Da ya gane ba nama ba ne, sai haushi ya kama shi. Can kuma sai ɗaya daga cikin jikokinsa ya fara kuka a inda suka ɓuya. Da ya gane inda suka ɓuya, sai ya yi kukan kura ya auka musu, amma bai cafki ko ɗaya ba. Sai ’ya’yan nasa da jikokin suka fito da gudu, suka kama hanyar dajin da ke kusa da garin, shi kumayana bin su.

    Suna cikin gudu a dawan nan sai ya kama ɓarin jikinsa ya cinye, har dai ya zama saura ƙashi a jikinsa kawai. A hakan yake bin su da gudu yana cewa: “Dun kwalak, ka dun kuci kal.” Da suka isa wani guri a cikin dajin, sai suka tarar wuta tana cin ciyawa, sai suka keta ta cikin wutar a guje.

    Saboda yawan wutar, har ta kama cin hanya. Da uban nasu wanda ya zama ƙwarangwal
    ya isa wurin wutar nan, sai ya faɗa cikinta, wuta kuwa ta cinye ƙasusuwansa, ya ƙone ƙurmus. ’Ya’yan nan nasa da jikokinsa sun sami tsira. Da gari ya waye, sai wasu mata masu neman tokar miya suka tarar da tokar wannan maye a kan hanyar, ba su san ta mutum ba ce.

    Sai ɗaya daga cikinsu ta ce su deɓi tokar miya. Sai suka ɗiba, suka koma gida. Sai ɗaya daga cikin matan ta haɗa tokar za ta yi miya da ita. Bayan ta ɗora tukunyar miya da tokar a ciki a kan wuta, sai ta ji miyar tana cewa: “Ki juya ni a hankali, domin wuta ta ƙona ni da yawa.” Da ta ji haka ba ta ce uffan ba, kuma ba ta daina girki ba, har sai da ta gama.

    Da ta gama, ta zuba, ta kai wa mijinta abincinsa a akushinsa. Data je ajiye akushin sai ta ji an ce: “Idan za ki ajiye ni, ki ajiye ni a hankali don wuta ta ƙona ni da yawa?” Da mijin ya ji, sai ya kira matarsa ya ce mata: “Na ji kamar miyar tana magana.” Sai ta dubi mijin tana murmushi ta ce: “Kai anya, ba kunnenka ba ne kuwa?”

    Sai mijin ya sa hannu zai buɗe akushi ya fara cin tuwo da miya, sai miyar ta ce: “Idan za ka deɓe ni, ka deɓe ni a hankali, don wuta ta ƙona ni sosai.” Da mijin ya ji haka, sai ya dubi matar ya ce: “To ashe ke mayya ce ban sani ba.” Sai matar ta ce: “A a ai a cikin jeji na samo tokar miya.”

    Sai mijin ya ɗauki miyar ya kwara mata a ƙirji. Nan take ƙirjinta ya fitar da haƙora gatso-gatso, abin gwanin ban tsoro. Da mijin ya ga haka, sai ya kore ta, sai ta shiga daji, ta koma can da zama. Duk wanda ya je dajin da take zai tarar da ita tana yawo, tana cin fari da kwaɗi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Tsautsayi ba a sa maka rana.
    • Mai mugun hali tun a duniya sai ya ɗanɗana kuɗarsa.
    • Aikin da ba a yi shi da kyakkyawar niyya ba ƙarshensa nadama.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Tatsuniyar Binta ’Yar Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani Sarki a wani gari mai mata biyu, kowacce tana da’ya. Yarinya ɗaya sunanta Binta, ɗayar kuma Falmata. Sarki yana ji da’ya’yan nan nasa, to amma fa ya fi son Binta don ita ce ƙarama, kuma ’yar amarya.

    Ana nan, rannan sai Sarki ya tafi wani gari mai nisa, kuma zai daɗe a can. Bayan ya tafi da ’yan kwanaki, sai ciwo mai zafi ya kama amaryarsa, watau mahaifiyar Binta. Da ta lura ciwon kamar ba wanda za ta tashi ba, sai ta kira kishiyarta ta gaya mata cewa tana jin ba za ta tashi ba, amma idan ta cika, tana roƙonta ta kula da’ya’yansu cikin amana.

    A cikin tausayi kishiyar ta ce da ita: “Zan yi bakin ƙoƙari na in kula da su.” Bayan kwana biyu da yini ɗaya, sai amaryar Sarki ta rasu. Sarki dai bai dawo daga tafiyar da ya yi ba har wasu ’yan kwanaki suka wuce. Rannan sai kishiyar uwar Binta ta sa ta ɗauko ruwa a rafi a cikin wani masaki, kuma ta gaya mata lallai a rafin Apko mai cinye mutane za ta ɗebo ruwan, watau ba a ɗaya rafin mai lafiya ba.

    Ɗaya rafin mai lafiya wanda daga shi mutanen suke ɗaukar ruwa sunansa Diddire. Binta ta ɗauki masaki ta garzaya wajen kabarin mahaifiyarta, tana kuka tana waƙa, tana cewa:

    “Baba, baba, babar Binta,

    Kishiyarki ta ce in je Apko in ɗebo ruwa,

    In je Apko ko in je Diddire?”
    Daga cikin kabarin sai ta ji mahaifiyarta ta amsa mata dawaƙatana cewa:

    “Ki je Diddire,

    Kada ki je Apko,

    Domin Apko zai apka da ke.”

    Sai Binta ta tafi rafin Diddire ta ɗebo ruwa. Da kishiyar uwarta ta ga ba ta ɗebo ruwan Apko ba, sai ta hau ta da duka. Ta ma zubar da ruwan da ke cikin masakin, ta ce lallai maza ta je ta ɗebo mata ruwa daga kogin Apko, kuma ta gaya mata cewa idan ta kuskura ta ɗebo mata ruwan Diddire, to za ta yanka ta.

    A kan dole Binta ta ɗauki masakin ta tafi rafin Apko ɗiban ruwa. Tana shiga za ta ɗebi ruwan, sai rafin ya cinye ta. Tana nan a cikin ruwa, har wasu ’yan kwanaki. Ita kishiyar uwarta ba ta sa an je nemanta ba, kuma ita ba ta je ba. Ko fadawa ma ba ta gayawa ba, har ranar dawowar Sarki.

    A ranar da Sarki ya dawo sai fadawa da jama’ar gari suka fita bayan gari suna yi masa barka da zuwa. Masu tambura suka goce da kiɗa, ana yi masa kirari ana cewa: “Baban Binta ya dawo, Sarki baban Binta ya dawo.” Da Binta ta ji ana buga tambarin babanta, ga shi kuma ba za ta iya fita daga ruwan ba, sai ta kama kuka da waƙa tana cewa:

    “Falmata ce ’yar Sarki,

    Babanta ya dawo,

    Falmata kin ji daɗi,

    Falmata ’yar Sarki.”

    Sarki ya sa ido ko zai ga Binta a cikin masu tarye, amma bai gan ta ba, kuma ya saɓa idan ya yi tafiya ya dawo akan ɗoro ta a kan doki, a kai ta gabansa, su gaisa. Ya sake dubawa bai ga Binta ba sai Falmata. Sai hankalinsa ya tashi, har dai ya kasa daurewa ya tambayi fadawansa inda Binta take.

    Sai suka ce ai Binta ta ɓata, ba wanda ya san inda take. Suka ƙara da cewa ai ma yau kwana goma sha tara kenan da uwarta ta rasu. Hankalinsa ya tashi, amma ya yi
    ta maza, ya shanye halin damuwar da yake ciki. Da ya shiga gida, sai ya kira uwargidansa, ya tambaye ta inda Binta ta je.

    Sai ta ce ba ta sani ba, tun da dai ta fita yawo ba ta sake komawa gida ba. Yana jin haka, sai ya sa aka shiga neman Binta. Wasu daga masu nemanta suka bi ta rafin Apko. Da fari ba su ga alamun kowa a can ba, to amma daga baya sai suka ji muryar mutum na waƙa a cikin rafin. Da suka kasa kunne da kyau, sai suka ji ana waƙa ana cewa:

    “’Ya’yan uwa kada ku zo Apko,

    Idan kun zo zai apka da ku,

    Ni kishiyar uwa ta aiko ni nan,

    Har ya apka da ni.”

    Da masu nemanta suka ji haka sai kawai suka koma suka shaida wa Sarki abin da suka jiyo a kogin Apko. Sai Sarki yace da su da sauran fadawansa su je tare da shi bakin rafin ya ji. Nan da nan suka dunguma, kuma suka tarar Binta tana yin wannan waƙar. Sarki ya kasa kunne, kuma daga ƙarshe dai ya fahimci cewa muryar Binta ce.

    Sai nan da nan ya ce da Sarkin maroƙa ya shiga gari ya yi yekuwa cewa duk wanda ya fito da Binta dagakogin Apko za a ba shi dawakai da dukiya mai yawa. Da fari ba wanda ya ce zai gwada, amma can sai wani tsoho ya zo ya ce zai shiga ruwan ya tsamo ta. Sai wasu mutanen garin suka ce: “Amma tsohon nan da rigima kake.

    Ga mu nan duk da ƙarfinmu mun kasa, ballantana kai da ka tsufa?” Sai Sarki ya ce: “A bar shi ya gwada.” Tsoho ya faɗa ruwa, zuwa wani ɗan lokaci sai ya fito da Binta a hannunsa. Da Sarki ya ga ’yarsa sai ya ji kamar ya zabura da gudu ya rungume ta saboda murna da farin cikin da yake ciki.

    Amma sai ya nuna halin manya, ya jure. A cikin murna da farin ciki Sarki da fadawansa da jama’arsa suka yi ta gode wa tsohon nan. Da aka koma fada ya sa aka kwanto dawakai Asbin da kili da fari da ja da baƙi da ingarma da kuru da dai dawakai iri-iri masuyawa da dukiyar da ba a taɓa ganin irinta ba a ƙasar, aka ba tsoho.

    Bayan an tashi daga zaman fadanci Sarki ya shiga turakarsa, sai ya kira matarsa da Falmata, ya tambaye su yadda aka yi Binta ta faɗa ruwa. Sai suka yi shiru. Da dai ya gane munafunci suka yi, sai ya kore su, ya ci gaba da rayuwarsa da ’yarsa Binta. Shi ya sa duk wanda ya je garin zai ji ana cewa: “Binta ’Yar Sarki.” Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alkawari kaya ne.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Tatsuniyar ’Ya’yan Sarki Da Ƙadangare

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani Sarki da ’ya’yansa mata su biyu kyawawa. Amma tun suna ƙanana ya hana su fita waje domin tsaron lafiyarsu. Kullum suna gida har suka girma, suka isa aure. Ganin sun kai munzalin aure, sai ya bari suka ɗan fara fita waje.

    Ana nan, rannan dai Sarki ya ce zai aurar da su. Manema suka fito. Wannan ya zo, a ce a a, bai yi ba. Wancan ya zo, a hana shi. Wata rana dai sai Sarki ya ce a tara mutane, duk wanda ya kira sunan ɗaya daga cikinsu, to shi za a ba wadda ya faɗi sunanta. Shi
    ke nan aka sa ranar tara mutane don a ji wanda zai faɗi sunan.

    Matasa da sauran waɗanda ba su wuce auren budurwa ba, kowa ya shiga neman sunayen ’yan matan; abu dai ya gagara. Sai Biri ya sami labari kuma ya ce ya san dabarar da zai yi. Sai ya je ya samo mangwaro nunannu kyawawa guda biyu. Da ya make mangwaron nan biyu, sai ya garzaya cikin lambun Sarki inda yaran suke hira, ya zauna a kan bishiyar da suke zama a gindinta ya shiga jira.

    Da suka fito, sai ɗaya daga cikin ’yan matan ta je gindin bishiyar da Biri yake kai, sai ya jefa mangwaro ɗaya. Da ta gani sai ta ɗauka tace: “Kirindi zo ki ga wani nunannen mangwaro na samu.”Wannan ya sa Biri murna saboda ya ji sunan ɗaya daga cikinsu. Da ɗayar ta doshi wajen wadda ta kira ta don ta je ta ga mangwaron Kirindi, sai ya jefa ɗaya mangwaron, sai ita ma ta ganshi.

    A cikin murna da ɗoki ta ce: “Ai ni ma na samu Karanda.” Biri na ji sai ya kama murna yana cewa: “Yawwa ai ni zan aure su tun da na ji sunayensu.” Bayan lokacin da Sarki ya yanka wa mutane ya cika, sai aka tara mutane ana tambayar su ko sun sami sunan ’yan matan.

    Wannan ya zo ya ce kaza ne, a ce masa a a, wancan ma ya zo bai canka ba. Haka dai aka yi ta fama har aka zo kan malam Biri. Ana zuwa kansa sai aka ji a cikin raɗa saboda tsoro ya ce: “Kirindi da Karanda.” Sai Ƙadangare da ke gefensa ya ji, sai kawai ya yi farat da ƙarfi ya ce: “Kirindi ce da Karanda.”

    To shi kuma Sarki ya riga ya yi alkawarin duk wanda ya faɗi sunayensu, zai ba shi su aure. Ba tare da ɓata lokaci ba, aka ba Kadangare auren ’ya’yan Sarki. Ashe Biri ya ji haushin ƙwacen da Ƙadangare ya yi masa, kuma ya saɓi laya sai ya ɗauki fansa a kan Ƙadangare.

    Saboda haka bayan an gama bikin amaren Ƙadangare sun tare a gidansa, sai
    rannan Biri ya haura dangar gidan gonar Sarki inda Sarki ke kiwo. A cikin dabbobin da Sarki ke kiwo kuwa, akwai wata babbar kazarsa wadda ya fi so a kan duk sauran abubuwan da yake kiwo a gonar.

    Sai Biri ya kama wannan kaza ya yanka, ya fige, ya dafa ya cinye. Da ya cinye ya sha ruwa, sai ya kwashe duk gashinta da ƙasusuwanta ya je ya haura dangar gidan Kadangare ya zuba. Gari na wayewa, sai labari ya je ga Sarki cewa an sace masa kaza. Sai ya sa fadawa su bi gida-gida su nemo kazar nan kafin a zahar.

    Fadawa na shiga gidan Kadangare, sai suka tarar da gashin kazar Sarki da ƙasusuwa. Suna ganin haka, sai suka kai wa Sarki labari. Saboda kunya da kara irin ta manya, da Sarki ya ji cewa a gidan surukinsa ne aka sami gashi da ƙasusuwan kazarsa, sai ya ce a bar maganar, kuma ya hana a hori Kadangare.

    Biri dai bai ji daɗin haka ba. Duk domin ya yi ramuwar gayya, sai ya yanka akuya ya dafa aka yi romo mai kayan yaji. Ya ɗauka ya kai gidan Kadangare, romo da naman akuya suna tafasa saboda zafi. Da Kadangare ya buɗe mazubin, sai ya ga naman akuya da romo, ga ƙamshinsa ya cika gari.

    Sai kwaɗayinsa ya tashi, bai yi wata- wata ba sai ya kai bakinsa. Yana ɗosana bakinsa kuwa sai yaƙone, ya ja baya. Matansa na fitowa sai hankalinsu ya tafi kan mazubin nan. Da suka buɗa, suka ga naman akuya ne a cikin romon da ya sha kayan yaji, sai su ma suka kwasa, suna kai wa bakunansu sai zafi ya sa kowacce ta ƙwala ihu, ta tofar da wanda ta guntsa.

    Dukkansu uku, watau Kadangare da matansa biyu ba wand abai ƙone ba. Da Biri ya ga haka, sai ya fita daga inda ya maƙe, ya kama hanya ya tafi yana dariyar ƙeta da jin daɗi, ya bar su da jinya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kowa ya cuci wani zai ga mummunan sakamako.
    • Duk abin da ka samu ta hanyar rashin gaskiya ba za ka moreshi ta hanyar jin daɗi ba.
    • An ɓata goma ɗaya ba ta gyaru ba.
    • Rabon kwaɗo ba ya hawa sama.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Tsurondi

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Wayo

    Tatsuniyar Kurege Da Wayo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani lokaci da aka yi yunwa, ba abinci. Wuya ta sa Kura da Maciji da Alade da Kurege suka haɗa kai, suka haɗu domin su haɗa gwiwa su yi noma tare. Sai suka zaɓi wani fili a dajin da suke, suka gyara, ya zama gonarsu.

    Ana nan, jim kaɗan kafin damina ta faɗi, sai Maciji ya ce shi ne zai yi sassabe, watau zai gyara gona, ya sare lallagowa ya kawar da yayi. Alade ya ce: “Ni zan yi mana huda.” Kura ta ce: “Ni zan nome mana gonar.” Kurege kuwa sai ya ce: “Ni kuma zan nemo mana irin shukawa.”

    A daidai lokacin da ya dace, sai Maciji ya tuge bishiyoyin gonar ya ƙone. Alade ya yi musu huda. Kura ta nome. Kurege ya tafi neman irin shuka a kasuwa, sai ya ga wata mata ta tara dawa da masara da gyaɗa da wake. A daidai lokacin da ta tashi tafiya gida sai Kurege ya ruga, ya je gabanta ya kwanta kamar ya mutu.

    Da matar ta gan shi sai ta ce: “Kai ga nama ya samu. To amma fa idan na ɗauka zai cinye mini dawa ta kare da wuri.” Sai ta tafi ta bar Kurege, ba ta ɗauka ba. Da Kurege ya ga haka sai ya tashi ya kama gudu, ya sha gaban matar nan ya kwanta. Da ta ga wannan Kuregen ba ta san na baya ba ne sai ta ce: “Allah ne ya ba ni.”

    Sai ta ɗauki Kurege ta sa a bakin ƙwaryarta, ta shiga gefen daji domin ta samo ɓawon kargo ta ɗaure Kuregen ko ta ji daɗin tafiya da shi gida. A lokacin da ta ajiye ƙwarya ta je ta yo ɓawon kargo sai Kurege ya ɗauki ƙwaryar nan cike da irin dawa ya gudu.

    Da matar nan ta dawo, sai ta ga ba ƙwarya, ba Kurege. Hankalinta ya tashi, kuma ranta ya ɓaci. Haka dai matar nan ta kama hanyar gida da ɗan abin da ba a rasa ba, tana kuka. Shi kuwa Kurege ya kai iri suka shuka tare da abokan nomansa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Idan an hada kai komai zai zo cikin sauki.
    • Iya ruwa fidda kai.
    • Neman araha kan sa mutum ya rasa abin da yake hannunsa.
    • Kwadayi mabudin asara/wahala.

    Karanta Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Tatsuniyar ƊanAuta Da ’Yar Gwaggo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wani mutum yana da ’ya’ya biyu mace da namiji. Macen ce babba, namijin ne ƙarami. Ita sunanta ’Yar Gwaggo, shi kuma sunansa Ɗan’auta. Da iyayensu za su rasu sai suka kira ’Yar Gwaggon suka ce: “Za mu bar miki ƙaninki Ɗan’auta. Kada ki ba shi wahala, duk abin da yake so ki ba shi; kuma duk abin da ya ce zai yi, kada ki hana shi; ki bar shi ya yi.”

    ’Yar Gwaggo ta ce: “To na ji.” Sai iyayen suka kwanta, suka rasu. To da ma iyayen sun bar musu dukiyar abinci da kadarori. Bayan ’yan kwanaki da rasuwarsu sai Ɗan’auta yace su tattara dukiyar da abincin da gidan baki ɗaya su ƙona. Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan muka ƙona kuma me za mu ci, kuma a ina za mu zauna?” Sai Ɗan’auta ya ce: “Ba su baba sun ce idan ina son komai ki ba ni ba, kuma duk abin da zan yi kada ki hana ni?”

    Sai ta ce: “To shi ke nan, ka tashi mu tara kayan a ƙona.” Suka tara kayan da abincinsu rumbu-rumbu, suka ƙona. Da yunwa ta fara damun su sai ’Yar Gwaggo ta ce to su tafi bara. Suka kama hanya har gidan Sarki sai suka tarar da ’ya’yan Sarki suna wasan kirbe-kirbe, sai yace shi ma sai ya yi.

    Sai ’Yar Gwaggo ta ce: “Haba Ɗan’auta, wannan fa gidan Sarki ne, kuma ’ya’yan Sarki suna wasa. Idan aka kama mu fa?” Sai ya ce: “Ba su iya da baba sun ce duk abin da na ce zan yi ki ƙyaleni ba?” Sai ta bar shi ya shiga wasan ’ya’yan Sarki. A cikin wasan ya ɗaga ɗaya daga cikinsu, ya ƙwala da kasa sai cinyarsa ta karye.

    Sai Sarki ya sa fadawa su kama shi. Ganin haka sai ’Yar Gwaggo ta kama hannun ƙanenta suka kama gudu, har cikin jeji, dogarai suna bin su. Can sai suka hau kan wata bishiya, suka ɓuya. Da dogarai suka zo sai suka rasa hanyar da suka bi, sai suka ce bari su huta a gindin bishiyar nan. Su Ɗan’auta na kan bishiyar.

    Da ɗaya daga cikin dogaran ya kwance rawaninsa domin ya sha iska, ga shi ya aske kansa ƙwal-ƙwal yana ƙyalli, sai ɗan’auta ya auna kan dogarin sosai, sai kawai yace wa ’Yar Gwaggo: “Zan yi kashi.” Tsoro ya kama ’Yar Gwaggo, domin idan dogaran nan suka ji motsi za su kama su. Sai ta ce: “Haba Ɗan’auta, idan ka yi kashi za su gan mu, su kama mu fa.”

    Sai ya ce: “Ba iya da baba sun ce duk abin da zan yi ki ƙyale ni ba?” Sai ta ce: “To shi ke nan yi kashinka.” Sai ya tuɓe wandonsa ya auna daidai kan dogari sai ya ɓarke da kashi. Da kashi ya zuba kan dogari sai ya ce: “Wannan wane ɗan iskan tsuntsu ne ya yi mini kashi?”

    Da suka ɗaga kai sama sai ga su Ɗan’auta da ’Yar Gwaggo, sai suka fara sarar bishiya, saura kaɗan ta faɗi, sai ga wata ’yar tsuntsuwa za ta wuce, sai ’Yar Gwaggo ta ce: “‘Yar tsuntsuwa ki taimake mu mana.” Sai tsuntsuwar ta ce: “To ku hau bayana.” Suka hau bayan ’yar tsuntsuwa, ta tashi da su sama suka fara tafiya.

    Bayan sun fara nisa a can sama, sai Ɗan’auta ya ga gindin tsuntsuwa na ta motsi, yana budewa ya rufe. Sai kawai ya ce zai tsokale gindin tsuntsuwa. Yayarsa ta ce: “Haba Ɗan’auta, ita da ta taimake mu. Da an kama mu an kashe. Ka yi haƙuri mana.” Sai ya ce: “Ba inna da baba sun ce idan na ce zan yi abu kada ki hana ni ba?”

    Sai ta ce: “To ka yi.” Sai ya sa kara ya tsokale gindin tsuntsuwa. Sai ta juyar da su, suka faɗa cikin wani babban rafi. Suka yi ta iwo har suka kai bakin ruwa. Sai suka fita a daidai wani ɗan ƙauye. Da suka shiga ƙauyen sai suka fara neman masauki. Sai suka haɗu da wata ’yar tsohuwa suka gaya mata su baƙi ne masu neman masauki.

    Sai tace: “To zan ba ku masauki, amma fa a garin nan ba a fita da daddare don akwai wani dodo da yake cin mutane; har sarki ya yi alƙawari zai ba duk wanda ya kashe dodon rabin gari kuma ya aura masa ’yarsa.” Sai suka ce: “To shi ke nan.” Da dare ya yi sai Ɗan’auta ya ce shi fa sai ya ga dodon da yake hana mutane fita.

    Yayarsa ta yi, ta yi da shi kada ya fita waje, ya hura wuta a gefensa. Da wuta ta ruru, sai ya saka duwatsu bakwai a cikinta, har suka yi jawur. Sai ya zauna a tabarmarsa, ’yar tsohuwa kuma don tsoro sai ta shiga randarta ta buya a ciki. Da dodo ya iso gari ya shiga waƙa yana cewa: “Wa ya yi da ni a garin nan, Wa ya yi da ni, ni dodo in cinye shi?”

    Sai Ɗan’auta ya mayar masa yana cewa: “Na yi da kai a garin nan, Na yi da kai ni Ɗan’auta.” Da tsohuwa ta ji sai ta fara zawo a cikin randar don tsoro. Sai dodo ya nufo inda Ɗan’auta yake. Da Ɗan’auta ya ga ya buɗe baki, sai ya ɗauki dutsen nan da ya yi jawur da wuta, ya jefa a cikin bakin dodo.

    Sai dodon nan ya hadiye. Ya ci gaba da matsowa, shi kuma Ɗan’auta ya ci gaba da jefa duwatsun nan, har ya zo kan na ƙarshe. Da ya jefa na bakwai, sai kawai dodon ya faɗi matacce. Da Ɗan’auta ya ga haka, sai kawai ya koma ya kwanciyarsa. Da gari ya waye sai aka aika wa Sarki cewa an kashe dodon da ke damun mutanen gari.

    Sarki kuwa ya ce duk wanda ya kashe dodon za a ba shi rabin gari, kuma a aura masa ’yar Sarki. To da ma shi Ɗan’auta ya manta takalmansa a inda ya yi faɗa da dodo. Da aka tara mutane suka zo suka yi ta gwada takalma amma bai yi ba, sai da suka nemi baƙin da suke garin.

    Da Ɗan’auta ya gwada takalma sai suka yi daidai da shi. Nan take aka ba shi rabin gari, Sarki kuma ya cika alƙawari, wato ya ba shi auren ’yarsa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wauta ne a sakar wa yaro linzami ya yi abin da ya ga dama.
    • Mai wayo ya fi mai zafin nama cin nasara.
    • Ya kamata a karɓi bako da hannu bibbiyu don ba a san alhairindazai kawo ba.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Sarki

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu