Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Kammalawa Daga Cikin Littafin Ka San Kanka

    Kammalawa Daga Cikin Littafin Ka San Kanka

    Warwara

    Duk da na bayyana muhimmancin mutum ya gano kansa, zan iya cewa ba dole sai ka yi hakan ba. Gano kai wani aiki ne babba mai matuƙar wahala, da in ba ka yi sa’a ba zullumin da za ka shiga a ƙoƙarin gano kanka zai iya lahanta maka ma rayuwa, ya hana ka jin daɗinta.

    Kamar yadda na fara ba da labari a farko, na daɗe ina son gane ni wane ne, kafin na gano kai na har ciwon damuwa sai da na yi, na ma fara karɓar magani a asibiti na ga abun ba mai ƙarewa ba ne na watsar, amma ban karaya ba, na ci gaba da tambayar kai na da kuma ƙoƙarin nemo amsoshin tambayoyin.

    Ba zan ce iya ƙoƙarin gano kai na ne ya sa ni a damuwa ba, abubuwa ne da yawa suka haɗu, amma dole ko dai rashin sanin ni wane ne ya taimaka, ko kuma son gano ni wane ne ya ƙara ingiza abun. In kana ganin ba lallai ka iya jure wahalar da take cikin aikin gano kanka ba, ba kuma za ka iya rayuwa cikin haɗarin rashin sanin kanka ba, to ina ganin abu ɗaya za ka yi.

    Ka bi wanda yafi ka sanin kanka sau da ƙafa. Duk abin da kake son sani ya turo an sanar da kai, duk abin da kake son aikatawa ya turo an koya maka. Na san za ka fahimci inda na dosa, ina nufin ka zama mutumin kirki mai biyayya wa Allah da manzonsa (tsira da aminci su tabbata gare shi) domin in dai ka tsaya kan hanyar da suka ɗauraka a kai, dole za ka amfanu kuma za ka amfanar, za a ƙaru da zuwanka duniya, kuma duk abubuwan da na lissafa a baya za su dinga zuwa maka a ɗabi’ance (naturally) ba tare da wani hoɓɓasa ba, kamar dai abin da ake cewa “autopilot”.

    Idan ka yi wannan ka hutasar da kanka yawan tunani. Duk da cewa ita ma fa wannan hanyar ba sauƙi ne da ita ba, domin kana buƙatar ilimi da kuma aiki da ilimin, ilimi na gaske ba na wasa ba, aiki na gaske ba na wasa ba. Sai ka san ibada da mu’amala da haƙƙoƙin mutane a kanka da haƙƙoƙinka a kansu, da dabarun zaman lafiya da mutane, da yadda rayuwarka a cikinsu za ta amfane su kamar yadda ta magabata ta ke amfanarmu.

    A iya ilimina (wanda ɗan kaɗan ne) ban san wani mutum da ya yi wata bajinta ba a duniya da bai zo wata gaɓa da ya san kansa ba. Kowa in za ka saurare shi, ko za ka karanta littafi ko rubutunsa ko tarihinsa za ka fahimci cewa daga cikin sa’ar da ya yi a rayuwa akwai gane shi wane ne da ya yi da wuri.

    Don haka ko wanda ya zaɓi yin rayuwarsa kan tsari mai kyau zai zo gaɓar da zai san kansa, ko kuma ya dinga rayuwa kamar ta wanda ya riga da ya san kansa ko mai daren daɗewa. Akwai wani hadisi da sahabbai suke tambayar Annabin Allah mai tsira da aminci kan cewa tunda Allah ya riga da ya ƙaddara ƴan wuta da ƴan aljanna, ai ba buƙatar kowa ya yi komai, sai ya jira ƙaddararsa, sai ya ba su amsa da cewa “ku yi aiki, kowa za a sauƙaƙe masa abin da aka halicce shi don shi”.

    Wannan yana nuna mana cewa ba a taɓa kafa hujja da ƙaddara, ko a zauna ana jiran rayuwa ta faru, manufar halittar shi ne ka rayu, ba ka zauna jiran rayuwar tana wucewa ba (waɗanda suka mutu a wurin kare addini Allah yace kar mu ɗauka a mace suke, a raye suke, wataƙila saboda sun mutu a kan manufa da bin tafarki, Allah ne mafi sani).

    Don haka in ba za ka iya sanin kanka ba, to ka bi Allah ka huta, in za ka iya sanin kanka kuma ka samu riba biyu kenan, ka san kanka, kuma kana bin Allah a yadda kake don haka komai zai dinga zuwa maka a sauƙaƙe. Manufar rubuta wannan ɗan ƙaramin littafin shi ne karkato da hankalinmu kan yin rayuwa da manufa da tsari, ba kara zube ba.

    In muna kara zube yanzu muka fara ganin cin kowanne irin kashi, ba za mu taɓa kwarjini ba, balle mu cimma wani abu, mu da ƙorafe-ƙorafe da ganin laifin juna mun ɗaura kenan har illa masha Allahu. In ka samu wannan littafin kada ka karanta shi ka ajiye shi, ka yi ƙoƙarin yin aiki da wasu abubuwan da ka ga za su iya dacewa da taka rayuwar.

    Sani ba aiki ba ya canja komai, bambancinsa da rashin sani kaɗan ne. Allah na ke
    roƙo ya ba mu dacewa duniya da lahira ya kuma azurta mu da kyakkyawan ƙarshe.
    Kada a manta da yaɗa wannan saƙon dan amfanar ƴan’uwa gaba ɗaya, musamman matasa ƴan’uwana da ke ta faɗi tashin ganin sun gano kan rayuwa.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Yadda Manufar Rayuwarka Take

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Manufar Rayuwarka Take

    Yadda Manufar Rayuwarka Take

    Manufar Rayuwarka
    Wannan kusan zan iya cewa shi ne ma ya kamata ya zo a farko, amma na jinkirta shi ne saboda amsar da ka samu daga sanin kai wane ne ita za ta haska maka manufar rayuwarka. Kowa akwai abin da Allah ya halicce shi ya yi a wannan duniyar, wanda ya gano na sa da wuri kuma ya duƙufa a kai shi ne yake cimma nasarori da wuri.

    Idan ka bibiye littafin nan tun daga farko, za ka gano wata gaskiya guda, babu irinka a duniya. Kafin a samu wani da ƙwayar halittarku ta zo ɗaya, shekarunku, iliminku, gogewarku, abokanku, iyayenku, makaranta da unguwarku duk ɗaya abu ne mai matuƙar wahala.

    Kenan kai a matsayinka na wanda babu irinsa akwai abin da za ka yi da rayuwarka da ba lallai wani ya yi irinsa sak ba. Ba kowa ne yake iya gano manufar rayuwarsa ba ko da ya san kansa, amma aƙalla dai zai zama ya samu wata hanya da yake bi, tunda ya san shi wanene, zai gane ina ya kamata ya dosa.

    A lokacin da yake kan hanyar ne kuma Ubangiji zai ta haskaka masa yana nuna masa abubuwa. Wani lokacin za ka yi ta yin wani abu ba ka ɗauke shi a bakin komai ba, sai
    rayuwa ta yi nisa sai ka ga ashe wannan abin kamar an shirya ka ne don ka zama wani da shi a gaba. Wani lokacin kuma kwatsam wani abin zai faɗo rayuwarka, in ka ba shi lokacinka da tunaninka sai ka ga hanyar tana ta ƙara faɗaɗa.

    Yana da kyau mai ƙoƙarin gano manufarsa ya amsa waɗannan tambayoyin. Ni wanene? Daga ina nake? Ina zan je ni? Yanzu a ina nake? Me nake yi yanzu don isa wurin? Lallai waɗannan tambayoyi matukar an dage da yinsu ba za a samu zaman lafiya ba sai an isa wurin. Kuma hakan ake buƙata.

    Ita rayuwa duk lokacin da ta ga wani gurbi ba a cike shi da komai ba, sai ta cike wa mutum da wani abu da ba zai amfane shi ba. Kamar yadda basirar da aka ƙi yin komai da ita take nemawa mai ita abin yi, haka rayuwa take raba mana ayyuka ba tare da mun shirya musu ba. Kafin mu ankare kuma sun zame mana jiki sai mu ma ɗauka dama su ne ya kamata mu yi ta yi.

    Abin dai da yafi muhimmanci shi ne mu ayyana wa kanmu wata hanya da muka ɗauka muke son bi, wannan zai sa komai na mu ya dinga tafiya a tsari, in ma hanyar ba mai ɓullewa ba ce ba mu da asara, za mu samu darussa da dama, kuma ta haka za mu lalubo mai ɓullewar. Kowa nan duniya da ka gani da gwaji ya kai in da ya kai, wanda yake tsoron faɗuwa ba ya taɓa zama gwani.

    Duk lokacin da aka yi zancen manufa dai ya zama kana tuna cewa Allah ne ya halicce ka, kuma yace ka bauta masa, kuma yace in ka bauta masa zai maka sakamako da aljanna, kenan ya zama dole ya zama koma mene ne za ka yi kana kawo waɗannan abubuwan a farko.

    Duk layin da ka ɗauka ka ga ba zai kai ga wannan ba daga ƙarshe, wannan ba layin kamawa ba ne, ka yi ƙoƙari ka watsar da shi ka nemi wani. Allah yana da kyauta, duk abin da za ka yi in ka yi da niyyar ya ba ka lada babu abin da zai hana ya baka lada sai in har ka saɓa masa ko ka saɓawa koyarwar manzonsa.

    A taƙaice dai jin daɗin lahira ne yake zama kan gaba cikin tunanin mai manufa da kuma aiki yadda addini yace a yi, ko da kuwa a yanzun baƙar wahala yake sha, tunda ya san sakamakonsa yana can. Abubuwan da za su taimaki mutum a kan manufa sun haɗa da kyautatawa Allah zato.

    Duk inda kake tsammaninsa a nan yake kamar yadda ya faɗa a hadisul Ƙudsi. Bayan wannan sai mutum ya so kansa, ka da ka raina kanka duk yadda kake, domin kana da wani abu da za ka iya bayarwa ba tare da ka ma sani ba. Daga nan sai tsaida hankali kan ƙananun abubuwa na kusa, kada ka shagaltu da tunanin manyan abubuwan da za ka yi, har hakan ya hana ka yin ƙanana.

    Na sha shagaltuwa da tunanin manyan abubuwan da yakamata ace na yi ko ina yi, a haka lokacina zai tafi, ban yi ƙanana na kusa da ni ba, kuma babban ma ba yi zan yi ba. Yanzu da na fara ƙananan sai haske yake ta zuwa mini, nake samun matakala da za tai ni zuwa ga sauran.

    Ba dole sai ka shahara da wani abu ba za ka ba da gudunmawa, amfanin manufa shi ne kawai ya zama an ƙaru da kai ko yaya ne. In dai ana ƙaruwa da mutum kuma hakan ya sa a gaba to ya riga da ya samu manufa, ko da ba a san shi a dandalin sada zumunta ba (in hakan ba ya cikin burinsa kenan).

    A matsayinmu na bayi, waɗanda ba mu san ƙaddararmu ba, aiki shi ne na mu, zartarwa kuma na mamallakin ranar sakamako ne. Ganin damarsa ne ya cika mana burukanmu tun a nan, ganin damarsa ne kuma ya mana tanadi a can, ba a masa dole, ba a kuma kwanciya da sa ran shi zai yi, za mu yi, za mu jira zartarwarsa ba tare da ƙosawa ba, in bai ba mu ba sai mu sake gwada wani layin, wataƙila a can rabon yake.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Yadda Za Ka Tambayi Kanka Da Kanka

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Za Ka Tambayi Kanka Da Kanka

    Yadda Za Ka Tambayi Kanka Da Kanka

    ❖ Wacce Baiwa Kake Da Ita?

    Sanin wannan rabe-rabe na mutane zai haska maka kai wanene, daga nan sai ka tambayi kanka, menene ƙarfi na? Wacce baiwa ce Allah ya mini da mutane duk sun sallama in dai a wuri kaza ne in dai ba ni ba sai dai a yi maleji?

    Menene a ɗabi’ance yake zuwa mini da sauƙi? Rubutu ne? Karatu ne? Gudu ne? Hadda ne? Iya magana ne? Haƙuri ne? Juriya ne? Naci ne? Son jagoranci ne? Lissafi ne? Da dai duk wata baiwa da ka san kana da ita.

    Wani yana da basirar ƙirƙirar sabon abu, wani kuma basirarsa tana cikin kwaikwayo ne, in dai za a yi a gabansa sai ya kwaikwaya, wani kuma saurin koyo ne da shi, in dai an koyar da shi to sai ya gane, wani yawan bincike ne da shi, duk abin da ake so a binciko zai iya.

    Babu wani da Allah ya yi shi ba wata baiwa, in ma mutum bai gane baiwarsa ba to ita baiwar za ta kai shi zuwa wani wuri da take kai irin masu baiwar. Misali mutum zai iya tsintar kansa a halin yin waƙe-waƙe, ko wasan barkwanci, ko rubutu duk wannan yar manuniya ce da ke nuna cewa mutum yana da basirar ƙirƙira.

    Abin da ya rage kawai ya tsaya ya nutsu yaga mai zai yi da wannan baiwar da yake da ita. Zai iya zuwa ya koyi aikin hannu kowanne iri ne, zai iya shiga harkar binciken fasaha don ya samar da wanin sabon abu.

    Wanda yake da baiwar hadda ko yawan karatu ya ɗauko hanyar ilimi da malumta, ya rage ya nutsu ya san wanne ɓangare ne na ilimi in ya yi zai fi zuwa masa da sauƙi, kuma mutane za su fi amfana da iliminsa. Ba malumta ba kaɗai, duk wanni fanni da zai buƙaci ƙarfin iya kiyaye bayanai komai yawansu.

    Wanda yake da baiwar iya magana ko jan ragama ya san Jagoranci zai zo masa da sauƙi, don haka duk inda ya samu wata dama da zai zama jagora ya yi ƙoƙarin jan ragamar, saboda wannan zai sa ya ƙara samun gogewa a harkar mulki da hulɗa da jama’a. Idan na yi maganar jagoranci ba na nufin mutum ya fito takara ko ya zama mayen mulki (ba a son mutum ya dinga neman mulki), abin nufi a wurin da ya samu kansa da ya tabbatar in bai tsaya tsayin daka kan jagorancin ba tafiyar za ta gurgunce.

    Abin dai shi ne, ba wata baiwa da ba ta da amfani, abu mafi wahala shi ne a gano ta, bayan an gano ta kuma a san inda za a yi amfani da ita. A wannan mataki iyaye da makusantan mutum suna da rawar da za su taka, waɗanda aka gano inda suka fi karkata tun suna ƙanana kuma aka taimake su a kan hakan sun fi saurin cimma nasara sama da waɗanda aka bar su suna ta tsilla-tsilla.

    ❖ Me Kake Jin Daɗin Yi/Me kake so?

    Bayan ka gane ƙarfinka da rauninka na halitta abu na gaba da za ka nutsu ka tambayi kanka shi ne menene kake jin daɗin yinsa. Duk abin da kake jin daɗin yi yana haska maka kai wane ne, domin son wani ƙin wani ne, yadda kake son abin haka wani kuma yake ƙinsa, kenan da kai da shi iri ɗaya ne da shi ma ya so.

    Shi wannan ɓangare sai ka durfafe shi kamar mai nazarin kimiyya, ma’ana yadda wanda ya shiga ɗakin gwaje-gwaje yake nutsawa cikin bincike, ya yi ta gwada abubuwa kafin ya gano daidai haka kai ma za ka yi. Idan ƙwallon ƙafa kaɗai kake bugawa ba za ka san daɗin ƙwallon kwando ba, har sai ka buga dukka biyun da ƙwarewa iri ɗaya kafin ka gane wacce ta fi maka daɗi.

    Wanda yake saurarar karatun sheikh Sudeis kaɗai ba zai iya cewa ga karatun da yafi daɗi ba har sai ya saurari na sheikh Shuraim. Don haka kar ka gajiya da lura da kanka a duk wani aiki da ka yi don ka gane wanne ne in ka yi shi ko lokacin da kake yi kake jin wani shauƙi na musamman.

    Haka nan za ka san me kake so ne ta hanyar gwada abubuwa da yawa. Ba za ka san kalar abincin da ka fi so ba sai ka ɗanɗana abinci da yawa. Wanda iya tuwo yake ci ba shi da hurumin cewa ya fi son tuwo duk cikin abinci har sai ya ɗanɗana farfesun naman kai ya ji. Don haka wannan fannin yanabuƙatar nutsuwa sosai kafin mutum ya gane mai yake so.

    Wannan kuma fa ba ya nufin ka shagaltu da gwada abubuwa kaɗai, kana ci gaba da
    rayuwarka ne za ka dinga ganewa. Idan kallon fim ko kallon ƙwallo ko danna waya ko yawan bacci ko zaman majalisa ne abin da ka fi jin daɗin yi fa? Gaskiya saboda Allah mutum a irin wannan halin babu inda zai je, dole ya tashi tsaye ya natsa da tambaya da
    lura da aikata wasu abubuwan har ya gano wasu abu da yake jin daɗi.

    Ya kamata a wannan gaɓar mutum ya tambayi kansa kan abubuwan da yake jin daɗi tun yana yaro, in ya manta ya tambayi makusantansa, saboda lokacin da muke yara ba mu gurɓata da komai na duniya ba, muna nan a tsarkake yadda Allah ya halitto mu, don haka amsoshinmu da dama kan sanin kanmu suke komawa kan yarintarmu.

    ❖ In Ba Kuɗi A Duniya Me Za Ka Yi?

    Idan da a ce yau za a wayi gari ba kuɗi a duniya, ko kuma ka samu duk kuɗin da kake buƙata har ka mutu, me za ka yi? Wannan tambayar amsa ta yana da matuƙar muhimmanci saboda yawancin mutane kuɗi ne yake mantar da su kansu. Wani yana sha’awar ya zama uba nagari, wani miji nagari, wani ɗa nagari to amma saboda neman kuɗi sai ya rasa lokaci da ikon cika waɗannan burukan.

    Wani koyarwa yake so amma saboda cin kashin da ake yi wa malamai sai ya gwammance ya buɗe shago. Wani ƙere-ƙere yake sha’awa, to amma likitoci suna samun albashi mai yawa, don haka ya gwammanci ya yi ta zama a asibiti ko da hakan ba ya sa
    shi jin yana wata uwa da rayuwarsa.

    Wani ilimi yake buƙata, to amma mawaƙa sun fi kowa samun kuɗi dan haka ya bar makaranta ya shiga sana’ar waƙa. Duk waɗannan abubuwan da na lissafa kuɗi ne ya karkatar da hankalin mutum daga haƙiƙaninsa, da kuɗi ba matsala ba ne da wataƙila wannan fannin zai ɗauka.

    ❖ Menene Cin Nasara A Wurinka?

    Muna rayuwa a wata duniya da ake ɗauka cewa tara dukiya shi ne cin nasara saboda kallon talabijin da fina-finai. Amma cin nasara daga mutum ne. Kowanne mutum a can ƙasan zuciyarsa ya san menene in ya samu ko ya aikata ya ci nasara. Yana da kyau a lokacin da kake ƙoƙarin gano kanka ka amsa wannan tambayar, menene nake ɗauka a matsayin cin nasara?

    Kada ka yaudaru da abin da mutane suke ɗauka a matsayin cin nasara, ka tsaya dai iya kan tambayar kanka mene ne in na yi na ci nasara. Shi samar da ma’anar nasara a rayuwa yana da matuƙar amfani, saboda cin nasara ba abu guda ɗaya ba ne, sai an samu gamsuwa a fannoni da dama na rayuwa kafin a samu gamsuwar an ci nasara.

    Tun daga kan ɓangaren addini, iyali, abokai, aiki/sana’a, lafiyar jiki, mutanen da ake hulɗa da su duk sai mutum ya iyakance mene ne cin nasara a ciki. Wacce irin mata zan aura na ci nasara? Me zan dinga yi na addini kullum da zai sa ni cikin masu nasara? Waɗanne irin abokai ya kamata na dinga hulɗa da su? Wanne mataki zan kai a sana’a ta na zama na ci nasara?

    Lafiya cikakkiya na ke buƙata ko kuwa ko da ina laulayi ma ina ɗaukar kaina a matsayin na ci nasara? Wannan fa duk kai a karan kanka ne za ka amsa su, domin cin nasara a
    kowanne ɓangare na rayuwa yana da alaƙa da kai wanne irin mutum ne, me kake so, me ka zaɓi ka tafi a kai, me kake yawan tunani a kai.

    ❖ Yanzu A Ina Kake?

    Tambaya ta gaba da za ka amsa ita ce yanzu a wanne mataki kake a rayuwa? Wanne irin ilimi ka tara? Wani mataki ka kai a sana’arka? Menene kake da ƙwarewa a kai? Mutumin da bai san a ina yake ba ba zai iya sanin shi wane ne ba. Ita wannan tambayar ta matakin da kake yanzu za ta taimaka maka wajen kamanta wurin da kake da ma’anar da ka ba wa cin nasara.

    Sannan za ta zama maka wata matakala da za ka taka ko wani sitiyari da za ka juya akalar rayuwarka da shi. Misali, idan daga cikin ma’anar da ka ba wa cin nasara akwai ƙwarewa a sana’arka, sai ka dubi inda kake yanzu ka ga ba ma ka ɗauko hanyar
    ƙwarewar ba, ko kuma ba ma a sana’ar da ya kamata kake ba. Wannan zai sa ka fara tunanin matakan da za ka ɗauka don ka ƙware, ko kuma hanyar da za ka bi don canja sana’a ko ƙarawa da wata sana’ar.

    ❖ Me Yake Ɓata Maka Rai?

    Ɓacin rai motsin rai ne mai ƙarfin gaske, a lokuta da dama mu kan ga abubuwa da yawa da ranmu yake ɓace a kansu. Wasu za mu iya sauya su amma ba mu taɓa gwadawa ba, wasu kuma sun fi ƙarfinmu, wasu kuma za mu iya amma mun fi jin daɗin mu jingina wa wasu lefin, mu ba wa kanmu hanzari.

    Sau da dama abubuwan da suke ɓata mana rai suna haska mana mu waɗanne irin mutane ne, mene ne burinmu, kuma da za mu samu dama mai za mu iya aikatawa? Don haka yake da muhimmanci mutum ya dinga lura da mene ne a cikin al’umma yake yawan ɓata masa rai.

    Idan lalacewar ilimi yana damunka kuma kana yawan surutu a kan hakan to wataƙila Allah ya maka wata baiwa ne a ɓangaren ilimin, da za ka tsaya ka yi nazarin mafita kuma ka aikata hakan da sai kaga an samu waraka, kai kuma jin daɗinka zai zama gaban kwatantawa domin ka warware wata matsala da take ci maka tuwo a ƙwarya.

    Idan lalacewar tarbiyya ce ta dame ka, kuma ranka yana ɓaci a kan hakan to wataƙila za ka iya zama jagora na kawo sauyi a wannan ɓangaren. Idan rashin wutar lantarki ne yake damunka wataƙila kana da wani abu da za ka iya yi a kai ba ka sani ba. Haka dai za ka yi ta duba abubuwan da suke damunka kana musu kallon “a maimakon a ce ina jiran wani ya zo ya ceto mu, in da ni zan yi ceton ta wanne ɓangare ne zan fi ba da gudunmawa?”

    Akwai mutanen da su dai burinsu a gaza ne su bayyana an gaza, ba lalle abin yana damunsu ba, babbar alamar gane su shi ne kullum surutu suke amma ba sa komai a kan matsalar. To in ka samu kanka a wannan halin abu ɗaya (1) za ka yi, shi ne ka tambayi kanka ko kana da iko kan wannan abin? In ba ka da iko to ka ɗauke hankalinka daga wurin, in kuma kana da iko ka sa himmar kawo gyara.

    A taƙaice dai muna buƙatar mu dinga tunani a kan abubwuan da suke ɓata mana rai don mu ga ta ina za mu iya kawo gyara. Elon Musk haɗarin da duniya ta shiga na gurɓacewar yanayi yana damunsa don haka ya zage dantse yana ta aiki tuƙuru dan ganin an samar da wata duniyar da mutane za su iya rayuwa, sannan ita ma wannan ɗin a ga ya za’a kakkaɓeta daga wannan yanayin.

    Steve Jobs hankalinsa yana tashi in ya tuna girman Computer ya kai girman ɗaki, don haka ya yi ta aiki dan ganin computer ta zama za a iya yawo da ita a hannu ko aljihu. Na kasance ba na jin daɗi irin yadda muke rayuwa, ilimi muna hango shi a can nesa, da nima na tsaya ina jiran gwamnati da shuwagabanni su yi wani abu a kai, amma daga baya na gane cewa ni ma fa akwai ta inda zan ba da gudunmawa, don haka na duƙufa da bincike da kuma yaɗa sakamakon binciken nawa cikin harshen da kowa zai gane don ya zama ilimin ya zo kusa da mu.

    Waɗannan su ne tambayoyin da za ka yi wa kanka kuma ka amsa su da kanka dan gano kai wane ne, babu amsar da ba daidai ba, duk abin da ka gano a nan to daidai ne matuƙar ka tambayi kanka da gaske. Abubuwan da ka kasa gano amsarsu sai ka ci gaba da bincike ta hanyar karatu ko sauraren masu karatu. Wasu kuma amsoshin daga makusantanka da abokananka ne za ka samu amsarsu, kada ka yi ƙasa a gwiwa wajen
    tambayarsu.

    Wasu daga cikin tambayoyin nan sun zo a littafin “Discover yourself na Scott Schewefel”, sai dai misalan da tsarin sun sha bamban, amma za a iya komawa can don ƙarin bayani.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Karanta Ya Ake Sanin Kai?

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ya Ake Sanin Kai?

    Ya Ake Sanin Kai?

    Kamar yadda na sha faɗa a rubuce-rubuce na, mutum haɗin gambiza ne na ƙwayar halittarsa, tarbiyyar da ya samu daga gida, iliminsa, abokanansa, wurin da ya tashi da gogewarsa a rayuwa.

    Su waɗannan abubuwan su suke sa wa mutum ƙauna ko ƙin wani abu, su suke taimakawa mutum wajen yanke shawara, su suke taimakon mutum kan zaɓinsa da ayyukansa, su suke haskawa mutum abubuwan da zai iya yi cikin sauƙi da waɗanda sai ya wahala.

    Wanda yake son ya san kansa yana da kyau ya fara daga ƙwayar halittarsa, domin ita take zuwa da duk wasu halayensa da ya gada a wurin iyayensa da kakanninsa. Don haka ni ma zan fara da shi, ina mai cirowa daga litattafan masana a wannan fanin.

    ❖ Ka San Yanayinka Na Halitta

    Shi yanayin mutum shi ne halayen da aka haife shi da su, waɗanda ya gada daga iyaye da kakanninsa. Kafin ya shiga duniya ya koyi wasu dabarun. Tim Lahaye (marubucin littafin why you act the way you do) ya kasafta mutane zuwa gida huɗu (4).

    Bibbiyu, biyun farko su ne mutane masu surutu da hayaniya (extroverts) sauran biyun kuma su ne shiru-shiru waɗanda ba su cika shiga mutane ba (introverts). Zan kawo dukkanin kashi huɗun haɗi da rauni da ƙarfin kowanne, ina mai cirowa daga wannan littafin.

    SANGUINE

    A ɓangaren masu surutu akwai waɗanda ake kira “Sanguine”, waɗannan su ne irin mutane masu yoyon magana ɗin nan, ba sa iya riƙe bakinsu, duk inda suka shiga dole sai an san suna wurin, akwai su da haba-haba da mutane, ga su kuma ba wuyar sabo, ga saurin ƙulla abota. Ba su san jimami ba, kuma komai suna iya mayar da shi raha, sun yarda da tatsuniyar dawwama cikin farin ciki a rayuwa.

    Ƙarfinsu: suna da saurin sabo, sun iya ba da labari, ba sa gajiya da surutu, suna rayuwa a yanzu (tuna baya ba ya damunsu balle fargabar gaba), suna da nuna tausayawa da alhini kan abu marar daɗi na wani, suna nuna shauƙi kan komai, ga su da raha da kuma shiga cikin ayyukan sa kai dumu-dumu, saurin ƙulla abota, da fara magana in kun haɗu.

    Rauninsu: ba sa iya tursasa kansu su yi abin da ya dace, in ka ba su aiki da wuya ka ga sakamako yadda ya kamata, yanayinsu yana saurin canjawa daga walwala zuwa tausayawa, in ka shiga wani hali sai sun fi ka nuna jimami don haka ma ana iya zargin ko na ƙarya ne in ba a fahimce su da kyau ba, ba su da tsari, sun fi sauran nau’in mutanen girman kai, kuma cikin sauƙi suke samun kansu cikin yaudara, ƙarya da cutar mutane don su ɓoye rauninsu, sannan suna da ƙarawa komai gishiri (kambaba abubuwa).

    CHOLERIC

    Nau’i na biyu cikin masu surutu su ne “Choleric”, shi choleric bai kai Sanguine surutu ba, shi ma yana da saurin sabo da jama’a, shi ma’aikaci ne, yana da zummar cimmawa ko azama, yana zama jagora, yanke abin da zai yi ba ya masa wahala, haka ma yanke wa waninsa, yana wadatuwa da kansa, yana da buruka kuma yana tsara yadda zai cimma su.

    Ƙarfinsa: ƙarfin gwiwa, wadatuwa da kai, hangen nesa, duk abin da ya sa a gaba ana ganin ci gaba (progress), yanke shawara ba ya ba shi wahala, jagora ne, akwai shi da naci, ba ya jira, in ma ba ku yi ba zai yi da kansa.

    Rauninsa: ba ya nuna ƙawa zuci/motsin rai (emotion) dan haka bai cika nuna tausayi ba, yana ganin komai zai iya yi da kansa ko ba taimako, yana danne na ƙasa da shi da musu kama-karya, ya iya ƙeta, bai cika yafiya ba, yana da saurin fusata dan haka ma yake yawan faɗa da mutane, kuma ya iya cin fuska da baƙar magana, tunzura mutum ma yakan iya sa shi nishaɗi.

    MELONCHOLY

    Nau’i na gaba wanda shi ne na farko cikin mutane shiru-shiru shi ne meloncholy, waɗannan su ne irin mutane ma su basira ɗin nan, wanda kowa yake mamakin baiwarsu, akwai su da lissafi, sadaukar da kai, da son ganin komai ya cika ɗari bisa ɗari 100%. Ba su da saurin ƙulla abota amma in suka ƙulla abota da kai ba za su ci amanarka ba, yanayinsu yana saurin canzawa dan haka sun fi duk sauran saurin shiga damuwa.

    Duk da ba su da surutu amma in suka samu wuri za ka rantse ba su ba ne (ko da kuwa a gaban kyamara ne ko wurin wani taro). Akwai su da tattali da rowa, in an ɓata musu
    rai suna da fushi amma ba kamar choleric ba, su a zuci za su cigaba da tafarfasa dan haka suna iya ɗaukar fansa ma.

    Ƙarfinsu: ‘ƴan baiwa ne, akwai su da basira, suna da lissafi, suna son ƙyaleƙyale, suna iya tursasa kansu su yi abin da ya dace, suna da zurfin tunani da tsari, ba su cika son hayaniya ba, kaɗaici yana ba su damar zurfafa tunani, ba su cika yin raha ba saboda komai gaske ne a wurinsu(da muhimmanci suke ɗaukarsa), suna da baiwar ƙirƙira da bincike, duk aikin da suka sa a gaba sai sun ga ƙarshensa, sun fi sadaukar da kansu kan abin da mutane za su amfana ko da su suna cutuwa.

    Rauninsu: saboda zurfin tunaninsu cikas suke fara hangowa game da komai da za su yi, caccanzawar yanayinsu ya sa suna saurin shiga da kuma daɗewa a damuwa, saboda suna son yin komai ɗari bisa ɗari (100%) ya sa ba a cika burge su ba, su da kansu ma suna barin ayyukan da suka ga ba za su cika yadda suke so ba, ba sa shiga mutane, suna kallon rayuwa a yadda ya kamata a rayu ba a yadda take a zahiri ba, basirarsu ta sa suna da saurin zargi da munanan tunani kan abubuwa, suna da saurin kushe abu
    tare da caccakar abin da bai kai mizani ba a ma’auninsu.

    PLEGMATIC

    Kaso na ƙarshe su ne plegmatic, su waɗannan shiru-shirunsu har ya fi na meloncholy domin ba wani shauƙi da za su samu kan su a ciki da zai sa su zama ma su surutu. Da wuya ka ga sun yi fushi ko an ɓata musu rai, suna da mugun sauƙin kai don haka sun fi sauran daɗin zama, suna da kakaci amma ba su cika dariya ba ko da sun yi kakacin, ba sa wuce iya abin da aka sa su, ba su cika son ɗaukar nauyin komai ba, sun fi jiran rayuwa ta zo ta same su.

    Ƙarfinsu: nutsuwa da rashin hayaniya, suna da sauƙin kai da daɗin sha’ani, za ka iya dogara da su, sun iya sasanta mutane, suna da tsari, akwai su da kakaci, suna kallon rayuwa a zahiri, ba sa yin abu ba tare da tunani da kuma kyakkyawan tsari ba, ba sa fara aiki da kansu amma in dai an sa su sai sun kammala shi, suna da son tsafta, ba su cika shiga sha’anin mulki ba, amma duk lokacin da aka zaƙulo su aka ba su mulki, suna yin mulki da ƙwarewa ta ban mamaki.

    Rauninsu: ba sa iya zaburar da kansu, suna da ganda, suna da son kansu, akwai su da rowa da tsoro, suna da yawan damuwa da zullumi kan abubuwa (gujewa ɗaukar nauyi yana farautarsu), ba sa iya saurin yanke mai za su yi balle su yanke wa wani, kullum cikin ƙoƙarin kare kansu suke daga cutuwa ko asara dan haka da wuya su ɗauki kasada, suna da turjiya da tawaye, za ka iya musu bayanin mai kake son su maka, su yi kamar sun yarda amma da sun juya baya su yi a yadda suke so.

    Tim Lahaye bai tsaya a iya kasa mutane gida huɗu ba, ya ƙara bayani da cewa kowanne mutum haɗin gambiza ne na kashi biyu cikin huɗun, kowa ya haɗa ɓangare biyu amma ɓangare ɗaya yana iya fin rinjaye, akan samu ma su haɗa uku amma su suka fi ƙaranci, dan haka yace mutane za su iya kasuwa gida goma sha biyu (12).

    A taƙaice dai kai tsaye mutum ba zai iya gane wanne yafi rinjaye a tattare da shi ba, amma daga bayanan da suka gabata zai fuskanci inda ya fi karkata in ya zauna ya nazarci rayuwarsa. Abu na gaba da zan ƙara shi ne, su waɗannan ɗabi’u na halitta koyaushe suna tare da mutum har ƙarshen rayuwarsa domin gadonsu ya yi, amma
    iliminsa, tarbiyyarsa, imaninsa da aƙidunsa su suke mayar da shi mutum.

    Dan haka yana daga cikin amfanin gane ƙarfi da rauni na halitta mutum zai san ina zai karkata a rayuwa, sannan zai san waɗanne halayya ne zai zama a ankare da su dan kar su dinga ɓata masa hulɗa da jama’a. Misali, sanguine dole ya yi aiki a kan rashin iya sauraren mutane, ya koyi kama bakinsa ya ji suma me za su ce, choleric dole ya koyi dena yin ƙarfaƙarfa da danne na ƙasa da shi, saboda wannan zai sa su daina ganinsa da
    ƙima.

    Meloncholy dole ya koyawa kansa kyakkyawan tunani kan abubuwa, in ba haka ba basirar ta sa ba za ta masa amfani ba, phlegmatic sai ya koyi zaburar da kansa ko zama wurin da za a dinga yawan zaburar da shi in ba haka ba zai tsinana komai ba a rayuwarsa. Wannan raba mutane da Tim Lahaye ya yi ba lallai ya zama cif-da cif ɗari
    bisa ɗari (100%) ba amma a cikin duk rabe-raben da ake yi ana ganin cewa wannan na san ya fi tattara kowa da kowa.

    Manzon Allah tsira da aminci su tabbata gare shi ya ce “ Allah ya halicci Annabi Adamu daga wata damƙa da ya yi daga ƙasa (a wurare mabambanta), don haka ‘ƴan’adam an halicce su a gwargwadon haɗe-haɗen ƙasar. Sai ya zamto a cikin mutane akwai ja, akwai fari, akwai baƙi akwai kuma tsaka-tsakin dukkaninsu, akwai mai kyan hali, akwai mai munin hali, akwai mai sauƙin lamari, akwai mai wahalar sha’ani” (Abu dawud da Tirmizi, kuma sun ce hadisi ne kyakkayawa).

    Akwai wani jan hankali, ko da ka ga halin wani da ka sani kada ka yi gangancin faɗa masa ko da kuwa abokinka ne, domin in ya ga raunin irin wannan mutumin ba zai yafe maka, kuma da wahala ka iya gamsar da shi cewa ba iya bayanin ba kenan, dan haka gara ka bar shi ya gano da kansa in yana da buƙata, sai a kula.

    ❖ Ta Ya Zan Gano Kaina Daga Wannan Rabe-raben?

    Kusan komai da muke yi ya dogara ne da irin tunanin da muke yi, shi kuma tunani ba komai ba ne face tambaya da amsa, tambaya ce kake yi wa kanka a zuci kuma kake amsa ta da kanka a matsayin tunani, don haka yana da kyau ka dinga yi wa kanka tambayoyi ma su kyau.

    Da farko abin da za ka fara tambayar kanka shi ne, ina cikin ma su surutu ko ba na ciki? Idan ka san kana da yawan zuba a ko ina to kana cikin ma su surutu kenan dan haka za ka zama kana tsakanin Sanguine da Chloric. Daga nan sai ka sake tambayar kanka wanne irin surutu ne da ni? Ina hana sauran mutane magana saboda surutuna ko kuwa ina ɗan sararawa su ma su yi? Ina da tausayi in ana ba da labari ko wani ya shiga wani hali ko kuwa ba ruwa na? ina da son girma da nuna iko ko kuwa?

    Idan amsarka ta zama e a tambayoyi biyun farko, ta zama a a, a tambaya ta uku akwai yiwuwar ka zama sanguine, saɓanin haka kuma choleric. Idan dukka e ne ko dukka a a kuma wataƙila kai gamayyar biyun ne. Idan kuwa ɓangaren shiru-shiru kake za ka iya farawa da tambayar kanka ko kana son komai ya zama ɗari-bisa-ɗari? Ka iya lissafi? Kana da zurfin ciki da kawaici? Kana nuna halin ko in kula a kan komai?

    Tambayoyi biyun farko ɗabi’un Melancholy ne, biyun ƙarshe na Phlegmatic, idan e ne amsarka a kashin farko a a a kashi na biyu ka zama Melancholy kenan, saɓanin haka kuwa Phlegmatic. A lura, kamar yadda na faɗa a baya, za ka iya samu amsoshinka duk su zama e ko duk a a, wannan alama ce da ke nuna duk ka haɗa bangarori biyun.

    Ta yiwu kuma ka ga wasu halayenka sun faɗo a gidan ma su surutu, wasu kuma a gidan marasa surutu, in haka ta faru sai ka sake duba sauran abubuwan da suka gabata a bayanin rauni da ƙarfi dan ka ga inda kafi karkata. Bayan ka gano gidan da ka faɗa a wannan kashe-kashen sai kuma ka amsa waɗannan tambayoyin da za su zo a babi na gaba.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Karanta Amfanin Sanin Kai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Sanin Kai

    Amfanin Sanin Kai

    Kafin na yi nisa cikin wannan littafin, yana da kyau na fara kawo kaɗan daga cikin amfanin sanin kai ga kowanne mutum da yake da mafarkin rayuwa mai kyau.

    ❖ Sai Ka San Kanka Za Ka Ci Gaba

    Babu wanda ya zo duniya da sani, kowa a gidan duniya ya san duk abin da ya sani. Haka nan babu wani da yake samun ci gaba sai ya ci gaba da neman sani, duk wanda ya tsaya da neman sani daga nan rayuwarsa take ƙarewa.

    Za ka yi mamaki idan na ce da kai ‘ƴan gargajiyar da muke gani a yanzu masu ilimi ne a zamaninsu, sun ƙi yarda su karɓi ilimin sabon zamanin da suke ciki ne ya sa ake musu kallon ‘ƴan gargajiya. Haka duk wanda ya ƙi ci gaba da neman ilimi zai zama a zamanin gaba.

    Mene ne alaƙar ci gaba da sanin kai? Sai ka san kai wane ne da matakan da ka taka na ilimi kafin ka san inda za ka ɗaura. Wanda ya san bai iya turanci ba misali, ba zai yi karambanin karanta littafin turanci mai wahala ba, in kuwa zai karanta da wuya ya tsinci wani abu. Inda iliminka ya tsaya daga nan za ka ɗaura in ka san kanka, in ba ka san kanka ba kuwa za ka iya kamawa daga ko ina sai abu ya yi nisa ka ga ashe akwai wani giɓi a baya da ka baro.

    Sanin kai wane ne zai haska maka wuraren da kake da rauni, da wuraren da
    Allah ya maka baiwa, hakan zai taimake ka ka mayar da hankali wajen inganta baiwarka sama da ƙorafi a kan gazawarka. Wanda ya mayar da hankali kan inda baiwarsa take shi ne rayuwarsa take ci gaba ba wanda yake ta faɗi-tashi da rauninsa ba.

    Hakan kuwa ba lallai ya zo da mamaki ba saboda ƙa’idar ita ce: duk abin da aka mayar da hankali kansa shi ne yake ƙara girma da haɓaka.

    ❖ Za Ka Dena Haɗa Kanka Da Wasu

    Muna rayuwa a wani zamani da bayanai suka yawaita, abubuwan da muke karantawa, kallo da saurare ba ƙaramin tasiri suke mana ba a rayuwa, don haka muke shafe shekaru ma su tsawo a rayuwarmu muna kamanta kanmu da wasu, muna ganin cewa mu ma ya kamata mu yi rayuwa irin yadda suke yi, har ma mukan shiga damuwa a dalilin hakan.

    Wanda ya san kansa ba zai tsaya damuwa da kwatanta rayuwarsa da ta kowa ba, ya san me yake so, ya san ina zai je, ya san kuma hanyar da zai kama domin isa wurin, to yaushe zai tsaya tunanin wane ba haka yake rayuwa ba? Sanin kaina ya taimaka min sosai wurin rayuwa irin wacce ta dace da ni, zan ga mutane suna yin abubuwa, amma saboda abubuwan ba su shalle ni ba, ba na fatan na zama su, ina so ni dai kawai na fi yadda na ke a jiya.

    ❖ Za Ka So Kanka

    Son kai yana daga cikin abubuwa mafiya wahala a wannan zamanin, mutum ya ji yana ƙaunar kansa a yadda yake ba tare da jin haushin gazawarsa ba. Yana daga cikin dalilin da ya sa malaman tarbiyya suke ba wa iyaye shawarar su dinga nuna wa yaransu ƙauna, yaba musu in sun yi abin kirki, yaba musu a cikin mutane in sun yi bajinta, ba su ƙwarin gwiwa, rashin gwale su ko disga su, neman shawararsu da ba su dama su yi wasu
    abubuwan da kansu (Dr. Aisha Hamdan: Nurturing Eeman in children).

    Wanda ba ya son kansa ba zai taɓa tsinana komai ba, zai cika kansa da tunanin gazawarsa da rauninsa dan haka sai wannan ya zama masa matsala. Wanda ya san kansa ya san wuraren da Allah ya fifita shi a kan sauran mutane dan haka zai gode masa kuma zai cigaba da aiki tuƙuru a wannan fannin. Haka nan kuma zai san wuraren da yake da rauni, don haka zai dinga taka-tsantsan a wannan ɓangaren.

    ❖ Za Ka San Abokanka

    Zaɓar aboki wani ɓangare ne mai wahala a rayuwa musamman ga mutane shiru-shiru irina, ba mu da saurin ƙulla abota. Amma duk da haka duk lokacin da muka san kanmu muna samun sauƙi wurin zaɓen aboki. Aboki wani jigo ne na rayuwa, ana tasirantuwa da shi matuƙa, dan haka ake so mutum ya yi taka-tsantsan wurin zaɓar abokai.

    Misali, a sanin da na yi wa kaina tunani ya fi aikina yawa, zan daɗe ina tunanin abu har sai na gano ba zai yiwu ba sai na watsar tun kafin na fara, da na ƙulla abota da Mallam
    Bahaushe wanda shi kuma yana aikin yana tunanin a lokaci guda, sai ya zama na tasirantu da shi na koyi haɗa dukka biyun ni ma daga gare shi.

    Wataƙila da ba mu ƙulla abota ba da wannan littafin ma yana nan zaune cikin tunanina har yanzu. Sanin kanka da sanin manufarka zai sauƙaƙa maka wannan ɓangaren na
    rayuwarka, za ka yi abota da wacce ta ku ta zo ɗaya, za ka yi haɗaka da wanda za ku ƙarfafi raunin juna, za kuma ka ci gaba da mutunci da sauran mutane, domin ƙa’idar dama ita ce “ba a ce sai kowa ya zama abokinka ba, amma za ka iya yin mutunci da kowa”.

    ❖ Za Ka Koyi Yi Wa Mutane Uzuri

    Wanda ya san kansa yana saurin sanin cewa mutane kowa da yanayin halittarsa, yadda yake ba haka kowa yake ba, kuma yana lura ya gane ya mutane suke, hakan yana taimakonsa wajen yi musu uzuri.

    Kafin na samu haske kan ni wanene wannan yana daga cikin ɓangaren da ya fi wahalar da ni, sai in kasa gane me yasa mutane suke abu iri kaza, ko meyasa suke son su ga ina yin abu iri kaza, ko meyasa su ba sa lura da kaza da kaza.

    Wannan Ilimin yana daga cikin abubuwan da suka ɗaga darajar Ma’aiki mai tsira da aminci kan sauran shuwagabannin duniya. In kana bibiyar tarihinsa za ka ga yana bambance sahabbansa ko wurin sanya su aiki yana mai la’akari da yadda suke. In ana buƙatar zafi ba ya neman sayyadina Abubakar, sayyadina Umar yake nema, haka nan in ana buƙatar wata maslaha ko wani abu na sauƙin kai, ba ya neman sayyadina Umar sai dai ya nemi sayyadina Abubakar. A rubuce-rubucena na “Iya ruwa…” na kawo
    makamancin wannan misalin.

    ❖ Za Ka Ɗauki Alhakin Rayuwarka

    Sanin kai yana ragewa mutum yawan ƙorafi da ɗaurawa wasu lefin matsalarsa. Wanda ya san kansa zai gwammaci ya mayar da hankali kan abin da zai amfani rayuwarsa sama da ba wa kansa hanzari ba gaira ba dalili. Kai ne ya kamata ka zama a kujerar mai tuƙi a motar rayuwarka ba a kujerar mai zaman banza ba (Sean Covey: 7 habits of highly effective teens).

    ❖ Rayuwarka Za Ta Yi Sauƙi

    In ka san kanka komai zai zo maka da sauƙi. Misalin wanda ya san kansa kamar misalin me yin bulaguro ne, ya san inda za shi, ya san a ina zai samu mota, ya san wacce hanya za a bi. Idan ka san kanka komai za ka san irin na ka, tun daga kan abinci, tufafi, abun hawa, wasa, kai hatta kallo da zuwa wuraren nishaɗi, za ka je ko aikata abin da bai ci karo da kai waye ba ne, balle ka samu ƙunci.

    Za ka rage damuwa da kallon da mutane za su maka don kai ka san abin da ba su sani
    ba game da kanka (kamar yadda na yi tsokaci a baya, akwai lokacin da dole sai ka saje da su don maslaha).

    Kana buƙatar wani cikin waɗannan abubuwan a rayuwarka? In amsarka e ce to mu je zuwa, in kuwa ta zamto a a, ina mai ba ka haƙuri wannan littafin ba na ka ba ne.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Ka Ɗauka Ka Sani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ka Ɗauka Ka Sani

    Ka Ɗauka Ka Sani

    Gabatarwa

    Da sunan Allah mai Rahama mai Jin ƙai.
    Abin da za ka karanta mai yiwuwa ya iya canja maka rayuwa, yana da kyau ka samu wurin da babu kowa ka nutsu, ka kashe tv, ka kashe data, domin karanta wannan ɗan littafin a cikin cikakkiyar nutsuwa.

    Ba haka kawai na faɗa ba, ni ganau ne ba jiyau ba, na sha fama da abubuwa da dama a rayuwa, ga shi dai babu abin da na nema na rasa a gida, amma kullum ina ganin rayuwata tana shan bamban da ta sauran jama’a.

    Na daɗe ina yi wa kai na tambayoyi game da rayuwa, wasu daga cikin irin tambayoyin sun haɗa da:

    • Me yasa wasu mutanen surutu da shiga mutane ba ya musu wahala wasu kuwa yake musu?
    • Me yasa wasu sun gwammance su zama kullum suna su kaɗai wasu kuma ko da kuɗi ba za su iya ba?
    • Me yasa wasu duk abin da in dai a aji za a koyar ba abin da zai hana su ganewa wasu kuma sai an nuna musu shi ɓaro-ɓaro sun gani ko ma sun taɓa?
    • Me yasa wasu suke da saurin sabo da ƙulla abota wasu kuma sai an ja daga?
    • Me yasa wasu sun fahimci rayuwa da wuri wasu kuma har sun fara gangarawa amma ba su san inda suka dosa ba?
    • Me yasa wasu suke da naci, duk abin da suka sa a gaba sai sunga abin da ya turewa buzu naɗi, wasu kuma daga sun fara kamar ana mintsininsu suke bari?
    • Me yake sa mutum ya ji ga shi dai yana rayuwa kuma yana cimma abubuwa amma ba ya ganin ma’anar rayuwar ta sa, wani da bai kai shi ba kuma yana masa ganin ya kai wani mataki har yana sha’awarsa?

    Ba iya tambayoyin ba kenan, wannan kaɗan daga cikinsu ne, in kai iri na ne mai yawan zama yana ƙoƙarin gano wani abu ba mamaki ka taɓa yi wa kanka wasu daga cikin tambayoyin nan. Ko ka samu amsa ko ba ka samu ba, ni dai abin da nake fahimta shi ne, akwai lokacin da mutum yake matuƙar buƙatar ya san kansa, sanin kansa ne zai ba shi damar iya amsawa kansa mafi yawancin tambayoyinsa.

    Wasu tambayoyin ko da ka tambayi makusantanka, ko wasu da kake ganin sun fi ka, za ka ga ba za su ba ka amsa a yadda kai kake kallon abun ba, domin yawancin jama’a suna magana ne suna masu la’akari da yadda su suke.

    Wannan dalilin kaɗai zai iya hana abin da za su faɗa ya iya gamsar da kai. Amma idan kai ma ka san kanka fa? Za ka san a yadda za ka musu tambayar, kuma za ka fahimci a yadda suka kalli abun sannan ka alaƙanta amsarsu kai ma da yanayinka.

    Ni ba masanin kimiyya ko halayyar ɗan Adam ba ne, ni mai sha’awar rubuce-rubuce ne kawai, a wannan ɗan littafin na yi ƙoƙarin tattara abubuwan da na ci karo da su a halin binciken da na yi ta yi game da sanin kai na.

    Tambayoyi da dama na samu amsarsu, waɗanda ban samu ba kuma ina ci gaba da nemansu. Jin daɗin da nake yi a yanzu da na fahimci kaina ya wuce misali, haka kawai don mutane suna yin abu ba zai sa ni na yi ba, in ba ni da buƙatarsa (wannan ba ya kore siyasa ta rayuwa, in ka tsinci kanka a wurin da kowa yake da jela kai ma ka samu tsumma ka ɗaura, in ba haka ba za a dinga kallonka a matsayin barazana har a iya maka illa ta inda ba ka yi tsammani ba).

    Abubuwan da na ke sa ran za ku ƙaru da su a wannan ɗan littafin ga su kamar haka:

    • Meyasa ba ka san kanka ba
    • Muhimmancin sanin kai
    • Dabarun sanin kai
    • Amsa wasu tambayoyi da za su bayyana maka kanka
    • Muhimmancin samar da manufar rayuwa
    • In ba za ka iya sanin kanka ba to ka yi…

    Abin da na ke buƙata daga kai mai karatu shi ne wannan littafin na rubuta shi ne a matsayin wata ƴar ƙaramar tunatarwa ga kaina da sauran mutane da nufin ya yaɗu a tsakankaninmu mu ma su jin yaren Hausa. Don haka in ka samu kuma ka karanta kada ka bar shi a zaune haka nan, ka turawa abokananka ko da guda 3 ne domin su ma su amfana.

    Idan ka karanta wannan littafin ba ka ƙaru da komai ba, na bar “link” na whatsapp ɗina a kowanne shafi na littafin, za ka iya min magana don bayyana min kura-kuren da ke cikin littafin, da kuma bubuwan da suka sa littafin ya gaza wurin amfanar da kai.

    Idan ka ƙaru sosai kuma kana sha’awar cigaba da samun rubuce-rubuce na, ka ziyarci shafinmu na fesbuk da yake saman kowanne shafi domin mu ci gaba da ƙaruwa da juna.
    Allah nake roƙo ya amfanar da duk wanda wannan littafin zai isa gare shi, sannan ya ba mu ikon yin aiki da abubuwan da suke ciki ni da ku gaba ɗaya.

    Ka Ɗauka Ka Sani

    Sau da dama in na fito daga gida zan ga mutane a zazzaune suna hirar duniya ko a ƙarƙashin bishiya ko a kan wani dakali ko benci. Cikin irin hirarrakin nan da suke zai yi wuya ka ji babu labarin wani a ciki.

    Misali idan hirar ƙwallo suke za ka ga sun san komai game da gwaninsu, sun san haihuwarsa, garinsu, iyayensa, yaushe ya fara buga tamola, ƙungiyoyin wasannin da ya bugawa wasa, kofi nawa ya taɓa ɗauka, yanzu a wacce ƙungiya yake, nawa ne albashinsa da sauransu.

    Haka nan in hirar siyasa suke yi, komai na wannan ɗan siyasar sun sani, in hirar malamai ce ma haka, kowanne hali suke ciki suna sane. Haka nan idan ‘ƴan wasan kwaikwayo ne ko ma su sarauta. Abun ba ya tsaya a iya shahararrun mutane ba ne kaɗai, har waɗanda ake unguwa ɗaya da su, waɗanda suka kai, da waɗanda ba su kai ba za ka ga duk an san komai nasu.

    Wani abun ban mamaki shi ne da za ka kalli wannan mutumin shi a karan kansa, ta hanyar nazarin halayyarsa za ka fahimci ya san kowa ban da mutumin da ya fi cancanta ya sani, wato kansa.

    Ba haka kawai mutane suke nuna halin ko in kula da sanin kansu ba, saboda daɗewar da suka yi da kansu ne ya sa suka ɗauka sun san kansu, don haka suka mayar da hankalinsu kan sanin sauran mutanen duniya.

    Wannan kuwa ba abun mamaki ba ne, domin bincike kan bincike na masana ya tabbatar da cewa mutum halitta ce da dole sai ta yi imani da wani abu, in ba ta samu abun da za ta yi imani da shi ba sai ta ƙirƙiro abubuwa, ko ta dinga zato da tsammani kan wani abu, sannan ta mayar da zaton nan gaskiya a zuciyarta (Andrew Newberg: why we believe what we believe).

    Wataƙila wannan dalilin ya sa mutane da yawa suke ganin sun fahimci kansu, idan kana/kina cikin mutanen da suke ta ƙoƙarin ganin sun fahimci kansu amma sun rasa mafita saboda ƙarancin bayanai ko taimakon da zai haskaka musu su waye, to wannan littafin na ka/ki ne.

    Idan kana cikin mutanen da sun riga da sun ɗauka sun san kansu, amma hakan bai taimake ka wajen tsinana wani abu a rayuwa ba, yana da kyau ka ɗan duba wasu shafuka kaɗan cikin littafin nan. Idan ka fahimci kanka, kuma ka gamsu haka kake amma kuma ka kasa yin komai da rayuwarka duk da haka, akwai shawarwarin da zan kawo a gaba da za su taimaka maka. Sai a biyo ni domin shan karatu.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Sababbin Karin Maganar Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Juyin -Juya Hali A Rubuce-rubucen Littattafan Adabi

    Juyin -Juya Hali A Rubuce-rubucen Littattafan Adabi

    Duk da cewa maza su suka. fara rubuce tun 1933 Mukhtar (2004). Amma wacce ta fara Rubuta ƙagaggen Labari na Hausa ita ce Hafsatu Abdulwaheed, Abdalla Uba Adamu (2024). Mace ta farko ‘Yar Arewa da fara rubuce-rubuce a Hausa da Fulatanci ita ce Dadasare Abdullahi Uwargidan Dr. R M. East takan taimaka wa Maigidanta Jaumisare (R.M. East) da labaran da akan saka a Jaridar Gaskiya Ta fi Kwabo da kuma tace labaran. Dadasare (2019)

    Waɗannan su ne wasu daga cikin talife-talifen wannan marubuciya wacce babu shakka ta yi namijin ƙoƙari a wannan nau’i na Adabin na tailfin Hausa da Fultanci. Bayan sai ita Zuwaira Isa wacce ta rubuta ƙagaggen littafi a 1972 sannan tana ‘yar makaranta a Rikkos can jos amma ba a buga ba sai daga baya, mai suna Ɗaki Ba Ya Tashi Jinka Ya Zauna.

    Ya iso kasuwar ta Kano tun 1992, to sai bayan shekaru uku ne wato a 1995 littafin Bilkisu ya fara bayyana kamar yadda aka gani a jerin littattafan nata, a sama. Ita kuma Bilkisu it ace ta fara rubuta littafai masu na Hausa, kimanin guda ashirin cikin shekaru uku zuwa huɗu.

    Littattafan zuwaira Isa Danlami Jos sun haɗa har da:

    • Zuwaira Isa daki Ya Tashi Jinka Ta Zauna (1992) Gaskiya corporation Ltd.Zaria.
    • Zuwaira Isa Labarin So (1995) littafi na 1-3 City Publishers Jakara, Kano.
    • Zuwaira Isa Sants in Soyayya (1996) littafi na 1-3 city Business Centre Daneji, Kano.
    • Zuwaira Isa  kissar Mata (1996) City Publishers Goron Dutse Road Jakara,Kano.
    • Zuwaira Isa  Wahala Siraxin Masoya (1997) Sauqi Bookshop and Publishing Company Sabon Gari,Kano.
    • Zuwaira Isa  ‘Ya’ya Mata (1999) littafi na 1-3 M Square Telecomm,Zoo Road, Kano.

    Sauran littattafan wannan marubuciya da muka ji labarinsu amma ba su zo hannuna ba har lokacin da zan buga wannan littafi sun haɗa har da:-

    • Zuwaira Isa  A Lallaɓa Auren Zamani
    • Zuwaira Isa  Mowar Mata
    • Zuwaira Isa  Ƙwarya Ta Bi Ƙwarya
    • Zuwaira Isa  Kara Da Kiyashi
    • Zuwaira Isa  A Ci Duniya Da Tsinke
    • Zuwaira Isa  Duniya Labari, Ciwon ƙauna, ƙishirwar Bege (d.s.)

    Bayan waɗannan, mata marubuta, daga cikin maza kuma waɗanda suka fi fice kamar yadda wallafe-wallafe ya nuna akwai Nazir Adam Salih da kuma Ado Ahmad Gidan Dabino. Wasu daga cikin littattafan Nazir Adam Salih sun haɗa da:-

    • Nazir Adam Salih  Me Ya Fi Kuxi? Kamnas Publishers, Kano.
    • Nazir Adam Salih  Kibiyar Ajali littafi na 1-2 (1996) City Business Centre Daneji, Kano.
    • Nazir Adam Salih  Naira Da Kwabo littafi na 1-2 (1998) Jet Age Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Birnin Sarauniya (1998) Qamnas Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Ta Leƙo Ta Koma (b. kw.) Qamnas Publishers Kano.
    • Nazir Adam Salih Mutuwar Kasko (1999) Layeet Printers Kano.
    • Nazir Adam Salih  Aljani Ya Taka Wuta (2000) Jet Age Printers Kano.
    • Nazir Adam Salih A Ci Bulus (b. kw.)
    • Nazir Adam Salih  Kudi Da Maciji (b. kw.)
    • Nazir Adam Salih  Damisar Takarda (2000) Jet age Printers Kano.

    Amma shi Ado Ahmed Gidan Dabino shi ma ya taka muhimmiyar rawa a cikin wannan nau’in adabi inda littattafansa suka fito kamar haka:-

    • In Da So Da Ƙauna (1991) Gidan Dabino Ado Ahmed  Publishers, Kano.
    • Masoyin Zamani I (1993) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Wani Hanin Ga Allah (1994) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Kaico! (1996) Gidan Dabino Publishers, Kano.
    • Duniya Sai Sannu (1997) Gidan Dabino Publishers, Kano. Mukhtar (2004)

    Adabin Kasuwar Kano

    To amma a cikin shekarar 1984 wata al’adar rubuce-rubuce ta ƙagaggun littattafai ta kunno kai wadda aka sa wa suna Adabin Kasuwar Kano, a Turance “Kano Market Literature”. An sami wani jigo na soyayya inda ya yi tasiri sosai da sosai a cikin wannan adabin. Daga cikin waɗanda suka share fage akwai irin su littafin;

    • Rabin Raina littafi na ɗaya(1984) na Talatu Wada Ahmed
    • Soyayya Gamon Jini (1986) na Ibrahim Hamza Abdullahi
    • In Da Rai (1987) na Idris Imam
    • Budurwar Zuciya (1987) na Balaraba Ramat Yakubu
    • Kogin Soyayya (1988) na A.M. Zahraddeen
    •  Idan So Cuta Ne (1989) na Yusuf M. Adamu.

    (Duba muƙalar Yusuf M. Adamu 1996).

    Bayan wannan an sami mace a karon farko wacce ta yi fice a cikin rubutun adabi na Hausa inda ta rubuta ƙagaggun littattafai a ƙalla sama da guda ashirin (20) a cikin shekaru huɗu rak. Wannan kuwa ita ce uwargida Bilkisu Salisu Ahmed Funtuwa, wadda kafin ta yi aure ake kira Bilkisu Ibrahim. Nabature Funtuwa.

    Ita dai wannan marubuciya ta yi fice a kan waɗannan rubuce-rubuce ba ma kawai tsakanin mata ba, hatta cikin mazan ma na wannan nau’in adabin babu wanda ya kamo ta. Binciken da muka yi, ya nuna cewa. Makaranta littattafan wannan nau’in adabin har bincikawa sukan yi ko sabon littafinta ya fito su yi maza su karanta don kada wani ya ba su labarinsa. Kaɗan daga cikin irin waɗannan rubuce-rubuce nata sun haɗa har da:-

    • Bilkisu S.A.F Allura Cikin Ruwa, (1995) Gidan Dabino Publishers Kano, Nijeriya.
    • Bilkisu S.A.F Sirrin Ɓoye littafi na 1-2 (1996) City Publishers Jakara Kano, Nigeria
    • Bilkisu S.A.F Wa Ya San Gobe littafi na 1-3 (1996) City Pulishers Jakara Kano, Nijeriya.
    • Bilkisu S.A.F Ƙarya Fure Take, littafi na 1-2 (1996) Nabila Surayya Bookshop.
    • Bilkisu S.A.F Gaskiya Na Mafaɗinta littafi na 1-2 (1997) Printed
    • Bilkisu S.A.F Kyan Ɗan Maciji littafi na 1-2 (1997) Printed
    • Bilkisu S.A.F In Da kwaɗayi littafi na 1-2 (1998).
    • Bilkisu S.A.F Ki Yarda Da Ni (b. kw) littafi na 1-2
    • Bilkisu S.A.F Sa’adatu Sa’ar Mata (b. kw)
    • Bilkisu S.A.F Maryamu (1999) littafi na 1-2
    • Bilkisu S.A.F Mugun Zama (1999) littafi na 1-2 Anti Bilki Bookshop Kano
    • Bilkisu S.A.F Kowa Ya Raina Tsaiwar Wata (1999) littafi nal-2 Anti Bilki Bookshop Kano.

    Kammalawa

    A taƙaice, takardar wata tafarki ce a fagen adabin Hausa, musamman ta fuskar rubuce-rubucen da suka shafi tarbiyya da gyaran halaye. Saboda haka Littattafan ƙagaggun Labari ba wai labaran soyayya kawai suke ba, har ila yau suna nuna irin rawar da adabi ke takawa wajen sauya tunani da ɗabi’a.

    A matsayin shawara, akwai buƙatar a ci gaba da nazarin irin waɗannan marubuta domin fahimtar tasirin rubuce-rubucen Hausa wajen gina tarbiyyar matasa da inganta al’ummar Hausawa gaba ɗaya. Duk waɗannan suna jan kunne ne da a tarbiyyantar da mutune su yi aiki da tarbiyya a cikin mu’amalarsu da mutane.

    Ana cusa tarbiyya wajen horar da mutane ko ilimantar da su, ko ta hanyar rubutu, domin a gano kaifin hankalin mai karatu idan da buƙatar gyara a gyara maka ko a cusa musu labarai na ban tausayi ko na jin ƙai ko ta hanyar yi musu tarbiyyar ta ta hanyar gargajiya misali Karin Magana da Tatsuniya ko kuma ta hanyar gaya musu wani labari mai daɗi na baka ko a rubutaccen ƙagaggen labari wanda kuma shi ne muka yi magana kai.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Samuwar Rubutun Ajami

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    Mijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe

    EPILOGUE

    Bayan shekaru 3. An yi auren Afaf an kai ta gidanta, yaron da ta aura ƙanin abokin Abbanta ne, da kanta ta je ta kai wa Khadeeja katin bikin nata wanda ta karɓa cike da girmamawa. Ta yi mata magiya a kan ta je amma duk da haka ba ta je ba, domin ba ta son abinda zai haɗa ta da Naja da dangin Mustapha a cikin taro.

    Kuma duk yanda Mustapha ya so ya saka ta a cikin shawarar bikin Afaf ɗin da inda zai sayi furniture haka ta zame da wayo da dabara har ya gaji ya rabu da ita. Yana nan dai yana bibiya da kuma addu’ar ta yarda su mayar da aurensu. Yana zaune a ɗakinsa a kan dadduma yana hutawa bayan sallar la’asar kwana biyu bayan auren Afaf haka kawai ya ɗauki waya ya kirawo Khadeeja.

    Ya gyara zama ya jingina da bangon da ƙofar ɗakin take jiki ta yanda idan aka buɗo kofar aka shigo zai zama yana bayan ƙofar kenan. Bayan ta amsa suka gaisa suka shiga hirarrakinsu, tana tambayarsa labarin biki. A haka har yace ‘Kin ga da kin yarda ai da tare da namu za a ɗaura.’

    Ta yi dariya tace ‘Kai kuwa ka ƙi ka bar maganar nan. ‘Ba zan bari ba Khadija, har sai kin amince. Ko na tsufa ma sai na dawo da ke ko da takaba ne kya yi min sai mu haɗu a aljannah. Dariya kawai ta yi don ba ta da amsar da za ta ba shi. Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Duk wani condition da kike so Khadeeja ki saka na yi miki alƙawarin zan cika in dai za ki zama mata ta.

    Just one more chance Khadeeja, ki daina wahalar da zuciyata haka. Ta yi murmushi mai sauti ba tare da ta ce masa komai ba; tabbas yana nema ya gamsar da ita ta sake amincewa da aurensa, amma a halin yanzu ba ta san amsar da za ta ba shi ba. Ya gaji da shirun kuma yana ji a jikinsa cewa kalamansa sun fara yi mata tasiri.

    Ya katse shirun yace ‘Gobe da safe zan shigo, ok? ‘Ok, Allah ya kai mu. Amma ina da programme da safe so ka bari sai bayan azahar. ‘Ok, I will take you out to lunch then. No execuses. Ta yi dariya ‘Ka dai san ba zan je ba ko? Kada ma ka fara wata rigimar daban.’ ‘In dai rigima ce ai a wajenki na koya. I will see you tomorrow at lunch.’ Ya ajiye wayar ba tare da ya bari tace wani abu ba.

    Ko da ba za ta yarda ya fita da ita lunch ɗin ba ya fi so ta bar shi ya kwana da murnan zai fita da Khadeeja gobe, in ya so idan ya je office ɗin su yi faɗan da suka saba. Tana tsaye a jikin ƙofar ɗakin tana jinsa, duk abinda ya faɗa tana ji. Sai da ya ajiye wayar sannan ta banka ɗakin ta shiga a fusace.

    Firgigit ya juyo ya kalli ƙofar da aka mako, yace ‘Ya haka kamar za ki fizge ƙofar? Me ya faru ne? Ko wani abun ya biyo ki? Ta tsaya tana masa kallon raini tana jijjiga, sai da gaji da kallon nasa sannan a fusace tace ‘Mustapha na gaji da wulaƙancin da kake mina a kan matar nan, shekara huɗu ana abu ɗaya saboda tsohon naci. Wallahi babu ruwan Allah da kun taɓa aure alaƙarku haramtacciya ce.

    Kuma idan ma zina kuke Allah zai kama ku. Faɗan nata bai harzuƙa shi don ya saba ji, idan ma ba ta ji yana waya da Khadeejan ba kullum cikin duba masa waya take. Ba sa magana ta whatsapp don haka kullum cikin duba calls take, da zarar ta ga call ɗin Khadeeja to sai ta yi wannan masifar. Ya miƙee ya naɗe daddumar yana cewa ‘Kada ki kuskura ki jefi khadeeja da wannan kalmar yanzu ranki zai ɓaci, kuma kin sani.’

    Ta riƙe ƙugu tana dan zare ido tana cewa ‘Ohh! Yanzu kai ka fi son Khadeeja kenan dan kanka, kai na jefe ka da koma menene amm kada na jefi Khadeeja ko? To wallahi da kai da ita baku isa ba…. ‘Ke kika sani.’ Ya faɗa tun kafin ta ƙarasa faɗin abinda take faɗa, ya ajiye daddumar ya kewayeta ya fice daga ɗakin.

    Ta juyo ta bi bayansa da kallo cike da takaici sannan ta wuce ta zauna a gefen gado ta zuba fuskarta a tafukan hannunta ta fashe da kuka. Wannan wane irin wulaƙanci ne, tana murna ya saki kishiyarta amma kullum suna tare, ita kuma tana nan ya kulle ta a gida. Wannan wace irin musiba ce? So take ta ware rana ta je ta sami Khadeejan a office ɗin nata ta tara mata mutane amma dai tana tsoron kada Mustapha ya sake ta a kan hakan; don yanzu ta ga kamar ma ba a haiyacinsa yake ba.

    To yanzu babu aure a tsakaninsu yana mata wannan tsohon nacin idan kuma ta dawo ya za a yi? Ita menene makomarta ya dawo da rabin ransa me ƙaunar ‘yayansa. Ta ɗora hannu a ka ta sake rushewa da kuka.

    END

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Huɗu

    Dole tana ji tana gani ya kafa mata doka idan dai har zai ci abinci to parlor ɗin kasa zai ci. Babu yanda ba ta yi da shi ba yaran su dinga hawowa sama amma yace ba za su hau ba tunda ita saman take so a bar mata, haka ta haƙura ta saka masa ido saboda abun yana nema ya zama matsala a tsakaninsu.

    Duk wani taimako da aiki da malamai za su yi mata tana kan yi sai dai abun ya ƙi yi, idan ya yi kamar zai kama sai kuma ya sake botsare mata. Idan dai tana son ganin walwalarsa to ta yi wa yaran nan yanda suke so kuma ba tare da ta yi masa wani ƙorafi ba. Burinta ɗaya yanzu a aurar da Afaf domin haka ne kawai take ganin za ta sami natsuwa a gidan nan.

    Don a halin da ake ciki komai zai yi da Afaf yake shawara, wasu lokutan ko ta ba shi list ɗin cefanen gidan sai ya tambayi Afaf abinda take buƙata ita da kannenta ya siyo musu. Idan kuma ya kawo kayan sai ya tsaya a ƙasa Afaf ɗin ta ware nasu kayan sannan ya hau mata sama da sauran. Haka dai take haƙuri, musamman da yake ya iya lallaɓa ta ya tsara ta kawai dai ya nuna mata yaran nan nasa ba za su taɓu ba.

    Haka rayuwarsu ta cigaba.

    Duk yanda yake jin zai samu Khadeeja ta saurare shi ya gagara, ga shi kuma sai a yanzu Allah ya jarrabe shi da ƙaunarta. Kusan kullum sai ya yi mata waya, idan ta ga dama ta ɗauka idan kuma ba ta ga dama ba ta ƙi ɗauka. Ya mayarwa kansa duk Juma’a da yamma sai ya je gidan duba Hammad, sai dai hakan bai ba shi damar ganinta ba.

    Domin idan ya je ko da ya yi mata waya haka za ta saka a buɗe masa parlor ɗin baƙi ta turo masa Hammad, har ya gama hirarsa da Hammad ya tafi ba za ta fito ba. Don haka wasu lokutan sai kawai ya rutsa ta a office inda dole ta zauna su gaisa har su ɗan yi hira. Abu ɗaya ne yake hana shi zaƙewa a kan maganarta saboda har yanzu yana jin kunyar Baffanta, bai san da wane bakin zai je yace masa ya sake ba shi auren Khadeeja ba.

    Shi yasa ya dage yake ƙoƙarin ganin ya gamsar da Khadeejan ta je wa Baffan da maganar da kanta. Kwanci tashi har shekara ta zagayo. Tun da ya gama haɗa takardun yake cike da farin ciki, haka ya kwana cike da zaƙuwa sabodan yanda yake son gari ya waye ya je ya sami Khadeeja ya yi mata albishir.

    Yana fita office ɗinta ya fara tsayawa, ya yi sa’a kuwa ta riga ta zo. Kamar yanda ya saba a cikin office ɗin ya same ta tana zaune tana editing script ɗin da za ta yi amfani da shi wajen gabatar da show ɗinta. Yana shiga ya tura ƙofar sannan ya yi wa kansa mazauni a kujerar gabanta cike da walwala. Bayan sun gaisa yace ‘Kina jin daɗinki fa, kin ga yanda kike sheƙi kuwa.

    Ta yi dariya tace ‘Don Allah ka bari, haba. Ko waya ma ba ka yi min ba kace min za ka zo to da ka zo na riga na shiga studio fa? Shi ma dariyar ya yi yace ‘Sai na jira ki mana. Ai idan kina son na daina zuwa wajen nan to ki yarda mu mayar da auren mu mu huta, in ba haka ba dole kullum na zo nan na yi attendance don duk masu shirin yi min shigar sauri su ganni su san ina nan ba fashi.’

    Ta sunkuyar da kai don ba ta san me zata ce masa ba, amma dai yawan zuwan nashi office ɗin ya fara gundurarta. Ba wai don ba ta so a gan shi ba ne kuma ba wai tana jin ya isa ya hana ta kula wanda take son kulawa ba; kawai dai tana so ya ɗan ba ta space tunda ita dai ta gama magana a kan lallai ba za ta koma gidansa ba kuma har yanzu hakane a ranta.

    Muryarsa ce ta katse mata tunanin da ya kirawo sunanta, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta kawar da kai. Yace ‘Ki sauwaƙe mana wahala ki yarda mu mayar da aurenmu, duk wani abu da ya ɓata miki rai a baya na yi miki alƙawarin ba za ki sake gamuwa da shi ba a zamanmu.’

    Ta jijjiga kai ‘Na fahimce ka Mustapha, amma dai ka yi haƙuri. Ba wai kai ne ba zan aura ba, auren ne gaba ɗaya ba zan yi ba. Don Allah ka daina wannan maganar, ka mayar da hankali wajen kula da iyalinka. Ka ga yanzu ni babu aurenka a kaina, idan ta ji kana zuwa wajena zaku iya samun matsala. Ka zo kai ba ka sami natsuwa da ta gidan ba kuma ni ba aurenka zan sake yi ba.’

    Ya jijjiga kai don ba ya son wannan maganar, shi yana ji a jikinsa Khadeeja matarsa ce shi kaɗai don haka duk tsawon lokacin da za ta ɗauka tana yi masa yanda zai jure. Ya zaro envelope daga aljihunsa ya ɗora a kan tebur ɗin ya tura mata gabanta yana murmushi yana cewa ‘Wannan na zo kawo miki daman. Ta ɗauko tana dubawa tana cewa ‘Me na samu?’

    Ta zaro takardun daga envelop ta fara dubawa; kujerar Hajji Mustapha ya ba ta. Tana dubawa tana murmushi saboda yanda tunanin za ta je Hajji ya faranta mata zuciya. Ta ninke takardu ta fara mayarwa cikin envelop ɗin a daidai lokacin da murmushinta ya ragu. Ta tura masa gabansa tace ‘Na ji daɗi Abban Hammad, na gode Allah ya ƙara arziki da rufin asiri.

    Amma ka yi haƙuri ba zan iya karɓa ba, ba wai don na raina ba ko wani abu. Na gaya maka ba zan sake aurenka ba so ka ga babu wani dalili da zai sa na karɓar maka kujerar Hajji. Kuma ko na karɓa ma Baffa ba zai taɓa barina na je ba sai dai a ɗaura mana aure kafin na tafi; kuma wannan ba zai yiwu ba. Please ka yi haƙuri! Amma na gode sosai.’

    Kafin ta gama bayanin fuskarsa ta canza gaba ɗaya, ba tare da ya ɗauki takardun ba yace ‘To ki karɓa mana Khadeeja ki bari a ɗaura mana auren, please ki daina guduna haka. Ta sunkuyar da kanta cikin damuwa tace ‘Ba gudunka nake ba, amma dai ba zan iya ƙara aure ba.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci. Jimawa kaɗan yace ‘To yanzu ya kike so a yi? Ni da sunanki na biya wannan kujera. Ka yi hakuri ba zan iya karɓa ba. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Kafin su yi magana aka ƙwanƙwasa ƙofar, ta amsa ta ba da izini aka shiga. Wata mace ce abokiyar aikinta ta ɗan leƙo tace ‘Anti Khadeeja yallaɓai yace ke ake jira a studio za a fara.’

    ‘Yanzu zan shigo.’ Ta faɗa tana shirin miƙewa. Ta dubu Mustapha tace ‘Bari na je kada ka sa a kore ni aiki. Ya yi dariya shi ma ya miƙe, sai dai tana kula da shi bai ɗauki takardun ba. Ta miƙa hannu ta ɗauka sannan ta zagayo ta tsaya a gabanshi, ta miƙa masa takardun tana murmushi tana cewa ‘Ka yi haƙuri ka tafi da wannan, wallahi ba zan iya karɓa ba.

    Idan na karɓa ba zan iya da rigimar Baffa ba tunda na san ba zan aure ka ba. Ka yi haƙuri please. Ya miƙa hannu ya karɓi takardun yana tsare ta da ido kamar mai binciken wani abun a idonta, har sai da ta kawar da nata idon. Ta wuce ya biyo ta a baya suka fito daga office ɗin, suka jero har zuwa reception sannan ta yi masa sallama ya fice ita kuma ta miƙe ta nufi studio ɗin.

    Tana fatan Allah ya sa dai kada ta kwafsa saboda yanda Mustapha ya jagula mata lissafi; me za ta yi da kujerar makansa? Wato ma shi har yanzu tunani yake saboda kujerar Makka yasa ta ƙi komawa gidansa? Bai ma san wacece ita ba kenan, zaman da suka yi tare bai sa ya fahimce ta ba.

    Ba ta buƙatar kujerarsa kuma ta san tabbas idan ba aurensa ta kuma yi ba ko kashi ta kai gida tace shi ya ba ta sai sun yi rigima da Baffa, kuma ba ta shirya ƙarya ba saboda Mustapha wanda take so ya rabu da ita ya daina damun rayuwarta.

    Tana tashi daga waje aiki ta wuce gidan Yaya Mama, ta yi sa’a yaran duk sun tafi islamiyya don haka ta sami Yaya Mama ita kaɗai. Bayan sun gaisa Yaya Mama tace ‘Bari na samo miki ruwa ko lemo. Ta dafe cinyarta tace ‘Bar shi kawai sai da na tsaya na ci abinci sannan na ƙaraso.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta fara ba ta labarin kujerar Makkan da Mustapha ya kawo mata ɗazu. Sai da ta gama ba ta labarin suka sheƙe da dariya a lokaci guda sannan tace ‘Wai ni zai saya da kujerar Makka ɗan rainin hankali. Yaya Mama tace ‘Ai kuwa ɗan rainin hankali lamba ɗaya, wato tunda kin ce ya sake ki saboda kujerar Makka bari ya biya ki sai ki yarda ya mayar da aurenku.’

    ‘Ashe kin gane. Suka cigaba da hira suna tuna abubuwan da Mustaphan ya yi a baya. Sai da Magriba ta fara kawo jiki sannan Khadeeja ta fara shirin tafiya. Bari na wuce kada magriba ta yi min a nan. ’Yaya Mama ta dafa hannunta tace ‘Khadeeja, idan fa za ki koma gidan Mustapha kin san babu wanda zai hana ki ko? Don ni ina ganin ma gara ki koma can ɗin tunda kin ga ko babu komai ga Hammad.

    Kuma na ga har yanzu ba ki da wani manemin; duk da ma duk wanda za ki aura mijn wata ne don haka kin ga dole ki zauna da kishiya. Ni ina ga gara gidan Mustaphan tunda dai ya yi nadama har yana ƙoƙarin ya faranta miki. Nan take ta ɓata rai, ta zare hannunta ta ɗan matsa daga kusa da ita sannan tace ‘Ba zan taɓa komawa gidan Mustapha ba, aure kuma ba ya gabana balle na fara damuwa da rashin manemi.

    Idan Allah ya saka ina da rabon aure a gaba to duk wanda Allah ya sa shi ne mijina zan aura amma fa in sha Allahu ba zan sake auren Mustapha ba. Mutumin da ya ɗauke ni ne kawai a matsayin solution to his problem. Ko yanzun ma da yake ta ƙoƙarin na koma gani ya yi ƙiriƙiri matar tasa ta kasa kula masa da gidan da yara kamar yanda na yi.

    Shi yasa ya lallaɓo ya mayar da ni cikin wahalar da Allah ya raba ni da ita. Ba zan koma na, can su ƙarata. Ta miƙe ta ɗauki jakarta, don haka ita ma Yaya Maman ta miƙe. Ta san idan ta fiya takurawa da maganar yanzu za su yi faɗa don haka sai ta ƙyale ta suka yi sallama ta kama hanya.

    Wunin ranar gaba ɗaya bai yi masa daɗi ba. Ko da dai bai sa ran Khadeeja za ta karɓi kujerar ba tare da an kai ruwa rana ba amma kuma bai sa ran za ta ƙi karɓa haka gaba ɗaya ba ba tare da wata ƙofa ta sulhu ba. Haka ya wuni a office ɗin babu walwala. Sai da yamma ta yi sannan ya kwashi kayansa ya koma gida.

    Yana shiga ɗakinsa ya ajiye takardun hannunsa a kan mudubi; takardar kujerar da ya ba wa Khadeeja ce a sama tare da wasu takardun na office. Tunda ya je sallar magriba masallaci ya dawo ya yi zamansa a ƙasa shi da yara. Da farko ta ɗan zauna a wajensu ana hira gaba ɗaya, daga baya kuma sai ta tashi ta haye sama ta bar su.

    Ɗakinsa ta shiga don ta samu ta huta domin nan ne kawai idan ta rufo ƙofar Rukayya ba za ta so ta buga ta tashe ta ba. Har ta wuce mudubin sai kuma ta koma da baya, ta sa hannu ta ɗauki envelope ɗin da ta ja hankalinta. A buɗe take don haka sai kawai ta zaro takardun ta fara karantawa.

    Nan da nan kanta ya kulle; tabbas wannan sunan Khadeeja ne. To me hakan yake nufi?Suna tare kenan yanzu ta zama bazawararsa ko me? Tunda idan ba wata alaƙa ce tsakaninsu ba me zai saka har ya biya mata kujerar Makka? Kenan ma ita Mustapha zai rainawa hankali, ya saki matar sannan ya koma yana bin ta? Gaskiya ba za ta yarda ba.

    Ta ɗaga kanta ta hango wayarsa tana chaji a kan bedside durowa; nan da nan ta ajiye takardun ta ƙarasa ta ɗauki wayar. Ta riga ta san PIN ɗin don haka kai tsaye ta buɗe ta fara duba whatsapp; sai dai har ta gama dubawa ba ta ga sunan Khadeeja ba. Tana duba calls ta ga sunan ‘Sweetheart’ shi ne sunan da ya yi saving lambarta tun yana zuwa zance kuma bai taɓa canzawa ba.

    Bayan rabuwarsu Najan ta goge ta saka maman Hammad amma ba ta san yanda aka yi ya mayar ba. Ta mayar da wayar ta ajiye cike da damuwa da takaici. Ta tashi ta dawo ɗaya gefen gadon ta zauna ta zuba tagumi; tabbas za su yi rigima da Mustapha don ba zai yiwu ba ya dinga zagayawa wajen tsohuwar matarsa suna raina mata hankali.

    Sai wajen ƙarfe tara na dare ya hawo saman, lokacin ya je sallar isha’i ya dawo kuma sun gama cin abinci da yara. Zuwa lokacin ita ma ta gama duk abinda take yi ta kwantar da yara tana kwance a kan gadon ɗakinsa sanye da rigar bacci ta miƙe kafa tana kallo a waya ya shiga ɗaki. Bayan ta amsa sallamarsa ta mayar da hankali kan wayar hannunta.

    Kai tsaye ya wuce ciki ya canza kayansa sannan ya zauna a kan carpet ɗin da ke gaban gadon ya miƙe ƙafa ya janyo computer ɗinsa ya kunna ya kama aiki. Yawanci idan dai har yana da aiki to ya kan kai dare sosai a zaune yana aikin, ita kuma ba za ta iya jira ba. Don haka ta miƙe ta zauna ta ajiye wayar da take hannunta ta yi gyaran murya sannan tace ‘Uhm, na ga wata takarda, wai Maman Hammad ka biyawa Makka?’

    Bai yi mamakin jin tambayar daga gareta ba duk da bai sa rai da ita ba, amma dai ya san ya manta ya ajiye takardun a kan mudubinsa. Ba tare da ya bar aikinsa ba yace ‘Eh ita na biyawa, akwai matsala ne. Cike da neman rigima tace ‘To kuma a yanzu meye tsakaninka da ita tunda na ga dai babu aure. Ko kuma kun mayar da auren ne ni ce ban sani ba.’

    Har yanzu hankalinsa yana kan aikin yace ‘Ba mu mayar ba muna dai kan hanya. To shi ne kuma ka biya mata Hajji. Ya ɗago ya dube ta yace ‘Eh, akwai matsala ne? ‘Gani dai na yi bai dace ba tunda babu aure a tsakaninku. ‘Wannan ra’ayinki kenan. Ta kula so yake ya yi mata wulaƙanci don haka ta miƙe ta zauna sosai tace ‘Ina fatan dai ka san yanzu ita ɗin ba muharramarka ba ce.

    Kuma ina fatan ka san ba zai yiwu ina nan gida ina maka biyayya wai ni matar aure ba ka dinga zagayewa wajen tsohuwar matarka wadda ka saka da hannunka, ba zan ɗauka ba gaskiya.’

    Ya ɗago ya kalle ta rai a ɓace yace ‘Sai ki ɗau mataki a kai. Ta kula kamar haushinta yake ji sai dai ba ta san dalili ba, don lafiya ƙalau suka rabu da safe ya ajiye ta a office sannan ya fice; to meye ya harzuƙoshi hakan daga yin magana? Kada fa ka gaya min magana daga tambaya, na dai gaya maka ba zai yiwu ba ina nan ka kulle ni a gidanka a dinga ganinka a gari kana yawo da wata matar banzan.

    Ta faɗa tana miƙewa tsaye. A fusace yace ‘Khadeejan kike cewa matar banza saboda wulaƙanci? Sai dai kafin ya rufe bakinsa ta fice daga ɗakin ta rufe masa ƙofar; wanda wannan ɗabi’arta ce idan dai ya ɓata mata rai sai ta gaya masa magana mai zafi sannan take fita daga inda yake. Ya yi tsaki ya cigaba da aikinsa don so yake ya gama aikin kafin ya kwanta.

    Haka rayuwarsu ta cigaba. Khadeeja ta ƙi yarda a mayar da aurensu sannan shi kuma ya kasa tunkarar Baffanta da maganar don ya san ba za a yi mata auren dole ba. Amma kuma ya ƙi ya daina bibiyarta; har ta kai ba ya iya sati bai neme ta yaganta ba. Idan ya je gidansu wajen Hammad ta ƙi fitowa to tabbas zai same ta a office. Waya kuwa daman ba ta yankewa don idan ma ta ƙi ɗauka haka zai yi ta kiranta har sai ta gaji ta ɗauka.

    Duk wata kalma da zai yi amfani da ita wajen ganar da ita ta yarda su mayar da aurensu ya yi amma ta sanar da shi ba za ta iya komawa ba. Duk lokacin da ta ji kamar za ta haƙura su koma idan ta tuna yanda yake banzatar da ita a gidan kuma ta tuna yanzun ma sai da ya rasa yanda zai yi da gidan sannan ya fara nemanta sai kawai ta ji ta fasa.

    Tana sane da duk wata rigima da ta faru a gidan tunda kusan duk Asabar a wajenta Habib yake wuni, duk abinda ya dame shi sai ya je ya same ta ya gaya mata. Lokaci zuwa lokaci tana samun masu nuna sha’awar aurenta sai dai auren gaba ɗaya ya fice mata daga rai; don haka yawancinsu ba ta ma bari su zo gidansu.

    Kuma duk inda ta je idan dai ba an santa a wajen ba to tana gabatar da kanta ne a matsayin matar aure don ma kada wani ya zo mata da wata magana; don haka mutanen da suka santa sai suka kasu kashi biyu, wasu suna ganin tana da aure wasu kuma suna ganin ba ta da aure. Amma kuma yawancin mutane kasa tambayarta suke yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Uku

    Kansa a cike yake saboda rashin bacci ga damuwa, don haka yana shiga office ɗin ya rufo ƙofar ya kwanta a kan 3-seater ɗin da take wajen. Yana rufe ido ya fara nadama; ya aka yi ya saki Khadeeja? Ya aka yi ya bari har ta gama idda bai mayar da ita ba? Tunda dai ai da ya mayar da ita ya san ba ta da wani zaɓi dole ta zauna da shi tunda ba za ta saki kanta ba.

    Tunda yake da Khadeeja bai taɓa ganin wata damuwa game da yaransa ba, ga shi wata takwas kacal da ta bar su gidan yana neman ya gagare shi. A da ya yi zaton Naja za ta fi ta kulawa da su musamman yanda ya ga tana nuna ƙauna garesu kafin ya aureta.

    To me ya canza mata ra’ayi har aka kai inda ba su da damar da za su ci abinda suke so a gidan ubansu? Lallai dole ya ɗau mataki. Haka ya wuni a office ɗin cikin rashin sukuni; yana tunani halin da yaransa suke ciki a gida sannan kuma ga shi zuciyarsa taƙki ta ƙyale shi da tunanin Khadeeja.

    Tabbas da Khadeeja tana nan da babu yanda za a yi ya wuni a office yana tunanin halin da yaran suke ciki. Domin ya tabbatar duk halin da suke ciki to ita ma tana cikin wannan halin a tare da su. Ya tuno lokacin da tace ba za ta yi musu girki ba yanda suka gaya masa gari suka sha kuma garin ma tare da ita suka sha.

    Ya yi dariya a fili; tabbas Khadeeja tana da rigima amma ta iya rigimarta. Ya tabbatar babu yanda za a yi ta ci kaza ta bar yara da baƙin shayi. Haka ya zauna yana aiki yana tuno rigimarsu da Khadeeja yana murmushi shi kaɗai. Bai taɓa zaton zai yi kewar rigimar Khadeeja ba amma yanzu tabbas kewar rigimar tata yake yi.

    Ƙarfe ɗaya da rabi daidai suka idar da sallah a farfajiyar office ɗin su. Yana shiga office ɗinsa ya zauna a kan kujerarsa ya tura ta baya kaɗan yana juyawa ya ɗauki wayarsa wadda take kan tebur ɗin ya lalubo lambarta ya dannan mata kira, ya kara a kunnensa bayan da ta amsa yace ‘Hello.’

    Bayan sun gama gaisawa yace ‘Kina ina ne? Da mamaki a muryarta tace ‘Ina office mana, akwai wata matsala ne? Murya a sanyaye yace ‘No, babu matsala kawai dai ina son ganinki. Zan iya zuwa office ɗin yanzu? ‘Umm! Akwai matsala ne? Ta sake tambaya. Ya yi ‘yar dariya ‘Babu matasala fa, akwai dai maganar da nake so mu yi. Zan iya zuwa, minti talatin kawai ya isa. ‘Ok, ina jiranka duk da dai na kusa tashi.’

    Ya ajiye wayar ya miƙe ya ɗauki mukullan motarsa ya kama hanya. Yana sane ya ƙi ya kirawo ta da ya isa don so yake ya shiga ya same ta a office ɗin nata, don haka bayan ya ajiye motarsa sai ya fito ya shiga gidan talabijin ya tambaya. Ba tare da ɓata lokaci ba aka nuna masa office ɗin nata.

    A hankali ya ƙwanƙwasa ƙofar, daga ciki muryarta ta ba shi amsa ‘Shigo a buɗe ƙofar take. Ya tura ƙofar ya shiga da sallama. Tana zaune a kan kujerar zaman mutum ɗaya wadda take gefe guda, da jakarta a gefenta tana ta danna waya; da alama ta gama shirin tafiya gida. Bayan ta amsa sallamarsa ya mayar da ƙofar ya rufe sannan ya ƙarasa ya yi wa kansa mazauni a kujerar da take kusa da wadda take zaune a kai.

    Bai san dalilin da yasa ganinta ya saka shi jin daɗi ba amma dai ya san ya ji daɗin ganinta. Cikin girmamawa ta gaishe shi kamar babu wata damuwa a tsakaninsu. Bayan ya amsa tace ‘Allah ya sa dai ba wata matsala don tunda kace za ka zo nake ta tunani.’ Ya yi murmushi yace ‘Babu wata matsala, kawai dai ina son ganinki ne.’

    Ta ɗan yi gajeren murmushi tace ‘Uhm, to gani. Ya yi dariya yace ‘Kamar dai kina kora ta. Ba korarka nake ba, kawai dai ina son na tafi gida don wallahi na gaji. Ya gyara zama; ya rasa ma ta inda zai fara domin ganinta ya goge masa duk zantukan da ya tsaro zai zo ya gaya mata. ‘Yara suna kewarki.’ Ya faɗa bayan ya gama nazarin ta inda zai fara.

    Nan da nan murmushinta ya ƙara faɗi, tace ‘Allah sarki ni da Hammad ma muna kewarsu. Don ma Yaya Habib yana zuwa gidan Mommy yana gaishe mu. Ya girgiza kai domin Habib bai taɓa gaya masa yana zuwa wajen Khadeeja ba, bai ma taɓa yi masa maganar Khadeejan ba tun bayan da suka rabu.

    ‘Ya Hammad? Ba ya kukan makaranta?’ Ya tambaya. ‘Baya yi, ka san ya haɗa wayon yayyinsa gaba ɗaya.’ Ta faɗa tana dariya. Suka yi shiru na ɗan lokaci; ita duk ta ƙosa domin so take ta tafi gida yayin da shi kuma ya gyara zama yana kwaso hira. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yace ‘Khadeeja. ‘Na’am.’ Ta amsa tana kallonshi.

    ‘Wai me yasa kika ce na sake ki? Ya tambaya yana tsare ta da ido. Ta sunkuyar da kai tana murmushi, ta ɗago ta kalle shi suka haɗa ido sannan ta sake yi masa wannan murmushin nata wanda yake ɗauke da ma’anoni daban daban tace ‘Right question at the wrong time; amma dai zan ba ka amsa.’

    Ta sunkuyar da kai a daidai lokacin da murmushin fuskarta ya gushe, ta ɗago suka sake haɗa ido sannan ta gyara zama tace ‘Gajiya na yi Musatapha. Ka san idan mutum wanda bai iya swimming ba ya faɗa ruwa to zai yi ta ƙoƙarin ganin ya fita da rai ko, amma duk daɗewa zai gaji. To haka ce ta faru da ni.

    Soyayya ce ta saka na aure ka, amma idan dai ba na manta lissafin ba tun a shekarar farko na rasa soyayyarka. Haka na dinga kokawar janyo attention ɗinka ko za ka fahimce ni amma ba ka ko kalli inda nake ba; kai dai abinda kake so kawai shi kake so. Na haƙura ina zama da kai a haka saboda I was ok with just sleeping beside you every night; sai kuma ka ɗauko aure.

    Duk wani abu da nake so daga wajenka a lokacin ka ɗauka ka ba ta ina kallo. Haka na cigaba da kokawar samun attention ɗinka, ina ƙoƙarin ganin ka yi mana adalci amma hakan bai samu ba. Na tuna tun ina ni kaɗai ma ka fara kasa yi min adalci to balle yanzu mun zama mu biyu; ni da rabin ranka. So I gave up, ba zan iya ba, na gaji da faɗan da ba shi da ranar ƙarewa don na gane bana ma gabanka.

    Shi yasa na nemi saki kuma Allah ya taimake ni ka ba ni kuma ka bar ni har na gama idda. Idanuwansa suna kan fuskarta har ta gama ta yi shiru, ya cije leɓe yace ‘Kuma ba ki gaya min ba Khadeeja? How did I not see all this? Ta yi dariya tace ‘Da wanne yaren zan gaya maka?’

    Suka sake yin shiru na ɗan lokaci. Ta danna wayarta ta kalli agogo sannan tace ‘Time yana tafiya, wallahi so nake na tafi gida don na gaji. ‘Oh, sorry Suka sake yin shiru na ɗan lokaci sannan yace ‘Khadeeja yi haƙuri mu mayar da aurenmu, in sha Allahu haka ba za ta sake faruwa ba.’

    Ta miƙe tsaye tana dariya tace ‘Ka yi haƙuri Mustapha amma aure ba zan sake yi da kai ba, babu wannan zance don Allah kada ka sake yinsa. Shekarun da muka yi Allah ya amfana su kuma Allah ya sa kaffara ne amma kada Allah ya maimaita mana. Ya dafe kansa da hannuwansa biyu na ɗan lokaci sannan ya sauke hannuwan ya miƙe tsaye.

    Ta buɗe ƙofar ya fice sannan ta biyo bayansa suka fito daga office ɗin. Suka jero suka fito harabar office ɗin. Nan suka tsaya yana ta faman lallaɓata ta bari ya kai ta gida amma ta ƙi; yana ji yana gani ta tare taxi ta hau. Sai da ya tabbatar ta zauna a bayan motar sannan ya zagaya ya ba wa direban taxi ɗin kuɗinta. Suka ja mota shi ma ya koma ya shiga motarsa ya kama hanya.

    Ya dai ji tace ba za ta taɓa sake aurensa ba amma tabbas bai yarda ba, yana ji a jikinsa in sha Allahu za ta yarda su mayar da aurensu. Yanda zai yi da baffa ne ma yafi damunsa domin ya san tabbas Baffa ba zai saurara masa ba. Haka har ya isa gida yana wannan tunanin, sai dai yana saka ƙafarsa cikin gidan ransa ya ƙara ɓaci. Bai san a yanda zai je ya sami yaran ba sannan kuma ita kanta Najan yana jin haushinta do ba zai taɓa ba ta dama ta wulaƙanta masa yara ba.

    Ana cikin kiran sallar magriba ya shiga gidan, don haka ko zama bai yi ba ya ɗaura alwala ya ja Habin suka wuce masallaci. Ko da aka idar da sallar a can ya tsaya wajen magidantan unguwar suna hira, har sai da suka yi sallar isha’i sannan suka tashi daga hirar kowa ya koma gida.

    A parlor ɗin kasa ya sami yaran suna harkokinsu, ya wuce ya haye sama. Tana zaune a parlor tana jiransa saboda ba ta son yanda tun da safe ya ƙi ya ko kalli inda take. Ita idan ana faɗa ta fi so a yi hayaniya kowa ya faɗi abinda yake ransa, amma ya ma ƙi ya tambaye ta me yasa ta yi wa yaran haka balle ta samu ta yi masa bayani.

    Ba ta jin ya amsa sannu da zuwan da ta yi masa, idan kuma har ya amsa to tabbas ita dai ba ta ji ba. Ba tare da ya kalli inda take ba ya shige ɗakinsa. A fusace ta miƙe ta bi bayanshi. Yana tsaye a gaban mudubi yana rufe durowa ta shiga ta turo ƙofar, ta tsaya a bayan ƙofar ta rungume hannu tace ‘Ga abinci can a dining table.’

    Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki sauka da shi ƙasa a can zan ci ni da yara. Ta sunkuyar da kai ‘To bari nace su hawo sai ku ci a nan, duk da su ma na zuba musu nasu abincin kuma duk tuwon ne dai. ‘Ba sai sun hawo ba ni zan sauka, ki ɗauka ki kai can.’ Ya faɗa sannan ya juya ya zauna a gefen gado.

    Ta ƙarasa ta zauna a kusa da shi, ta dafa gwiwarsa ta dan marairaice tace ‘Don Allah ka ba wa Hajia haƙuri, wallahi abinda ta gani ba haka ba ne. Kai ma ka san babu yanda za a yi na ci wani abu na hana yara. Hawowa ne ba su yi ba na ajiye musu nasu a kitchen kuma da ka shiga za ka gani.’

    Ya kalle ta sheƙeƙe yace ‘Ai ba yau kika fara ba, kuma ba yau na fara yi miki magana ba. Babu wani haƙuri da zan ba ta idan kin gyara halinki su yaran za su gaya mata ai. Mugun halin da kike nuna musu kuma ki cigaba kada ki fasa. Ya miƙe zai fita, ta kama hannunsa ita ma ta miƙe tana cewa ‘Don Allah ka yi hakuri, yaran da nake hidimarsu tun kafin na aure ka kuma yanzu ribar me zan ci idan na yi musu mugunta?’

    ‘Ni ma shi ne abinda nake mamaki, wataƙila daman ba don Allah kike yi ba ko kuma zuga ki aka yi kika canza hali ni ban sani ba. Abinda na sani kawai shi ne kusan tun da Khadeeja ta bar gidan nan kika dage sai kin raba rayuwarki da ta yaran nan, ina kula da yanda kike ƙoƙarin ganin ba su hawo benen nan ba saboda tsabar samun waje…’

    ‘Don Allah ka dai wannan maganar, wallahi kai ma ka san ba haka ba ne. Na ga dai ko gidan waye akwai part ɗin mai gida inda ba a bari yara su shiga, amma in sha Allahu ba zan sake hakan ba tunda na ga kai ba haka ne tsarinka ba.’ Ta katse shi cikin ƙosawa. Ya zare hannunsa da ta riƙe ya miƙe yana cewa ‘Ki kawo min abincin parlor ɗin ƙasa yanzu.’

    Ya fice ba tare da ya saurari amsarta ba. Haka ta gama zumɓura baki ta sauko ta kawo masa abincin nan parlor ɗin ƙasa inda ya zauna suka ci da yaran; duk da sun nuna masa su ma tuwo aka ba su irin nashi. Haka ya kafa mata dokar idan dai yana gidan to a parlor ɗin ƙasa zai dinga cin abinci wajen yara, babu roƙon da ba ta yi masa ba a kan ya bari yaran su dinga hawowa saman ana cin abincin tare amma ya ƙi ya saurare ta.

    Ya kula cewa ganin saman bene take kamar wani abu na musamman don haka ya yanke shawarar bar mata saman benen ita kaɗai. Ya yanke shawarar a ƙasa zai dinga zama hira kuma a nan zai dinga kallo yana cin abinci, in ya so idan zai yi bacci ya dinga hawa saman ya kwanta. Ta yi yanda take so da saman ita kaɗai.

    Yana sane ya ƙi zuwa gidan Hajia a ranan sai washegari; ya san idan ya je zancen nan bai huce ba Hajia da Alaji haɗuwa za su yi a kansa har sai ya rasa abinda yake masa daɗi. Don haka washegari yana tashi daga office ya wuce gidan Hajia. Bayan sun gaggaisa ya sami Alhaji a parlor, yana gama amsa gaisuwarsa yace ‘Mustapha me yake faruwa ne a gidan naka? Ban ji daɗin bayanan da na samu daga wajen Habib ba kuma sai ga Hajia ta je ta gani da idonta. Me yake faruwa ne?’

    Ya gyara zama ya shafa kansa sannan yace ‘Wallahi Alhaji ‘yar matsala ce aka samu kuma na ma yi mata magana in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya tashi daga kashingiɗar da yake yana cewa ‘Yar matsala? ‘Yar matsala fa kace Mustapha? An bar yara a ƙasa kamar masu zaman kansu amma kana cewa ‘yar matsala? Gidan naka har ya kai an raba tukunya, ta marayun yaranka daban ta matar gida daban.

    Anya kuwa Mustapha? Rashin uwa ai ba hauka ba ne da za ka wulaƙanta su saboda Allah ya ɗauki ran mahaifiyarsu. Ya sake shafa kansa ‘Wallahi Alhaji akasi aka samu kuma in sha Allahu hakan ba za ta sake faruwa ba. Ya kawar da kai cike da damuwa ya yi shiru, jimawa kaɗan ya cigaba ‘Ita Khadeeja ya wajen nata da Muhamadun? Kana zuwa dai?’

    Ya gyara zama yana murmushi ‘Eh, ina zuwa. Jiya ma na je. ‘To ya kamata dai ka san yanda za a yi ku daidaita tsakaninku tunda dai ka ga ita ba a taɓa samun wata matsala tsakaninta da yaran nan ba, haɗawa ta yi ta riƙe su tun kafin ma ta sami nata. Kuma da ta sami natan ma babu abinda ya canza. Ka ga ita ce ta zama uwa ta gari a wajensu tunda ga su ƙalau da tarbiyyarsu.’

    ‘Haka ne Alhaji, in sha Allahu za mu daidaita. ‘Ya kamata dai ka san abun yi tunda ka san dai yanzu a kasuwa take, idan ba ka maida hankali ba wani zai iya yi maka shigar sauri. Suka ƙarasa hirarrakinsu sannan ya yi musu sallama ya wuce office.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Talatin Da Biyu

    Edita@rumasau-kallamu