Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Waƙa Mai Taken Abokin Tafiya

    Waƙa Mai Taken Abokin Tafiya

    1. Rabbi ban hikima basira,

    Baituka zan so na tsara,

    Kyauta aiki kan mu lura,

    Don mu ɗau hanya ta tsira,

    Duniya har ran tsayawa.

    2. Zan rubutun baituka ne,

    Kan Hadisin Musɗafa ne,

    Don misali ya saɓa ne,

    kan gudanmu a duniya ne,

    In ajal gu nai ya zowa.

    3. Ga mutum ga ‘yan uwansa,

    Su Uku da suke a gunsa,

    Zai tafi gun khaliƙinsa,

    Yai biɗar ɗaukinsu gunsa,

    Don su ne ya ƙyale kowa.

     

    4. Sai ya dubi gudansu yac ce,

    “Wane loto ya yi fauce,

    Me gare ni za ka zam ce,

    Taimaka min don na dace,

    Ban da kai ban nemi kowa.”

     

    5. Sai ya ce “Zan jinyatar ka,

    Zan tsaya nai hiddimar ka,

    In ko rai ya kau gare ka,

    Za na yo sutura gare ka,

    Zan biye ka zuwa kushewa.

     

    6. “Har da ni za ai saka ka,

    Ƙabbari a zamo rufe ka,

    Addu’a zan yo gare ka,

    San da duk an ambace ka,

    Zan tuna ka ina yabawa.”

     

    7. Wanga shi ne dangi nasa,

    Duk iyali har ɗiyansa,

    Za su ɗauke shi su kai sa,

    Sai su dawo can su bar sa,

    Fin haka ba sa iyawa.

     

    8. Ɗan uwa na biyu gare shi,

    Za ya nemi garai kira shi,

    Sai ya ce mar “Wane ga shi,

    Lokacina ya tuƙe shi,

    Zan tafi ba dawayowa.

     

    9. “Kanka nai duk rayuwata,

    Don biɗar ka na yo mutunta,

    Don na samu abin bajinta,

    Me kake amfanuwa ta,

    Yau na samu abin riƙewa?”

     

    10. Sai ya ce “Ai ni gare ka,

    Lokacin ruhi gare ka,

    Garkuwa kuma irli naka,

    Duk  buƙatu zan biya ka,

    Har ka zam ka zarta kowa.

     

    11. “In ko rai ya kau gare ka,

    Mun rabon hanya da ni ka,

    Za ka tai gun khaliƙinka,

    Ni ko ‘yan gado gare ka,

    Za su ɗau ni su zam rabawa.

     

    12. Wanga shi ne dukiyarsa,

    Wadda ya ba rayuwarsa,

    Duk wahalta ya yi don sa,

    Sun rabu bai ba shi fansa,

    Ko gare shi ya taimakawa.

     

    13. Ɗan uwa na Uku ya nema,

    Yac cane mar “Wane kai ma,

    Kai sani yau babu dama,

    Dawwamar ruhi jiki ma,

    Za na amsa kiran da anwa.

     

    14. “Me kake amfanatarwa,

    Don na zamto ƙetarewa,

    Zanguna da suke tahowa,

    Kwai haɗar da rikirkicewa,

    Zan buƙaci ka agazawa?”

     

    15. Sai ya ce “Duk inda za ka,

    Dukka zango ban barin ka,

    Tun kushewa ƙabbarinka,

    Zan cire kewa gare ka,

    Ran zuwan ‘yan tambayawa.

     

    16. “Ran tsayo gun khaliƙinka,

    In ka tashi ina biyar ka,

    Zan yiwo rana gare ka,

    Can a mizanin awonka,

    Zan shiga yai nauyayawa.”

     

    17. Wanga shi ne nasa aiki,

    Wanda ya yo shi na kirki,

    Kyautatar bauta ga Sarki,

    Kyauta niyya babu surki,

    Shi yake yin dawwamewa.

     

    18. Ko fa aiki bai yi kyau ba,

    Ya ƙazanta bai fari ba,

    Zai lazimci mutum a turba,

    Ƙabbari ba zai bari ba,

    Dole shi za yai riƙewa.

     

    19. Babu amfaninsa zai ci,

    Zai zamo babban kumurci,

    Yai ta saran sa yana ci,

    Hakka zai wanzu a ƙunci,

    Har zuwa ranar tsayawa.

     

    20. Gun awo muni na aikin,

    Sai ya rinjayi na kirkin,

    Rabbi tserar mu tafarkin,

    Muna aiki wanda kaidin,

    Shaiɗana ke shiryatarwa.

     

    21. ‘Yan uwa lallai mu farka,

    Tanadin aiki mu ɗauka,

    Wanda zai bi mu ya haska,

    Ƙabbarinmu har mu farka,

    Don fita ranar tsayawa.

     

    22. Ran da tarin dukiyarmu,

    Kaddarori dangi namu,

    Ba su amfani gare mu,

    Sai fa mai kyau ayyukanmu,

    Ba riya ba goratawa.

     

    23. Kar mu ruɗu yawan mutane,

    In a kan hanyar ɓata ne,

    Gwamma mun ɗau mai mutane,

    ‘Yan kaɗan in shiryata ne,

    Don mu samu abin riƙawa.

     

    24. Mun yi roƙo Jalla Sarki,

    Sa mu dace wajje ɗaki,

    Mui kulawar kyauta aiki,

    Don mu dawwama kan tafarki,

    Wanda ba zai karkacewa.

     

    25. Nasiru G. Ahmadu ne,

    Kowashe almajiri ne,

    Mai biɗar ƙarin sani ne,

    Shi ya saƙo baitukan ne,

    Ayyuka mui kyautatawa.

    Alhamdu lillahi.
    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.
    Edita@rumasau-kallamu
  • Waƙa Mai Taken Ladubban Tsuguno

    Waƙa Mai Taken Ladubban Tsuguno

    1. Da sunan Rabbi mai baiwa gare mu,

                       Da nau’o’in ni’imta ba musawa.

    2. Salati da sallama ga Rasulu Ɗaha,

                       Da ya ceto mu bin hanyar ɓacewa.

    3. Cikin ni’imar da Rabbi ka yi gare mu,

                       Fitar najasa ga mu don tsarkakewa.

     

    4. In ban da haka jiki za tai zamanta,

    Guba ce wallah za tai illatarwa.

    5. A don haka gode Allah ya wajabta,

    Bisa ni’imar ga kullum mui ta yowa.

    6. Musulmi an buqƙaci ya yo ladubba,

    Ya bambanta da gayyar kafirawa.

    7. Idan ya buƙatu banɗaki ya zaga,

    Da Bismillah ake son yai shigewa.

    8. Ya sanya ƙafar hagu yayin shigarsa,

    Ya zam addu’ar tsari daga jinnatawa.

     

    9. Idan ba ka ambaci Allah shigarka,

    Al’aurarka sukan riƙa kallatawa.

    10. Hijabi naka Basmala du’a’i,

    Idan ka yi ba su duba ko tsayawa.

    11. Kada ka shiga da sunan Rabbi Allah,

    Jikin zobe waninsa an hanawa.

    12. Idan sarari ka je don tsuggunawa,

    Cikin dajin Ilahu ka zam kulawa.

    13. Ba a tsuguno a kan hanyar mutane,

    Da inwoyi na amfani ga kowa.

     

    14. Ƙasan bishiya da ‘ya’ya ta yi ban da,

    Da gefanni na gulbi mai wucewa.

    15. Da ramukka tana yiwuwa da jinnu,

    Da yin bawali ruwa mai dawwamewa.

    16. Ka nesaci duk idanu kar su gan ka,

    Ko sauti mai fita wari jiyowa.

    17. A nemi wuri da babu ruwa bisansa,

    Bai zam shi faƙo ƙasa mai taurarewa.

    18. A zancen Hausa ma an ce Mugunta,

    Fitsari kan faƙo zai fallatsowa.

     

    19. Ba a cire riguna ko janye wando,

                       Sai an yi kusan isa ƙasa za a yowa.

    20. Ba a fuskantuwar Qibla a yayin,

                       Da an tsuguna a fili mui kulawa.

    21. Hakan nan ba ta baya an hana shi,

                       In ba sutura ko banɗaki ginewa.

    22. A yayin ko fitar najasa ana so,

                       Qafar hagu za a ƙarfafa dogarewa.

    23. Ba a magana a yayin tsuggunawa,

                       Abin karhantuwa an tsawatarwa.

    24. Tsarkin bawali akan fara gabanin,

    Muhallin gayaɗi sai mui kulawa.

    25. Idan najasar ta ƙare fita a tashi,

    Kada a jima yawan nishi anaiwa.

    26. Ba a tsarki da hannun dama yayin,

    Wanke najasa hagun za ai sakawa.

    27. Ko da da Tishu ya zamto za a goge,

    A yo da hagu kafin da ruwa biyewa.

    28. Hakan ne ma bin so in ya samu,

    Gudun hannu taɓar najasa ya yowa.

     

    29. Ba a sanya ƙashi don goge najsa,

    Ko ko tutu na dabba an hanawa.

    30. Kaza da dukansa dangogin abinci,

    Da duk abu mai darajja ba a yowa.

    31. Shi ma bawali a yo Istinjimari,

    Kafin tsarkin ruwa ya zamo biyewa.

    32. A zam addu’a idan za ai fitowa,

    Da banɗaki a bayan tsuggunawa.

    33. Mu zam gode wa Allah don raba mu,

    Da duk najasa da mun zam kasayewa.

     

    34. Kaza najasar ruwa da mukai bawalta,

    Aminta don gare mu yai daɗowa.

    35. A nan zan dakata ya ‘yan uwana,

    Kurenmu Tabaraka yai garafawa.

    36. Ya Rabbi daɗo salati babu haddi,

    Ga Manzo naka jikan Hashimawa.

    37. Idan an tambayi mai tsara waƙar,

    Nasir Ahmad iri na Bukar ya yowa.

    38. Baitoci Arba’in Biyu babu waƙar,

    Dubu Biyu sha Tara Maris na yowa.

    Alhamdu lillahi

    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.

    Karanta Tarihin Marubuci Nasiru Garba Ahmad

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tsokacin A Kan Littafin Garina Abin Alfaharina

    Tsokacin A Kan Littafin Garina Abin Alfaharina

    “Garina Abin Alfaharina.” Littafi ne da ya zamo tamkar madubin da ke haskaka zuciyar al’umma, domin a cikinsa an ɗaura labarin a kan gaskiya, haɗin kai, da sadaukarwa. Gari fitila ce, amma mutane su ne wutar da ke haskakata (kunna ta).

    Marubucin ya zubo bayanai cikin hikima, ya zana halaye da ɗabi’u a matsayin tubalin gina al’umma. Har ila yau, al’umma ba ta tashi da cigaba, sai da haɗin kai. A wannan littafin an nuna mana cewa “Gari na bunƙasa ne da mutanensa”, domin ba gine-gine ba ne kaɗai suka gina gari ba, hasalima zuciyar mutanenta ce.

    Ga Malam Yahaya Garba, Malam Mammaada, Malam Surajo Yunusa, Malam Aliyu Labaran, Malam Magaji Ƙofa, Malam Idi Ɗanlula da sauran malamai, waɗanda suka zama tamkar katanga ga iska, suna tsayawa a kan ilimi da tarbiyya.

    Haka kuma marubucin ya kawo wasu matasa masu kirki; Dakta Mujaheed da Salmanu Faris, Alhaji Abubakar Suleiman, Barrister Anas Lawal Audi, waɗanda suka yi tsayawan tsayin daka ga ‘ƴan siyasa, don ganin an samar da cigaba a garinsu.

    Kuma sun tabbatar da haka, domin sai da suka miƙa kundin buƙatun al’ummarsu ga duk ɗan siyasan da yake neman ƙuru’arsu kafin su zaɓe shi.

    Lafiya uwar jiki, babu mai fushi da ke in ji Ɗan Hausa, a cikin littafin an ga lokacin da Dakta Ado Zakari, Dakta Murtala Muhammad, Dakta Khalid Gambo da Hajiya Gude suka tsayin daka wajen warware wasu cututtuka a garin gami da sadaukar da ilimin su, don amfanuwar garin.

    Abin da ya fi jan hankali shi ne yadda marubucin ya sassaƙa turakun zaman lafiya tsakanin ƙungiyoyin addini, wato Tijjaniya, Izala da Shi’a. Kamar yadda ake cewa: “Idan ruwa ya yi yawa, sai ya zama teku.”, kuma ” Zaman lafiya ya fi zama ɗan Sarki.

    Saboda, gari yana samun cigaba ne a lokacin da aka samar da zaman lafiya (tsaro), ilimi, sana’a da kasuwanci da sauransu. An hango wasu harsunan mutane, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu don cigaban garin ta fuskar tsaro, an kuma zayyano wasu gwadabe na samar da tsaro da cigaban gari.

    Shi ya sa wannan littafin ya kasance tamkar gorar ruwan sanyi ne ga mai tafiya a cikin sahara.

    Danna nan don karanta Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Mai Taken Jakadan Allah

    Waƙa Mai Taken Jakadan Allah

     

    1. Allahu ba ni dubun basira mayyawa,

                                 In yi baitukan bege ga ɗan Adanani

    1. Ga munasaba ta watan Rabi’ul Lawwali,

                                 Wata na samun Sayyidul kaunaini.

    1. Kafin zuwansa duniyar ga baƙi ƙirin,

                                 Duk ta nutse a duhun ɓata tai muni.

    1. Tauhidi loton babu shi sai nadiran,

    Kaɗaita bautar Rabbu tai nuƙusani.

    1. Sai kame-kame ake cikin kogin ɓata,

    Bautar wanin Allah da bin shaiɗani.

    1. Sai zulmu ko a ina da danne haƙƙuna,

    An juya shar’un Rabbana Mannani.

    1. A wanga hali Ɗaha ya zo duniya,

    Don tsarkake ta ga dukkanin ɗuguyani.

    1. Ta tsatson ababen zaɓuwa gun Rabbana,

    Nasaba da halayen ƙwarai ihsani.

    1. Ya zo a tsarkake ba ƙazanta ko kaɗan,

    Ya girma kamamme ga duk buɗlani.

    1. Mai gaskiya aka san shi fai har baɗini,

    Da riƙon amana sun kira shi Amini.

    1. Allahu ya zaɓe shi don manzantaka,

    Ta isar da Tauhidi ga dukkan kauni.

    1. Ya ba da dukkan rayuwarsa wajen isar,

    Saƙo na Tauhidi a san gufrani.

    1. An tsangwame shi a Makka har dangi nasa,

    Da dukan Sahabbai masu bin Rahmani.

    1. Yai shekara har Sha Uku a cikin matsi,

    Laifinsa Tauhidi da ƙin ausani.

    1. Ya bar garinsa na haihuwa a bisa haka,

    Haka ma Sahabbai nasa sun hijrani.

    1. A Madinatu Yasrib ya zauna har zuwa,

    Ƙarshe na rayuwarsa bisa ga amani.

    1. Qur’ani an saukar garai don shiriya,

    Bautar Ilahu da kyauta dukkan shani.

    1. Rayuwarsa ta zam bauta Rabbil izzati,

    Koyar da Qur’ani gami da bayani.

    1. Mai tausayi ga dukan halitta ya zamo,

    Mai kyauta hulɗa ne ga duk insani.

    1. Mai yafiya ga dukan kure ne Musɗafa,

    Mai tarbiyantarwa bisa ihsani.

    1. Mai tsai da adalci ga kowa Annabi,

    Mai ƙyamatar haƙƙin wani a yi danni.

    1. Mai koya shar’a aikace don ai biya,

    Bai bar a keta umarnukan Rabbani.

    1. Mai ƙas da kai ne babu girman kai ga shi,

    Mai girmamar babba da ma sibyani.

    1. Mai yin hidimtawar iyali nasa ne,

    Haka ma sahabbansa bila firƙani.

    1. Mai son lumana ba shi son ce-ce-ku-ce,

    Bai yaƙi kowa sai bisa burhani.

    1. Mai murmushi ne shi ga kowa Sayyadi,

    Kowa gare shi yana zuwa ya yi zauni.

    1. Mai yin du’a’in shiryuwar umma yake,

    Don sauƙaƙar tsayuwa gaban Rahmani.

    1. Kyawun halinsa ya ba Sahabbai kwaikwayi,

    Suka ɗabbaqa su a ko’ina ba zanni.

    1. Sun tarbiyantu gare shi baban Ƙasimu,

    Suka yaɗa Tauhidi a ƙauye birni.

    1. Sun keta dazukka Hamada sun isar,

    Sun ƙetare Kogi da dukkan Tsauni.

    1. Haka Tabi’ai suka bi a wannan hidima,

    Ta yaɗa saƙonnin farin addini.

    32.Matsayinsa gun Allahu mai girma yake,

    Tamkar ya shi babu cikon Manzanni.

    1. Duk Manzani izuwa mutanensu kaɗai,

    Ya taƙaita saƙon Rabbi kan imani.

    1. Shi ko Rasulullahi dukkan duniya,

    Allah ya ce ya isar da Alqur’ani.

    1. Haiwanu dabbobin tudu da na Maliya,

    Bayan dukannin ‘yan Adam wal Jinni.

    1. Ceto a ranar tsayuwa shi za a ba,

    Farko gabanin dukkanin Manzanni.

    1. An ba shi tafkin Kausara mai waraka,

    Ga dukan ƙishi Manzo jinin Adanani.

    1. Saƙon da an masa ya isar mun tabbata,

    Kamar da Rabbi ya ba shi ba nuƙusani.

    1. Musulunci ya ratsa dukannin duniya,

    Lungu da saƙo sai tilar Qur’ani.

    1. Ya Sayyadi baban Ruqayya da Ɗayyibu,

    Mun shaida ka yi isar da duk saƙonni.

    1. Ya mai yawan zikiri da bautar Rabbana,

    Mun yarda Allah ɗai yake Wahadani.

    1. Ya mai yawan jinƙai ga dukkan talikai,

    Ka ceci al’umma ga bin ausani.

    1. Ya Sahibas Siddiƙi Umar naka ne,

    Suruki wajen Usmanu Zun-Nuraini.

    1. Ya surukin Haidar Aliyu mazan ƙwarai,

    Kakan tagwaye Alhasan da Husaini.

    1. Ya wanda zai karɓi Luwa’ul Hamdi ran,

    Tsayuwa ga Allah Sahibat Tijjaani.

    1. Ya wanda zai ceci Musulmi na ƙwarai,

    Ranar hisabi da awon mizani.

    1. Ya Sayyadi Allah muke roƙo ya sa,

    Mu mutu bisa ga biyar Kitab was Sunni.

    1. Ya Abba Fatima Albatulu Habibuna,

    Allah ya ba mu zama da kai a Jinani.

    1. Allah muna yin hamdala munka zamo,

    A cikin Musulmi khiiratul adyani.

    1. Allah ka tsai da mu siraɗul mustaƙim,

    Izuwa macewa kar mu zam khusrani.

    1. Allah ka dumata zuciyarmu bisa biyar,

    Manzo naka da ka bai wa Alqur’ani.

    1. Allah muna a cikinsa ƙarshen zamani,

    Mai haɗari da yawan biye shaiɗani.

    1. Allah tsare mu da makarul a’adaa’i,

    Na son mu raunata har mu bar imani.

    1. Allah ka dawwama son Rasulu a zuciya,

    Ya zamo abin koyinmu dukka shu’uni.

    1. Begen masoyi ya halatta ga taliki,

    Balle Rasulu da Rabbi ya yi umarni.

    1. Yabon gwani ko wajibi haka anka ce,

    Manzo gwani na gwanaye ne ba zanni.

    1. Aikin da ya yi wa duniya tamkar ya shi,

    Ba a yo ba har yau in akwai wane ni?

    1. Kullum salati gare shi kar mu sake da yi,

    Guzuri gare mu manauyayin mizani.

    1. Sallaa alaikallahu ya khairal bashar,

    Wa ’Alika wa Sahabi wal ikhwani.

    1. Mai tsara waƙar Nasiru G. Ahmadu,

    Mai son Rasulu hasanarsa da rauni.

    Alhamdu lillahi.

    Wannan waƙa an ciro ta ne daga littafi mai suna TASKIRA wanda Nasiru G. Ahmad ya wallafa.

    Karanta Yadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

    Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

    1.

    A yau mun taru cikin alkunya,

    Domin girmama gwarzonmu mai dubayya,

    Haske ya sake yalwata cikin Hausaniya,

    Da samun Farfesa Mu’azu a mai kyan halayya.

    2.

    Ka jima kana hura wutar hikima,

    Kana tsarkake harshenmu ba taƙama,

    A makarantu sun ɗauki darusa ba gardama,

    Sun zame wa ɗalibai hasken tafarki mai tsunduma.

    3.

    Mu’azu Sa’adu, ginshiƙin Hausar mu ta dauri,

    Ka ɗaukaka harshen da kakanni suka bari.

    A yau an saka maka rawanin girma tuturi,

    Ka zama damina mai sanyaya shuka ba fari.

    4.

    Salmanu Faris Kudan na taya ka murna,

    Da wannan matsayi mai jan hankalina,

    A madadin marubutan Arewan zaurena,

    Muna yi maka fatan ƙarin nasarori da zayyana.

    5.

    Girmanka ya zama abin jingina ba wariya,

    Ƙwararrun marubuta suna sanya ka a zuciya.

    Ka zama tubalin da ya ƙara ɗaure ginin Hausaniya,

    Harshen da ke ɗaukaka Arewa da Nijeriya.

    6.

    Muna yi maka addu’ar fatan alheri,

    Rayuwa mai cike da ƙarin annuri.

    Allah Ya saka maka cikin mafi alheri,

    Ya ƙara nisan kwana bisa tsari.

    Karanta Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

    Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

    1. A yau Arewa ta wayi gari da annuri,

    An kunna fitilar da ta daɗe da alheri,

    Gwarzon ilimi Mu’azu Sa’adu mai annuri,

    Ya ɗaukaka harshe cikin nutsuwa bisa tsari.

     

    2. Ranar nan ta zamo alfahari ga dukkanmu,

    An ɗaga rawani a kan ƙashin kaifin basirarmu.

    Ka hau kujerar Farfesa cikin ladabinmu,

    A ɓangaren harshen Hausa mai cike da tarihinmu.

     

    3. Ka zama jagoran harsunan Nigerian Languages,

    A Jami’ar Sule Lamiɗo, Kafin Hausa mai darajas.

    Ka ɗauki nauyin harshe da ƙarfin halis,

    Kana koya wa duniya kima da martaban Hausas.

     

    4. Ka reni ɗalibai da armashi da hikima,

    Ka zuba ilimi kamar ruwan sama.

    Darussanka sun zama turakun hawa sama,

    Sun gina ƙarni masu zuwa tun kafin anjima.

     

    5. A fagen nazari ka zama tamkar tauraro,

    Kana haskakawa masana masu sauraro,

    Littattafanka sun zama ginshiƙai abin dogaro,

    Duk inda ake Hausa, za ku taho har ɗan goro .

     

    6. Ka zama madoga ga marubutan Arewa,

    Mai tsarkake harshen har da rera wa,

    Ka zama ginshiƙi da ba ya dusashewa,

    Wanda ya daidaita harshenmu cikin dubawa.

     

    7. Ni Salmanu Faris Kudan, mai buƙata,

    Na miƙa wannan waƙa a madadin marubuta,

    Mu na yi maka barka da wannan babban kyauta,

    Allah Ya ƙara maka lafiya ban da kunyata.

     

    8. Rayuwarka ta zama izina ga matasa,

    Ga waɗanda ke neman hasken don yai tasa,

    Ka nuna musu cewa aiki ne jawur ga matasa,

    Su ne hanyoyin da ake hawa don tasa.

     

    9. Duniyar Hausa ta yi murna da annushuwa,

    Ta ƙara jin ƙima da samun ɗaukakawa,

    Nasara irin taka ta zamo abin dubawa,

    Ga duk mai son zama abin koyi a rayuwa.

     

    10. Malam Mu’azu, Allah Ya yi maka albarka,

    Ya ƙara nisan kwana da nutsuwa a gare ka,

    Ya zuba hikima wacce ba ta yankewa gare ka,

    Ka ɗaukaka fiye da yadda kake yanzu da albarka.

    Danna nan don karanta Tsokaci A Kan Littafin Salmanu Da Salma

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tsokaci A Kan Littafin Salmanu Da Salma

    Tsokaci A Kan Littafin Salmanu Da Salma

    Littafin “Salmanu da Salma” littafi ne na soyayya da aka gina bisa tubalin kimiyya da ilimi. Marubucin ya nuna cewa soyayya ba motsin zuciya ba ne kawai, tana buƙatar fahimta, haƙuri da haɗin kai.

    Babban jigon littafin shi ne soyayya, wacce ta haɗu da ilimi, inda jaruman ke fuskantar ƙalubale tsakanin burin rayuwarsu da  kuma soyayya. Labarin ya nuna yadda ilimi ke taimakawa wajen yanke shawara mai kyau a rayuwa.

    Salmanu jarumi ne mai son kimiyya da burin samun nasara, yayin da Salma ke ta kasance mace mai hankali, ilimi da juriyar zuciya. Rikice-rikicen da suka shiga sun sa labarin ya zama mai jan hankali.

    Kuma an yi amfani da kalmomi masu sauƙin fahimta, waɗanda suka dace da kowane mai karatu. Saƙon littafin shi ne cewa soyayya ta gaskiya tana bunƙasa ne, idan an haɗa ta da ilimi da mutunta burin juna.

    Karanta Tarihin Farfesa Abdallah Uba Adamu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ga Tsoro Ga Ban Tsoro

    Ga Tsoro Ga Ban Tsoro

    “Ubangiji (Allah) ya halicci mutane, Samuel Colt ya dai-daita su”

    – Sammuel Colt (1836)

    12/08/2024

    SHIMFIƊA

    Samuel Colt ya faɗi wancan maganar ce bayan ya ƙirƙiri ƙaramar bindigar hannu (Revolver), don ya nuna mahimmancin abin da ya ƙirƙira. Sannan dan ya nuna rashin fifikon wani a kan wani idan kowa ya mallaki bindiga.

    Allah SWT ya ce: “Kada ku kashe kawunan ku, Allah mai rahama ne a gareku” (Q4:29). Allah Ta`ala ya ce: “Wanda ya kashe Mumini da gangan, sakamakonsa jahannama zai tabbata a cikinta…” (Q4:93). A Hadisi Manzon Allah SAW ya ce:” Baya tare da mu wanda ya ɗau makami a kan mu”

    Waɗannan ayoyi da hadisi da wasu masu tarin yawa suna hani ne game da kisan kai. A ayar farko Allah sai da ya nuna shi kansa mai rahama ne ga bayinsa, wato rashin tausayi ne da imani a zuciya ya ke sanya wani ya kashe mutum ɗan uwansa.

    A aya ta biyu kuma Allah ya nuna sakamakon wanda ya yi kisan kai ba da wani dalili na shari`ah ba. Manzon Allah ya faɗi cewa ba ya tare da Shi (Manzon Allah SAW) sannan ba ya tare musulmi gaba ɗaya wanda ya ɗau makami don zubar da jinin musulmi.

    MAKAMI A HANNUN FARAR HULA

    Hasashe ya tabbatar da cewa a duniya akwai ƙananan makamai kimanin milliyan ɗari Takwas da Saba`in da Biyar (875M) yawancin su a hannun fararen hula da gama-garin mutane.

    Kimanin miliyan ɗari (100) daga cikin waɗannan makaman suna Afirka, har da ƙasar mu Najeriya. Sannan kashi Arba`in (40%) na daga cikin mace mace a duniya sanadiyyar amfani da waɗannan makaman ne.

    Yaɗuwar ƙananan makamai musamman bindiga, wata matsala ce da duniya take fama da shi a yanzu. Bincike ya tabbatar da cewa abubuwan da suke ke janyo yaɗuwar ƙananan makamai sun haɗa da yaƙe yaƙe -rashin zaman lapiya a ƙasashe daban daban, da ayukan ta`addanci.

    Na biyu taɓarɓarewar dokokin ƙasashe da rashin ƙarfin gwamnatoci. Na uku ƙaruwar kamfanonin ƙirƙiran makamai a duniya. Waɗannan dalilai suna janyo ƙaruwar laifuffukan da suka haɗa da kashe-kashe, fashi da makami, kashe kai, ƙaruwar ayyukan ta`addanci da sauransu.

    Wannan matsalar ta shafi duniya gaba ɗaya, kullum ayyukan ɓarna da ke afkuwa cikin ƙasashe daban daban suna tabbatar da haka. Manyan ƙasashe irin su Amurka, kullum suna fama da irin waɗannan matsaloloin na amfani da ƙananan makamai wanda sanadiyyar su kullum ake rasa rayuka masu yawa.

    Duk da Amurka tana da dokar mallakar makami. Amma wannan matsalar ta addabi Amurka. Babban misali a nan shi ne yadda wani matashi mai suna Thomas Mathew Crooks ya kai wa ɗan takaran shugabancin ƙasar Amurka Donald Trump hari da bindiga, hakan ya yi sanadiyyar tsinke masa saman fatan kunnensa na ɓangaren dama.

    Wannan harin ya faru ne ranar 13 ga watan Yuli, 2024 a birnin Pennsylvania yayin da Donald Trump ya ke tsaka da yaƙin neman zaɓensa a zaɓen da ya gabata. Najeriya ɗaya ce daga cikin ƙasashen duniya da kuma Afirka da ke matuƙar fama da wannan matsala ta yaɗuwar ƙananan makamai a hannun gama-garin mutane da fararen hula, musamman a waɗannan shekarun.

    Ƙaruwar yaɗuwar makamai a hanun gama-garin mutane a Najeriya za a iya danganta shi daga lokacin da aka fara fasa bututun mai da kuma masu sace fararen fata suna garkuwa da su, musamman a kudancin ƙasar nan a baya.

    Zuwa rigingimun addini a Arewa ta tsakiya a farkon shekarun 90s, rigingimun Tibi da Jukun, sannan rigimar Boko haram/ISWAP da `yan ta`adda masu garkuwa da mutane a Arewa maso gabas na ƙasar nan, waɗannan rigingimu sun ta da zaune tsaye da kawo rashin kwanciyar hankali, sun janyo rasa rayuka masu yawa tun daga shekarun 2008 har zuwa yau.

    Gwamnatoci, ba za a ce ba sa taɓuka komai ba, amma a gaskiya, ayyukan `yan bindiga daɗi da masu tarzoma sun yi tsanani fiye da ƙima. Mutane har gani suke kamar sun fi ƙarfin hukumomi saboda wasu dalilai.

    Samuel Colt da ya ce Allah ya halicci mutane, shi kuma ya daidaita su. So yake ya fito da wani abu mai mahimmanci a fili. Duk wanda yake aikata aikin ta`adanci dan kawai yana riƙe da makami, toh ba fa ya fi wanda ya ke yi wa ta`addancin ƙarfi ba ne, kawai dan yana riƙe ne da makami.

    Duk lokacin da wanda ake yi wa ta`addanci shi ma ya riƙe makami, to sai dai kowa yi ta kansa, a lokacin kowa daidai yake da kowa, ba wanda zai yi wa wani ta`addanci, sai dai a yi kare-jini-biri-jini. Don haka kowa sai ya sa kowa cikin zullumi da tsoro.

    Masu riƙe da makamai sun sani, idan kowa zai sami makami toh su kansu ba za su ji daɗin rayuwar su ba kamar yadda suke yinta a yanzu, saboda yadda suke farautar sauran mutane, haka suma za a rinƙa farautar su.

    A irin wannan yanayi, sai rayuwa ta zama tamkar rayuwar dabbobi a daji wanda Allah ya ba shi sa’a shi ke nan, ba wanda ya ke da tabbacin rayuwarsa. Kowa kullum cikin zullumi da rashin kwanciyar hankali. Rayuwa ta zama ba komai ba, mara daɗi, gajeriya mai cike da tsoro.

    RUFEWA

    Allah SWT ya sanya rahama a cikin zuciyoyin halittarsa musamman ɗan adam, shi yasa za a ga Uwa yadda take tarairayar `ya`yanta. Wannan rahamar ce ta ke sanya mutum ba ya iya kashe ɗan uwansa haka kawai idan wannan rahamar tana cikin zuciyarsa. Shi ne abinda Allah ya ke nuni da ayar a aka ambata a farko.

    Shi kansa Allah da ya halicce mu, bai zama mai ɗaukan ranmu haka kawai ba, sai ajalin da rubuta mana ya yi. Duk wanda ya kashe wani, ya sani ba zai tabbata a duniya ba shi ma wata rana sai ya mutu, ya bar duniyar.

    A hadisin Manzon Allah SAW a fili ya faɗi cewa duk wanda ya ɗau makami ya yi kisan kai, to ba ya tare da Mu (wato ba ya tare da Manzon Allah SAW da kuma sauran muminai). Shin idan mutum ya mutu amma ba ya tare da Manzon Allah SAW, ina ne makomar sa?

    A aya ta biyu Allah ya ja kunnen mu da nuna mana sakamakon wanda ya aikata aika aikan kisan kai, makomar sa wutar jahannama kuma zai tabbata a cikin ta har abada. Shin wannan abin da Allah ya faɗa shin akwai wanda ya ke ganin ba haka ba ne? Ko kawai tatsuniya ce da labarin ƙanzon kurege?

    Duk musulmin da ya yi imanin akwai ƙiyama, akwai hisabi sannan akwai sakamako, to ya tabbata abinda Allah ya faɗi gaskiya ne to ba zai yarda ya kusanci wannan mummunan aikin ba, ba zai yarda ya ɗau ran wani mutum ba.

    Dukkan musulmi da yake rayuwa a wannan duniyar, na farko dai ya san zai mutu, toh buƙatar sa in ya mutu ya sami rayuwa mai daɗi da take cike da ni`ima wadda tafi ta nan duniyar. Rayuwar lahira ta aljannah ba a samun ta da saba wa Allah, musamman da mummunan aika aika na kashe ran ɗan Adam.

    Allah muna roƙonka ka shiryar da mu, Ka ganar da mu hanya mai kyau, Ka tabbatar da mu a kan ta, sannan Ka ba mu rayuwa mai kyau a nan duniya da rayuwa mafi kyau a lahira. Amin.

    Karanta Ayyukan Ta’addancin Matasa A Kano: Aure, Yawan Haihuwa Da Tarbiyya A Wata Mahanga

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Atini Yake (Dysentery)

    Yadda Atini Yake (Dysentery)

    Idan mutum na fama da atini yakan rasa samun sukuni, sannan a kodayaushe ya kan ji kamar kashi ya matse shi sosai tare da jin kamar zai yi shi a wando, amma kuma yana zuwa banɗaki sai ya ji ya kasa yin kashin ko ya yi ɗan kaɗan!!

    Idan ya kasance kana fama da wannan matsalar ko ka taɓa yin ta a baya, daure ka karanta wannan gajeren rubutun domin sanin  abin da ke kawo maka wannan matsala.

    ABUBUWAN DA KE KAWO ATINI:

    1. Kumburin magudanar Kashi (rectal inflammation): Rectal inflammation kan sa mutum atini sosai, bayan atini waɗansu daga cikin Alamominsa sun ƙunshi kashin jini da majina.

    2. Basir (Haemorrhoids): Basir Yana daga cikin abinda kan sa mutum atini sosai, musamman kafin ya yi tsiro, wani sa’in Kuma yakan sa mutum kashi mai tauri (constipation), kashin jini da sauransu.

    3. Infectious dysentery ko ɓacewar ciki: A lokacin da cikin mutum ya ɓaci bayan cin wani abu, mutum zai ta atini sosai sannan ya kasa sukuni a waje ɗaya.

    1. Kansar magudanar kashi (Rectal tumour): Duk mutumin da ke fama da rectal cancer kan zo da kashin  jini, kashi mai tauri(constipation) bayan atini.
    2. Pelvic Inflammatory diseases (sanyin Mata): Alamomin PID sun haɗa da ciwon mara, ƙaiƙayin gaba tare da fitar da wani irin ruwa mai wari daga gaban mace (vaginal discharge,) haɗe da zazzaɓi wani sa’in. Wani lokacin yakan haɗu da sanyin mafitsara, hakan zai sa ki yawan fitsari da rana ko yawan tashi da daddare (sau uku zuwa huɗu) domin yin fitsari, zafi yayin fitsari (dysuria), ganin jini a fitsari (haematuria) da sauransu.
    3. Kansar babban hanji (Tumour of descending colon): Alamominta sun ƙunshi atini, gudawa ko kashi mai tauri bayan rama da waɗansu alamomi na cutar kansa.
    4. Ulcerative colitis: Ulcerative colitis na daya daga cikin cututtukan da kansa kumburin Hanji. A lokacin da hanji ya kumbura mutum zai ta fama da atini da gudawa mai ɗauke da majina da jini wani sa’in.

    ME YA KAMATA MUTUM YA YI?

    Duk mutumin da ke fama da wannan ya kamata dai ya je asibiti domin masana abun su yi cikakken bincike a kan abin da ke janyo masa wannan matsalar. Binciken da masana za su iya yi maka a asibiti: likita zai iya saka yin waɗannan binkicen:

    1. Proctoscopy or sigmoidoscopy 

    2. Ko rectal biopsy a lokacin da likita ke zargin kansar magudanar kashi

    3. Coloniscopy with biopsy and Barium enema a lokacin da likita ke zargin alamomin colon cancer

    4.High vaginal swab (HVS), Abdominal Ultrasound Scan (USS) a lokacin da likita ke zargin sanyin Mara wato PID.

    MAGANIN DA LIKITA ZAI MAKA A ASIBITI:

    Maganin da likita zai maka ya danganta da abin da bincikensa ya gano:

    • Idan yakasance Infectious dysentery ne, likita zai ba ka Analgesia domin rage raɗaɗi, zai iya saka maka ruwa (iv fluids) tare  Antibiotics Wanda ya danganta me abun da test ɗin stool mcs ya nuna.
    • Idan Rectal inflammation ne likita zai iya ɗora ka a kan magunguna kamar steroid suppositories ko 5-ASA enemas, sannan zai iya ƙara makaa ruwa (fluids IV ) idan ka kasance ka yi amai sosai, likita zai ba ka antibiotics saboda infection.
    • Idan mutun na fama da PID ne toh likita zai iya ba ka waɗannan magungunan kamar analgesia domin rage raɗaɗin zafin. Ruwa (fluids IV) a lokacin da ya ga jikinka na buƙata empirical antibiotics.
    • Haemorrhoids (Basir) likita zai ba ka magunguna sannan zai ce ka dinga yin Sits bath (wato Zama cikin ruwan gishiri) ko kuma idan ya yi tsauri sosai ya yi maka aikin da ake kira Haemorrhoidectomy.
    • Idan ya kasance Rectal tumors ne ko colonic tumors toh likita zai iya buƙatar yi maka aiki ko ɗora a kan magungunan kansa. (cytotoxic drugs) ko ya yi maka  radiation therapy.

    Daga Cikin bayanan da na yi za a ga na ɗan yi bayani a kan magani na yi hakkan ne kasancewar akwai ɗalibai ‘yan uwana. Allah Ubangiji ya ba mu Lapia da zaman lapia Amin ya rabb

    Danna nan don karanta Yadda Zubar Jini Yake Bayan Haihuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Zubar Jini Yake Bayan Haihuwa

    Yadda Zubar Jini Yake Bayan Haihuwa

    Mahaifar Mace wato “Uterus” a sanda ta ɗauki ciki babu wani guri a jikin halittar ɗan adam da jini ke kai-komo ba tare da ƙaƙƙautawa ba irin wannan gun…. Saboda ƙoƙarin jiki don ganin ya samarwa da abinda ke cikin iska, jini, abinci da kyakkyawan yanayi. Guri ne da ake kira “No go Area” in dai da sunan wargi ne, saboda ko ya hatsari ya faru ana iya shiga uku.

    A duk minti ɗaya na agogo wato sekons 60 sai jini adadin Milimeter 800 zuwa dubu (1liter) ya shiga mahaifa ya fita. Wato dai kwatankwacin ledar pure Water 3 zuwa 4 na jini a duk minti. Shi ko jini baki ɗaya a jikin mutum an yi ƙiyasin ba ya wuce lita 5. Ka ga kenan a minti biyar kacal duk adadin jinin da ke jikin mutum ke shiga ya fita daga cikin Mahaifa. 

    Toh wannan ne yasa ko ya mace ta haihu jini ya ɓalle minti 4 zuwa 5 kacal ta mutu ta gama. Abun ba ya buƙatar ɗaukar lokaci, domin kafin a ankara an yi ta an ƙare. Shi yasa zubar jini bayan haihuwa da ake kira post partum hemorrhage ke kashe mata a karkara da birane ba ji ba gani, domin ko kuna raye a inda manyan asibitoci suke jinkiri kaɗan na abin hawa, ko shawarwarin ya za ai, ko cinkoso a hanya na iya kawo mutuwa ɓagatatan. 

    Toh yanzu Mace masu ciki sun saka kansu cikin wata musiba ta shan wani ruwa da suke wa laƙabi da “RUWAN NAƘUDA” ko a sakaya a riƙa faɗin “RUWAN ADDU’A”. Da ake karɓarwa mata a ba su su sha da sunan naƙuda ta zo musu a gurguje su haihu nan da nan abinda muke kira “PRECIPITATE LABOR.” 

    To alal haƙiƙa ku sani wannan ba wani ruwa ba ne illa ruwan musiba, ruwan guba, ruwan ta-da zaune tsaye, wallahi, wallahi, wallahi duk macen da ke marmarin tafiya lahira a dalilin haihuwa, ko take da burin ta sha da ƙyar tare da ja wa mijinta da iyayen ta asarar manyan kuɗaɗe ba tare da shiri ba, ko take da burin daga haihuwa ɗaya kar ta kuma har abada…

    Toh ta je a ba ta wannan ruwan ta riƙa sha, tunda Allah ya ba ku hankali don ku yi tunani amma sam kun mai da ƙwaƙwalenku tamkar tsumma. Kowanne tarkace yanzu kawowa ake mata su kuma su ɗiba babu lissafi. Shi wancan ruwan wasu muggan sinadarai ake sa mishi masu aiki irin na “Okzitosin” da nan da nan ke sa mahaifa ta fara harbawa tana jijjiga domin juye abinda ke cikinta, tana fisga tana talewa ƙarshe musibar da ake shiga FASHEWAR MAHAIFA yake haddasa wa inda nan da nan Mace kan fita hayyacinta, ta nufi lahira.

    Amma masu ba da irin wannan ruwan wasu ma iyayen yaran ne ke kawo musu. Sun kashe ‘ya’yansu ba tare da sun san su ne suka kashe su ba, sai dai a ce ta haihu amma jini ya ɓalle Allah ya yi mata rasuwa. Karya ne ku kuka kashe ta, kuma akwai shari’a gaban Allah. Kun ba ta abinda ba ku da ilimi kansa, kun ƙi kuma saurarar masana ku ji jan hankalin da suke game da irin wannan muggan al’adun.

    A ƙalla na sami mata uku da suka mutu a wannan tsakanin dalilin shan wannan ruwan naƙudar. Sannan na sami mutum 2 tsakanin nan ‘ƴar shekara 17 da ƴar 21 wanda suka sami fashewar mahaifa, duk da ba su mutu ba sun sha da ƙyar to amma dai hakan na nufin ba su ba kuma ɗaukar ciki ballantana su haihu a duniya, in mahaifa ta fashe ba batu ne a ɗinke ta ba, ta riga ta yi condemn.

    Kuma abin takaici duk jariran nasu sun mutu tun a ciki, shikenan in ba mazajen ƙwarai ba ne shin wa zai zauna da macen da ba zata iya haihuwa ba a irin wannan rikitaccen zamanin namu? Sabuwar amaryar shekara ɗaya a ce ka gane ba ita ba kuma haihuwa dole sai kai shirin kuma sabon aure in kana son haihuwa. 

    Toh wannan ba shi ba ne ma ƙarshen damuwar, ba su ba kuma iya riƙe fitsari, yanzu rayuwarsu za ta dauwama ne da robar fitsari a jika, hanyar kashi ta ɓulle ta dubura ta haɗe da farji. Tsabar wauta da rashin hankali, yarinyar da ko haihuwar fari ba ta yi ba amma da zarar ta sami juna biyu shikenan anta mata aiken abubuwa iri-iri ana ta sha, wannan maganin zaƙi, wannan maganin ciwon mara da dai sauran su.

    Ya kamata idon ya buɗe ku gane me duniya take ciki, kar ki laminci ganganci da rayuwarki. Lallai mu hankalta. Babban abin damuwar har ‘yan boko ko matan da kake ganin suna da ilimi su ma sukan auka cikin irin wannan ɗebe-ɗeben, a haka na sami mace me Masters amma ta je wai an ba ta maganin fibroid a Islamic CHEMIST. An ce idan ta sha zai narke, ƙarshe ga shi fibroid bai narke ba dukkan mararta ta zazzage.

    Dole aka cire mahaifar aka zubar, sannan ba ita ba kuma haihuwa, sannan mafitsararta “Bladder” ta fashe ba za ta gyaru ba, fitsari yanzu ta cikin farjinta yake fita, haka zalik kashi ma wani na fita ta duburarta wani kuma na biyo ta cikin farjinta duk. Yanzu me ya fi wannan tashin hankali, kin je kin kashe kuɗi kin illata kanki a banza da wofi.

    Hakance dai ke faruwa a fannin breast cancer, mace na fama da ciwon nono amma taita biye-biyen masu magunguna a loko suna karɓe mata kuɗi, ba za ta je asibiti ba sai abu ya gama lalacewa nono ya fara wari, in cancer ta gama yaɗuwa inda sai de mutuwa kurum. Don haka Lallai Yan Uwa Mata ku yi hattara, lafiya ta wuce wasa wallahi in kunne ya ji……

    Karanta Yadda Hawan Jini Yake (HYPERTENSION)

    Edita@rumasau-kallamu