Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Yadda Hawan Jini Yake (HYPERTENSION)

    Yadda Hawan Jini Yake (HYPERTENSION)

    Jini ruwa ne mai launi ja-zur da ke kewaya sassan jikin dabbobi masu ƙashin baya (vertebrates), kamar mutane (humans), mage (cats), ƙadangare (reptiles), tsuntsu (birds), kwaɗo (amphibians), kifi (fish), da sauransu.

    Bincike ya tabbatar da cewa banda mutum, akwai dabbobin da suke kamuwa da matsalar hawan jini. Amma wannan matsalar tana maganar hawan jinin mutum ne.

    Jini yana gudu da ƙarfi a cikin jijiyoyin jikin mutum idan zuciya ta feso shi. Aikinsa shi ne isar da kayan abinci zuwa sassan jiki, da fitar da ruwan dattin jiki ta hanyar fitsari ko zufa.

    Ƙarfin tafiyar jini yana buɗe jijiyoyi (arteries), kuma shi ne “blood pressure”. Akwai adadin blood pressure da ake buƙata wanda ba zai cutar da jiki ba. Idan ya yi yawa shi ne “hypertension”, kuma matsala ne. Idan ya yi kaɗan shi ne “hypotension” shi ma matsala ne. Idan ya yi daidai shi ne “normotension”, kuma shi ake buƙata.

    NA’URAR AWON GUDUN JINI (BLOOD PRESSURE MEASUREMENT DEVICE)

    Na’urar awon gudun jini ita ce “sphygmomanometer”. Tana da jakar ledar “polyester” da “nylon” mai suna “inflatable arm cuff”, wacce ake hura ma iska da ƙwallon roba mai suna “bulb pump”. Sa’annan tana da fuska (screen) mai nuna sakamakon awon, wato “pressure gauge”.

    A maƙale da ita akwai na’urar jin sautin bugun zuciya da jin gudun jini (stethoscope). Lokacin yin awon, ana ɗaura inflatable arm cuff ɗin a damtsen hannu, a hura iska a ciki. Cuff ɗin zai matse damtsen. Hakan zai sa na’urar ta iya ɗosano ƙarfin gudun jinin, ta nuna shi a screen, kuma za a ji sauti bugun zuciyar ta stethoscope.

    Nau’rar awon iri biyu ce:

    1. Ta farko ita ce na’urar da ake sarrafa ta da hannu (manual blood pressure monitor): Tana da stethoscope, inflatable cuff, da pressure gauge, kuma iri biyu, kamar haka:

    a. Mercury sphygmomanometer, wacce ake ganin sakamakon awon a jikin tsinken ruwan “mercury” a tsakiyarta.

    b. Aneroid sphygmomanometer, wacce take amfani da “spring” da “gauge”.

    2. Ta biyu ita ce na’urar da ke sarrafa kanta: (digital blood pressure monitor): Tana da maɗosanin bayanai (sensor) wanda yake ba ta damar yin aiki da kanta (automatic). Tana da inflatable cuff, amma ba ta da stethoscope. Idan aka ɗaura inflatable cuff ɗin, za ta hura iska da kanta ta hanyar motorized pump. Sai screen ɗin ya nuna sakamakon awon.

    KARANTA SAKAMAKON AWON GUDUN JINI (READING OF BLOOD PRESSURE MEASUREMENT)

    Sakamakon awon yana da lambobi biyu ne.

    1. Lamba ta farko ita ce ta sama, kuma ana kiranta “systolic”. Tana nuna ƙarfin gudun jini ne lokacin da zuciya ta kumbura domin ta feso shi.

    2. Lamba ta biyu ita ce ta kasa, kuma ana kiranta “diastolic”. Tana nuna ƙarfin gudun jini ne lokacin da zuciya ta sace bayan ta feso shi.

    Lambobin awon suna fitowa ne da alƙaluman millimetre of mercury (mm Hg).

    Tun farko na faɗi cewa sakamakon awon blood pressure iri uku ne:

    (a) Gudun jinin da ya yi sama, wato hypertension.

    (b) Gudun jinin da ya yi daidai, wato normotension.

    (c) Gudun jinin da ya yi ƙasa, wato hypotension.

    Matsakaicin gudun jini da ake buƙata (normal range of blood pressure) ya danganta da shekaru ko yanayin mutum ne. Wato ana buƙatar lambar sama (systolic) da lambar ƙasa (diastolic) su kasance tsakanin da’irori kamar haka:

    1. Jariri: Systolic = 72 mm Hg zuwa 104 mm Hg.

    2. Ɗan shekara 1 zuwa 2: Systolic = 85 mm Hg zuwa 113 mm Hg. Diastolic = 37 mm Hg zuwa 69 mm Hg.

    3. Ɗan shekara 3 zuwa 5: Systolic = 91 mm Hg zuwa 120 mm Hg. Diastolic = 46 mm Hg zuwa 60 mm Hg.

    4. Ɗan shekara 6 zuwa 12: Systolic = 96 mm Hg zuwa 131 mm. Diastolic = 55 mm Hg zuwa 62 mm Hg.

    5. Ɗan shekara 13 zuwa 17: Systolic = 80 mm Hg zuwa 120 mm Hg. Diastolic = 45 mm Hg zuwa 80 mm Hg.

    6. Ɗan skekara 18 zuwa 50: Systolic = 120 mm Hg zuwa 130 mm Hg. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 85 mm Hg.

    7. Mace mai juna biyu: Systolic = 120 mm Hg zuwa 130 mm zuwa. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 85 mm Hg.

    8. Tsoho: Systolic = 120 mm Hg zuwa 140 mm. Diastolic = 80 mm Hg zuwa 90 mm Hg.

    TASIRIN HAWAN JINI KO SAUKAR JINI DA ALAMOMINSU (EFFECTS AND SYMPTOMS OF HYPERTENSION OR HYPOTENSION)

    Tasirin hawan jini ko saukar jini yana bambanta a tsakanin mutane, kamar haka:

    1. Jarirai: Ba a cika samun hawan jini ga jarirai ba. Idan aka ga jariri da hawan jini, to, lallai an haife shi da nakasar zuciya ne (heart defect), ko matsalar ƙoda (kidney problem). Alamominsa su ne yawan kuka, kasa shan nono, da rashin girma. Sa’annan ba a cika samun saukar jini ga jarirai ba.

    Idan aka samu, lallai dalilinsa zai zamo rashin ruwan jiki (dehydration), ko zubewar jini (blood loss), ko ciwon zuciya (heart disease). Alamominsa su ne rashin shan nono, rashin walwala, da koɗewar fata (pale skin).

    2. ‘Yan shekara 1 zuwa 10: Ba a cika samun hawan jini ga yara masu wannan shekarun ba. Idan kuwa ya same su, alamominsa sune ciwon kai (headache), gajiya (fatigue), riƙewar numfashi (shortness of breath), haɓo (nose bleeding), sanƙarewa (seizures), da rashin gani (vision problems). Idan ba a magance shi ba, zai iya lalata zuciya, ƙoda, da ƙwaƙwalwa.

    Haka nan ba a cika samun saukar jini ga yara masu wannan shekarun ba. Idan aka samu, alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), saurin bugawar zuciya (rapid heartbeat), da rashin ƙwarin jiki (weakness). Rashin magance shi zai iya lalata aikin ƙwaƙwalwa (impaired brain function), tsumburewa (growth retardation), da rikicewa (hypoxia).

    3. ‘Yan shekara 11 zuwa 17: Ana samun hawan jini ga matasa masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), zafin kirji (chest pain), da zafin jiki (abdominal pain). Idan ba a magance shi ba, zai iya lalata zuciya, ƙoda, da ƙwaƙwalwa, da jijiyoyin jini.

    Kuma zai iya kawo shanyewar tsagin jiki (stroke). Haka nan ana samun saukar jini ga matasa masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), zafin ƙirji (chest pain), da zafin jiki (abdominal pain). Rashin magance shi zai iya lalata zuciya, ƙoda, ƙwaƙwalwa, da jijiyoyin jini.

    4. Baligai ‘yan shekara 18 zuwa 50: An fi samun hawan jini ga masu wannan shekarun. Alamominsa su ne ciwon kai (headache), jiri (dizziness), da rashin gani sosai (blurred vision). Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa ciwon zuciya (heart disease), shanyewar tsagin jiki (stroke), da lalacewar koda (kidney failure).

    Haka nan an fi samun saukar jini ga baligai masu wannan shekarun. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da gajiya (fatigue). Rashin magance shi zai iya lalata ƙwaƙwalwa (impaired brain function), rikicewa (hypoxia), da gigicewa (shock).

    5. Tsofaffi: An fi samun hawan jini ga tsofaffi. Alamominsa su ne ruɗewa (confusion), mantuwa (memory problems), kasa tafiya (difficulty in walking). Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa ciwon zuciya (heart disease), shanyewar tsagin jiki (stroke), da cutar mantuwa (dementia).

    Haka nan an fi samun saukar jini ga tsofaffi. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da ruɗewa (confusion). Rashin magance shi zai iya lalata ƙwaƙwalwa (impaired brain function), rikicewa (hypoxia), da gigicewa (shock).

    6. Masu juna biyu: Ana matuƙar samun hawan jini ga mata masu juna biyu har yakan kai matakin farko na ciwon jijjiga (preeclampsia). Alamominsa su ne kumburin jiki (abdominal swelling), ciwon kai (headache), rashin gani sosai (blurred vision), da ciwon jiki (abdominal pain).

    Idan ba a magance shi ba, zai iya haddasa haihuwar bakwaini (preterm birth), haihuwar ƙanƙanin jariri (low weight of newborn), da matsaloli masu yawa ga uwa da jaririnta. Haka nan ana matuƙar samun saukar jini ga mata masu juna biyu. Alamominsa su ne jiri (dizziness), suma (fainting), da gajiya (fatigue).

    Rashin magance shi zai iya hana samar da isasshen jini ga jariri a cikin mahaifa (impaired blood flow to fetus), ƙanƙancewar jariri (fetal growth restriction), ko ɓari (miscarriage). Idan ciki ya tsufa, to, saukar jini alama ce ta preeclampsia.

    RABE RABEN HAWAN JINI (TYPES OF HYPERTENSION)

    Hawan jini ya rabu gida biyu:

    1. Hawan jini na asali (primary or essential hypertension): Shi ne wanda ba a san asalin abinda yake kawo shi ba, amma tsarin rayuwar mutum take haɓaka shi, kamar cin gishiri da yawa, rashin motsa jiki, tsufa, shan giya, ƙiba, gado, da sauransu.

    2. Hawan jini mai dalili (secondary hypertension): Shi ne wanda wasu cututtuka ko amfani da wasu magunguna yake kawo shi, kamar matsalolin ƙoda, zuciya, ƙwaƙwalwa, da magungunansu.

    MAGANI (TREATMENT)

    Magance hawan jini yana da matuƙar alaƙa da tsarin rayuwar mutum, kamar motsa jiki, rage ƙiba, cin abinci mai kyau, da shan magani bisa umurnin likita. Shi ma saukar jini magance shi yana da alaƙa da magance abubuwan da suke kawo shi, kamar yawaita shan ruwa, da kauce ma abubuwan da jikin mutum yake bijire musu.

    Karanta Bayani A Kan Budurci Da Kuskuren Da Ake Yi A Kan Rashinsa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Shida

    Tana jiyo motsin shigowar Mustapha gidan amma ba ta yi zaton zai tafi da sauri ba, don haka ma ta jira sai da ta gama abinda take yi tunda ta jiyo shi da Baffa a tsakar gida. Sai dai ga mamakinta ko da ta fito Baffa ta tarar shi kaɗai, yana shirin shigewa mota ta yi sauri ta karasa.

    Tace ‘Na ji kamar kai da Mustapha ne, ko har ya tafi ne? Ya tsaya yana riƙe da murfin mota yana cewa ‘Shi ne, matar tasa ce ta fara gwada masa tutsun nata shi ne ya taho kawo ƙara da sassafe. Ikon Allah, Khadija Iya-rigima. Me ta yi kuma?’

    Nan ya ba ta labari kamar yanda Mustapha ya ba shi, ya ƙara da ‘Na ce su zo bayan Magriba don ita ma yanzu zan kirawo ta na sanar da ita kada ta yi taurin kai, kin san hali. Ta yi dariya ‘To Allah ya kai mu, ai an auna arziƙi ma da aka ɗauki lokaci haka ba ta fara rigimar ba. Suka yi dariya ta yi masa a dawo lafiya ya wuce sannan ta koma ciki.

    Sai da yamma ta yi sannan ta kirawo Khadeeja a waya, bayan sun gaisa tace ‘Me ya haɗoki da Mustapha ne ya kawo ƙararki da sassafe ne? Ta yi dariya sannan ta ba ta labari, bayan ta gama ji tace ‘Ikon Allah, to neman mata Mustaphan yake yi kenan ko kuwa dai aure yake nema?’

    ‘Ni ma ban sani ba Mommy, amma dai ko ma menene ai da akwai cin fuska a ce ina yawo a taxi ita kuma tana yawo a motar mijina; at least ya bari ta aure shi sai ya ba ta wannan ikon. Kuma sannan idan ita ce za ta dinga yi masa hidimar yaransa ai sai ta karɓa gaba ɗaya ni kuma na huta gaba ɗaya.’

    Mommy tace ‘Um! Da wannan, amma dai ki bari a bi abun a hankali. Saura kuma idan kun zo ki yi shiru ki ƙi yi wa Baffa bayani ya yanke miki hukunci in ma ya ga dama yace ki ba wa Mustaphan haƙuri. Ta yi ‘yar dariya ‘Ba zan yi shiru ba Mommy. Suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Sai dab da magriba ya dawo gidan, ya yi mamaki da ya jiyo Rashida da Afaf a kitchen suna ƙoƙarin dafa abincin dare; a tunaninsa tunda ya san Baffa ya gaya mata yana nemansu ya kamata a ce ta shiga hankalinta. Bayan ya amsa sannu da zuwansu ya wuce ɗakinta; ƙofarta a rufe take, ya saka mukullinsa ya ji har yanzu ba ta cire mukullin ba don haka ya daure ya ƙwanƙwasa.

    Sai da ta gama yauƙinta sannan ta buɗe ta rige hannun kofar ta matsa ya shige. Ya so ya zare mukullin kofar to amma sai ya ga idan ya zare ai duk da haka ba lallai ta dinga fita daga ɗakin ba balle ma ta dinga yin hidimar da ta saba; tunda dai wulaƙanci ne kawai ta shirya za ta yi.Don haka ya bi bayanta suka shige ɗakin, tun kafin ta gama zama a inda ta tashi yace ‘Baffa ya gaya miki mu je yana nemanmu ko?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘Ƙarfe nawa za mu je? Ya so a ce ta ba shi dama su yi magana su kashe wannan rigimar in ya so ya kirawo Baffa yace masa sun shirya amma sai dai ga alama ta fi so su je wajen Baffan. Yace ‘Da na dawo daga masallaci sai mu je.’

    Ya juya ya fice daga ɗakin ba tare da ya saurari amsarta ba. Ta bi bayansa da harara tana dariya; wato shi uban ‘yan son kai har yanzu bai ga laifinsa ba don haka ita yake tsammani ta ba shi haƙuri kenan. Tabbas yau sai ta ƙure wannan son zuciyar na Mustapha duk da har yanzu wata zuciyar tana gaya mata kada ta je ta yi wa mijinta tonon asiri a wajen iyayenta.

    Yana dawowa daga masallaci ya same ta a shirye, ko zama bai yi ba suka sallami yara suka fice daga gidan. Suna shiga gidan suka sami Mommy wadda ta ba su umarni su ƙarasa parlor ɗin baƙi domin Baffa yana can yana jiransu. Yana zaune a kan kujera 3-seater don haka Mustapha ya zauna daga gefen damansa jikin 2-seater ita kuma Khadija ta koma ɗaya gefen jikin single seater ta zauna.

    Bayan Baffa ya amsa gaisuwarsu ya dubi Khadeeja yace ‘Dije, me ya haɗa ki da maigidanki ne kika daina kula shi shi da yaransa? Ta sunkuyar da kai cikin sanyin murya tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba. Kafin Baffa yace wani abu Mommy ta shigo da sallama Nabila tana biye da ita ɗauke da tray wanda aka jera ruwa da lemo a kai, don haka Baffa ya tsaya ya amsa sallamarta.

    Ta nunawa Nabila inda za ta ajiye tray ɗin daga kusa da Mustapha, ta ajiye ta gaida Mustaphan sannan ta miƙe ta fice daga parlor ɗin ita kuma Mommy ta kara ta zauna a kan kujerar da Khadija take zaune a ƙasanta. Ya juya ya gaida Mommy, bayan ta amsa Baffa ya sake duban Khadeeja yace ‘Ya aka yi Dije ina saurarenki.’

    Tace ‘Baffa ba daina kula su na yi ba fa. To ai ya ce kusan kwana uku kenan ba kya kula kowa sai dai kawai ki kulle kanki a ɗaki kin bar yara da mai aiki sannan kuma gari yana wayewa sai ki fice ki tafi makaranta. Kawai saboda ya tura sakatariyarsa ta je makarantar yara kun haɗu.’

    Ta faki ido ta share ƙwalla; ya riga ya ba wa Baffa kanun labaran don haka duk yanda take son ta kare mutuncinsa ba zai yiwu ba domin ita ma dole ta kare kanta a wajen mahaifinta. Ta gyara zama tace ‘Wallahi Baffa ina bakin ƙoƙarina wajen kula da gidan da yaran, kuma babu laifi duk mun sami fahimtar juna da yaran gaba ɗaya.

    Duk wata hidimarsu ni nake yi, kuma ni ce nake ɗauko su daga makaranta ranar da ba na nan kuma sai mai-aikina ta ɗauko su. To shi ne ranar Monday suka yi open day a makaranta; ni ce na saba zuwar musu don haka tun weekend suka gaya min, shi kuma na manta ba mu yi maganar ba.

    Don haka gari na wayewa da na shirya zan tafi school sai na tsaya makarantarsu. Shi ne sai na ga har ya tura sakatariyarsa ta je musu. Baffa ya yi dariya yace ‘To ai babu komai Dije, wataƙila don ba ku yi maganar ba ne kuma kin ga ita ɗin ai sakatariyarsa ce zai iya saka ta wannan aikin duk da dai personal ne.’

    ‘Ni Baffa ba zuwanta ne ya ɓata min rai ba…’ nan ta ba shi labarin yanda ta ga sakatariyar a motar Mustapha ɗin da kuma yanda tunda ta aure shi sau ɗaya ya taɓa kai ta makaranta a motarsa da kuma yanda ko ta shirya ba ya yarda ya fita da ita. Da kuma yana wasu lokutan tana tsaye a bakin titi yake dawowa daga kai su; ba ta sani ba ko yana ganinta amma ita dai tana ganinsa.

    Baffa ya kalli Mustaphan ya kalli Mommy sannan ya kalli Mustapha wanda ya yi tsamo-tsamo don bai za ta Khadija za ta kawo wannan maganar ba; shi da ya ga ta daina damuwa ya rage mata hanya ma ya zata ta haƙura gaba ɗaya don haka bai san tana jin haushinsa a kan wannan ba.

    Yace ‘Ikon Allah, yanzu a ce a ki ragewa mutum hanya sai ka ce wani wanda ake jin haushi? Ko dai akwai wata matsalar ne Mustapha?’ Nan da nan ya fara gyara zama kansa a ƙasa cikin rawar murya yace ‘Babu wata matsala, em… dama yawancin lokutan ne ai ba ta shiryawa da wuri su kuma yaran idan 7:30am ta yi rufe musu gate za a yi.

    Umm.. shi yasa dole muke tafiya, kuma wasu lokutan ma idan na kai su gidan nake dawowa sai daga baya nake fita. Tace ‘Baffa ai ko ya dawo zai fita idan nace ya rage min hanya sai ya san abinda zai faɗa wanda zai sa ba zai tafi da ni ba don haka ma tun tuni na daina tambayarsa.’

    Suka ɗan yi shiru na ɗan lokaci Mustapha yana ta ƙoƙarin haɗa ido da ita yayin da ita kuma take ta ƙoƙarin kauce masa don ko gefen da yake ba ta kalla ba. Baffa yace ‘Shikenan abinda ya saka ki fushin ko akwai wani abun?’ Kana jin muryarsa kuma ka kalli fuskarsa za ka san ransa ya sosu matuƙa, domin karsashi da rahar da ya fara wannan tattaunawar da su duka babu.

    Har ta gyaɗa kai Mommy ta zungure ta da kafa, ta dago suka haɗa ido. Ta sunkuyar da kanta tace Baffa ita sakatariyar tasa kuma na tambaye shi menene a tsakaninsu; idan ma aurenta zai yi ai sai ya gaya min ba wai kawai na dinga ganinta a motarsa ba tana yawo a gari ni ina yawo a tasi.

    Saboda ni dai yanda na ga ta nuna alaƙarsu ta fi ƙarfin ta office kawai, don yaran ma duk sun santa ni kaɗai ce a gida na fara ganinta ranar. Baffa ya mayar da idonsa kan Mustapha wanda ya yi sauri ya sunkuyar da kansa ƙasa, ji yake kamar ya zura da gudu don bai taɓa zata Khadeeja za ta kawo waɗannan maganganun a gaban Baffa ba.

    Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa yana sauraron abinda Mustaphan zai ce, shi kuma ya sunkuyar da kai ya yi shiru kamar wanda ruwa ya ci. Mommy ce ta gaji da shirun ta yi gyaran murya tace ‘Uhm, ai gara ka gaya mata idan auren sakatariyar za ka yi ka ga tunda dai na san cewa ta san ka kai ka ƙara auren.’

    Ya gyara zama yana shafa ƙeya yace ‘A a ba ma shi ba ne, kawai dai da na aiketan ne to kuma ana ɗan wahalar mota shi ne na ce ta je a motata tunda ta iya tuƙi. ’Jimawa kaɗan Baffa yace ‘Allah ya sauwaƙe. ’Mommy tace ‘Amin dai.

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci, sannan Baffa ya kirawo sunan Khadeeja, ta amsa ta dube shi suka haɗa ido sannan yace ‘Ki yi hakuri Dije, kin ji. Ta gyada kai shi kuma ya ɗan numfasa sannan ya cigaba ‘Ki yi hakuri ki bi mijinki, kin ji bayanin da yayi. Kuma idan ma yace zai auri waccan yarinyar wannan bai kamata ya zama matsala ba tunda dai kin san duka wani namiji mijin mace huɗu ne.

    Ki yi haƙuri ki cigaba da hidimarki kamar yanda kika saba, kin ji. Batun kai wa makaranta kuma kin ga shi ‘yayansa yake zubawa a mota yake kai su a makaranta kuma tabbas haka ya kamata uba nagari ya kasance, don haka idan kika gama shirya masa nashi yaran ke ma ki shirya ki yi min waya sai na zo na kai ki tunda dai ke ma ‘yata ce; kai ki makaranta kuma ba baƙon abu ba ne a wajena.’

    Ya gyara zama ya ɗago kai a razane ‘A a Baffa a yi haƙuri ai ba sai an yi haka ba, in sha Allahu za mu dinga tafiya ma. Dama ai ba ta gaya min ne shiryawa kawai take tace ta tafi. Kada ka damu, zan dinga zuwa ina kai ta wannan aikina ne.’ Baffa ya ba shi amsa rai a ɓace.

    ‘A yi haƙuri Baffa, in sha Allahu ba za sake ba, ni ɗin ma zan dinga kai ta. A yi haƙuri.’ Mommy tace ‘Ke kuma ki yi haƙuri da yaranki tunda su ba su yi miki komai ba, ki kula da su ku zauna lafiya. Shi ma kuma kin ji bayaninsa, ki je ku yi zamanku lafiya kamar yanda kuka saba saboda Allah. Ita rayuwar aure haƙuri ce, ku dinga haƙuri da juna.

    Kuma nan gaba ko wata matsala ta taso muku ku yi ƙoƙari ku kashe ta a tsakaninku. Toh.’ Ta amsa cikin sanyin murya. Jimawa kaɗan suka yi wa Baffa da Mommy sallama suka fice; Khadeeja ta so shiga cikin gidan wajen Nabeela amma Mommy tace kada ta shiga ta bar shi yana jira idan ta shirya ta dawo su yi hirar.

    Tunda suka shiga motar bai ce komai ba sai muzurai kawai yake, don haka ita ma zuciyarta wasai take. Ta ji daɗin yanda Baffa ya nunawa Mustapha cewa ita ma da gatanta; duk da dai har yanzu tana jin cewa ba za ta ɗorawa kanta jiransa ya kai ta makaranta ba balle ta ɗorawa kanta damuwa.

    Suna shiga gidan ta wuce ɗakinta shi ma ya wuce nashi ɗakin. Sai da ta yi sallah sannan ta fito wajen yaran; zuwa lokacin Shukra har ta riga ta yi bacci. Bayan ta tabbatar sun ci abinci ta wuce kitchen, ta kirawo Rashida tana tambayarta me suka dafa da daddare. Ta gaya mata indomie suka dafa saboda haka Afaf tace, ta nuna mata indomie ɗin da ta saka a flask ta ajiyewa Abbansu.

    Ta riga ta san ba ya son indomie, musamman idan ta fara sanyi kuma ita ma yunwa take ji ba ta son cin indomie mai sanyi. Don haka Rashida ta taya ta ta gyara busasshen kifi ta dafa musu jollof sphageti mai rai da lafiya. Nan da nan gidan ya ɗauki ƙamshi; zuwa loakacin yaran duk sun kwanta.

    Ta jera abincin a dining table sannan ta haɗa masa shayi mai kayan ƙamshi irin wanda yake so sanna ta wuce ɗakinsa ta tura ƙofa ta shiga. Saura kaɗan ta yi dariya saboda ganin yanda ɗakin ya yi kaca-kaca; ga ƙura ga kaya da tarkacensa ko ina. A ranta tace mutum sai kace kuturu, ya sa hannu ya gyara makwancinsa kawai ya gagare shi.

    Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Ga abinci can na saka a dining,’ Dama tunanin abincin yake don yunwa yake ji sosai; ya riga ya san indomie suka dafa tunda jiya ma ita suka dafa don haka ya riga ya fara tunanin yanda zai yi sai kuma tace masa ga abinci. Ya dube ta ya ɗan sassauta fuskarsa yace ‘Yanzu zan fito.’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba ta juya ta fice, ya bi bayanta da kallo yana murmushin yaƙe. Ya rasa daɗi zai ji ta ba shi abinci wanda hakan yake nuna za ta cigaba da hidimarta; ko kuwa haushinta zai ji saboda yanda ta yaga shi a gaban Baffanta. Haka dai ya taso ya fito, babu kowa a parlor ɗin don haka ya zauna ya ci abincinsa ya ƙoshi; irin ƙoshin da ya kwana biyu bai yi ba.

    Sai da ya gama cin abincinsa ya huta sannan daga baya ya je ya kullo gidan ya shiga ɗakinsa; har ya kwanta kuma ya tashi ya bi bayan Khadeeja. Ya kula idan ya biye mata ba za ta neme shi ba, ko ba komai kuma yana so su yi magana ya ƙara kwantar mata da hankali game da maganar Naja don ba yanzu yake so ta sani ba. Sannan kuma yana so ya nuna mata rashin jin dadinsa game da yanda ta je ta kunyata shi a gaban Baffa.

    Duk yanda yaso ta taso su koma ɗakinsa su kwana kamar yanda ya saba bai samu ba, daga haka ya gane idan ya fiye takura mata zata sake ɗauke musu wuta; don haka sai ya haƙura ya zubar da duk maganganun da ya taho da niyyar gaya mata. Ya haƙura suka kwana a nan ɗakin nata tunda tace ta fara bacci ba ta son canza ɗaki.

    Tun asuba ta tashi kamar yanda ta saba, nan da nan ta shiga hidima da yara da taimakon Rashida. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo ta a kitchen, don haka cike da walwala ya wuce ɗaki ya koma bacci kamar yanda ya saba.

    Ƙarfe bakwai na safe yana fitowa kowa ya shirya yayin da Khadeeja take kai wa da kawowa tana jera masa nasa abincin a dininga table. Bayan ya amsa gaisuwar yaran yace ‘To kowa ya ɗauki kayansa mu wuce ko? Nan da nan suka miƙe suka fara ficewa. Ya dubi Khadeeja wadda take fitowa daga kitchen yace ‘Ba ki shirya ba ke, ko sai an jima za ki tafi?’

    Da murmushi tace ‘No, yau ba mu da lecture ba zan je ba. ‘Ok.’ Ta yi musu a dawo lafiya suka wuce. Bayan ya dawo haka ya yi ta tambayarta idan ta san za ta je makaranta ta gaya masa ya jira ta ya tafi da ita ya kai ta; sai da ta tabbatar masa ba za ta fita ba sannan ya fita ya tafi office.

    Washegari ranar Juma’a ce; kamar yanda ya saba yana kwance a ɗaki bayan ya dawo daga masallaci yana rage bacci kafin a gama shirya yara ya kai su makaranta. Wayar Khadeeja ce take ta faman ringing a ɗakin tana katse masa bacci, baya son tashi don haka ya yi tsaki ya gyara kwanciyarsa.

    Sai dai wayar da ta tsinke sai a sake bugowa; to waye ma yake kiranta da wannan safiyar bayan ko wayewa garin bai gama yi ba? Wayar tana fara ringing a karo na uku ya mirgina ya miƙa hannu ya ɗauko wayar daga kan durowar gefen gado. Ya kallin screen ɗin inda sunan wanda yake kiran ya bayyana “Baffa” ya karanta a fili yana wattsakewa.

    To me yasa Baffan Khadeeja yake kiranta yanzu? Allah ya sa dai ba wani abun ne ya faru a gidan nasu ba. Nan da nan ya sauko daga kan gadon ɗauke da wayar ya nufo kitchen inda Khadeejan take faman zubawa yara abinci suna tsaye kowa yana karɓar nasa. Ya miƙa mata wayar wadda take ringing yana cewa ‘Ki amsa Baffa ne yake ta kiranki kin baro wayar a ɗaki.’

    Tana karɓa ta amsa ta kara a kunnenta; yana tsaye yana kallonta yana tsoron kada a ce wani abu ne ya faru a gidan nasu. Bayan sun gama gaisawa da Baffan tace ‘A a Baffa, ina nan ne muna shirin makaranta ni da yara.’

    Daga ɗaya ɓangaren Baffa yace ‘Ƙarfe nawa ne lecture ɗin naki Dije? ’Tace ‘Karfe takwas. Idan nazo 7:30am ai kin gama shiryawa ko? ‘Eh Baffa. ‘To ki shirya idan na ƙaraso zan yi miki waya ki fito na kaiki makarantar sai na wuce office. ’Cike da girmamawa kamar wadda za ta tsuguna a wajen tace ‘To Baffa na gode, Allah ya ƙara lafiya.’

    Ta ajiye wayar bayan ya amsa, kafin ta yi wani abu Mustapha yace ‘Lafiya ƙalau dai naga Baffa yana kiranki da safe. Ta miƙawa Habib shayinsa da ta haɗa masa tana cewa ‘Uhm zai zo ya kai ni school ne shi ne yake tambayata ƙarfe nawa zai zo. Habib ya karɓi shayinsa ya fice yayin da Mustaphan ya matsa kusa da ita cike da kulawa da damuwa yana cewa ‘Makaranta kuma?

    Ba nace zan dinga kai ki ba? Yanzu ke saboda rashin tausayi sai ki taso shi da wannan safiyar kawai don ya kai ki makaranta? Ke abu ba zai wuce a wajenki ba? Ta juya cikin halin ko in kula tana cewa ‘Shi ne ya karɓi timetable ɗina yace zai dinga zuwa yana kai ni ko? Ai a gabanka ya faɗa.’

    ‘Kuma a gabanki na ba shi haƙuri ai; wannan wanne kalar abin kunya ne ina nan kuma ina da abin hawa amma za ki taso Baffa ya zo ya kai ki makarnta don Allah? Dariyace take son ta ƙwace mata saboda yanda duk ya muzanta kamar ma Baffa yana tsaye yana kallonsa. Kafin ta ba shi amsa ya ɗauki wayar tata ya dannawa Baffa kira ya miƙa mata waya yana cewa ‘ki gaya masa zan kai ki ba sai kin yi min wulaƙanci ba.’

    Kafin ta yi magana har Baffan ya ɗauka, don haka ta kara a kunnenta tace ‘Um Baffa ka bari ma Abban Afaf zai kai ni makarantar. ’Yace ‘Ah, kin tabbata dai ko? ‘Eh Baffa, ga su ma tare za mu fita gaba ɗaya shiryawa muke.’

    Ya zare wayar daga hannunta kafin ta sake magana ya kara a kunnensa cike da girmamawa yace ‘Baffa za mu tafi tare in sha Allahu, zan dinga kai ta. A yi haƙuri. Yace ‘To, to babu laifi. Allah ya yi muku albarka. Ya ajiye wayar yana harararta yana cewa ‘Yanzu zan je na shirya, ke ma ki shirya sai mu fita gaba ɗaya ko kuma idan na kai su sai na dawo kafin nan kin ƙarasa sai mu wuce.’

    Tace ‘Um, ka ga babu komai fa, za ku iya tafiya ma sai na wuce kawai ba sai na gayawa Baffan ba.’ Ya kakkafe ta da ido yana harararta har sai da ta sunkuyar da nata idanun, ya juya yana cewa ‘Ki shirya nace. ’Ya fice ya bar ta a nan. Ta yi dariya ta cigaba da aikinta.

    Ba ta da zaɓi haka ta shirya suka fita tare, kuma daga wannan lokacin ya zama ko da wanne lokaci zata makaranta haka yake barin abinda yake yi ya zo ya kai ta. Sai dai idan ta gama abinda take yi kawai sai ta hawo motar haya ta dawo.

    Karanta  Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyar

    Da asubar fari ya tashi, bayan ya gama alwala ya fito da niyyar tafiya masallaci ya ƙarasa ƙofar ɗakinta ya murza hannun ƙofar ko zai ji ta a buɗe amma sai ya ji ta a rufe, sai dai ya hango fitila ta ƙasan ƙofar ɗakin a kunne. Don haka ya kaɗa kai ya wuce masallaci ya san ta riga ta tashi.

    Tun kafin ta tayar da sallah cikinta yake ƙugi saboda jiya ba ta ci abincin dare ba ta kwanta, don haka tana idar da sallah ta gama azkar ɗinta ta buɗe ƙofar ɗakin ta fito ta wuce kitchen; a lokacin Rashida da su Afaf babu wanda ya tashi domin dama ita ce take tashin Rashida kafin ta yi sallah su kuma su Afaf bayan ta idar da sallar.

    Tana shiga ta ɗora ruwa kofi ɗaya ta jira ya tafasa, ta haɗa shayinta mai kauri a babban kofi ta ɗauki burodi ta gutsura ta ɗauka ta nufi ɗaki. A falo ta ci karo da shi ya shigo daga masallaci, ya dube ta yace ‘Shayi za ki sha da sanyin safiya kuma.’

    ‘Um.’ Ta ba shi amsa sannan ta wuce ɗakin. Da hanzari ya bi ta don kada ta rufe ƙofar, ya cimmata a daidai lokacin da take zama a kan dadduma tana ajiye shayin nata. Ko kallon inda yake ba ta yi ba balle ta nuna ta san mutum ya shigo. Ya ƙarasa ya zauna a gefen gado yana cewa ‘Sai kin gama za ki taso yaran ne? Akwai school fa.’

    Ta gutsiri burodi ta tsoma a shayin sannan tace ‘Ba ni da lecture sai 9am so idan na gama zan ɗan koma ne na rage bacci zuwa kamar 8am sai na tashi na shirya. Ya ɗan yi dariya a kaikaice don ya san kwanan zancen, yace ‘Haba dai, ai kya daure ki shirya yaran kafin ki koma ki kwanta ko?’

    ‘Oh, ai kuma ka cire al’amarinsu daga hannuna ka saka a hannun sakatariyarka kamar yanda ka sanar da ni a aikace jiya don idan ban manta ba ma ita ce ta kawo muku dinner. Ko ba komai ma ka huta da mita ta. Ta ɗauki kofin sahyinta ta cigaba da kurɓa.

    Ya ɗan tsaya yana ƙare mata kallo saboda yanda ya kasa fassara yanayin fuskarta domin kamar ranta ba a ɓace yake ba kamar ma dai tana cikin yanayi na nishaɗi. Yace ‘Common Khadija, na riga fa na gaya miki cewa ban same ki a waya ba shi yasa nace ita ta je ko? Ko da wani abu ma ai sai ki shirya su idan na kai su makaranta sai mu ƙarasa maganar kin ga lokaci yana ƙurewa.’

    ‘Babu ma wani abu, na riga na fahimci saƙon. Ya miƙe yana cewa ‘To don Allah ki fito ki shirya su kin ga idan suka makara rufe gate za a yi. Ta cigaba da shan shayinta kamar ba da ita yake magana ba, ya fara kosawa don haka kamar a hasale yace ‘Kina ji ina miki magana ko?’

    Ta kalle shi suka haɗa ido tace ‘Na ji. Ya kalli agogon bangon da yake ɗakin ya ga ƙarfe shida saura kwata, ya juya ya fice ba tare da yace komai ba. Ya wuce ɗakin yaran don ya kula so take yi su makara. Idan ya taso su in ya so sai su zo da kansu su gaya mata ta taso ta shirya su.

    Yana ficewa ta tashi ta tura ƙofar a hankali ta mayar ta kulle ta bar mukullin a jiki, domin yau babu wanda za ta shirya sai dai a yi duk abinda za a yi. Tana zama a kan daddumar ta ji Nasreen tana buga mata ƙofa tana cewa ‘Anti mun tashi. Har ta gaji da bugun ta ruga banɗaki ba a buɗe mata ba.

    Ya fito daga ɗakin nasu Rashida tana biye da shi, ya dube ta yace ‘Je ki taya mana ku shirya yara, kun kusan makara fa. Ta wuce kitchen yayin da ya nufi ɗakin Khadeeja, ya murza hannun ƙofar yana turawa ya jita a rufe ‘Ya juyo da mamaki yana hango kitchen yana cewa ‘Ko kina kitchen ne?’

    Ya wuce ya nufi kitchen ɗin, yana shiga ya dubi Rashida yace ‘Ba ta fito ba? Tace ‘Eh. Ya yi tsaki ya juya ya fice. Ya koma kƙfar ɗakin nata ya ƙara ƙwanƙwasawa, sai sai har ya gaji da ƙwanƙwasawa ba ta buɗe ƙofar ba, yana kallo ta ƙasan ƙofa ya ga duhu alamar an kashe fitilar ɗakin. Ya ja tsaki ya wuce ɗakinsa, yana shiga ya ɗauki wayarsa ya fara kiran lambarta.

    Sai dai har ya gaji da kira ba ta ɗauka ba. Don haka ya ajiye wayar a kan gadon ya fito daga ɗakin ya wuce kitchen, yana shiga ya tarar da Rashida tana tattare fulawar da ta kwaɓa jiya za a yi shawarma wadda Khadija ta bar ta a nan a buɗe ta kwana har ta bushe. Yana shiga ta bar abinda take yi ta tsaya tana kallonsa.

    Yace ‘Ya ba ki fara komai ba kika tsaya kina kallona? Uhm ai ban san me zan fara ba. Me kuke yi ke da ita idan za ta shirya ‘yan makaranta? Um, ai ita ce take yin abincin ni taya ta nake yi, kuma yanzu ban san me za ta dafa ba. Mtsewww!’ Ya ja tsaki sannan ya juya kamar zai fice sai kuma ya dawo yace ‘Ki ɗora ruwan shayi mana da abincin tafiya makaranta.’

    Ya juya zai fita tace ‘Um to abincin makarantar me za a dafa? Ya kalle ta cike da takaici; wai wannan wacce irin daƙiƙiyar yarinya ce? Yace ta dafa abincin ma sai kuma ya gaya mata abincin da za ta dafa. Kamar zai fice kuma sai ya tsaya yace ‘Ki dafa indomie. ‘To.’ Ta amsa jikinta na rawa ta juya ta shige store domin ɗauko indomie.

    Yana dawowa parlor ɗin ya jiyo Afaf tana hayaniya da Shukra a kan shiryawa, har ya nufi ɗakin sai kuma ya fasa ya wuce ƙofar ɗakin Khadeeja ya ƙwanƙwasa ƙofar a hankali yana cewa ‘Khadija ki buɗe mana. Babu wanda ya ba shi amsa don haka ya koma parlor ɗin ya zauna yana jiyo hayaniyar yaran a ɗakinsu suna shiryawa.

    Jimawa kaɗan ya tashi ya nufi ɗakin inda ya sa hannu ya fara ƙoƙarin taya su shiryawa. Nan da nan suka gama sannan ya taso su a gaba suka fito inda ya saka su a gaba suka sha shayi da burodi sannan a gurguje Rashida ta zuba musu indmie ɗinsu a flask ya tasa su a gaba suka fice.

    Khadeeja tana jin fitarsu da mota ta fito daga ɗakin a shirye ta sallami Rashida ta sanar da ita idan ya dawo ta fice ta tafi maƙota in ya so idan zai fita sai ya yi mata magana ta dawo; Haka suka saba tunda Shukra ta shiga makaranta; idan dai ba tare da yara zai fita ba sai dai Rashida ta je maƙota ta jira idan ya gama zai fita sannan ta dawo ta shiga gidan.

    Bayan ta gama sallamar Rashida ta fice ta tafi makaranta. Suna dab da ƙarasawa makarantar aka rufe gate ɗin, gaba ɗaya masu gadi da sauran ma’aikatan suka shige ciki suka rufe ƙofa; wanda hakan yake nufi babu yaron da zai sake shiga. Ya tsaya ya cije leɓe na ɗan lokaci sannan ya kunna motar suka kama hanyar komawa gida.

    Nasreen tace ‘Mun makara, ga shi ba mu taɓa makara ba. Yace ‘E, kun tsaya kuna ta faɗa ba ku shirya da wuri ba. Afaf tace ‘Abba Anti ba ta da lafiya ne? Ya shafa kansa yana cewa ‘Eh, ba ta jin daɗi. Shigowa gidan suka tarar da Rashida a tsaye a bakin ƙofa kamar yanda ta saba jiransa, tana ganin su ta bi su suka shige.

    Shi kuma Abbansu ya ƙarasa ƙofar ɗakin Khadeeja ya fara ƙwanƙwasawa yana yi yana cewa ‘Khadeeja da Allah ki buɗe mana. Rashida ta fito daga ɗakin su Afaf tace ‘Antin ta tafi makaranta. Ya kalle ta da mamaki yace ‘Makaranta? Yaushe? ‘Bayan kun fita.’

    Ya wuce ɗakinsa ya bar ta a nan. To me Khadija take nufi ne? Daga yin abu ta ma ƙi ta zauna a yi magana tana ta wulaƙanci, ga shi har ta sa yara sun rasa makaranta. Yanzu ga shi dole ya fita ya bar su a gidan su kaɗai abinda ba ya so. Amma wannan wulaƙancin na Khadeeja fa ya fara yawa, ta ma ƙi ta saurare shi gaba ɗaya. Yanzu ya take so a yi?

    Haka ya wuce ɗakinsa ya zauna ya fara kiran wayar Khadeeja amma har ya gaji da kira ba ta ɗauka ba. Ya duba lokaci ya ga karfe takwas da rabi, ga shi yana da meeting ƙarfe tara. Don haka a gurguje ya tashi ya shiga wanka ya shirya. Ko abinci bai tsaya ci ba ya fice ya bar yaran.

    Babu wanda ta gayawa yanda suka yi da Mustapha, don ko su Rahma ba ta cewa komai ba; su kuma da suka kula ba ta son magana sai kawai suka ƙyale ta. Haka ta yi zamanta a makaranta har wajen ƙarfe biyar na yamma sannan ta kamo hanya ta dawo gidan. Tana shigowa yara suka fara yi mata oyoyo; da murnarta ta amsa sannu da zuwansu kamar yanda ta saba.

    Ta kalli Afaf tace ‘Bari na je ɗaki na sha magani na huta, kaina ciwo yake yi. Ba tare da ta saurari amsarta ba ta shige ɗakin ta turo ƙofa. Sai bayan sallar isha’i sannan ya dawo, lokacin Afaf ta sa Rashida ta dafa musu taliya sun ci abincin dare saboda Khadeeja tace kada wanda ya sake buga mata ƙofa.

    Yana shigowa gidan ita ya fara tambaya suka ce masa tana ɗaki, sai dai ga mamakinsa yana taɓa ƙofar ya ji ta a rufe. Nasreen ce ta sanar da shi cewa tace a daina buga mata ƙofa ba ta da lafiya. Don haka shi ma sai kawai ya ƙyale ta ya cigaba da harkokinsa har sai da yara suka kwanta.

    Wajen ƙarfe goma na dare ya sake ƙwanƙwasa mata ƙofar, ta yi banza da shi ba ta ce komai ba. Ya matsa jikin ƙofar yace ‘Wallahi Khadeeja idan ba ki buɗe ƙofar nan ba zan ɓalla ta. Tana daga ciki ta ɗauki ‘yar saman rigar baccinta ta saka sanna ta zo ta buɗe masa ƙofar tana riƙe da wayarta tana chatting.

    Ta koma ciki ta ƙarasa kan gado ta zauna ta miƙe ƙafarta ba tare da ta ce masa komai ba. Yana daga tsaye ya ƙare mata kallo sannan yace ‘Wai wanne irin wulaƙanci ne wannan kike yi ne Khadeeja? Kin bar min yara sun makara a makaranta kuma kin fice kin bar gida ba tare da wani bayani ba?’

    ‘To ai ka san dai yau ina da lecture ko?’ Ta ba shi amsa sannan ta sake mayar da hankali a kan wayarta. To don me ba ki tashi kin shirya yara ba kuma da kika dawo kika sake rufe ƙofa kika bar su. Au wai Najan ba ta zo ba? Ai na zata ta yi musu komai tunda yau ita ce da aiki.’

    Ya cije leɓe sannan ya ja dogon tsaki ya fesar da iska saboda yanda Khadeeja take ƙure shi ‘Na gaya miki babu komai a tsakanina da ita sakatariyata ce kawai, don Allah wai me kike so na yi miki ne a kan wannan maganar. Idan kuma don ta je makarantar yara ne to ki yi haƙuri ba za ta sake zuwa ba, babu wata alaƙa tsakanina da ita dama sai ta office.’

    ‘Ai na ga alama.’ Ta faɗa ba tare da ta daina kallon wayara ba. A fusace yace Khadeeja ni nake miki magana kina danna waya ko kallo ban ishe ki ba? Ta ajiye wayar a gefenta ta kalle shi tace ‘Shike nan, na ji duk abinda ka faɗa. Please kada ki sake rufe ƙofar nan, kuma ga yara can sun kwanta da safe ki tashe su da wuri kada su makara.’

    ‘Ok. Har ya juya zai fita ya ɗan tsaya yace ‘Kuma kin san ke ma ba a nan kika saba kwana ba. Ok. Ya fice ya bar ta.Ta murguɗa baki kamar yana kallonta tace ‘Ɗan rainin hankali, ba ka yi laushi ba tukunna ka je ka ɗauko Naja ta zo ta dinga yi maka hidimar kai da yaran. Yana fita ta zame ta yi kwanciyarta sai dai ba ta rufe ƙofar ba.

    Tana jinsa ya dawo ɗakin ya leƙa fuskarta ta yi kamar bacci take, don haka ya fice ya bar ta bayan ya kashe mata fitila. Ya yi zaton kamar yanda ta amsa masa da daddare za ta tashi ta shirya yara, sai dai abinda ta yi jiya shi ta sake maimaitawa. Ta saka mukulli ta kulle ɗakin, ya buga har ya gaji ba ta buɗe ba.

    Don haka ba tare da ɓata lokaci ba ya tsaya a kan yara suka shirya ya kwashe su ya kai su makaranta. Kafin ya dawo ta fice ta bar masa Rashida a gidan. Takaici ne ya sake kama shi; to me Khadeeja ta mayar da shi ne? Wannan wane kalar taurin kai ne take yi haka? Kuma me take nufi?

    Yanzu me take so ya yi mata; yaya ma zai yi da ita don gaskiya idan ba so take ya doke ta ba bai san me zai yi mata ba. Haka ya shirya ya fice ya nufi office. Har ya kusa ƙarasawa office ɗin dabara ta faɗo masa; ya karkata kan motar ya nufi gidan su Khadeeja.

    Gara ya je ya kai ƙararta waje Baffa in ya so su tsawatar mata don shi yanzu idan ba duka ba bai san me take so ya yi mata ba. Ya ci sa’a ya sami Baffa yana shirin fita, bayan sun gaisa Baffa yace ‘Lafiya kuke dai na ganka da sassafe ko?’ Nan ya mayar masa da abinda ya faru da kuma yanda Khadeejan take rufe kanta a ɗaki, sai dai ce masa ya yi ya rasa Khadeejan ne a waya shi yasa ya tura sakatariyar tasa.

    Baffa ya yi dariya yace ‘Kishi ne nasu na mata ya motsa, ka san a kan wata macen komai son da matarka take maka to za a ji kanku. Kada ka damu bayan Magriba ka ɗaukota ku zo nan. Zan kirawo ta don ma kada tace za ta yi taurin kai. To Baffa, na gode.’

    Ya yi musu sallama ya fice yana jin daɗin matakin da ya ɗauka tunda ya san ko babu komai Baffa zai yi mata faɗa kuma ya san dole ta shiga hayyacinta. Suna shirin shiga lecture wayarta ta yi ƙara, tana dubawa taga Baffanta ne don haka ta ja da baya ta nemi waje ta amsa. Bayan sun gaisa yace ‘Khadeeja, na cewa Mustapha ku zo bayan magriba ke da shi kin ji ko?’

    Tace ‘Um Baffa yau? Wani abu ya faru ne? Babu abinda ya faru, ku dai zo ɗin. To Baffa in sha Allahu za mu zo, in ya dawo zan gaya masa. Kada ki damu na gaya masa ma, yanzu ya bar nan. Ta amsa suka yi sallama da Baffa tana dariya, don ta san inda zancen ya dosa, ta gane Mustapha ƙararta ya kai duk da ba ta zaci haka ba.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Huɗu

    Kwanci tashi cikin wannan rayuwar da Khadeeja take a gidan Mustapha har ta gama level 2 a karatunta ta shiga level 3, kuma shekararsu biyu kenan da Rashida mai aikinta. Zaman dai haka ake yinsa cikin dagewa da dagiya; idan Mustapha yana son buƙatarsa a wajenta sai ta ji kamar ba shi ba saboda yanda yake kwantar da kai ya samu buƙatarsa ta biya.

    Amma kuma da zarar ta yi maganar karatunta ko wani abu da zai sa ta fita daga gidan ba tare da ta tafi da yara ba to sai ya nuna ɓacin ransa. Domin a halin yanzu kowa a danginsu ya santa da ‘yayanta domin tare ake ganinsu ko bikin wa ake yi. Gidan Mommy kuwa sun mayar da shi kamar gidan kakarsu, kuma da yake sun sami karɓuwa sai suka sake sakewa.

    Karatunta yana tafiya daidai tunda ta saka auduga ta toshe kunnenta daga duk wata mita ta Mustapha, sai dai kawai kullum a gajiye take daga aikin gida da kuma aikin tunanin abinda za ta yi Mustapha ya daina nuna mata halin ko in kula. Yaran ba su saba ba ta matsala ba a da, amma zuwa yanzu duk tana neman ta rasa kansu; musamman Afaf da Nasreen.

    Idan dai aiki ta saka su ba za su ce ba za su yi ba amma idan ba su ga dama haka za su yi kunnen uwar shegu da ita sai dai ko ta yi aikinta ko kuma ta sa Rashida ta yi mata. Sannan kuma yanzu Afaf ta ƙulla ƙawance da Samira ‘yar wajen Yaya Jidda, don haka kusan duk wani motsi na Khadeeja Afaf sai ta gayawa Samira wadda take kai wa uwarta rahoto na kai tsaye; don haka ne ma matsawar da Yaya Jidda take wa Khadeejan ta ƙaru.

    Sai dai a yanzu ba wannan ne damuwar Khadeeja ba, babbar damuwarta ita ce rashin haihuwa. Tun bayan da ta yi ɓari a loakcin corona ko ɓatan wata ba ta sake yi ba ga shi ana neman shekaru biyu. Zaman gidan ba ya mata daɗi, ba ta jin daɗin yanda yaran suke mata, musamman Afaf wadda a da take tunanin sun zama ɗaya. Tana fatan ita ma Allah ya ba ta nata ‘yayan waɗanda za su kalle ta a matsayin uwa.

    Ta riga shi kwanciya kamar yanda suka saba saboda yanda ta kula idan ta zauna jiransa su kwanta tare ita ake cuta tunda dole ta tashi kafin asuba ta shirya yara. Sai wajen sha biyu saura sanna ya gama abinda yake ya kwanta a kusa da ita, ta juya ta gyara kwanciyarta.

    Yana kwance amma ya ɗaga waya yana chattinga kamar yanda ‘yan kwanakin nan ta kula kullum kafin ya kwanta sai ya yi chatting. Ta miƙe ta je ta yiwo fitsari, ta sha ruwa sannan ta dawo ta kwanta, zuwa lokacin ya gama chatting ɗin ya ajiye wayar yana azkar. Ta kwanta ta gyara kwanciyarta, bayan da ta kula ya gama azkar ɗin ta lalubo hannunsa ta riƙe cikin sanyin murya tace ‘Abban Afaf.’

    ‘Umm.’ Ya amsa yana kallonta duk da hasken da yake cikin ɗakin bai kai ya kawo ba. ‘Uhm, gaskiya ina son zuwa asibiti na ga gynae doctor.’ Ta faɗa tana wasa da hannunsa wanda ta riƙe. Ya riƙe hannunta a cikin nasa ya ƙara ba ta hankalinsa yace ‘Baki da lafiya ne?’

    ‘No ba wani specific issue. Ka san dai kwanaki nace maka ina son na je a duba a ga abinda yasa har yanzu ban sake samun ciki ba, kada na je wata matsala ce na yi ta zama gara na je a duba. Ya gyara kwanciya ya ƙara matsowa kusa da ita ‘Kina dai so ki ɗorawa kanki damuwa, har yanzu fa ba a yi shekaru biyu da ɓarin ba.

    Iya wannan ya isa ya sa ki san cewa lafiyarki ƙalau, kawai Allah ne bai kawo ba tunda wancan ɗin ma ba asibiti kika je kika samo ba ko? Na sani, amma dai gaskiya ina so na je a duba ni ɗin na sami nutsuwa. Tunda ka ga idan na je aka ce min lafiyata ƙalau ai dawowa zan yi kawai na cigaba da addua’a, idan kuma matsala ce sa na nemi maganinta.’

    ‘Babu wata matsala kina dai son tonowa kanki matsalar. Ke yanzu ma da kike neman ciki ido rufe ya za ki yi da karatun? Tunda ga shi kin shiga level 3 kuma ke da kanki kina cewa ya fi wahala. Ya za ki yi da laulayi ga karatu? Ko har kin mata ne? Ai zai fi sauƙi idan ma dole ne sai kin je asibitin ki bari ki gama karatun kafin ki kwantar da kanki.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan tace ‘Ina son zuwa gaskiya, amma dai ina jin zan bari mu gama exams ɗin wannan semester in ya so kafin a koma hutu sai na samu na je. To Allah ya kai mu.  Tana son ta haihu duk da dai Mommy ma tace mata lafiyarta ƙalau amma ita gaskiya tana so ta je a duba ta.

    Kuma yanda Mustapha yake gwada mata halin ko in kula idan ana maganar haihuwa ya sa gaba ɗaya ta fara tunanin ko bai damu da ta haihu ba; to ya ma za a yi ya so ta haihu tunda shi masoyiyarsa ta haifar masa yara har uku? Haka ta yi ta saƙe-saƙe tana juyi, sai gefin asuba sannan bacci ya ɗauke ta.

    Kamar kullum yana shiga office ɗin yau ma damuwarsa ta yaye; musamman yanda ƙamshin turarenta ya yi wa ƙofofin hancinsa maraba bayan da ya shiga office ɗin nasa ya rufo ƙofar. Wannan ya tabbatar masa da cewa ta riga ta zo office ɗin wataƙila wani office ɗin ta je. Ya ajiye jakarsa a kan table ya ƙarasa ya zauna a kan kujerarsa cike da farin ciki.

    Sabuwar sakatariyarsa Naja’atu Musa Bello; watanta uku da fara aiki amma soyayya mai ƙarfi ta ƙullu a tsakanisu. Duk wata damuwa da Khadeeja za ta ɗora masa da ya shigo office ɗin ya ganta yake mantawa da ita, idan kuma an tashi daga office ko a ranakun da babu aiki ya kan je gidansu zance. Duk da dai manya ba su riga sun shiga zancen ba amma dai yana ji a jikinsa Naja’atu tasa ce.

    Bai daɗe da zama ba ta turo kofar ta shigo, daga tsaye ta sakar masa kyakkyawan murmushinta wanda ba ya gajiya da kalla. ‘Ranka ya daɗe barka da shigowa.’ Ta faɗa tana juya ƙwayar idonta. ‘Good Morning my dear.’ Ya amsa yana ta faman murmushin da yake barazanar ƙarawa bakinsa faɗi.

    Ta ƙarasa ta zauna a kujerar gabansa, sannan ta ɗauki file a kan teburin ta miƙa masa. Nan take ya buɗa ya fara karantawa yana mata tambayoyi tana yi masa bayani. Bayan sun gama ya ajiye file ɗin a gefe ya dube ta yace ‘To meye labari? Ta yi dariya ta sunkuyar da kai a kunyace tace ‘Komai normal. Good. So na yi mana order ɗin lunch ko? Don na san ko an ce ki zo mu je mu ci a waje ba kya son zuwa eateries, sai shopping ko?’

    Ta yi dariya tace ‘Gara dai a yi order ɗin. Ba damuwa, ki yi mana order ɗin sai ki turo min account number na tura kuɗin.’ Yes Boss, an gama. Suka yi dariya gaba ɗaya. Tana shirin tashi yace ‘Yauwa, gobe ana open day a school ɗin su Afaf, please idan kika shigo around 10am sai ki je musu, ki jiyo min duk bayanansu da performances ɗin su.’

    Ta gyara zama tace ‘Uhm, ok. But Madam ba ta nan ne ko ba ta jin daɗi? Ya gyara zama ya fara lilo a kujerar da yake kai yana kallonta sosai sanna yace ‘No, lafiyarta ƙalau but na dai fi son ke ki je ki jiyo min komai. Cike da farin ciki ta sake faɗaɗa murmushinta tace ‘Yes Sir, Allah ya kai mu. Kuma Allah ya sa kada ka sa yayata ta ba ni query saboda na shiga aikinta duk da dai ni ma ‘yayana ne.’

    Ya yi dariya ‘Kada ki damu, ba ki da matsala da ita. Suka sake ɗan taɓa hira sannan ta fice ta koma office ɗinta cike da farin cikin yanda alaƙarsu take tafiya ita da ogan nata. Ba za ta taɓa bari Mustapha ya kufce mata ba don ta ga mijin aure. Ta gama degree ɗinta har ta yi masters, saurayinta na ƙarshe har sun zo gaisuwa haka kawai ya daina zuwa sai ji kawai ta yi ana bikinsa da ‘yar uwarsa.

    Duk da ta san ba wasu shekaru ne da ita masu yawa ba domin shekarunta 28 kacal, amma dai ta san an matsu ta yi aure a gidansu; musammam ummanta wadda aikin ma so ta yi ta hana ta sai ta yi aure. Sai ga shi ashe mijin yana wajen aikin. A hankali suka saba, har suka kai yanzu da take jin za ta iya cewa ta fi matarsa sanin halin da yake ciki da inda yake a kowanne lokaci.

    Don haka ma take jin cewa ƙwace shi a wajen Khadeeja kamar ƙwace goruba ne a hannun kuturu, domin tun yanzu tana jin ta fara samun nasara tunda kullum ita yake kawowa ƙarar Khadeejan sai ta ba shi haƙuri, ta riga ta fahimci irin zaman da suke yi da Khadeejan don haka ta gama shirya musu; lokaci kawai take jira.

    Ƙarfe sha ɗaya take da lecture don haka sai da ta gama shirya yaran dukansu suka fita makaranta sannan ita ma ta ƙarasa ayyukanta ta shirya. Ƙarfe goma da minti biyar tana zaune a gaban mudubi tana gyara fuska ta tuna jiya da daddare Shukra ta ce mata Anty tace kowa ya zo da Mommy ɗinsa open day 9am to 11am sannan sai a zarce da sports.

    Kuma idan dai ba ta manta ba ma Afaf ta gaya mata duk da section ɗin su Afaf ɗin daban da na su Shukra. Sai dai ba su yi maganar da Abbansu ba, bai gaya mata ita ce za ta je ko shi ne zai je ba gaba ɗaya ta manta ba ta tambaye shi ba. Ta miƙe ta ɗauko wayarta wadda take ajiye a gefen gado ta dannan masa kira.

    Sai da ta kirawo sau uku duka wayar ba ta shiga ba, don haka ta yanke hukuncin idan ta fita sai ta fara tsayawa a makarantar tasu tukunna kada ta je sai ta wuce makaranta ya bugo waya yace ita ce za ta je ya jiƙa mata aiki. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta saka jilbab ɗinta me kalar lilac sanna ta saka baƙin sneakers ɗinta ta sallami Rashida sannan ta wuce.

    Tana zuwa makarantar kai tsaye ajinsu Shukra ta wuce, duk malaman nasu sun santa saboda zuwa ɗaukansu don haka ba tare da ɓata lokaci ba aka ba ta bayanan Shukra da kuma results ɗinta na CA. Tana gamawa ta ja hannun Shukra suka wuce ajinsu Nasreen inda nan ma aka haɗa mata komai, Nasreen tana cikin waɗanda za su yi wasan tsere don haka ba ta samu ta fita daga aji ba Khadeeja ta ja Shukra suka nufi secondary section don ta karɓo sakamakon Afaf da Habib.

    Tun kafin su ƙarasa kofar secondary section ɗin ta hango Afaf tare da wata mata sanye da baƙar abaya da brown envelops a hannunta, suna tafe suna hira; ga dukkan alamu a dai malama ce a nan makarantar duk da ita Khadeeja ba ta taɓa ganinta ba. Da suka ƙara matsowa kusa Shukra ta zare hannunta daga na Khadeeja tana cewa ‘La, Anti Naja ce ga su nan ita da Yaya Afaf.’ Ta ƙarasa wajensu da gudu.

    Da fara’arta ta cimmusu, suna haɗuwa ta ƙara faɗaɗa murmushinta cike da girmamawa tace ‘Sannu Anti. Cike da mamaki ita ma ta ɗan yage baki mai kama da murmushi tace ‘Yauwa, sannunmu. Ya aiki ya yaran?’ ta kula da yanda ta ke magana kamar da ƙyar don haka kafin ma ta ba ta amsa ta mayar da hankalinta ga Afaf tace ‘Yaya Afafa mu je na karɓo muku CA report ɗinku ke da Habib na wuce don ni ma school zan je.’

    Ta ɗan ɗaga gira cikin halin ko in kula tace ‘Anti Naja ta karɓar mana ai, dama na su Shukra za ta je ta karɓa yanzu. Ta kalli Afaf ɗin sannan ta kalli malamar da aka kira Anti Naja tana mamaki tace ‘Me yasa? Anti ai da kin bar shi na zo gashi sun saka ki aiki. Ta kawar da kai ta ɗaga gira tana cewa ‘No ba wani aiki, ai Abbansu ne yace na karɓar musu.’

    Ita ma Khadeeja ta dan zaro ido tace ‘Oh, ya zo kenan ko yaushe yace a karɓar musu?’ Afaf ta fahimci Khadeeja ba ta san Naja ba kuma ba ta ma san da zamanta ba, sabanin ita da ƙannenta waɗanda a cikinsu za ta iya cewa Shukra ce kawai ba ta san Naja ba ko kuma ta santa amma ba ta san wacece ita ba. Ta ɗan yi gyaran murya tace ‘Anti ba fa malamarmu ba ce, sakatariyar Abba ce kuma shi ne ya turo ta daga office ta zo mana open day ɗin.’

    Mamakin Khaddeja ya ƙaru, ta sake ƙarewa Naja kallo na ɗan takaitaccen lokaci sannan ta buɗe baki za ta yi magana sai kuma ta fasa. Ta ɗan yi murmushi da gefen baki sannan ta kalli ƙasa ta ɗago suka haɗa ido da Najan wadda take mata kallon da ta kasa fassarawa sanna tace ‘Oh, ok, Umm.’

    Kafin ta ce wani abu Habib ya ƙaraso wajen yace ‘Yauwa Anti kin ƙaraso? Dama ke nake jira; don Allah zo mu je ki cewa uncle ni ba na son basket ball team ya bar ni na shiga football team. Haka kawai wai saboda ni dogo ne sai na yi basketball. Kafin Khadeeja ta yi magana Najan tace ‘Au shi ne ba ka gaya min ba Habib, ai da ka gaya min na yi masa magana.

    Dama Anti nake jira.’ Ya faɗa cikin halin ko in kula ya zari envelop guda ɗaya daga hannun Najan ya miƙawa Khadija yana dariya yace ‘Anti guess what? Ta ɗan yi murmushi yayin da suka bar Naja da baki buɗe, tace ‘What? Ya zaro takarda ɗaya ya miƙa mata yana cewa 38 naci a Hausa yau don haka yau da shawarma zan yi dinner ko?’

    Ta karɓa tana dariya sannan ta ba shi hannu suka tafa tace ‘Iyye, ai dole ka ci shawarma tunda yau ka wuce gori. Haba ko kai fa, kullum komai ka ci A da B amma a Hausa ka dinga cin D da F. Ya miƙawa Khaddeja envelop ɗin yana cewa ‘To za ki ga Uncle ɗin? Tace ‘No, tunda yanzu ka ga kun riga kun fara games ina jin ka bari sai gobe sai na zo na gan shi.

    Kafin nan mun tattauna a kan football da basketball ɗin kuma mun yi magana da Abbanka ko? Ya gyada kai ‘Eh, haka ne. Naja ta yi sauri tace ‘Idan kina sauri ne ai sai na je naga Uncle ɗin. Tace ‘No ba sauri nake ba, kamar dai goben zai fi dacewa kawai. Habib ya katse su yana miƙawa Khadeeja envelope ɗin yana cewa ‘Anti sai mun dawo, goben kya zo kawai.’ Ya wuce ya bar su a nan.

    Naja ta miƙawa Khadeeja hannu tana cewa ‘Ki kawo na tafi wa da yallaɓai takardun tunda office zan koma. Ta ɗan yi murmushi tace ‘No ina ga gara ni na tafi masa da su tunda a gidansa zan kwana. Ta ɓata rai tace ‘Um, sai an jima. Ta wuce riƙe da takardun Afaf da suke hannunta Afaf ɗin tana biye da ita suna hira.

    Khadeeja ta bi bayansu da kallo tana mamaki; to yaushe ya yi sabuwar sakatariya? Tunda da dai ta san sakatarensa namiji ne. kuma har yaushe sakatariyar ta kai matsayin ta zo wa yara open day har tana wani cewa a ba ta takardu ta kai masa? Tukunna ma; kamar dai yaran nan sun sa wannan sakatariyar, ita ce ba ta santa ba.

    To kenan har ya yi introducing ɗinta a wajen yaransa a matsayinta na wa? Me yasa suka kwana tare bai ce mata tazo open day ba kuma bayan ya fita ma ya kasa kiranta? Wanda tunda ta aure shi duk wata harkar makarantar yara ita ce take zuwa kuma shi yake saka ta ta zo. To me yasa wannan ya sa sakatariya? Naja? Ba ta son ta yanke hukunci cewa akwai wani abu tsakanin Mustapha da Naja amma dai tabbas tana da tarin tambayin da zai amsa mata.

    Sai da ta raka Shukra aji sannan ta nufi fita daga makarantar. Tun kafin ta gama fitowa daga cikin ginin makarantar zuwa farfajiyar wajen da ake ajiye motoci ta hango su, tana riƙe da hannun Afaf suna magana har suka ƙarasa bakin motar gefen direba ta sa mukulli ta buɗa motar; ta dan ja baya ta labe. Me take gani ne? Motar Mustapha? To shine ya kawo ta ko me? Tana nan a laɓe ta hango su; Naja ta buɗe motar ta zauna a kujerar direba sannan ta yi wa Afaf sallama ta ja motar.

    Sai da ta karanta lambar motar a fili domin ƙara tabbatarwa motar Mustapha ce; kanta ya ɗaure gaba ɗaya. To me hakan yake nufi? Ya aiko sakatariyarsa ta zo wa yara open day kuma a motarsa. To haɗa kuɗi suka yi suka sayi motar a tare? Ko kuwa dai tsabar ƙauna ce ko rashin hankali ya sa suke sharing motarsa da sakatariya? Me yasa bai aiko ta a motar haya ba ko a motar office? Wato motar da ita idan dai makaranta za ta ko a rage mata hanya ba ta isa ya yi ba ita ce ya ba wa sakatariya take yawo a gari.

    Kai! Gaskiya Mustapha ya raina ta. Ta yi sauri ta fito daga inda ta raɓe lokacin da ta hango Afaf ta nufo wajen. Ta yi mata sallama sannan ta wuce ta fice daga harabar makarantar. A bakin titi ta tsaya, motocin haya sai tsayawa suke ba tare da ta hau ba; gaba ɗaya ma ta manta inda za ta saboda yanda zuciyarta take zafi; me Mustapha yake nufi da ita?

    Har ta juya za ta koma gida saboda yanda take jin ba za ta iya zuwa lecture ɗin ba sai kuma ta tuna idan ta je gidan me za ta yi? Rufe kanta kawai za ta yi a ɗaki ta yi kukan da ba zai mata maganin komai ba; don haka ta sake juyawa ta koma bakin titi ta hau motar BUK. Ta kalli waje ta tagar motar, ta yi murmushi ita kaɗai; wai ita ce a motar haya yayin da ga wata can tana yawo a motar mijinta.

    Ta kawar da kai ta share ƙwalla. Ko da ta ƙarasa makarantar ta san an riga an yi nisa da lecture ɗin kuma ko ta shiga ma ta san babu abinda za ta gane, don haka kai tsaye ta wuce hostel ɗakinsu Rahma inda suka saba zuwa su huta; duk da dai ta san suna wajen lecture amma ta san inda suke ajiye mukullansu. Tana shiga ɗakin ta yi watsi da kayanta ta faɗa gadon Rahma ta kwanta ta fashe da kuka.

    Sai wajen ƙarfe ɗaya da kwata sanna suka shigo ɗakin suka same ta a kwance ta ci kuka ta ƙoshi. Suna shiga Farida tace ‘Haba Malama, tun ɗazu muke kiranki a waya kin ƙi ɗaga wa ashe kina nan abunki. Suka ƙarasa suka faɗa kanta Asiya tace ‘Ko dai abun ya zo ne a tanadi goro da ledar amai. Ta sake fashewa da sabon kuka.

    Suka yi tsuru-tsuru. Rahma ta shafa bayanta tace ‘Kawata kina faɗar mana da gaba fa, don Allah me ya faru? Ko Babe ba shi da lafiya ne? Haka suka yita jero mata tambayoyi, ita kuwa ta yi banza da su har suma suka gaji suka yi shiru, suka zauna kawai suna jiranta. Sai da ta yi mai isarta sannan ta ba su labarin abinda ya faru.

    Rahma tace ‘kada fa na yi ashar ƙawata, kut! Wannan wanne kalar wulaƙanci ne mutumin nan yake miki? Farida tace ‘Motar da yake ƙyashin ɗaukanki ya je ya ba wa budurwa ko ma karuwa take yawo a titi? Lallai an gaida uban Afaf. Rahma tace ‘Gaskiya idan ya dawo yau ya kamata ya yi miki bayani na ganewa, duk da babu wani explanatin da zai sa na yarda babu wani abu a tsakanishi da ita ba sakatariya ba ko DG ce wallahi.

    Ya yi miki bayani kuma kema ki karanta masa; wannan ai zubar da mutunci ne kina yawo a motar haya wata side chick tana yawo a motar mijinki? Mijinki na sunna fa, Haba! Gaskiya dai ya kamata ki san yanda za ki yi ki ƙwaci kanki a hannun mutumin nana tunda shi ga alama bai san mutunci ba.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bar ta ta bi abun a hankali. Ta kalle ta rai a ɓace ‘A hankali Amina? Shi a hankali kika ga yana yi min? Ni budurwarsa take cewa wai na kawo takardun yara ta kai masa saboda tsabar samun waje? Haba mana! Farida tace ‘Toh shi dai na gani, aure ai ba hauka ba ne. Wallahi ya kamata ki dage ki gaya masa abinda yake ranki tunda dai an daɗe ana ruwa ƙasa tana shanyewa, ai ba siyo ki ya yi a bakin rimi ba da zai mayar da ke kamar wata sokuwa.’

    Amina tace ‘Don Allah ku bari a bi abun a hankali, miji fa ba kamar saurayi ba ne haba!’ Rahama ta ja hannun Amina tace ‘Taso ‘yar uwa mu nemo abinci wannan batun na masu aure ne ba namu ba kin ji. Haka ta wuni a makarantar nan Amina tana ba ta baki yayin da Farida da Rahma suke ƙara jaddada mata ya kamata ta ɗauki mataki idan ba haka ba rainin zai wuce haka. Sai bayan la’asar sannan ta kwaso kayanta ta dawo gidan.

    Wunin ranar haka ta ƙarasa shi cikin ƙunci, sai da ta cewa yara ba ta da lafiya sannan suka ƙyale ta don kowa yana so ya ba ta labarin sports day. Rashida ce ta ƙarasa duk wata hidimar gida da ta yara, har abincin ma da ba ya so Rashidan ta girka yau cewa ta yi ta girka don a yanda take jin ko ta dafa ba zai yi daɗi ba.

    Sai bayan sallar magriba sannan ya dawo gidan, bayan ya gama hayaniya da yara ya wuce ɗakin ya same ta. Tana kwance ba ta ko juyo ta kalle shi ba don haka ya yi zaton bacci take yi. Sai kawai ya kintsa ya fice daga ɗakin. Ba ta son yi wa yaro alƙawari ta karya don haka tun da ta dawo ta sa Rashida ta haɗa mata duk wasu kayan da take buƙata na haɗa shawarma sanna ta kwaɓa mata fulawar, yanda idan ta fito bayan isha’i sai ta haɗa shawarma kamar yanda ta yi wa Habib alƙawari idan ya yi passing Hausa.

    Suna zaune shi da yaran ta wuce su ta shiga kitchen, nan da nan ta fara ƙoƙarin ɗorawa. Tana daga kitchen ta jiyo yana amsa waya yana kwatancen gida; ta ja tsaki a fili tana fatan Allah ya sa ba baƙo zai yi ba don ko me zai yi ba za ta gaisa da wani baƙo ba balle ta ba shi ko da ruwa. Sai dai ya yi duk abinda zai yi. Kafin ta gama wannan tunanin ta ji shi yana cewa yanzu zai fito, inda ba tare da ɓata lokaci ba ta ji fitarsa.

    Jimawa kaɗan ya shigo da leda ya wuce ya same ta a kitchen tana yayyanka fulawa za ta fara gasawa. Ya miƙa mata ledar yana cewa ‘Ga wannan shawarma ce; sakatariyata ce Naja ta aiko delivery man ya kawo a ba wa yara. Sai ki duba ki zubo a tray mu ci don na ji kamar da yawa’Ta kalle shi da jajayen idanuwanta waɗanda suka koɗe saboda kuka da tsabar mamaki; ta yi murmushi mai ɗaci sannan ta kashe wutar abinda ta ɗora a wuta ta nufo shi yayin da ya miƙa ledar a zaton za ta karɓa.

    Ta bigi kafaɗarsa ta wuce ta shige ɗaki ta bar shi a nan tsaye. Ya bi bayanta da kallo cike da tsananin mamaki saboda Khadeeja ba ta taɓa yi masa irin wannan wulakancin ba; kuma a gaban yara don duk biyo shi suka yi da suka ji yana maganar a juye a ci. Nan take ya ajiye ledar kan sink sanna ya bi bayanta ɗaki; yana shiga ya same ta a tsaye a gaban mudubi tana cika tana batsewa kamar ma jiransa take yi.

    ‘Wannan wane irin wulaƙanci ne ina miki magana za ki yi min tsaki a gaban yara saboda raini.’ Ya tambaya cikin jin kai da isa. Ta kalle shi ta ɗauke kai tana murmushin takaici tace ‘Ji na yi kamar zagina ka yi. Kallon takaicin da yake mata ya koma na mamaki, ya tsare ta da ido kuma ita ma ta ƙi ɗauke nata idon. Yace ‘Ni na zage ki? Ko kuwa dai ke kika zage ni?’

    Ba tare da ta ba shi amsa ba tace ‘Wacece Naja Mtseww!’ ya ja tsaki sannan ya cigaba ‘Sakatariyata ce; shi ne kike nema ki zage ni saboda nace ta kawowa yara abu? Ba ka gaya min ka mayar da ita wakiliyarka a makarantar yara ba, har sai da na je musu open day sannan sai na ganta wai kai ka tura ta. Har tana cewa wai na ba ta takardun yara ita kace ta karɓo.’

    ‘Eh, ai ni nace ta karɓo tunda na fita ban gaya miki ba. Kuma ka kasa yi mi waya kamar yanda kafin yau duk abinda kake so a yi na yaran kake min waya ko da ina sama jannati ne na je na yi? Ya fara hasala saboda yanda take maganar a tsiwace ga wani kallon raini da take masa.

    ‘Ba fa na son wulaƙanci khadeeja; ni na tura ta ta karɓo ko ban isa ba ne? Na zata za ki yi murna tunda kullum cikin ƙorafi kike da mitar hidimar yaran saboda kina gani ba ke kika haife su ba, ke naki karatun ne a gabanki. Ta yi murmushi tace ‘Ka isa har ka yi yawa, kuma alhamdulillahi tunda an sami mai karɓa ta yanzu kam zan huta da wasu abubuwan. Kuma na gane ni ce ban isa na shigar maka mota ba shi yasa ita da kake ganin mutuncinta ka koya mata mota har ga shi nan ta kai ta ɗauki motarka ta fita yawo.’

    Ta ɗaga ƙafa za ta shige banɗaki sai kuma ta tsaya ta kalle shi suka haɗa ido sannan tace ‘Bayan hidimar yaran sai kuma wacce hidimar take maka? Ko ma dai ka aure ta ne ni ce ban sani ba? Ba fa na son iskanci Khadeeja! Kina ji nace miki sakatariyata ce kike wannan maganar banzar. Na aike ta don haka na ba ta mota ta ta je ta dawo, shi ne kike wannan rashin kunyar?

    Idan da kina hidimar yaran ba tare da ƙosawa ba ai babu wanda zan nema. Na san idan na gaya miki sai kin yi mita don haka na nemi wadda za ta yi cikin walwala na saka ta, sai dai duk abinda za ki yi ki je ki yi amma idan kika zage ni wallahi ba za ki ji da daɗi ba. Ta yi murmushi ‘Hmmm! Ka fi ƙarfin zagi yallaɓai, amma tabbas ka yi yanda kake so don haka ni ma zan yi yanda nake so.’

    Ta juya ta shige banɗaki ta turo ƙofar ta bar shi nan tsaye. Haka ya gaji da tsayuwa ya juya ya fice daga ɗakin; tana jin fitarsa ta fito ta saka mukulli ta kulle ɗakin ta bar mukullin a jiki ta koma ta kwanta. Tun a office Naja’atu ta sanar da shi haɗuwarsu da Khadeeja, kuma ita kanta sai da ta nuna rashin jin daɗinta a kan ya san Khadeeja za ta je ya tura ta.

    Sai da ya yi ta faman ba ta hakuri sannan ya samo kanta. Bai taɓa zaton Khadeeja za ta ba shi matsala, don ya zata idan yace mata sakatariyarsa ce za ta fahimce shi, yanzu ga shi ita ma Khadeejan so take ya lallashe ta. Yana da niyyar auren Naja don sun ma yi magana da Alhaji kwanan nan ma za a kai kuɗin aure; kawai dai bai shirya gayawa Khadija ba saboda bai shirya ba, ya fi so sai magana ta tsaya an kusa biki sai ya sanar da ita.

    Kafin lokacin ya gama gininsa sai su tashi su koma don a can yake so amarya ta tare. Yanzun ma kuma da hakan ta faru ba gaya mata zai yi ba, idan ta gama fushin nata ya san me zai gaya mata. Tun yana saka rai za ta buɗe ƙofar ɗakin har dare ya fara yi ba ta buɗe ba, yara har sun gaji da tambayarta. Haka ya sa Rashida ta ba su abinci sannan ta taya su suka shirya suka tafi suka kwanta, shi ma ya shiga ɗakinsa ya kwanta yana sauraron lokacin da zai ji motsinta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th Nuwamba 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th Nuwamba 2025

    Fassarar huɗubar Juma’a kai daga Masallaci mai alfarma, ta yau Juma’a 16 Jumadal Ula, 1447 H / 07 November, 2025 M

    Mai Huɗuba:  Sheikh Dr. Abdallah bin Awwad Aljuhani

     Mai Fassara: Dr Abdullahi Yunusa Machina

    Transcribe: Aminu Bashir

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna yaba masa, muna neman taimakonsa, kuma muna neman gafararsa. Kuma muna neman tsarin Allah daga sharrukan kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi, to babu mai ɓatar shi, kuma duk wanda ya batar, to babu mai shiryar da shi.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa. ((Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronsa, kuma kada ku mutu face kuna musulmi)).

    ((Ya ku mutane! Ku ji tsoron Ubangijinku wanda Ya halicce ku daga rai guda ɗaya, kuma Ya halicci matarsa daga gare shi, kuma Ya yaɗa maza da mata masu yawa daga gare su, kuma ku ji tsoron Allah wanda kuke yi wa juna magiya da shi, kuma ku kiyaye yanke zumunta, lallai Allah Ya kasance Mai kula da ku ne)).

    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani! Ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacce take daidai, Zai gyara muku ayyukanku, kuma Ya gafarta muku zunubanku, kuma duk wanda ya yi ɗa’a ga Allah da Manzonsa to haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)).

    Bayan haka: Ina yi muku wasiyya da ni kaina da duk wanda ya ji maganata da jin tsoron Allah Mai girma da ɗaukaka, wanda Ya halicci bayi, kuma zuwa gare shi makoma take, kuma gare shi ake neman dacewa da shiriya, domin jin tsoronsa riba ce, kuma kariya ce daga azabarsa, kuma hanya ce ta samun kusanci zuwa gare Shi.

    Kuma ku kiyayi sauyawar ni’imar Allah gare ku, kuma ku lizimci jama’arku, kuma kada ku kasance ƙungiya ƙungiya, kuma lallai mafi wayo cikin mutane shi ne wanda ya yi wa kansa hisabi, kuma ya yi aiki don abin da ke bayan mutuwa, kuma ya nemi hasken da zai haskaka duhun kabarinsa da shi daga hasken Allah.

    Kuma lallai bawa ya ji tsoron Allah Ya tashe shi makaho ranar ƙiyama alhali ya kasance yana gani a duniya. Kuma ku sani cewa lallai duk wanda Allah yake tare da shi, to ba zai ji tsoron komai ba; kuma duk wanda Allah baya tare da shi, to wa zai yi fatan samun kariya daga gare shi koma bayansa.

    Ya ku taron muminai maza da mata: Lallai daga cikin manyan ni’imomin Allah ga halittunsa akwai cewa Ya shiryar da su kuma ya nusar da su zuwa ga yin imani da Shi, kuma Ya bayyana musu falalar da Ya yi musu, Allah Maɗaukaki ya ce: ((Gori suke maka don sun musulunta?; to ka ce: “Kada ku yi min gorin musuluntarku; a’a, Allah ne ma zai yi muku gori don Ya shiryar da ku zuwa ga imani, idan kun kasance masu gaskiya”)).

    Kuma imani da Allah Maɗaukaki shi ne tabbataccen gaskatawa da ƙudurta cewa lallai Allah shi ne Ubangijin dukkan komai kuma Mamallakinsu, kuma Mahaliccinsu, kuma Mai gudanar da su; da kuma cewa lallai Shi kaɗai ne wanda ya cancanci bauta, kamar Salla da Azumi da addu’a da fata da tsoro da ƙasƙantar da kai da rusunawa, da kuma cewa lallai Shi ne wanda ya siffantu da dukkan siffofin kamala, Wanda Ya tsarkaka daga kowane aibu da tawaya.

    Kuma ku sani – Allah Ya ya muku rahama – cewa lallai imani ba wata magana ce mai daɗi da ake furtawa da baki kawai ba, ko wasu burace-burace ba tare da aiki ba, bari dai, shi ne abin da ya tabbata a cikin zuciya kuma ayyuka suka gaskata shi, kuma shi furuci ne da harshe, da gaskatawa da zuciya, da kuma aiki da gaɓɓai da sassan jiki, yana ƙaruwa da ayyukan ɗa’a kuma yana raguwa da ayyukan saɓo.

    Kuma imani da Allah Maɗaukakin sarki shi ne tushen dukkan rabauta, domin ba a saukar da littattafai ba, kuma ba a aika manzanni ba, face don tabbatar da shi, da kuma dasa shi a cikin zukata, domin shi ne tushe mafi girma kuma rukuni na farko daga cikin rukunan imani guda shida.

    Kuma shi imani kyauta ce daga Allah, kuma ni’ima ce mai girma a rayuwar musulmi, ni’ima ce wacce take tsarkake shekaru, kuma ta sanya albarka a cikin rayuwa, kuma ta bada lamunin samun rabauta a lahira, kuma ta ɗaga darajar ma’abocinta a duniya da lahira, domin a cikinta ne rayuwa ta gaskiya da farin cikin lahira suke.

    Kuma wannan ni’ima babu wanda ya san ta sai wanda ya ɗanɗana ta, kuma babu wanda zai ji daɗinta sai wanda ya rayu a cikinta, kuma shi imani haske ne mai shiryarwa mai haskakawa, Allah yana ba da shi ga wanda Yake so daga cikin bayinsa, kuma Yana hana ta ga wanda Ya ga dama.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Ka ce: “Lallai Allah Yana ɓatar da wanda Ya ga dama, Yana kuma shiryar da wanda ya koma gare Shi)), kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa ya ce: (Duk wanda ya yarda da Allah a matsayin Ubangiji, kuma ya yarda da Musulunci a matsayin addini, kuma ya yarda da Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da alayensa a matsayin Annabi, to lallai ya ɗanɗani daɗin imani). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma imani na gaskiya wanda Allah yake so, shi ne tushen kowane alheri, kuma maɓuɓɓugar ɗaukaka, kuma asalin karama da daraja da jagoranci, ma’abocinsa yana rayuwa cikin ɗaukaka da farin ciki da ƙarfi da tabbata a kan hanyar gaskiya.

    Kuma haƙiƙa Allah Maɗaukaki ya yi wa masu imani da kuma ɗa’a alkawarin samun nasara da kafuwa a doron ƙasa a cikin bayani mai daraja inda Ya ce: ((Wannan bayani ne don mutane, kuma shiriya ce da kuma wa’azi ga masu taƙawa. Kuma kada ku yi rauni, kada kuma ku yi baƙin ciki, kuma ku ne mafiya ɗaukaka in dai har kun kasance muminai Idan ma wani miki ne ya same ku a jiki, to haƙiƙa miki irinsa ya samu mutanen Makka.

    Kuma waɗannan kwanaki ne da muke jujjuya su tsakanin mutane domin Allah Ya bayyanar da waɗanda suka yi imani, kuma Ya riƙi shahidai a cikinku. Allah kuwa ba Ya son azzalumai Kuma don Allah Ya tace waɗanda suka yi imani, kuma don Ya halakar da kafirai.))

    Kuma masu imani suna farin ciki da jiɓantar Allah Maɗaukaki a gare su, kuma suna ni’imtuwa da daddaɗar rayuwa, kuma Allah yana son su, kuma muminai ma suna son su, kuma Allah Maɗaukakin sarki yana basu kariya, kuma suna da albishir a rayuwar duniya da lahira, kuma imani na daga cikin mafi girman abababen da ke sanyaya musu zuciya yayin masifu, Allah Maɗaukaki ya ce: ((Ba wata musiba da za ta samu sai da izinin Allah. Duk kuwa wanda ya yi imani da Allah zai shiryi zuciyarsa. Allah kuma Masanin komai ne)).

    Kuma su ne ma’abota tsaro da kwanciyar hankali, kuma suna gaggawar zuwa ga imaninsu, kuma suna samun ƙarfi da shi cikin duk abin da ya same su na alheri ko na sharri, na ɗa’a ko na saɓo, na sauƙi ko na wahala. Kuma suna amfana da wa’azi da tunatarwa, kuma suna cikin kulawar Allah Maɗaukaki.

    Kuma imaninsu yana kare su daga faɗawa cikin alfasha, kuma da hasken imaninsu suke bambance tsakanin gaskiya da ƙarya, da shiriya da ɓata, da kuma bidi’a da sunna.
    Kuma haƙiƙa Allah Maɗaukaki ya yi musu alkawarin samun nasara da kafuwa, kuma su ne ma’abota buwaya da ɗaukaka, Allah Maɗaukaki Ya ce: ((kuma taimakon muminai ya zama haƙƙi ne a kanmu)).

    Kuma Mala’ikun da suke ɗauke da Al’arshin Allah Mai rahama suna nema musu gafara, kuma Allah Maɗaukaki yana shiryar da su da imaninsu zuwa hanya madaidaiciya.
    Kuma Allah Maɗaukaki yana musu albishir da samun aminci da farin ciki a duniya da lahira, da kuma dawwamammiyar ni’ima a lahira.

    Allah Maɗaukaki Ya ce: ((Lalle waɗanda suka ce: “Allah ne Ubangijinmu”, sannan suka tabbata, to mala’iku za su sauko musu lokacin mutuwa suna cewa: “Kada ku tsorata, kuma kada ku yi baƙin ciki, kuma ku yi farin ciki da Aljanna wadda kuka kasance ana yi muku alƙawarinta “Mu masoyanku ne a rayuwar duniya da kuma ta lahira; kuma a cikinta za ku samu duk abin da rayukanku suke marmari, za kuma ku samu duk abin da kuke nema a cikinta“Liyafa ce daga Allah Mai gafara, Mai jin ƙai”)).

    Bayan haka, ya ku muminai: Haƙiƙa hikimar Allah Maɗaukaki ta hukunta cewa Ya sanya wannan al’umma ta zamo mafi alherin ul’umma wacce aka fitar ga mutane, tana umarni da kyakkyawan aiki, kuma tana hana mummuna, kuma tana imani da Allah.
    Kuma Allah tsarki ya tabbata a gare Shi Ya umurce su da yin ayyuka nagari inda Ya ce: ((Kuma ku aikata ayyuka nagari, lallai Ni Masanina abin da kuke aikatawa ne)).

    ma’abocinsa dukkan alheri a duniya da lahira, kuma shi garkuwa ne da bawa yake kare kanshi daga sha’awace-sha’awace da shubuhohi da manyan fitintinu da shi, kuma shi waraka ne ga zukata.

    Wanda duk lokacin da mutum ya gafala daga barin shi saboda kwaɗayin wani abin duniya mai ƙarewa, sai rayuwarshi ta ƙuntata, kuma zuciyarshi ta kamu da jinya, kuma lallai idan ka dubi dayawa daga cikin koke-koke da damuwowi da baƙin ciki da tsoro da taɓarɓarewar al’amura a rayuwar mutane, za ka ga alamomin nisantar imani da Allah Mai girma da ɗaukaka da bijire wa addininsa da shari’arsa a cikinsu.

    A’uzu billahi minash-shaiɗanir-rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim: ((Waɗanda suka yi aiki nagari, na miji ne ko mace, alhalin suna muminai, to tabbas za mu raya su rayuwa mai daɗi, kuma tabbas za mu saka musu ladansu da mafi kyawun abin da suka kasance suna aikatawa)).

    Allah Ya amfanar da mu da Alƙur’ani mai girma, da shiriyar shugaban Manzanni, ina faɗi abin da kuka saurara, kuma ina nema mana gafar Allah, da sauran musulmi daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafarsa, lallai shi Mai yawan gafara ne Mai jin ƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah bisa kyautarsa da kyautatawarsa, kuma godiya ta tabbata gare shi bisa falalarsa da ni’imominsa, kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci ga bawanka kuma Manzonka Muhammadu da alayensa da sahabbansa.

    Bayan haka:

    Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku tabbatar da imaninku da Ubangijinku, kuma ku sani cewa lallai Imani da Allah Mai girma da ɗaukaka yana sanya yarda da Allah Mai grima da ɗaukaka a zuciyar mumini a kowane hali, kuma yardar bawa ga Mahaliccinsa shi ne farkon sababi daga cikin sabuban natsuwar zuciya, wacce ita ce asalin rabauta, domin da yardar mutum da kansa da abin da Allah Ya ƙaddara masa ne zai samu natsuwa a kan hali da yake ciki yanzu, da kuma yaƙininsa da lahira da sakamako na adalci ne zai samu natsuwa game da gobenshi.

    Ma’anar haka, shi ne cewa lallai mumini ba ya cizon yatsa a kan abin da ya shuɗe ta hanyar kuka ko baƙin ciki, kuma ba ya rayuwa cikin baƙin ciki a kan yanayi da yake ciki, kuma ba ya fuskantar gobe da tsoro, saboda a cikin addininsa akwai makamai da zai yi dogaro da su wurin dogewa a kan gwagwarmayar rayuwa, kuma ya fuskanci masifunta da raɗaɗinta da bala’o’inta da su.

    Saboda haka, ahir ɗinka kuma ahir ɗinka da rabuwa da yarda da Ubangijinka ko da daidai da ƙiftawar ido ne, sai darajarka ta faɗi a wurinsa, saboda akwai ƙarfin rai da yarda da shi, da natsuwar zuciya a cikin ƙulla alaƙa da Allah, Allah Maɗaukaki Yana faɗi a cikin littafinsa mai girma: ((Ya ku waɗanda kuka yi imani ku nemi taimako ta hanyar haƙuri da salla. Lallai Allah Yana tare da masu haƙuri)).

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan wani abu ya tsananta a gare shi, sai ya garzaya zuwa ga salla, kuma sallarsa ba ta kasance wani abu na al’ada ne kawai da yake yi ba, bari dai, ta kasance kaiwa maƙura ne wurin ganawa da Allah, har ma ya kasance idan lokacinta ya yi sai ya ce wa sahabinsa Bilal Allah Ya ƙara masa yarda: (Ka hutar da mu da salla), wato ita wannan salla ya ku muminai tana ɗauke da makullan rayuwa da wani sashi na hanyoyin rayuwa cikin nutsuwa, don haka, ku dogara da ita saboda ku rabauta.

    Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye shi, kuma ku ɗau izina daga waɗanda suka shuɗe gabaninku, kuma ku sani cewa lallai babu makawa sai kun haɗu da Ubangijinku kuma zai muku sakamako a kan ayyukanku ƙananansu da manyansu sai dai abin da Allah Ya gafarta shi, lallai Shi Mai gafara ne Mai jin ƙai, saboda haka, ku kula da kawunanku, ku kula da kawunanku, kuma ku nemi taimakon Allah, kuma ba mu da wata dabara ko ƙarfi face da Allah.

    ((Lallai Allah da Mala’ikunsa suna salati ga Annabi. Ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)). Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammadu da alayen Annabi Muhammadu, kamar yadda Ka yi salati ga Annabi Ibarahim da alayen Annabi Ibrahim, Lallai Kai Sha yabo ne Mai girma, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammadu da alayen Annabi Muhammadu, kamar yadda Ka yi albarka ga Annabi Ibrahim da alayen Annabi Ibrahim, lallai Kai Sha yabo ne Mai girma.

    Ya ku bayin Allah, ku Yawaita salati da sallama ga mafakar halittu a matsaya mai girma ranar alƙiyama, Annabinmu kuma mai cetonmu Annabi Muhammadu tsira da maincin Allah su tabbata a gare shi, kuma Ka masa sallama mai yawa.

    Kuma ya Allah Ka ƙara yarda da halifofi huɗu shiryayyu da sauran sahabbai gaba ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako, ya Allah Ka amfanar da mu da son da muke musu, kuma ya Allah Ka tashe mu a cikin tawagarsu, kuma kada Ka kautar da mu daga bin sunnarsu da tafarkinsu, ya Mafi karamcin masu karamci.

    Ya Allah Ka ƙarfafi Musulunci da musulmai, kuma Ka ɗaukaka kalmar gaskiya da addini da falalarka, ya Allah Ka taimaki shugabanmu kuma majiɓincin lamuranmu hadimin Masallatai biyu masu alfarma da gaskiya da dace da daidai, kuma Ka datar da shi ga abin da Kake so kuma Ka yarda da shi, kuma Ka yi riƙo da hannunsa zuwa ga ayyukan nagarta da taƙawa.

    Ka azurta shi da mashawarta nagartattu, Ka ɗaukaka addininka da kalmarka da shi, kuma ka sanya shi ya taimaki musulunci da musulmai, kuma ka haɗa kan musulmai bisa gaskiya da shiriya ta dalilinsa ya Ubangijin talikai, ya Allah Ka datar da shi da magajinshi da ‘yan’uwansa da mataimakansa zuwa ga gaskiya da shiriya, da dukkan abin da gyara ne ga bayi da ƙasa.

    Ya Allah Ka datar da shugabannin musulmai zuwa ga aiki da littafinka da sunnar Annabinka Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, Ka sanya su su zama rahama ga bayinka muminai, kuma ya Allah Ka haɗa kawunansu a kan gaskiya ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka ƙarfafa kariyarka ga ƙasarmu da dukkan ƙasashen musulmi, kuma ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da masu dako a kan fagage da iyakoki, kuma Ka zama Mai taimako da kawo ɗauki da agazawa da ba da nasarar a gare su.

    Ya Allah lallai muna tawassuli da yardarka, Ka tsare mu daga fushinka, kuma muna tawassuli da amincinka, Ka tsare mu daga azabarka, kuma muna neman tsarinka daga damƙarka, ba za mu iya ƙididdige yabo a gare Ka ba, Kana nan kamar yadda Ka yabi kanka.

    Ya Allah kada Ka mana uƙuba da munanan ayyukanmu, kuma kada Ka kama mu da abin da wawayen cikinmu suka aikata, kuma Ka isar mana a kan dukkan wani lamari da yake damun mu, kuma Ka zama mai taimako da ba da nasarar gare mu. Ya Allah Ka taimaki addininka, da littafinka, da sunnar Annabinka tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a kowane waje, ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah lallai muna neman gafararka, lallai Kai Ka kasance Mai yawan gafara ne, Ka sauko mana da ruwan sama mai yawa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah Ka saukar mana da ruwa, ya Allah lallai mu halittu ne daga cikin halittunka, kada Ka hana mana falalarka saboda zunubanmu.

    Ya Allah Ka gafarta mana, da iyayenmu, da dukkan musulmai maza da mata, da muminai maza da mata, rayayyu daga cikinsu da mamata. Ya Allah Ka karɓa daga gare mu, lallai Kai Mai ji ne kuma Masani, kuma Ka karɓi tubanmu, lallai Kai Mai yawan karɓar tuba ne Mai jin ƙai.

    Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buwaya daga abin da suke siffanta shi da shi, kuma aminci ya tabbata ga Manzanni, kuma dukkan yabo ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Kira A Kan Haɗin Kai

    Kira A Kan Haɗin Kai

    ‘Yan Najeriya muna cikin wani muhimmi lokaci. Wata mummunar fahimta tana shiga cikin al’ummarmu, tyana canza yadda muke kallon ‘yan-uwanmu da kuma rage darajar kanmu da ƙaunar ‘ƴan’uwanta da ta kasance tana bayyana mu.

    Dole mu dakata mu yi wa kanmu wata muhimmiyar tambaya: a cikin rayuwarmu ta yau da kullum don neman abinci da ci gaba, shin mun taɓa tunanin addinin manomi wanda ya noma shinkafar da muke ci? Shin muna tambayar addinin likitan da ya rubuta maganin da ya ceci rayuwarmu? Idan muka buɗe famfo, shin muna tunanin ko injiniyan da ya tsara tsarin ruwan yana da aƙidarmu?

    Amsar ba ta da shakku, ’A a’. Ba mu yi haka ba. Muna saye, muna ci, kuma muna rayuwa, muna dogaro ga juna a cikin hanyar da ba a iya rabuwa. Rayuwarmu ta yau da kullum shaida ce mai ƙarfi game da haɗin kanmu.

    To, me yasa, a wasu fannonin rayuwa, muka ƙyale a raba mu? Me yasa muke tallata bambance-bambancen addini alhali kuwa tarihinmu na gaba ɗaya ya faɗi wani labari daban?

    Mun yi yaƙi don ‘yancin kanmu tare, a matsayin mutane ɗaya tare da manufa guda. Mun zauna tare a cikin ajujuwa, muna koyo daga malamai ɗaya, muna mafarkin makoma guda ga Najeriya. Muna ciniki tare, muna murna tare, muna makoki tare.

    Wannan rarrabuwa ba hanya ba ce ta Najeriya. Guba ce da ke raunana mu da kuma hana mu ci gaba. Duk gidan da ya rabu da kansa ba zai iya tsayawa ba, balle ya ci nasara a rayuwa.

    Hanyar Ci Gaba: Komawa ga Ƙimar Mu Na Gaba ɗaya

    Don maido da girmanmu, dole ne mu zaɓi haɗin kai da juna. Ga yadda za mu iya farawa:

    1.  Yi Bikin Asalin Mu Guda: Ganin kanmu a matsayin ‘yan Najeriya—’yan’uwa maza da mata na al’umma ɗaya. Imaminmu wani ɓangare ne na asalinmu, ba makami da za a yi amfani da shi a kan maƙwabci ba.

    2.  Ƙarfafa Tattaunawa: Ƙarfafa tattaunawar addini a cikin al’ummominmu. Bari shugabannin mu na addini su yi wa’azin soyayya da haƙuri. Lokacin da muka yi hira, muna rushe ganuwar tsoro da rashin fahimta.

    3.  Mai da hankali kan Manufofi Guda: Talauci, jahilci, da rashin ingantaccen tsaro wannan ba sa bambanta tsakanin Musulmi da Kirista. Waɗannan su ne abokan gabanmu. Kamata ya yi mu karkatar da ƙoƙarinmu don yaƙar waɗannan, maimakon yaƙi da juna. Ci gabanmu gaba ɗaya ya dogara da ƙoƙarinmu gaba ɗaya.

    4.  Maido da Maganar Mu: Dole ne mu ƙi maganganun da ke neman raba mu. A shafukan sada zumunta da kuma a cikin al’ummominmu, mu zama jakadun zaman lafiya, muna raba labarun haɗin kai da abota waɗanda suka fi yawan labarun rikici.

    Najeriya ƙasa ce mai girma, mai albarka da ɗimbin albarkatun ɗan adam da na halitta. Ƙarfinmu yana cikin hadin kai. Kada mu ƙyale rashin fahimta ya canza mana tunani. Muna buƙatar juna don rayuwa da ci gaba.

    Mu zaɓi hanyar ‘yan-uwanta. Mu zaɓi hanyar haɗin kai. Mu zaɓi hanyar Najeriya ɗaya.
    A Haɗe Muke Da Ƙarfi, A Rabe Muke Da Rauni.

    Karanta Yaushe Ne Kwanakin Layya Suke Ƙarewa?

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Uku

    Ba a daɗe da sallacewa ba kuma aka buɗe gari, a hankali kowa ya koma harkokinsa. Ranar Lahadi da daddare bayan yara sun yi bacci; suna zaune a parlor shi yana kallon ball a TV yayin da ita kuma take chatting a waya; ta ɗago daga kallon wayar ta dube shi tace ‘Babe gobe fa za a koma makaranta.’

    Ba tare da ya ɗauke kai daga kallon TV din ba yace ‘Kin gaya min fa tun last week, kuma na siyo duk wani abu da ake buƙata. Ta gyara zama ta ajiye wayar tace ‘Ni ma zan shiga school ɗin na gano, wata ƙila an kafe timetable, amma sai wajen goma zan fita.’
    ‘Ok, to za ki dawo kafin 12:30pm kenan ko? Saboda ɗauko ‘yan makaranta tunda ni kin ga ina office.’

    ‘Eh, zan yi ƙoƙari na dawo kuma idan ban dawo ba ma kafin na fita zan je da Rashida ta ga makarantar tasu idan lokaci ya yi ban dawo ba sai ta je ta ɗauko Nasreen. Ya gyara zama ya kalle ta kamar a firgice ‘Wai wannan yarinyar ce za ta dinga ɗauko yaran daga
    makaranta kuma ta zauna ta zauna da su a gidan ita kaɗai?’

    Cikin halin ko in kula tace ‘To ya za a yi, ai ka ga dai ni ma dole na je makaranta ko? They will be fine fa, yarinyar tana da hankali sannan kuma ka ga ga Afaf tana nan idan ta dawo. Su ma ita da Habib na gaya musu idan an tashi daga makaranta su taho tunda na ga ko ni ce ma na je ɗauko su idan muka rasa napep a ƙasa muke tahowa.’

    Ya ƙare mata kallo sanna yace ‘Wai me kike faɗa ne? Su Afaf ɗin ne kike so su dinga tahowa daga makarantar su kaɗai kuma a ƙas, sannan har da Nasreen? Wadda sai an tashe ta da minti talatin sannan a tashe su? To babe ya za mu yi? Ai ka ga dai kamar Afaf ba shi da wani amfani a ce sai Rashida ta je sannan za su taho tare ko?

    Ni kuma duk lokacin da ta kama ina gidan zan je na ɗauko su. Suka yi shiru na ɗan lokaci kowa da abinda yake tunani. Jimawa kaɗan yace ‘Ni barin wannan yarinyar taki ma a gidan ita kaɗai gaskiya bai yi min ba, ya za a yi duk mu fice a barta ita kaɗai kuma a bar mata mukullin gidan? Ai idan muka dawo sai abinda muka gani kenan, za ma ta iya fara shigo da maza gidan ko a yi mata wayo a yi mana ɓarna idan aka gane ita kaɗai ake bari a gidan.’

    ‘To yanzu ya kake so a yi? Ka ga dai da ni da yaran ai dole duk mu je makaranta ko?’
    ‘Ni ma ban sani ba, kece za ki san yanda za ki yi. Za ki ma iya fita da ita ki rufe gidan in ya so sai ku dawo tare ki ɗauko yaran, duk yanda dai kuka yi. Amma dai gaskiya wannan tsarin na barinta a gidan bai yi min ba.’

    Ranta ya fara ɓaci; me yake nufi ne? So yake yace ta bar makarantarta kawai saboda ta zauna masa da yara ko kuwa mai aikin yake so ya korar mata? Wannan bayanin da yake yi ma sam ba zai yiwu ba gara dai ya sake lissafi ko kuma shi ya dinga baro office yana zuwa yana ɗauko su.

    Tace ‘Uhm, to ai ka ga ba ni nake rubutawa kaina timetable ba, wani malamin ma sai 1pm yake fara lecture kuma dole na yi attending idan dai ina son na gama degree ɗin. Sai dai ko ka kawo wata dabarar da kai kake ganin za a yi da ɗauko su in ya so ita Rashida idan zan fita sai na fita da ita duk lokacin da na gama lecture sai mu dawo tare.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ya tashi ya jefar da remote ɗin TV ɗin da yake hannunsa ya shige ɗaki. Ta bi bayansa da kallo tana mamaki; wai me mutumin nan yake nufi ne? Shikenan sai ta jingine rayuwarta ta zauna ta kular masa da yara? To ai ita ko ‘yayan da ta haifa ma haka ko tana so ko ba ta so za ta dinga barinsu da mai aikin ta tafi makaranta tunda dai haka ta ga masu yaran suna yi.

    Ko kuwa da yake ta auri tuburarre haƙura za ta yi da komai ta zauna sai yanda suka yi da ita? Haka suka kwana a wannan daren kowa da abinda yake ransa. Ko da gari ya waye tun asuba ta tashi ita da Rashida wadda ta taya ta nan da nan suka shirya
    yara sannan suka haɗawa kowa abinci.

    Kamar yanda ya saba sai ƙarfe bakwai da kwata sannan ya fito, zuwa lokacin sun shirya suna jiransa; ya kwashe su ya kai su ya dawo. Sai wajen ƙarfe tara da rabi sannan ya gama shirinsa, lokacin fitowarta kenan daga wanka saboda sai da ta tsaya ta gama abincin rana ta juye a flask sannan ta fara shirin. Ya same ta a ɗaki tana shafa mai riƙe da mukullin motarsa, yana daga tsaye a bakin kofa yace ‘Ni na fita.’

    Ta juyo da sauri tana cewa ‘La! Babe don Allah bari na yi sauri na saka kayana sai ka ba ni lift. No ba ta hanyarku zan bi ba, ki wuce kawai sai na dawo. Kada ki manta min da yara.’ Ya faɗa yana ficewa daga ɗakin. Ta bi bayansa da kallo da baki buɗe; lallai ma mutumin nan.

    Ƙiri-ƙiri dai shi baya son ya ɗauke ta a motarsa idan dai makaranta za ta, in banda haka ai ko ba hanyar makarantarsu zai bi ba ya sauke ta a bakin titi ya rage mata tafiya. Ta juya ta cigaba da shiryawa cikin sanyin jiki tana tunanin son kai irin na Mustapha. Allah ya so ta ma Baffa magana ya tura mata kuɗi kuma ya sanar da ita duk wata zai dinga turo mata kuɗi saboda karatunta, idan tana son wani abu sai ta yi masa magana.

    Tabbas ta san da a ce da Mustapha ta dogara da sai dai ta haƙura da karatunta ta zauna ta kular masa da yara. Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta fito ta sallami Rashida wadda ta bar su tare da Shukra bayan ta yi mata duk wani bayani da take buƙata sannan ta kama hanya zuciyarta cike da damuwa da wasi-wasi.

    Kafin sha biyu ta gama duk wani abu da take yi a makarantar sai dai ba ta son ta dawo ta ɗauko yara; ba wai yaran ne ba ta son ɗaukowa ba amma ba ta son ta ɗauko su Mustapha ya ga kamar faɗansa ne ya sa don haka duk lokacin da za ta fita ya za ta zai yi mata faɗa ta dauko masa yara.

    Don haka suka nemi inuwa ita da ƙawayenta suka zauna suna hira, sai wajen 1;30pm sannan suka ƙarasa masallaci suka yi sallah kowacce ta kama hanyara gida. Ko da ta zo gida ba ta tarar da wata matsala ba, Rashida ta kai Shukra gidan su Ummi ta ɗauko
    Nasreen daga makarantar kamar yanda ta ba ta umarni. Su kuma Afaf da Habib kusan tare da ita suka shiga gidan.

    Ko da ya dawo tana jin sa yana tambayar yaran wanda ya ɗaukosu daga makaranta suna ba shi amsa, musamman Shukra wadda yake ta tambayarta me suka yi ita da Rashida a gidan bayan Anti ta fita. Haka ta yi banza da shi ta cigaba da harkokinta.

    Haka suka cigaba da yi, sai ya zama kuma da yake ba a fara lecture sosai ba sati biyun farko kullum Khadeeja ba ta fita da wuri sanna kuma tana dawowa kafin ya dawo gidan, don haka matsalarsu da sauƙi tunda zai zo ya tarar da ita tana ta hidimar yara.

    Sati ɗaya da komawa aka kafe wa su Khadeeja timtable, kuma da yake babu lokaci sosai timetable ɗin a matse take. Haka dai suka cigaba da karatun. Ranar Alhamis shi ne take da lecture 8am to 6pm, don haka ta san dole ta shirya ta fita tare da yara. Tun dare ta gama komai, ta yi rabin aikin abincin safe sannan ta fitowa da kowa kayansa.

    Ta yi wa Rashida duk wani bayani da take buƙata tunda yaran idan sun dawo daga makarantar boko babu islamiyya don haka nan za su wuni a gidan. Tun kafin asuba ta tashi suka fara aiki tare da Rashida. Bayan Mustapha ya dawo daga masallaci
    sallar asuba ya same ta a kitchen, tana ta fama kai wa da kawowa tsakanin dankalin da take soyawa da kuma haɗawa yara abincin makarantarsu a lunch box.

    Bayan ya amsa sannu da zuwanta yace ‘Wai kin yi sallah kuwa? Na ga kamar a nan na bar ki fa. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, na yi sallah mana. Sauri nake na gama saboda yau 8am to 6pm ne da ni kuma 8am din nan idan Prof. ya riga ni shiga aji rufe min ƙofa zai yi wallahi shi yasa nake ta sauri don kullum sai ya yi attendance.’

    ‘Oh kenan yau sai 6pm za ki dawo gidan? Eh.’ Ta amsa a gajarce tana kwashe dankalin da ya riga ya soyu. Ya ƙara haɗe girar sama da ƙasa sanna yace ‘To a ina za ki bar yara wuni guda? Ba ta son hayaniyarsa don ba ta son abinda zai ɓata mata rai, ba tare da ta bar abinda take yi ba tace ‘A nan mana gidansu; Rashida za ta ɗauko Nasreen su kuma su Afaf idan suka dawo za su same ta a gidan sai su yi zamansu kafin na dawo, they will be just fine.’

    ‘Haba ai daɗewar ta yi yawa, kenan haka za su zauna su yi duk abinda suka ga dama ba tare da wata kulawa ba.’ Ya faɗa a fusace. ‘Kada ka damu Rashida za ta kula da su.’
    Kafin ya ba ta amsa suka jiyo ihun Nasreen daga ɗakinsu tana cewa ‘Wayyo Anti.’
    Ta riga ta san rigimar Nasreen, idan dai aka tashe ta da sassafe zuwa makaranta sai ta yi kuka ko ma waye ya tashe ta, shi ma kuma ya san da haka.

    Amma ba tare da ɓata lokaci ba ya nufi ɗakin da sauri. Ganin haka ita ma Khadeejan ta ajiye abinda take yi ta bi bayansa, kusan a lokaci ɗaya suka shiga ɗakin. Nasreen tana zaune a kan gadonsu da hawaye shaɓe-shaɓe a idonta yayin da Rashida take tsugune a gaban gadon tana riƙe da towel. Me aka yi miki kike kuka Nasreen?’ Ya tambaya kafin ya karasa shiga ɗakin.

    Khadeeja tana shiga ɗakin ta sauko daga kan gadon ta rungume ta tana cewa ‘Anteee.’
    Ya shafa kanta ‘Me aka yi miki? Cikin shagwaɓa tace ‘Rasheeda ce. ”Ya juya ya dubi Rashidan a fusace yace ‘Me kika yi mata? Nan da nan jikinta ya hau rawa tana gyara tsuguno, kafin ta yi magana Khadeeja ta shafa kan Nasreen tace ‘Nas me Rashida ta yi miki?’

    ‘Tashi na ta yi daga barci. To ai kin ga shirya ki za ta yi ki tafi school ko? Ko kina son ki makara Uncle ya koro ki gida ne? Ya yi tsaki ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake cewa komai ba. Ta lallaɓa Nasreen ta tura ta banɗaki sannan ta juyo za ta fito, kafin ta fito ta jiyo shi yana dawowa ɗakin yana cewa ‘Dankalin da kika bari a wuta ya kone, ki je ki duba na kashe miki wutar.’

    Ta wuce shi ta ƙarasa kitchen ɗin da gudu inda ta sami dankalin ya ƙone, ta kwashe sannan ta sake kunna wutar ta ɗora. Ya ƙaraso ya tsaya a kofar kitchen ɗin, ya ɗan ɗauki lokaci yana kallonta tana zubawa yara abincin rana wanda ta sauke a babban flask. Jimawa kaɗan yace ‘Kin ga irin abinda yasa bana son ki bar su da yarinyar nan ita kaɗai ko?

    Ya za a yi ta iya kula da yara tunda ga shi nan ba ta ma iya tashinsu daga bacci ba?’
    Ta kalle shi cike da mamaki tace ‘Nasreen ce fa, ko kai ne ma ka tashe ta sai ta yi rigima, ko ka manta ne? Kuma kai ne ka ce ba ka son Rashida ta dinga yi maka girki kuma ka ga dole abu ɗaya zan yi a lokaci guda ba zai yiwu ina girka muku abinci ba kuma ina shirya yara.’

    Ya juya ya fice ba tare da ya ce komai ba. Ta ja tsaki ta share ƙwallar da ta taru a gefen idonta sannan ta cigaba da aiki. Ba ta ma san me take ji ba, ƙoƙari kawai take ta fita daga gidan idan ta je makaranta ta samu ta yi tunani ta fahimci me take ji. Bayan ta gama abinci ta wuce ɗaki ta same shi bayan ta zubawa yara abinci suna ci.

    Yana kwance a gefen gado yana fama latsa waya ta wuce har ta kusa shiga wankan yace ‘Idan na kai yara dawowa zan yi kin sani, sai wajen 10am zan fita, ita wannan yarinyar taki haka za ki bar min ita a gidan daga ni sai ita? Cikin halin ko in kula tace ‘Eh, ita da Shukra za su zauna idan za ka fita kawai ka gaya mata don ta san cewa ka fita ta cigaba da aikinta.’

    Har za ta shige banɗakin yace ‘Gaskiya ba na so, kuma ke ma kin san bai dace ba ki bar ni a gida daga ni sai mai aikinki mace. Irin haka ne kuma idan an ce za a auri mai aikin ku ce ba ku yarda ba. Duk ɓacin ran da take ciki sai da ya ba ta dariya, duk da dai dariyar takaici ce tace ‘to ai ga ka nan ga ta nan ka aure ta mana, ai ita ma mace ce.’

    ‘Ni dai na gaya miki bana son ki bar ta a gidan idan ina nan tunda ke ba kya nan, ki sami inda za ki ajiye ta idan na fita sai ta dawo gidan. ‘Uhhm!’ Ta amsa sannan ta shige wankan cike da takaicinsa, har ji take kamar zuciyarta tana turiri. Zuwa makaranta lecture kawai ya zama wata drama.

    Nan da nan ta ƙarasa shiryawa ta shirya yaran, ta haɗa tea ta zauna tana sha. A haka Mustafa ya fito ya same su lokacin 7:15am. ‘Ku tashi mu je.’ Ya faɗawa yaran.
    Ta miƙe riƙe da kofin shayinta tace ‘Bari na ɗauko hijab dina na saka ku rage min hanya.’
    ‘A a za ki makarar da mu ne fa, ga shi ko shayi ba ki gama sha ba kuma kin san idan suka makara koro su za a yi.

    Ya juaya ga yaran wadanda sun riga sun miƙe kowa da kayansa a hannu yace ‘Mu je.’
    ‘Anti sai mun dawo.’ Suka faɗa sannan suka juya suka fice ya bi bayansu. Ta bi bayansa da kallo cike da mamaki; ta kasa gane motarsa ce ba ya son ta dinga shiga ko kuwa tsabar baƙin ciki ne a kan za ta fita yake hana shi rage mata hanya.

    To amma kuma yana kai ta unguwa, kodayake wannan fita ce da shi ya ga dama kuma kusan duk inda za ta tunda ta aure shi tare yake kai ta da yaran suna biye da ita. To me yasa idan dai makaranta za ta tafi sai ya san yanda ya yi ya tafi ya bar ta ba tare da ya ko da rage mata hanya ba?

    Haka har ta gama shirinta ba tare da ta samo amsar tambayarta ba; ta fito ta sami Rashida a kitchen tace ‘Idan babansu ya dawo ki koma ɗaki ki zauna in ya fita sai ki fito ki cigaba da aikin; idan Shukra ta zauna a wajensa shikenan idan kuma ta taho wajenki to don Allah kada ki bari ta yi kuka ya ji.’

    Ta yi mata sallama ta fice tana sauri saboda 7:20am ta riga ta yi kuma ba ta da tabbas ɗin za ta iya kai wa BUK kafin 8:00am. Ta kusa isa titi Mustapha ya karyo kwana ya shigo layin, ta ɗauke kanta daga kallon inda yake; ba ta sani ba ko ya ganta ko bai ganta ba.

    Ta ƙarasa titi cikin sanyin jiki ta hau Napep tambayoyi daban-daban suna ta yawo a kanta; wai ina babe ɗinta ne? Wanda yake son ta? Wanda kafin aurensu har so yake ya ɗauko ta daga makaranta ya kai ta unguwa ko ya kai ta gida don dai tana hana shi ne saboda ta san Baffa ba zai bari ba a lokacin. To shikenan soyayya ta ƙare ko me
    Mustapha yake nufi da ita? Shekara ɗaya fa kenan da ‘yan watanni da aurensu.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Biyu

    Ranar Sallah yana tashi ruwan shayi kawai ya sha ya shirya ya fice; bayan an idar da sallar idi kai tsaye gidan Mama ya wuce wajen yaransa. Yana gamawa da su ya wuce gidan Mommy wajen Khadeej; ko da dai ya ji haushin yanda ta yi zamanta a gidansu ta ƙi dawowa amma ya san ya yi kewarta.

    Duk wani haushi nata da yake ji ya riga ya huce, abu ɗaya yake so a yanzu shi ne ta dawo gida ya samu ya daina fama yawo shi da yaransa sai kace wasu waɗanda ba su da gata. Ya kalli kayan sallarta waɗanda ya taho da su ya kai mata ko za ta ƙara, ya kau da kai ya cigaba da tuƙinsa.

    Shi ya ga ma kamar ba ta damu da kayan sallar ba tunda da ita aka kai ɗinkin amma da yake ta so ta yi sallah a gida ko bi ta kansu ba ta yi ba sai ma ce masa da ta yi Baffa ya yi mata kayan sallah. Haka dai ya yi ta tunani kala-kala har ya ƙarasa gidansu Khadeeja.

    Lafiya ƙalau suka gaisa cikin mutunci kamar babu wanda yake jin haushin wani a tsakaninsu; ya shiga ya gaida Mommy sannan ya gaida Baffa. Suka dawo ita da shi suka zauna a parlor ɗin baƙi inda ba tare da ɓata lokaci ba ta kawo masa tuwon sallah da lafiyayyen zobo mai sanyi. Suka zauna yana ci tana yi masa hira.

    Bayan ya gama ya huta ya yi wa Baffa sallama inda Baffan ya sanar da shi jibi ya zo ya ɗauki matarsa. Suka fito tare da Khadeejan ta rako shi bakin mota. Tana tsaye riƙe da murfin kofar motar yayin da shi kuma yake zaune a kujerar direba ya juya kujerar baya ya ɗauko ledar da take ajiye a kan kujerar ya miƙa mata yana cewa ‘Ga kayan sallarki duk da na ga ba ki damu da su ba.’

    Ta yi ‘yar dariya tana tura masa ledar tace ‘Ka koma da su ka ajiye min a ɗakina tunda jibi zan dawo. Shi ma dariyar ya yi yana mayar da kayan yana cewa ‘Ko dubawa ma fa ba ki yi ba. Haba kayan da na riga na sansu, idan na dawo zan duba sannan na yi kwalliyar sallah ta.’

    Cike da farin ciki da walwala suka yi sallama sannan ya wuce gidan Hajia. Yana shiga gidan ya tarar da Hajia a parlor ɗinta suna hira ita da Yaya Jidda, yaranta kuma suna ta kai wa da kawowa a tsakar gidan. Bayan ya gaida Hajia ya yi mata barka da sallah ya juya suka gaisa da Yaya Jidda wadda take ta faman shan kunu tana basarwa saboda kar ya yi mata wata magana.

    Bayan sun gaisa sun ɗan taɓa hira da hajia ya dubi Yaya Jiddan yace ‘Yaya bari na ba ki account number ki turo min 10k ɗin da na tura miki ta yi wa yara sayayyar kayan shayi; tunda sun ce min ba a saya ba ko? Ta sake haɗe girar sama da ƙasa ta kalli hajia sanna ta kalle shi tace ‘Ban gane ba a siya ba, an siya mana.

    Kawai dai ba ranar da ka bayar ba don kafin ka turo kuɗin masu kantunan sun rufe. Shi yasa ba a samu an saya ba har sai ranar da aka sake buɗe gari, ranar da ka zo kenan ka kwashe su. Da safen da ka tafi da su ai da sun zo za su tarar da kayan komai an saya don har ciko ma nayi.’

    Hajia tace ‘Ai kuwa ka ga babu maganar dawo da kuɗi tunda an sayi kaya.’Takaici ya kama shi don ko ɗaya bai yarda da wannan zancen nata ba, ya kawar da kai sannan ya sake dubanta yace ‘Haka ne, to shi kenan, sai a ɗauko min ragowar na tafi da su tunda jibi yaran za su dawo har Khadeejan kuma ko suga babu a gidan sai na sake siya.

    Ki aika a ɗauko min su tunda kusan ma ba a yi amfani da su ba kenan tunda ranar da aka siyo ranar suka tafi. Kafin ta yi magana Hajia tace ‘To su sauran yaran gidan ba ‘yayanka ba ne da ba za a ba su ba, kayan shayin kawai ba wani abu.’ Ta dubi Jiddan tace ‘Ko da yake bari na barku wataƙila suna nan ki ba shi ya kai gidan nasa.’

    Ta sake kicin kicin sannan tace ‘Hajia kema dai kin san yaran nan ba za su bari ga kayan shayin har da Indomie su bari na ajiye ba tare da na ba su ba. Sai dai kawai idan biyansa zan yi na yi wa babansu waya ya biya abinda ‘yayansa suka ci tunda yana kallo suna ci kuma ya san ba shi ya siyo ba.’

    Hajia tace ‘A a ba za a yi haka ba, sai kace a garin matsiyata ake.’ Ta dubi Mustaphan tace ‘Kai Mustapha ka yi haƙuri, ba na son wannan rigimar taka. Wannan ma ai ba wani abu ba ne da za a ɗaga tunda daga yaranta har nakan duk ‘yayanka ne. Muryarsa a maƙogoro yace ‘Shikenan Hajiya.

    Ya miƙe tsaye yana cewa ‘Bari na je wajen Alhaji mu ci tuwon tare, ko da yake ma a ƙoshe nake me sanyin kawai zan sha. Yana shigewa Jidda ta kalli Hajia tace ‘Kin gani ko Hajia, a kan kayan shiya zai yaga min rigar mutunci, wallahi yaron nan har yanzu bai yi hankali ba.’

    Tace ‘Ya fi ki gaskiya, ya za ki karɓi kuɗinsa kuma ki dinga bar masa yara da yunwa?Hajia wallahi na gaya miki ƙarya yaran nan suke yi, kawai don sun san za a biye musu ne suke abinda suka ga dama. Idan banda haka ya za a yi na hana su abinci na ba wa su Nawwara tunda ai duk tare suke wuni suna wasansu; kawai dai suna so su nuna su ubansu mai kuɗi ne.’

    ‘Ki dai bi shi a hankali kin ji na gaya miki. Bari ma ya fito na ji sai yaushe zai kawo min yaran yawon Sallah ko kuma ni ma laifin naki ne ya shafe ni ya kai yaran wajen wadda da ba ya son ya bar mata su?’

    Haka yana ji yana gani ya haƙura ya ƙyale Yaya Jidda; daman ya riga ya san Hajia ba za ta taɓa bari a ga laifinta ba. Kamar yanda aka yi alƙawari ranar uku ga sallah tun wajen ƙarfe tara na safe ya tafi ɗaukan Khadeeja; da yake sun riga sun yi waya a shirye ya same ta don haka ba tare da wani ɓata lokaci ba ya ɗauko ta ita da mai aikinta Rashida suka kama hanya.

    Sai da suka tsaya a gidan Mama suka kwashi yara sannan suka wuce gidan Hajia. Nan suka zauna a parlor ana ta hira yayin da yara suke ta kai wa da kawowarsu. Jimawa kaɗan Yaya Jidda ta dubi Khadeeja tana nuna Rashida tace ‘Wannan yarinyar taki kuwa za ta iya wani aikin kirki? Kada fu ku je a kama ku da child abuse?’

    Ta yi dariya duk da yanda maganar ta ɓata mata rai tace ‘Ah haba dai, shekarunta fa sha biyar yaya don dai kawai ba ta da girma ne. Aiki kam ta iya sosai ko a gida ma Mommy ta koya mata.’‘To amma idan Habi ta dawo sai a mayar da ita ko? Tunda na ji Habi ɗin tace baku da wata matsala da ita kuma tana nan ita ma tana shirin dawowa.’

    ‘Uhm, sai a haɗa biyu ma tunda kin ga ga hidimar gida ga ta yara, kuma ina zuwa makaranta. Haba wace hidima ce sai an haɗa ‘yan aiki har biyu a wannan gidan? Hidimar har nawa take? Kafin ta ba ta amsa Mustapha ya shigo yana cewa ‘Ku tashi mu tafi ko, don na san kuna da aiki a gidan nan don duk ya yi ƙura.’

    Suka fara shirin miƙewa yayin da ita kuma Yaya Jidda ta kalli Mustaphan tace ‘Na ga kun samo ‘yar aiki, Baba Habi ma fa tana nan tana shirin dawowa. Yace ‘Ah ai kawai sai ki ce mata ta yi zamanta tunda dai gaskiya ba mu da inda za mu ajiye ‘yan aiki har biyu. Da nace ta mayar da wannan ɗin idan Baba Habi ta dawo?’

    ‘To ga ta nan ku yi magana idan ta fi son Baba Habi ɗin sai a mayar da wannan ɗin.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba Khadeeja tace ‘Uhm ai gara a bar wannan ɗin, in ya so in da wata matsala sai na yi magana a nan ɗin a kawo wata. Haka dai dole Yaya Jidda ta bar su suka tafi ba tare da ta iya gamsar da su cewa Baba Habi za ta dawo ba.

    Kamar yanda ya faɗa kuwa kaca-kaca suka tarar da gidan, sai dai suna shiga suka fara ƙoƙarin gyarawa. Kuma da yake yana ajiye su ya sake fita har da Afaf da Habib aka yi aikin, don haka cikin ƙanƙanin lokaci suka gama.

    A haka rayuwa ta cigaba; sai dai a ɓangaren Mustapha idan dai yana gidan ba a saka masa yara aiki, sai dai su su yi ta gara Rashida komai ita za su aika ko su saka. Khadeeja tana son ta tsawatar musu amma tana tsoron abinda ubansu zai ce tunda ta ga sun ɗan sami natsuwa babu wata hatsaniya, ba ta so ta ja rigima. Don haka haka ta zuba musu ido; abu kaɗan sai a ƙwalawa Rashida kira ko da kuwa aikin Khadeejan take yi dole ta bari ta je ta yi musu yanda suke so.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 31st Octoba 2025

    Fassarar huɗubar Juma’a kai daga Masallaci mai alfarma, ta yau Juma’a 9 Jumadal Ula, 1447 H / 31 October, 2025 M

    Mai Huɗuba: Sheikh Dr. Mahir bin Hamad Almu’aiƙili

    Mai Fassara: Usman Muhammad Ahmad

    Huɗuba ta farko:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Yake afuwa da yafiya kuma Yake gafarta zunubai, kuma Yake saka wa ma’abota kyautatawa, kuma Yake tunkuɗe musu tsanani da damuwowi, kuma Shi ne wanda Yake talala kuma Yake jinkirtawa don mai laifi ya tuba.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Tsarkakakke daga tawaya da aibuka Wanda Ya ce: ((Haƙiƙa kuma Mun halicci sammai da ƙasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, kuma wata gajiya ba ta shafe Mu ba)).

    Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, ma’abocin tafkin nan da za a tuzga masa, da matsayin nan da za a masa baiwarsa, duk wanda ya masa biyayya ya tsira, kuma duk wanda ya saɓa masa za a jefa shi a wuta, Allah Ya yi salati a gare shi, da alayensa, da sahabbansa, da matansa, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar da halittu za su koma zuwa ga Ubangijinsu a cikinta, kuma Ya yi masa sallama mai yawa.

    Bayan haka:

    Ya ku taron muminai! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah Maɗaukakin Sarki kuma ku masa biyayya, kuma ku sani cewa a gaba gare ku akwai mutuwa da ƙabari, da tashi daga ƙabari da taron filin alƙiyama da sakamako, wasu za su kasance cikin ni’ima da farin ciki, wasu kuma za su kasance cikin azaba da halaka – Allah Ya tsare mu – ((Lallai masu taƙawa suna cikin gidajen aljanna da ƙoramu () A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko)).

    Ya ku al’ummar musulmi!

    Lallai zuciya ita ce abin da Ubangiji Yake la’akari da shi daga bawa, don haka, duk wanda ya haɗu da Allah da zuciya kuɓutacciya, to haƙiƙa ya rabauta kuma ya tsira, kuma duk wanda ya haɗu da Shi da zuciya mara lafiya, to haƙiƙa ya taɓe kuma ya yi asara, kuma cututtukan zukata suna da yawa, kuma daga cikin mafi hatsarinsu akwai cutar ƙeƙashewa, saboda ma’abocin ƙeƙasasshiyar zuciya, yana kawar da kai daga tuba da komawa zuwa ga Allah, har ma a lokacin saukar bala’i da masifa, sai zuciyarsa ta zama makiyaya ce ta Sheɗan, kuma ba ta karɓar wa’azozin Alƙur’ani.

    Allah Maɗaukaki Yana cewa: ((Kuma lallai Mun aika da (manzanni) zuwa ga al’ummomin da suka gabace ka, sai Muka ɗora musu tsananin talauci da cutuka ko sa ƙasƙantar da kai To me ya hana lokacin da musibarmu ta zo musu, su ƙasƙantar da kai? Sai dai kuma zukatansu ne suka ƙeƙashe, Shaiɗan kuma ya ƙawata musu abin da suka kasance suna aikatawa)), kuma Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: ((To tsananin azaba ya tabbata ga masu ƙeƙasassun zukata da ba sa ambaton Allah. Waɗannan suna cikin ɓata mabayyani)).

    Kuma daga cikin sabuban tausasan zuciya da khushu’inta akwai dawwama a kan ambaton Allah, da tuntuntuni cikin ayoyinsa, da tuna mutuwa da magaginta, da ƙabari da matsansa da duhunsa, da ziyartar maƙabartu, da nazari game da lamuran ranar alƙiyama, ya zo a cikin littafin Ɗabaƙatul Hanabila cewa, wani mutum ya ce wa Imamu Ahmad: “Ta yaya zuciyata za ta yi taushi?”, sai ya ce: “Ka shiga maƙabarta, kuma ka shafa kan maraya”.

    Ya ku ‘yan’uwa masu imani!

    Ita rayuwa gajera ce duk yadda ta yi tsawo, kuma kwanakinta ‘yan kaɗan ne ko yaya suka yawaita, mai dace shi ne wanda ya rayu a cikinta a kan biyayya ga Ubangijinsa, kuma ya yi guzuri a cikinta don ranar haɗuwa da Mahaliccinsa, asararre kuwa, shi ne wanda ya bi son zuciyarsa, kuma ya yi burace-buracen samun kyakkyawar sakamako a wajen Allah, har mutuwa ta afka masa alhali yana cikin gafalarsa.

    Kuma bai mata shiri da aiki nagartacce da zai zama sababin kuɓutarsa ba, kuma masu barin wannan duniya iri biyu ne: Mamaci da zai huta daga wahalar wannan gida ta duniya, ya isa zuwa ga hutu a gidan matabbata, da kuma mamaci da bayi da ƙasa za su huta daga sharrinsa, kuma zai tafi ne zuwa ga mammunan makoma, kuma tur da makwanci.

    Hadisi ya zo a Sahihu Muslim, daga Abu Ƙatada Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bi ta wajen wata gawa, sai ya ce: (Wanda zai huta, da wanda za a huta daga gare shi), sai suka ce: Me kake nufi da wanda ya huta da wanda aka huta daga gare shi? Sai ya ce: (Bawa mumini zai huta daga cutarwar duniya da wahalarta zuwa rahamar Allah, shi kuma fajirin bawa bayi da ƙasa, da bishiyoyi, da dabbobi za su huta daga gare shi).

    Ya ku ‘yan uwa masu imani!

    Idan mutum ya mutu, to haƙiƙa alƙiyamarsa ta tsaya, domin ƙabari shi ne farkon matakan lahira, Allah Ya sanya shi ya zama wa’azi da izina, wacce zuciya za ta tausasa da ita, kuma ta tunkuɗe gafala, ta kuma taimaka wurin ƙoƙarin aikata ɗa’a, don haka, babu abin da zai amfanar da mutum a ƙabarinsa face aikinsa, hadisi ya zo a Bukhari da Muslim cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Abubuwa uku ne suke bin mamaci, sai biyu su dawo, ɗaya kuma ya wanzu tare da shi: Iyalansa da dukiyarsa da aikinsa za su bi shi, sai iyalansa da dukiyarsa su dawo, sai aikinsa ya tsaya tare da shi)).

    Don haka ne Usman Allah Ya ƙara masa yarda ya kasance idan ya tsaya a kan ƙabari, sai ya yi kuka, har sai ya jiƙa gemunsa, sai aka ce da shi: Kana tuna aljanna da wuta ba ka kuka, amma kana kuka saboda wannan? Sai ya ce: Lallai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ƙabari shi ne farkon matakan lahira, idan ya tsira a cikinsa, to abin da yake bayansa ya fi shi sauƙi, idan kuwa bai tsira ba, to abin da yake bayansa ya fi shi muni). Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ban taɓa ganin wani abu mai firgitarwa ba face ƙabari ya fi shi firgitarwa). Tirmizi ne ya rawaito a Sunan ɗinshi.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda mutum yana kasancewa a cikinsa shi ɗaya tilo, ba tare da aboki, ko masoyi, ko mai ɗebe kewa, ko abokin zama ba, kuma akwai matsa a cikinsa, da akwai wani da zai kuɓuta daga wannan matsar, da Sa’adu ɗan Mu’azu ya kuɓuta daga gare ta.

    Ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda akwai fitina a cikinsa, kamar fitinar Dujal koma wacce ta fi ta tsanani, ƙabari ya fi shi firgitarwa; saboda shi ko dai ya zama dausayi ne daga cikin dausayoyin aljanna, ko kuma rami ne daga cikin ramukan wuta – Allah Ya tsare mu – saboda haka, duk wanda ya kasance mai kyautatawa, to ƙabarinsa zai zama yalwa da farin ciki a gare shi, duk kuwa wanda ya kasance mai mummunan aiki, to zai zama kewa da baƙin cikin da damuwa a gare shi.

    Hadisi ya zo a Bukhari da Muslim, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Shi bawa idan aka sanya shi a ƙabarinsa, kuma abokansa suka juya suka tafi suka bar shi, har ma zai na jin ƙaran takun takalmansu, sai mala’iku biyu su zo masa, sai su zaunar da shi, sai su ce da shi: Me ka kasance kana cewa game da wannan mutumin, wato Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi?

    Sai ya ce: Na shaida cewa shi bawan Allah ne kuma Manzonsa, sai a ce da shi: Ka duba mazauninka a wuta, Allah Ya musanya maka shi da wani mazauni a aljanna), Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare ya ce: (Sai ya gan su gaba ɗaya, amma kuma kafiri ko kuma munafiki sai ya ce: Ban sani ba, na dai kasance ina faɗin abin da mutane suke faɗi ne, sai a ce da shi: Ba ka sani ba, kuma ba ka karanta ba, sannan sai a dake shi da guduma ta ƙarfe da ƙarfi a tsakanin kunnuwansa biyu, sai ya yi ihu da ƙarfi ihun da duk wanda yake kusa da shi zai ji ban da mutane da aljanu).

    Don haka ne ya zama daga cikin shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai neman tsari daga azabar ƙabari a kowace salla, kamar yadda ya zo a Sahihu Muslim, daga hadisin Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan ɗayanku ya yi tahiya, ya nemi tsarin Allah daga abubuwa guda huɗu, ya ce: Ya Allah ina neman tsarinka daga azabar wutar jahannama, da azabar ƙabari, da fitinar rayuwa da mutawa, da sharrin fitinar Dujal).

    A’uzu billahi minsh-shaiɗanir-rajim: ((Har sai idan da mutuwa ta zo wa ɗayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana  “Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faɗin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu Sannan idan aka busa ƙaho to fa babu wata dangantaka (mai amfani) a tsakaninsu a wannan ranar, kuma ba za su tambayi juna ba

    To waɗanda ma’aunansu suka yi nauyi waɗannan su ne masu babban rabo. Waɗanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waɗannan su ne waɗanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama)). Allah Ya albarkace mu da Alƙur’ani da sunna, kuma Ya amfanar da mu abin da ke cikinsu na ayoyi da hikima, ina faɗin abin da kuke sauraro, kuma ina nema mana gafarar Allah daga kowane zunubi da laifi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Ya kasance Mai gafara ne Mai jin ƙan.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah Mai tabbatar da zukata, Mai gafarta zunubai, ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi, kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, Mai yaye damuwa, kuma ina shaidawa lallai Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da Alayensa da Sahabbansa, da aminci mai yawa.

    Bayan haka, ya ku taron muminai!

    Lallai a cikin ziyartar maƙabartu akwai wa’aztuwa da ɗaukan izina da suke zaburar da mutum a kan tsoro da fargaba, da kuma gaggawa wurin ɗa’a da aiki, kuma duk wanda ya ji tsoro zai yi gaggawa, kuma duk wanda ya yi gaggawa zai kai ga matsayin da yake fata, saboda haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya kwaɗaitar game da ziyartar maƙabartu don wa’aztuwa da ɗaukar izina, ya zo a cikin Musnad na Imamu Ahmad cewa: Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na kasance ina hana ku ziyartar ƙaburbura.

    to ku ziyarce su domin za su tunatar da ku lahira), kuma ziyartar maƙabartu yana da hukunce-hukunce da ladubba, daga cikinsu akwai yin addu’a ga mamata, domin ƙaburbura cike suke da duhu, amma Allah yana haskaka su sakamakon addu’ar salihai daga cikin bayinsa, ya zo a cikin Sahihu Muslim daga hadisin Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda cewa: “Wata mata baƙa ta kasance tana hidima a masallacin Annabi, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya daina ganinta, sai ya tambayi inda take, sai suka ce: ta rasu, sai ya ce: (Me ya sa ba ku sanar da ni ba?)

    Kamar dai sun raina lamarinta, sai ya ce: (Ku nuna min ƙabarinta), sai suka nuna masa, sai ya yi mata salla, sannan ya ce: (Waɗannan ƙaburbura a cike suke da duhu ga ma’abotansu, kuma lallai Allah Maɗaukaki yana haskaka musu sakamakon addu’ata gare su), kuma ya kasance daga cikin shiriyarsa tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, idan ya zo maƙabarta, yana cewa: (Assalamu ala ahlid diyari minal muminina wal musulmin, wa yarhamullahul mustaƙdimina minna wal musta’akhirin, wa inna insha Allahu bikum lalahiƙun), Muslim ne rawaito shi.

    Ya ku taron ‘yan-uwa!

    Lallai ƙaburbura suna da alfarma, don haka ba ya halatta ga mutum ya taka su, ko ya zauna a kansu, ya zo a cikin Sahihu Muslim cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Mutum ya zauna a kan wuta ta ƙone tufafinsa har ta kai ga fatarsa, shi ya fi alheri gare shi sama da ya zauna a kan ƙabari).

    Haka kuma, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya hana fuskantar ƙaburbura yayin salla, da riƙar maƙabartu a matsayin wurin salla, ya zo cikin Bukhari da Muslim daga Aisha Allah ya ƙara mata yarda cewa: “lallai Ummu Habiba da Ummu Salama Allah ya ƙara musu yarda sun ambaci wani coci da suka gani a Habasha mai ɗauke da hotuna a cikinsa, sai suka ba da labarinsa wa Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi, sai ya ce: (Lallai su waɗannan mutanen idan wani mutumin kirki ya mutu a cikinsu sai su gina masallaci a kan ƙabarinsa, sannan su zana waɗancan hotunan, kuma waɗannan su ne mafiya sharrin halitta a wurin Allah a ranar alkiyama).

    Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Ku saurara! lallai waɗanda suka gabace ku sun kasance suna riƙar ƙaburburan annabawansu da salihansu a matsayin masallatai, lallai na hane ku daga yin hakan). Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku bayin Allah! Kuma hakan ya kasance ne saboda lallai shi wuce iyaka game da ƙaburburan salihai yana kai mutum ga yin shirka da Allah, ga babban malamin tafsirin nan, Abdullah ɗan Abbas Allah ya ƙara musu yarda, yana faɗi a ƙarƙashin fassarar faɗin Ubangiji Maɗaukaki: ((Kuma suka ce: kada ku bar ababen bautarku, kuma kada ku bar Wadda da Suwa’a da Yagusa da Ya’uƙa da Nasra)), ya ce:

    “Waɗannan sunaye ne na wasu mutane salihai daga cikin mutanen Annabi Nuhu, yayin da suka mutu, sai Shaiɗan ya yi wahayi ga mutanensu cewa su kafa hotunansu a wuraren da suke zama, kuma su sa musu sunayensu, sai suka yi haka, ba tare da suna bauta musu ba, har sai da waɗannan suka mutu, kuma ilimi ya bace, sai aka fara bauta musu”. Bukhari ne ya rawaito shi.

    Saboda haka, ya kai bawan Allah! ba ya halatta a girmama ƙaburburan salihai, ko a yi gini a kansu, bare kuma a riƙa kewaye su da ɗawafi, ko yanka ko bakance dominsu, ko kiran ma’abotansu, ko neman agaji a wajensu, a neman biyan buƙatu ko yaye damuwa, don haka mu ji tsoron Allah ya ku Musulmi, kuma mu taƙaita da abin da aka shar’anta ziyartar ƙaburbura saboda su, na wa’aztuwa da ɗaukan izina, da sallama ga mamata, da yi musu addu’a, kuma kada mu ƙirƙiro wani abu da zai fusata Ubangiji a wurin.

    Haƙiƙa ya zo cikin Musnad na Imām Ahmad cewa, Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce: (Na hana ku ziyartar ƙaburbura, to ku ziyarce su, amma kada ku faɗi abin da zai fusata Ubangiji), a wata ruwayar kuma: (Amma kada ku faɗi magana marar kyau), wato: maganar banza, kuma bai dace ga wanda ya je maƙabarta ya shiga cikin zancen duniya ba, ko yin dariya da barkwanci, bari dai, abin da ya dace shi ne ya yi tunani game da halin ma’abota ƙaburburan, haka kuma, ana so ya yi tunani a kan halinsa da makomarsa, da kuma cewa shi ma mai tafiya ne zuwa wurin da suka tafi.

    Sannan ku sani, ya ku taron muminai cewa, lallai Allah Ya umarce ku da wani umarni mai daraja wanda Ya fara da kansa, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna yin salati wa Annabi. Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi salati ga iyalin Annabi Ibrahim, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammad da matansa da zuriyarsa kamar yadda Ka yi albarka ga iyalan Annabi Ibrahim, lallai Kai ne Sha-yabo Mai girma.

    Ya Allah, Ka ƙara yarda da halifofi shiryayyu, Abubakar da Umar da Usman da Ali, da sauran sahabbai da tabi’ai, da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar alkiyama, kuma Ka haɗa mu tare da su cikin afuwarka da karamcinka da kyautarka, ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah, Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka sanya wannan ƙasa ta zama mai aminci da kwanciyar hankali da wadatar arziki da yalwa, da sauran ƙasashen Musulmai.

    Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da majiɓinta al’amuranmu, kuma Ka ƙarfafi shugabanmu kuma jagoranmu da gaskiya.

    Ya Allah Ka datar da shugabanmu hadimin masallatai biyu masu alfarma da gaskiya, tare da magajinsa amintacce zuwa ga abin da ɗaukaka ne ga Musulunci da gyaruwar Musulmai, da kuma abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, tare da dukkan shugabannin musulmai.

    Ya Allah, Ka kiyaye mana addininmu, da shugabancinmu da tsaronmu, ya Allah Ka datar da jami’an tsaronmu da sojojinmu masu tsaro a kan iyakoki da fagage.

    Ya Allah, Ka tabbatar da aminci da zaman lafiya da kwanciyar hankali da nutsuwa ga ‘yan-uwanmu a Falasɗinu.

    Ya Allah Ka kiyaye Masallacin Ƙudus, kuma Ka sanya shi ya kasance mai ɗaukaka har zuwa ranar alkiyama.

    Ya Allah, Ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, Ka kwaranye baƙin cikin masu bakin ciki, Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, kuma Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah, Ka sanya ƙaburburanmu su zama mafi alherin masauƙanmu bayan mutuwa, Ka sanya su su zamto dausayi daga cikin dausayoyin aljanna, saboda rahamarka, ya Mai ni’imtarwa, ya Ma’abocin ɗaukaka da girma.

    Ya Allah, Ka gafarta wa Musulmi maza da mata, da muminai maza da mata, rayayyunsu da matattu.

    ((Ya Ubangijinmu! Ka ba mu mai kyau a duniya da mai kyau a Lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta!).

    ((Ya Ubangijnmu! Ka karɓa daga gare mu, lallai Kai Mai ji ne kuma Masani. Kuma Ka karɓi tubanmu lallai Kai ne Mai yawan karɓar tuba kuma Mai jin ƙai)).

    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya game da abin suke siffanta Shi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Edita @rumasau-kallamu

  • Baɗi Ba Rai Kashi Na Biyu

    Baɗi Ba Rai Kashi Na Biyu

    Episode 2
    A short story by
    Sakina Yazid (Innar su Amal)

    Mutanen da suka fara dawowa daga maƙabarta ne suka gan ta, don haka ƙanin mahaifinta ya kama hannunta suka koma gidan tana biye da shi kamar wata marar hankali.

    Suna shiga farfajiyar gidan ta turje, ta ƙi ƙarasawa cikin parlor. Nan aka yi wa Ummanta magana inda suka fito ita da Maman Misbahu da ma wasu matan waɗanda suka haɗa da ƙawar Farida, Rabi’a wadda isowarta kenan.

    Ummanta ta ƙarasa kusa da ita ta kama hannunta cike da kulawa tace ‘Farida ki dangana mana, Allahn da ya karɓe shi zai ba ki wani. Ki taho mu shiga gida mu zauna. Ta fizge hannunta daga hannun Ummu tace ‘Ba zan shigo ba, ba zan sake shiga gidan nan ba in sha Allah.’

    Zuwa lokacin ragowar mazan sun ƙaraso har da Misbahu da babansa da Baban Farida. Suka tsaya suka yi cirko-cirko. Maman Misbahu ta ƙaraso ta dafa kafaɗarta tace ‘Idan ba ta son nan ɗin ai sai ku wuce gida. Ta sa hannu ta ture hannun Maman Misbahu daga jikinta tana mata kallo na ƙyamata.

    Ta dubi Umma ta tace ‘Ba zan je gidan ba, wane gidan zan je? Ba kwa buƙata ta ai tunda ba zan sake zama da Misbahu ba. Dole ya sake ni tunda ya kashe min yaro, kin ga kuma kuma ke da Abba ba kwa son bazawara. Don haka ba zan je muku gida ba, in sha Allah daga yau ba za ku sake ganina ba balle na janyo muku abun kunya.’

    Duk wanda yake wajen jikinsa ya yi sanyi, kowa ya kasa magana. Maman Misbahu ta daure tace ‘Ki yi haƙuri Farida a zauna a bi abin a hankali. Ta yi murmushi yaƙe ta juya tana fuskantar Maman Misbahun sannan tace ‘Dole ki ce na yi haƙuri tunda ke ɗanki yana raye, amma ni ya kashe min nawa ɗan.

    Kuma na san kamar yanda kika saba kariya za ki ba shi, sai dai ina miki albishir da cewa ba zai rayu har abada ba. Za mu tsaya a gaban Allah wanda shi kaɗai zai iya yi mana adalci. Ta juya ta yiwo tattaki ta ƙaraso gaban Misbahu ta tsaya, ta zuba masa ido har sai da ya gaji ya sauke nasa ƙwayar idon.

    Kana kallonsa ka san a jigace yake sannan kuma cikin tashin hankali. Ta share ɗigon hawayen da ya gangaro a fuskarta tace ‘Yanzu ka ji daɗi ko Misbahu? Ɗanka, kuma ɗana guda ɗaya ka kashe shi ka huta. Burinka shi ne ka cuzguna min ka saka ni a cikin ƙunci kawai saboda ni na nuna maka soyayya na aure ka. Yanzu ka ga sai ka je ka auri Shahida ka sake rayuwa.

    Na san cewa iyayenka za su ba ka kariya kamar yanda suke yi idan ka yi min wulaƙanci na kai ƙara, kuma na san duk taron mutanen nan da suke kallonmu ba za su iya yi min adalci ba tunda suma duka sun yarda da cewa duk abinda namiji ya yi ado ne; mace ita ce take laifi. Sai dai ina so ka sani daga rana irin ta yau duk lokacin da na yi sujuda sai na kai ƙararka wajen Allah; Allah ya yi maka abinda ka yi min kuma Allah ya saka mana ni da ɗana da ka kashe.’

    Ya runtse ido saboda yanda kalmar ka kashe ɗana take sukansa a zuciya. Yana matuƙar son Adnan, ya za a yi a ce shi ya kashe shi. Har yanzu ma ƙoƙari yake ya yarda cewa Adnan ɗin suka kai maƙabarta suka binne. Ta yi murmushi sannan ta cigaba ‘Ina jiran ka aiko min takardar saki na zuwa gobe. Ban san hukuncin da zan ɗauka ba amma tabbas duniyar nan ba za ta ɗauke mu ba ni da kai idan dai ka bari na sake ganinka ba tare da ka sake ni ba.

    Na tsane ka, bana fatan na sake ganinka a rayuwata. Ina fatan Allah ya hana ka farin ciki kamar yanda ka hana ni da kai da duk wanda yake goya maka baya. Ta matsa daga gabansa ta nufi waje; Ummanta ta bi bayanta da gudu ta sha gabanta tace ‘Ina za ki Farida, ki bari na ɗauko jaka ta mu tafi gida.’

    Ta kalleta tana share hawaye tana cewa ‘Ban san inda zanbi ba, amma wallahi ba za ni gidanku ba balle na janyo muku abun kunya a ce ‘ƴarku ta ƙi zaman aure. Na san dai ko gidan marayu na je za a karɓe ni a ba ni wajen da zan zauna na ƙarasa rayuwata wadda ina ji a jikina ba ta da yawa.’

    Ta raɓa ta gefen Umman ta wuce ta nufi gate. Umma ta tsaya a nan tana share hawaye ba tare da ta san abin yi ba. Gaɓa ɗaya mutanen da suke wajen duk an kasa motsi, kowa binta yake da kallo ana share hawaye. Rabi’a ce ta fito daga cikin matan nan tana riƙe da jakarta cikin hanzari ta ƙarasa ta dafa Farida; wadda ta kusa gate ta baya.

    Ta juya ta kalleta yayinda Rabi’an ta kama hannuwan Farida ta riƙe tana cewa ‘Ki zo mu je gidana Farida, don Allah ki zo mu tafi. Babu wanda zan bari ya ganki, kin ga gobe ma za mu wuce Abuja ba za su sake ganinki ba.’

    Ta kalli hannuwansu waɗanda suke a haɗe, cikin hawaye tace ‘Ba ki yi fushi da ni ba Rabi; ke da aka saka ni na daina kula ki saboda kada ki aure min miji kuma yanzu ba kya tsoron na biki gidanki, gidan mijinki? Ki bar ni kawai na shiga duniya Rabi, na gaji da kowa wallahi.’

    Ta jinjina hannuwansu tace ‘Ba zaki shiga duniya ba Farida, ai ni ba ki gaji da gani na ba ko? Shiru ta yi ta kasa ba ta amsa, don haka ta ja hannunta suka fice daga farfajiyar gidan kowa yana kallon su.

    ƘARSHE….

    EPILOGUE

    Mata da yawa suna zaune a gidajen aurensu cikin cin zarafi da ƙunci ba lallai duka ba. Wasu zagi ne da rashin girmamawa da kuma sauran nau’o’i na emotional abuse.

    Iyayensu ne ya kamata su ba su kariya a irin wannan lokacin to amma haƙuri kawai suke ba su; suna kuma mayar da su cikin halin da yake firgita nutsuwarsu. A mafi yawancin lokuta ma idan iyayen suka saka baki aka zauna da mijin matsalar za ta warware, sai dai idan iyayen ba su jajirce ba. To amma ba za a ko gwada ba. Haka ake zuba musu ido suna rayuwa cikin ƙunci – alone, sad and depressed.

    Iyayensu ba za su taimaka musu ba.

    Al’umma ba za su taimaka musu ba.

    But idan depression ya yi musu yawa har ya janyo suka aikata wani abu na assha a lokacin ne za ka san every single member of the society yana kallon su; domin kuwa za a yi assembly a tsine musu albarka.

    Ban sani ba, ba mu san depression ɗin ba ne ko kuma ba mu yarda yana iya saka mutum ya cutar da kansa ba ko ya cutar da wani. Da sun yi magana sai mu ce su yi haƙuri. Su fita daga harkar mijin su yi zaman ‘ƴa’ƴa. Idan sun matsa mu ce ƙaddararsu kenan.

    Haka za su ƙare rayuwarsu cikin damuwa. Babu abinda ban ji ba from real people
    “Mamaki nake idan na ga mutane suna walwala, su ba su san a cikin matsala ake ba ne?”

    “Mahaifina yace kada na kashe aurena na ba shi kunya, na yi zamana.”

    “Mahaifiyata tace ban isa na janyo mata magana a tsakanin kishiyoyi ba, babu me bazawara ba za a fara a kanta ba.”

    “Na rasa yanda zan yi da shi Anti, duk wanda na gayawa sai a ce na yi haƙuri. An ma rasa me yi masa ko da nasiha ne. To har tsawon yaushe ne zan yi haƙurin? Sai na mutu? Shikenan daga na yi aure nayi sallama da jin daɗi har sai na koma ga Allah?”

    Waɗannan maganganun fa real people ne suke faɗa, very young women; all less than 30.

    Are we alright? Is this fair? Idan muka cigaba da bari ‘ƴa’ƴanmu da ƴan uwansu suna azabtuwa a dalilin aure tabbas ba mu yi wa aure adalci ba kuma ba mu yi wa musulunci adalci ba.

    Ina mafita?

    Innar su Amal.

    Karanta Baɗi Ba Rai Kashi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu