Category: Tatsuniyoyi

  • Tatsuniyar Jika Da Kaka

    Tatsuniyar Jika Da Kaka

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    A can wani ɗan ƙauye da ke kusa da Gulbin Tattabaru, an yi wata yarinya da ke zaune tare da kakarta. Rannan yarinyar tana shara sai ta tsinci kurkunu ta bai wa kakarta ta ajiye mata. Da ta gama sharar sai ta je wurin kakar ta tambaye ta: “Kaka, ina kurkununa?” Kakar ta dubi jikarta ta mayar da jawabi: “Ai na cinye, jikalle.”

    Da jin wannan amsa sai yarinya ta fusata; ta ƙura wa kakar ido tace: “A gaskiya kaka ban yarda ba.” Daga nan ta ɗauki buta, ta cika ta da ruwa; ta kama wata kuka ta haye; ta yi zamanta ba niyyar saukowa. Da kakarta ta ga ya kamata ta sauko ta ci abinci, sai ta je kiran ta.

    Yarinya abu kamar da wasa, sai ta ƙi saukowa kakar ta kira maƙwabta da ƙawayen jikarta domin su sa ta ta sauko, ammaina, abu ya faskara. Sai ta ce da wasu samari: “Don Allah ku taimaka ku sare mini kukar nan tun da jikata ta ƙi saukowa.” Samari suka yarda suka debo gatura daga gidajensu.

    Kowa ya yi ɗamara suka fara saran kuka. Suna waƙar gayya, wannan ya sara idan ya gaji wannan ya karɓa, da haka da haka har suka ci ƙarfin kaurin bishiyar. Can da kuka ta nuna layin faɗuwa, sai kawai aka ga yarinyar ta fara rikiɗa, har ta zama kurkunu. A halin haka sai ta haifi ’ya’ya da yawa.

    Kuma nan take ta sake rikiɗa, ta koma mutum a kan bishiyar. Kowa ya buɗe baki sai kallon abin al’ajabi yake yi. Sai ta ce da kakarta da sauran mutanen: “Ga kurkunu nan da yawa ku ci ku ƙoshi, amma ki rage mini guda ɗaya kawai; daga nan sai ki koma gida, zan sauko.”

    Da kowa ya bar wurin, sai yarinya ta sauko ta kama hanyar gida. Tana isa gida sai ta yi wa kakarta bayani cewa: “Ai aljanun da ke zaune a kukar nan ne suka hana a sare ta, saboda haka ne ma suka rikiɗar da ni har na haifi kurkunu domin ki dawo min da shi a ƙyale musu gidansu.

    Kuma sun ce in gaya miki ki gaya wa Mai Gari kada a sake ƙoƙarin sare wannan kukar.” Kakar yarinya ta yi mamakin wannan bayani, kuma ba ta yi nawa ba ta je ta sanar da Mai Gari saƙon da aljanu suka aiko ta hannun jikarta. Shi kuma Mai Gari ya sa aka sanar da jama’arsa cewa kada wani ya kuskura ya sare kukar nan domin gidan mutanen ɓoye ne, abokan zaman lafiyarsu. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wasa tsakanin jika da kaka ba abu ne mai kawo ɓacin rai ba.
    • Wasu mutan ɓoye abokan zama ne ba abokan faɗa ba.
    • Komai za ka yi ka yi tunani kafin ka aikata shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Yan Matan Fangama

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Yan Matan Fangama

    Tatsuniyar ’Yan Matan Fangama

     Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana ’yan matan Fangama suka shirya za su biki a wani gari da ke kusa da su. Dabarar zuwan ita ce ko za su yi dace kowaccensu ta sami manemi, wata rana a yi nata bikin. Kowacce dai ta ci ado, abin gwanin ban sha’awa. Amma kafin su tafi sai da suka fita bayan gari domin kowacce ta tsinko wa mahaifiyarta goriba.

    Dukkanninsu sun samo goriba, in ban da ɗaya daga cikinsu. Ita ta nema, ta rasa. Shi ne bayan sun koma gida, sai mahaifiyarta ta ce lallai ta koma sai ta samo, in ba haka ba kuwa, ita babu tafiya biki. Ta rasa yadda za ta yi don ƙawayenta sun shirya za su tafi su bar ta.

    Haka dai ta jure ta koma wurin bishiyar goriba, ta roƙe ta. Da bishiyar ta ji bayaninta, sai ta tambaye ta: “Me za ki yi da goribar idan na ba ki?” Yarinya ta ce: “Zan kai wa mahaifiyata saboda ta ba ni kayan da zan sa mu je wani biki aure tare da ƙawayena.” Da jin haka bishiyar ta ce: “Ba zan iya taimakon ki ba, sai in kin roƙi girgije ya sako ruwa in sha.

    Idan na sha sai in zuba ’ya’yan da zan ba ki.” Yarinya ta durƙusa ta roƙi Ubangiji ya sauko da ruwa. Bayan wani ɗan lokaci kuwa sai aka kece da ruwa mai ɗimbin yawa. Goriba ta yi ’ya’ya, yarinya ta tsinka ta kai wa gyatumarta. Nan da nan uwar ta kawo kayan kwalliya da na alatu, masu kyan gaske ta ba ’yarta.

    Amma kuma tuni ƙawayenta cikin gaggawa sun tafi, sun bar ta a baya.Da yake tana cikin ɗoki, ba tare da kasala ba ta kama hanya ita kaɗai, har ta isa wurin bikin. Ta tarar ƙawayen ba su jima da zuwa ba. Samari kuwa sun cika wurin, saboda iyayen ma’auratan sun gayyato mutane da yawa.

    Aka yi ta shagali, suka ɗirki rawa, har suka gaji. Can a lokacin tsarince, sai wani saurayi kyakkyawa wanda ke tashen samu ya kira ta. Suka yi taɗi, ya yaba hankalinta. Daga nan suka shirya aure, da ta koma gida ta sanar da iyayenta, shi maya tura magabatansa gidansu.

    A takaice dai, aka ba shi ita, suka yi aure. Sauran ƙawayenta ma daga baya Allah ya ji kukansu, ɗaya bayan ɗaya suka sami maza, kowacce ta shiga ɗakin miji. Yanzu haka suna can har sun fara hayayyafa, kowacce na zaune lafiya da mijinta. Kuma wani abin ban sha’awa shi ne, har yanzu suna ƙawance da junansu. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mai nema yana tare da samu.
    • Ka so wa ɗan’uwanka abin da kake so ga kanka.
    • Biyayya ga iyaye takan kawo wa mutum buɗi da cimma burinsa na rayuwa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Garin Da Ba Maza Sai Mata

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Garin Da Ba Maza Sai Mata

    Tatsuniyar Garin Da Ba Maza Sai Mata

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wani gari da duk mazaunansa mata ne zalla, watau ba wani namiji ko ɗaya a cikinsu. Su matan a kullum sukan tafi rafi su yi wanka, su kuma ɗauko ruwa. Sai wani mutum daga wani gari mai nisa ya ji labarin wannan ƙauye. Ya ɗaura ɗamara, ya kama hanya da nufin sai ya je wannan gari mai ban mamaki.

    Ya yi tafiya mai nisa a cikin ƙungurmin daji kafin ya isa. Da zuwansa sai ya hangi wasu mata kyawawa suna wanka a rafi. Ya matsa har ya isa kusa da su, ya gama kallon su sarai, ba tare da sun sani ba. Da ya ga ba su gan shi ba, sai ya kwashe tufafinsu da ke dab da bakin kogin nan; ya hau bishiya, ya ɓuya.

    Can da matan suka gama wanka suka fito sai suka ga ba suturarsu. Suka duba nan suka duba can ba su ga kowa ba, suna ta mamakin abin da ya faru. Wasu suna ce ko aikin aljanu ne. Can sai wata daga cikinsu ta leƙa saman wata bishiya sai ta ga mutumin. Ita ce kuma ta fi duk sauran kyau.

    Shi kuma mutumin ɗan saurayi ne mai kyan gaske. Daga nan sai matan suka kama waƙa, suna cewa:

    “Kai saurayin nan, Kai saurayin nan,

    Don Allah ka maido mana da kayanmu nan.

    Kai saurayin nan, Kai saurayin nan,

    Ka ji kunyar mu, Ka dawo mana da kayanmu.”

    Nan da nan ya mayar musu da kayansu, amma banda na waccan mata da ta fi sauran kyau. Ya ce zai ba ta kayanta ne kurum idan ta yi masa waƙa mai daɗi, kuma ta ambaci sunansa. Sai ta yarda. Ta rera waƙar mai daɗi, sai dai ba ta ambaci sunansa ba, saboda ba ta sani ba.

    Shi kuwa ya ƙi ba ta kayan. Yana ta ja mata rai, har rana ta kusa faɗuwa. Da mahaifiyarta ta ga shiru ba ta koma gida ba, sai ta aiki ƙanwarta nemanta. Kanwar na zuwa bakin ruwa sai ta tarar da yayarta zindir, haihuwar uwarta. Tana ganin ƙanwar sai ta ce:

    “Akwai wani kyakkyawan saurayi a wurin nan wanda ya riƙe kayana; ya ce ba zai
    ba ni ba sai na ambaci sunansa.” To da man kanwar hatsabibiyace, sai ta yi wani siddabaru irin nata, ta ji kurum kamar daga sama an gaya mata sunan saurayin nan. Nan take ta sanar da yayarta, tace kuma ta yi wakar ta faɗi sunan ta ga abin mamaki.

    Da ta yi haka sai saurayi ya mayar mata da kayanta; ya sauko daga kan bishiyar;
    ya ɗora ta tare da ƙanwar a kan doki; ya karya linzami, ba su zame ko’ina ba sai a ƙofar gidan su yarinyar. Gyatumarsu da maƙwabta suka yi ta mamakin ganin namiji a garin saboda duk tsawon rayuwarsu ba wadda ta taɓa ganin namiji.

    Ba tare da ɓata lokaci ba mutumin ya nemi yarinyar da aure, aka ba shi. Aka yi aure da babban biki mai ƙayatarwa. Bayan can ya sami wuri ya gina gida mai ƙayatarwa a garin, shi da matarsa suka zama abin kallo, ba a zancen komai sai nasu. Bayan ’yan shekaru suka haifi ’ya’ya maza biyu.

    Wata rana mutumin ya ce zai je ganin gida, amma tare da ɗaya daga cikin ’ya’yan. Uwar ta ce su dawo lafiya. Suka je, suka komo. Bayan an kwana biyu mutumin ya ce zai sake ziyartar garinsu, amma a wannan karo yana so ya je tare da ’ya’yan duka, domin ya nuna wa danginsa su baki ɗaya.

    Wannan buƙata ta mutumin ta tayar da hankalin duk matan garin. Amma mahaifiyarsu, ta dage a kan cewa a bar mijin ya yi haka. Da mutumin ya je garinsu, sai ya yi zamansa, bai koma ba. Matar ta yi ta kuka saboda rashin ganin ’ya’yanta. Bugu da ƙari mutumin ya aiko da saƙo cewa ya saki matar.

    Bayan wani lokaci Ubangiji ya share mata hawaye. Wani ɗan Sarki daga wata ƙasa ya je garin, ya neme ta da aure, ta yarda aka ɗaura musu aure aka yi babban biki. Suna nan zaune, har ɗan Sarki ya gaji sarautar gidansu. Ba a jima ba shi ma ya rasu, ɗan da suka haifa da matar ya gaje shi.

    Ita kuma Allah ya ba ta tsawon rai, ta zauna tare da ɗanta cikin ni’ima. Waɗancan ’ya’yan nata na farko su ma sun zo sun girma suka matsa wa mahaifinsu ya bar su suna zuwa a kai a kai suna gaishe su ana musu alfarma. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wani hani ga Allah baiwa ne.
    • Soyayya gamon jini.
    • Mai haƙuri yakan dafa dutse.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Tatsuniyar Kanta Da Mugayen Abokananta

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Akwai wasu ’yan mata su goma sha biyu ƙawaye. A cikinsu har da wata ’yar Sarki mai suna Kanta. Ita kaɗai ce a wurin mahaifiyarta. Ita ce kuma ta fi kyau a tsakanin duk ’yan matan garin. Kowane saurayi a garin yana so ya aure ta, amma ta ƙi. A cikin waɗanda suke son ta har da wani maciji wanda ke zaune a cikin kogin da ke kusa da ƙauyen.

    Sauran ’yan matan suna kishin Kanta saboda farin jininta da kyauta. Saboda haka suka haɗa baki cewa za su ja ta zuwa kogin nan domin su kashe ta. Mahaifiyar Kanta ta gane duk ƙulle-ƙullen da ’yan matan suke yi game da ’yarta, saboda haka ta yi ta ƙoƙari ta kare ta.

    Duk lokacin da ’yan matan suka zo neman Kanta, sai ta ce da su ba ta nan. Wata rana sai uwar Kanta ta tafi wata unguwa ziyara. Ganin haka ’yan matan nan suka je har cikin gidan Sarki suka ja hankalin Kanta har ta amince za ta bi su kogin nan. Ta bi su da sunan kamun kifi za su.

    Da suka isa kogin, sai suka ga wani mangwaro mai ’ya’ya, kuma suka yanke shawara za su hau domin su tsinki na sha. Kanta ta ƙi hawa, amma suka matsa mata, har dai ta hau. Kowaccensu ta roƙi Kanta da ta tsinko mata mangwaro. Macijin da ke kogin nan ya ji hayaniya ta yi yawa, sai ya fito.

    Ya nufi inda ’yan matan nan suke. Da suka gan shi suka gudu, suka bar Kanta a sama. Macijin ya hau itacen ya same ta. Can daga baya ’yan matan suka koma wajenta, suka ga halin da take ciki. Da suka iso sai suka kama waƙa, suna cewa:

    “Kai macijin nan don Allah,

    Ka sassauta wa Kanta ta sauko,

    Kai macijin nan don Allah,

    Ka sassauta wa ƙawarmu Kanta ta sauko.”

    Kanta kuwa sai hankalinta ya tashi. Da mahaifiyarta ta dawo ba ta gan ta a gida ba, sai ta shiga nemanta. Ta shiga nan ta shiga can har dare ya yi ba ta gan ta ba. Ƙawayen Kanta kuwa suka koma gida dab da almuru, suka baro ta a kan mangwaron nan na bakin kogi.

    Allah da ikonsa sai ga wani ɗan tsuntsu fari ya zo ya sauka kusa da Kanta; sai ta roƙe shi, ta ce: “Kai ɗan farin tsuntsun nan, don Allah ka taimake ni ka kai saƙona ga iyayena. Babana shi ne Sarkin garin. Ka gaya musu cewa ina cikin matsala. Ƙawayena duk sun gudu sun bar ni da wani maciji wanda yake so ya haɗiye ni.

    Ina nema su kawo mini gudunmawa da wuri don su kuɓutar da ni daga wannan matsala.” Ɗan tsuntsu ya yarda; ya tashi sai fadar Sarki. Da ya isa gaban Sarki sai ya ce: “Mai martaba, na zo ne in ba ka saƙo daga ’yarka.” Da jin haka sai mamaki ya kama Sarki da matarsa.

    A gigice Sarki ya ce da ɗan tsuntsu: “Yi maza ka gaya mana saƙon.” Ɗan tsuntsu ya ce: “Mai martaba, ’yarka ce tana can dogon daji; tana kan wata babbar bishiyar mangwaro, kuma wani babban maciji ya kusa ya haɗiye ta.” Da jin haka, ba tare da ɓata lokaci ba Sarki ya tattara dogarawansa suka tafi ɗan tsuntsu na nuna musu hanya.

    Da suka isa sai suka tarar macijin ya fara barci. Ba tare da yin wani motsi da zai farkar da maciji ba, suka ce ɗan tsuntsu ya yi ƙoƙari ya goyo Kanta, ya sauko da ita. Ɗantsuntsu ya je wajen Kanta ya gaya mata zai goye ta. Ya juya baya ta ɗare, ya tashi fir, yana nishi, da ƙyar ya kai ta fada.

    Dogarai suka sulale, suka bar maciji na barci, suka isa fada lafiya. Washe-gari Sarki ya sa a kirawo duk ƙawayen ’yarsa. Suka zo fada. Da aka bayyana duk abubuwan da suka faru, sai ƙawayen Kanta suka tuba, tare da yin alƙawari ba za su sake yin irin wannan abu ba har abada.

    Suka roƙi Sarki ya yafe musu. Sarki ya yarda, ya yi musu afuwa. Ya kuma sa wasu samari su auri ’yan matan. Aka yi babban biki a fadar Sarki. Har yanzu waɗanda suka san an yi wannan biki sukan ce ba su taɓa ganin biki mai armashi da ƙayatarwa kamarsa ba.

    Amma fa wani abu shi ne, duk da shagalin da aka yi lokacin bikin nan cikin farin ciki, Sarki bai huce baƙi ɗaya ba; sai da yasa aka je aka kashe macijin nan. Zaratan da suka kashe macijin suka ɗauko mushensa suka kai fada. Maciji ne mai tsawon gaske, kuma ba wanda ya taɓa ganin irinsa a ƙauyen.

    An ce ya halaka wasu daga cikin zaratan da Sarki ya tura suka kashe shi. Sarki ya yi wa waɗanda suka mutu wajen kashe macijin alheri, wanda aka ba iyalansu, kuma waɗanda suka dawo lafiya daga cikinsu ya yi wa kowannensu aure. Mutanen garin kan yi bikin tunawa da waɗanda suka rasu saboda bajintar da suka yi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a rama kirki da mugunta.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.
    • Wayo ya kada sarkinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta tatsuniyar Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Tatsuniyar Dila Da Zomo

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Dila ya haɗu da Akuya. Bayan sun gaisa sai Dila ya tambayi Akuya ko za ta ba shi ɗaya daga cikin ’ya’yanta su je bakin kogi shan ruwa? Akuya ta amince amma fa da sharaɗi. Sharaɗin shi ne tana so Dila ya lura da ’yarta sosai kar wani mugun abu ya same ta. Shi kuma Dila ya amince da haka.

    Da Dila da ’yar Akuya suka isa bakin rafi sai suka tarar wuta na ci a wani rami da ke kusa da kogin. Tun da ’yar Akuya ba ta da cikakken wayo, sai Dila ya ce mata shi zai shiga ruwan, ita kuma ’yar Akuya ta shiga ramin da wuta take ci. ’Yar Akuya ta bi
    maganar Dila, ta shiga ramin, wuta ta cinye ta.

    Bayan Dila ya gama kiwo sai ya zaro naman ’yar Akuyar daga ramin, ya cinye. Ya kama hanya, bai tsaya ba sai gidan Akuya, ya fashe da kuka ya ce mata ruwa ya cinye ’yarta. Akuya ta haƙura, amma abin ya yi mata ciwo. Daga nan Dila ya tafi wurin Zomo, ya nemi a ba shi ɗaya dagacikin ’ya’yansu domin su je rafi.

    Aka amince, amma da sharaɗin cewa idan ɗan Zomo zai kai kifi da yawa gida. Dila da ɗan Zomo suka je bakin ruwa, suka shiga. Dila ya yi ta iyo, amma ɗan Zomo da bai iya ruwa ba, ya tsuguna yana kallo. Jim kaɗan Dila ya sa shi ya shiga ramin da ke can gefen rafin wuta na ci a ciki. Sai dai a wannan karon wayon Dila bai yi aiki ba.

    Ɗan Zomo ya ƙi shiga ramin. Maimakon ya shiga, sai ya tuɓe takalmansa, ya jefa su a ciki, ya koma gefe ya ɓuya. Dila kuwa sai ya shiga murna, yana zaton ɗan Zomo ma ya yi irin ta ’yar Akuya. Da Dila ya gama iyo sai ya zaro takalmin ɗan Zomo da ya sha wuta, ya cinye. Ya sha ruwa, ya kama hanya ya tafi gida.

    Tsammani yake naman ɗan Zomo ya cinye. Dila bai sani ba ɗan Zomo na ɓoye a cikin jakarsa. Saboda haka a lokacin da Dila ke kan hanyar komawa gida, sai ɗan Zomo ya kama waƙa yana cewa:

    “Dila ashe kai wawa ne,

    Dila ashe kai wawa ne,

    Ka cinye takalmina,

    Tsammani kake ni ka cinye.”

    Da Dila ya ji waƙa sai ya ce:

    “Ke jakata, ashe kin iya waƙa haka?”

    Bai tsaya ba, har sai da ya isa gidan Zomo. Ya je yana kuka sharaf- sharaf, hawaye sun cika masa fuska, kamar abin tausayi. Amma tun kafin ya yi wa iyayen ɗan Zomo ƙaryar kogi ya cinye musu ɗa, sai ɗan Zomo ya yi farat ya fito daga cikin jakar Dila. Tun kafin Dila ya ce da uwar Zomo ɗanta ya mutu a ruwa, sai ɗan Zomo yace:

    “Ƙarya yake cewa kogi ya tafi da ni. Abin da ya gaya mini shi ne in faɗa cikin wuta don wutar ta ƙone ni, wai shi zai yi iyo. Dabara na yi na tsira daga sharrinsa, domin da na shiga ramin, to da wuta ta cinye ni, ya sami nama ke nan. Maimakon in faɗa wutar ne na jefa takalmana.

    Shi kuwa Dila da ya fito daga iyo ya cinye takalman da suka sha wuta. To bai yi sa’a ba, mugun nufinsa ya ci tura.” Nan take sai ɗan Zomon ya kawo shawara cewa, lalle ne su shaidawa Sarkinsu saboda abin da ya faru da ’yar Akuya haka ya kusa faruwa da shi. Da suka kai ƙara, Sarki ya ba da umurni dogarawansa su kama Dila su je su fille masa kai a bayan gari. Haka kuwa aka yi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ba a rama kirki da mugunta.
    • Kowa ya ci amana sai amana ta ci shi.
    • Wayo ya kada sarkinsa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Tatsuniyar Gizo Da Kura

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Gizo ne yana yawonsa sai ya tarar da tarin kashi a wani wuri. Bai tsaya ba, ya tsallake ya yi tafiyarsa. Jim kaɗan sai Kura ta bi ta wurin, ita ma ta ga kashin, sai ta kama da ci, kuma ta ji kashin yana da daɗi, sai ta ce: “Lallai duk wanda ya yi kashin nan, namansa zai zama mai daɗin gaske.”

    Nan fa ta yanke shawara a kan sai ta gano wanda ya yi kashin. Saboda haka ta hau wani kututture ta shiga jira. Ta daɗe amma ba ta ga kowa ba. Haka ta haƙura; a cikin fushi ta kama hanyar barin wurin. Tana cikin tafiya sai ta ga wani tarin kashin a ƙarƙashin wata bishiya.

    Wannan kashi ya tayar mata da kwaɗayi; nan take dai ta cinye shi sarai. Ta yi gaba, sai kuma ga wani kashin. Shi ma ta cinye shi duka. Haka dai ta dinga tarar da kashi tsibi-tsibi tana cinyewa, ba ta rage ko kaɗan ba. Amma har yanzu tana mamakin wanda yake yin sa, saboda haka sai ta sake hawa wani kututture mai tudu tana jira.

    Nan ma ba ta ga kowa ba. Ganin haka, sai ta sake dabara, ta tona rami ta shiga fako. Nan ma ba ta ga komai ba. Daga nan sai ta buɗe bakinta, wai komai kashin ya zo ya shiga ciki ta cinye shi. Ba ta jima da bakinta a buɗe ba, sai Gizo ya je ya yi kashi, kashin kuma ya faɗa bakinta.

    Ta ji kashin Gizo da daɗi ta ce: “Ashe da man Gizo ne ke yin wannan kashi. Ko ina yakan sami naman da yakan ci ya sa kashinsa ya yi daɗi haka?” Kura dai ta ga gara ta ci gaba da fakon Gizo, sai ta sake hawa sama, ta shiga jiran komawarsa. Shiru, shiru. Gizo bai je ba sai washegari.

    Ya sake zuba kashi; yana gama yi sai Kura ta sauka ta yi kansa. Ta kama shi ta riƙe gam-gam; sai ta tambaye shi inda yake samun naman da yake ci. Da fari Gizo ya ce ba zai gaya wa Kura ba don yana tsoron kada a kashe shi idan ya faɗa. Kura ta ce: “Ko ka gaya mini ko kuma in kashe ka.”

    Saboda tsoro, sai Gizo ya ce: “To, za mu yi alƙawari a yau kawai. Wato zan gaya miki.” Kura ta amince; suka kama hanya Gizo ya kai ta inda yake samun naman. Da zuwansu wurin sai ya ce: “Buɗe, buɗe, buɗe.” Sai wata ƙofa ta buɗe, suka shiga. A ciki sai ga gwafanni da sanduna a kafe an rataye nama ba iyaka a jikinsu.

    Da shigarsu sai Gizo ya ce: “Rufe, rufe, rufe.” Nan take ƙofa ta rufe. Da yake masu tsaron ƙofar sun saba ganin Gizo, ba su hana su ba, kuma ba su nemi sanin abin da ya kawo su ba. Gizo ya kwaso nama da yawa ya ba Kura, ta ci, ta yi guzurin wani mai yawa. Daga nan suka fita, suka kama hanyar gida.

    Da dawowarsu gida Kura ta shiga tunanin komawa wurin naman nan ita kaɗai. Bayan kamar mako guda sai ta sami labarin Sarki ya tafi rangadi. Sai ta sami ’yar rakiya daga cikin danginta bisa cewa za su je ziyara ne. Suka kama hanya har suka isa inda suka je cin nama tare da Gizo.

    Ta yi irin maganar da ta ji Gizo ya yi a wancan lokaci: “Buɗe, buɗe, buɗe.” Sai ƙofa ta buɗe. Suka shiga, suka ci nama har suka ƙoshi, suka lafci wanda za su tafi da shi
    gida, sun ga banza ta faɗi. Ba da dadewa ba Sarki ya dawo daga rangadi. Ya tarar
    naman da ya yi tanadi ya ragu ƙwarai.

    Ya tambayi masu tsaro, amma suka kasa yin bayani mai gamsarwa. Sarki ya sa aka tara mutanen garin duka. Ya gaya musu ya yi alƙawari duk wanda ya gaya masa wanda ya sace masa nama zai aura masa ’yarsa. Gizo ya san masu gadi kan iya tona masa asiri, sai yace ya san wanda ya yi ɓarnar.

    Fadawa suka ce ya faɗa. Nan da nan ya nemi izini, aka ba shi domin ya je ya zo da wanda ya yi wannan ta’adi. Bai zame ko’ina ba sai a ƙofar ramin Kura. Da ya tambaya aka ce ta yi tafiya, sai ya ce: “Kash, ashe ba za ta sami irin naman da Sarki yake ba jama’ar da ya tara a fada ba kenan.

    Idan ta dawo a gaya mata ta je fada Sarki zai yi rabon nama mai yawa.” Da jin haka sai Kura ta fito daga inda ta ɓuya ta ce: “Gani. Ba inda na je. Mu tafi in sami rabona.” Suka fita. Ba su tsaya ba sai a fada. Da isarsu ’yan tsaron nama suka ce: “Ba shakka, Kura ce ta cinye naman Sarki.”

    Kafin ta farga, tuni an hau ta da bugu. Da aka kai ta ƙarshe, sai aka farke cikinta. Hanji da tumbi da uwar kashi da tubura da huhu da zuciya da kashi, duk suka zuba. Kura dai a taƙaice nan ta mutu. Sarki kuwa dama mai jan girmansa ne. Nan take ya cika alƙawari, watau Gizo ya zama surukinsa. Suka yi zamansu lafiya. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Iya gani iya ƙyalewa.
    • Alƙawari kaya ne.
    • Mai rabon shan bugu, ba ya jin kwaɓa.
    • Kowa ya daka rawar wani, ya rasa turmin daka tasa.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Tatsuniyar Tasalla Mai Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Tasalla mace ce wadda ke zaune a wani kauye mai suna Saladuna. Tana kiwon wani kifi babba. Ta daɗe da wannan kifin, har sun saba da juna. Tasalla tana ciyar da kifin a kullum gwargwadon ƙarfinta. Saboda sabon da suka yi da juna, har yakan riƙa yin tsalle cikin wasanni da ita.

    Wata rana Tasalla ta yi tafiya, sai mutanen ƙauyen suka kama kifinnan suka cinye. Kowa ya ji daɗin naman kifin. Da Tasalla ta dawo sai ta nemi kifinta ko sama ko ƙasa, ya ɓace. Ta yi ta tambaya da cigiya ko ta ji wani abu game da kifin, amma ba ta sami bayani daga bakin kowa ba.

    Nan take ta shiga kukan takaici. Wannan ya sa ta yi wani siddabaru da ya ƙarar da ruwan garin, kowa ya rasa ko da ruwan wanke ido, balle na wanka da girki. To amma akwai wani mutum ɗaya da Tasalla ke jin nauyi, kuma tana matuƙar ƙaunarsa.

    Sai aka turo mata shi domin ya roƙe ta, ko za ta warware siddabarun da ta yi suka rasa ruwan sha. Ga irin abin da yake cewa da ya tunkari inda take:

    “Tasalla, Tasalla, Ki ji tausayina,

    Ki sam min ruwa in sha.

    Ki ji tausayi na, Ki sam min ruwa in sha.”

    Sai ta mayar da jawabi tana tambaya:

    “Wane ne yake neman ruwa?
    Wane ne yake neman ruwan sha?”

    Sai mutumin ya ce: “Ni ne masoyinki, Ni ne nake roƙon ruwa in sha.” Tasalla ba ta amince ba. Tana fushi a kan cinye mata kifi, saboda haka ta hana mutumin ruwa. Sarkin garin da fadawansa suka ɗunguma suka je roƙon ta, amma ta ƙi sauraronsu. Ba yanda ba su yi ba, amma ta ƙi.

    Sai can uwarta ta zo ita kaɗai ta roƙe ta ruwan sha. Saboda ƙaunar da take yi wa uwar, sai ta daina fushin da take yi. Nan take ta warware siddabarun da ta yi, ruwa ya samu kowa ya wadata da shi. Daga bisani mutanen garin suka zo suna ba Tasalla haƙuri, kuma suka amince lallai sun yi mata laifi da suka cinye mata kifi.

    Duk mutanen garin suka ɗauki alƙawari za su nemo mata wani kifin. Bayan ‘yan watanni suka samo mata wani kifin. Sabon kifin yana da ruwan zinari, kamar dai wanda aka cinye; wannan yasa zaman lafiya tsakaninta da su ya tabbata. Kifin ya girma, kuma ya dinga hayayyafa. Daga ƙarshe dai har kifin ya zama ya wadaci mutanen garin.
    Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Soyayya da tausayi a rayuwar duniya ya haɗa da zaman mutum da halittar Allah ga baki ɗaya.
    • Soyayya tsakanin ɗa da iyaye tana da ƙarfi ƙwarai fiye da yadda mutum ke zato.
    • Ɗaukar abin wani ba da izininsa ba zalunci ne.
    • Tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan doka.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna na don karanta Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Tatsuniyar Kwaɗayi Mabuɗin Wahala

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana mutuwa ta je wani ƙauye da saniya da ta turke, tana neman wanda zai sayi wannan saniya a ƙauyen. Mutane suka tsorata baki ɗaya suka ƙi. Can Gizo ya dubi mutuwa ya ce shi yana so. Suka yi yarjejeniya a kan baɗi Mutuwa za ta dawo ta yanke kunnuwan Gizo.

    Wato kunnuwan sun zama kamar da su zai biya saniyar. Nan da nan sai Gizo ya yanka saniyar shi da matarsa Koƙi suka dafa, suka ci, suka ƙoshi. Da shekara ta kewayo sai ga Mutuwa ta zo fansar bashi. Ta fara cigiyar wanda ya sayi saniyarta. Ta shiga gari tana cigiya, har ta kai gidan Gizo.

    Gizo na nan amma kuma ya gaya wa matarsa Koƙi ta gayawa Mutuwa cewa ya yi tafiya. Amma kuma ya ɓuya ne a cikin ramar da aka shuka a tsakar gidan. Saboda haka da Mutuwa ta tambaya sai Koƙi ta gaya mata cewa ai mijinta ya yi wata doguwar tafiya bai
    dawo ba. Mutuwa ta yi mamakin jin haka, ta ce: “Yaya Gizo zai yi tafiya bayan kuwa mun yi alkawari a kan yau ne lokacin haɗuwarmu?”

    Saboda haka sai Mutuwa ta tuna da wata dabara wadda za ta yi ta kama Gizo. Sai ta tafi kasuwa ta sayo ganga ta zo gidan Gizo ta yi ta kaɗawa tana waka, tana cewa:

    “Ina Gizo, Koki ina Gizo?”

    Koƙi ta fito ta nanata cewa: “Ai maigidana ya yi tafiya yau da wata uku bai dawo ba.” Mutuwa ta san Gizo yana da wayo. Saboda haka ta cewa Koƙi: “Kin ga kuwa Gizo ya tafka asara. In da yana nan zan ba shi wata saniyar ne. Da mun yi haka din sai in tafi in dawo baɗi in karbi kunnuwa biyu.”

    Koƙi dai ta zauna a kan cewa maigidanta ya yi tafiya. Amma da Gizo ya ji zancen Mutuwa za ta ba shi wata saniyar, sai kwatsam ya fito yana cewa: “Ai ga ni nan; rabu da Koƙi, ƙarya take; ina nan.” Da fitowar Gizo sai Mutuwa ta kama shi ta yanke kunnuwansa. Ta kuwa yanke su a gurguje ta yanda Gizo bai san kowane ne ya yi masa wannan shigar sauri ba.

    Ya ma zaci ko Mutuwa ce ta turo ɗanta ya yi wannan aiki. Har yau an ce Gizo na can ƙauyen yana jinyar yanke masa kunnuwa da Mutuwa ta yi. Duk mutanen gari suka yi ta yi wa Gizo dariya da ba’a suna cewa: “Ai ga irinta nan. Kwaɗayi mabudin wahala.” A taƙaice dai, ba wanda ke tausaya wa Gizo a kan abinda ya same shi. Kurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Alƙawari kaya ne.
    • A halin zaman duniya ya kamata mutum ya tsaya ga magana guda don yawan canza magana yakan zubar da mutunci.
    • Kowa ya ci ladan kuturu, ya yi masa aiki.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Tatsuniyar Yelwa Da Tsohuwa Da Sarki

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata yarinya mai suna Yelwa. Tana da ƙawaye da yawa. Wata rana Sarkin garinsu ya umurci ‘yan matan garin su je rafi, su kamo kifi bisa sharaɗin cewa duk wadda ta kamo ta yi masa miya mafi daɗi, ita zai aura. Da man sauran ‘yan matan sun tsani Yelwa.

    Saboda haka bayan sun kamo kifi sai suka haɗa baki suka jefa ta a cikin kogin ta nutse. Da farko har ruwan zai tafi da ita, to amma ta yi sa’a, wata tsohuwa ta zo ta tsamo ta. Wannan tsohuwa kuwa tana da baiwa. Yelwa kuma ta kwashe labarin duk abin da ya faru ta gaya mata. NantTsohuwar nan ta ji tausayinta.

    Nan da nan ta kama wani ƙaramin kifi ta ba ta, kuma ta ba ta wata ‘yar tukunya, ta ce mata ta sa wannan kifi a cikin tukunyar ta rufe, ta kiwata shi. Washe-gari da Yelwa ta buɗe tukunyar sai ta ga wani babban kifi a ciki. Ta yi mamakin yadda kifin ya girma haka. Ta kama kifin ta dafa, ta ɗauka ta nufi fada.

    Kafin ta je an soma biki har an rufe ƙofa. Ta roƙi dogarai suka buɗe mata, ta shiga. Kafin zuwanta Sarki ya riga ya ɗanɗana dukkan miyar da ‘yan matan suka kai, amma babu wadda ya gamsu da ita. Saboda haka da Yelwa ta kai tata miyar, Sarki bai so ya ɗanɗana ta ba, sai da tsohuwar nan ta matsa kusa da shi ta raɗa masa cewa ya taɓa.

    Sarki ya taɓa ya ji miyar Yelwa zaƙi cakwai, abin ba dama. Ba da ɓata lokaci ba washe-gari Sarki ya bayyana mata buƙatarsa ta aurenta. Yace in ta yarda ta je ta shaida wa iyayenta a ɗaura musu aure nan da kwana biyu Yelwa ta tafi tana kuka saboda baƙin cikin maraici, domin tuni mahaifanta suka mutu.

    Ta fara batun zuci tana cewa: “Kaito, yaya zan yi da raina yanzu, ga ni ba ni da iyaye.” Can sai ta kama waƙa tana cewa:

    “Ke tsohuwa mai ceto,

    Ke tsohuwa mai baiwa,

    Sarki na so ya aure ni.

    Ke tsohuwa mai ceto,

    Sarki yana so ya aure ni,

    Amma ga shi ba ni da iyaye,

    Yaya zan yi a halin yanzu?”

    Can sai ga tsohuwar ta bayyana, ta ce mata ta daina kuka, kar ta damu, komai zai yi kyau. Ta umurce ta da ta je ta samo ƙwari biyu ta kawo mata. Da ta kawo sai tsohuwar ta mai da su mutane, mace da namiji, wato sun zama iyayen Yelwa ke nan. Daga nan suka tasam ma fada, aka ɗaura aure.

    Nan fa sai ƙawayen Yelwa suka ji kunya, suka nemi gafararta. Yelwa kuma ta yafe musu saboda halinta na haƙuri. Ita da ƙawayen suka zauna lafiya, har kowaccensu ta yi nata auren. Sai dai akwai ɗaya daga cikin ƙawayen mai mugun hali. Ba ta daina jin haushin rasa auren Sarki ba.

    Saboda ƙyashi da hassada, sai ta shiga ƙulle-ƙulle da haɗa husuma domin ta kashe wa Yelwa aure. Ba abin da take so a duniya kamar ta ga auren Yelwa da Sarki ya mutu. Wata rana ta kama hanya ta je fada da nufin kashe Yelwa, amma ba ta yi nasara ba. Dogarai suka kama ta.

    Duk da cewa ta so kashe Yelwa, amma ita ba ta so a hukunta muguwar ƙawar nan tata ba. Ta roƙi mijin a ƙyale ta domin ƙila ta gyara halinta. Sarki ya yarda, ya kuma tara mutanensa kaf ya shaida musu matuƙar ƙaunar da ke tsakaninsa da Yelwa. Ya tabbatar musu har ita kanta cewa a ko da yaushe iya ransa zai yi duk abin da ya dace don ya kyautata zama da soyayyar da ke tsakaninsu. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Taimakon Allah yana samun bawansa ta hanyoyi daban-dabaninda bai zata ba.
    • Yafe wa wanda ya musguna maka wani alheri ne da zai sa mai laifin ya canza halinsa nan gaba.
    • Rabo dangi ajali.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Tatsuniyar Tsohuwa Da ‘Yan Mata Uku

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wata tsohuwa mai ‘ya’ya uku mata. Sannu a hankali suka girma, har suka kai munzalin aure. Saboda haka ta ce da kowaccensu ta fid da mijin aure. Nan da nan Allah ya ba kowacce wanda za ta aura. Suka yi aurensu, kowacce ta tare a gidan mijinta a garuruwa daban-daban.

    Bayan ‘yan kwanaki kaɗan, sai tsohuwa ta ce ya kamata ta ziyarci kowacce a gidanta a garuruwan da suke. Ta fara da zuwa garin ‘yarta ta fari ta tarar kusan dukkan mutanen garin kowa maye ne. Ga shi kuma suna da jela da kunnuwa dogaye, kamar dodanni. Ta tambayi inda gidan ‘yarta yake. Mutane suka kwatanta mata.

    Da ta je gidan ‘yarta ta karɓe ta a cikin murna matuƙa. Ita ma ‘yar ta zama mayya, tana kuma da wutsiya da dogayen kunnuwa. Sai uwar ta tsorata. Ko da yake an karɓe ta da fara’a, ta yi tunanin cewa ya kamata ta koma garinsu da wuri. Ba da sanin uwar ba ashe ‘yar da mijinta sun shirya a kan za su cinye ta cikin daren.

    Da dare ya yi sai suka saɗaɗa cikin ɗakin da suka saukar da ita a ɓoye, amma suka tarar ba ta yi barci ba. Sai suka koma a kan cewa washe-gari za su ƙara yin ƙoƙari ko za
    su same ta ta yi barci. Ita kuma ganin haka sai ta shirya da sassafe za ta gudu ta bar garin. Gari yana wayewa, ko ban kwana ma ba ta yi da su ba, ta kama hanya.

    Ta shiga dajin Allah tana ta hanzari ba ta tsaya ba sai gidan ‘yarta ta biyu. Ita ma wannan ‘yar ta karɓe ta da murna ƙwarai, sai dai ta gaya wa uwar cewa a ƙauyen idan dare ya yi sukan rikiɗa su zama fari, su je su kwana a kan wata bishiya. Uwar ta ce ba ta damu ba, za ta bi su.

    Da dare ya yi dukkan mutane suka koma bayan gari suka rikiɗa, suka zama fari. Suka ɗunguma gaba ɗaya sai kan itacen da suka saba kwana. Tsohuwa dai ba ta bi su ba, ta zauna ita kaɗai a gida. Ba a daɗe ba hadari ya taso, aka yi ruwan sama mai yawa, ta jiƙe sarai. Da gari ya waye sai ta bar wannan garin ta nufi ‘yarta ta uku.

    Da ta je garin sai ta tarar mutanen suna soya naman shanu. ‘Yarta ta karɓe ta da hannu bibbiyu. Sun ɗan sammata naman amma da gargaɗin cewa kar ta cika cikinta domin a garin ba a ƙashi da fitsari. ‘Yar ta ce in fa ta karya dokar to Sarkinsu zai sa a kashe ta. Uwar ta yi banza da gargaɗin; ta ci naman sai da ta ƙoshi.

    Can cikin dare ta ta-da ‘yarta a kan cewa tana so ta je bayan gari. ‘Yar ta ce: “To, ba ga abin da na gaya miki ba. Daman na gaya miki abin da ke faruwa a garin.” Ba da ɓata lokaci ba ta ɗauki uwar ta kai ta bayan gari. Da gari ya waye sai mutanen garin suka dinga jin wari ta ko’ina, suka je suka shaida wa Sarki.

    Sarki ya ce lalle akwai wani baƙo da ya shigo garin. Da ‘yar ta ji haka sai ta yi maza ta ɗauke mahaifiyarta, ta raka ta har sai da ta bar garin. Sarki ya aika a nemo ta, amma ba su gan ta ba. Ta riga ta gudu. Tsohuwa tana kan hanyar komawa gida ne ta gamu da wani mutum. Bayan sun gaisa sai ta tambaye shi ko zai ci naman da ta yo guzurinsa.

    Ta ce da mutumin idan ya ci naman ya je garin ya yi kashi, zai sami wata kyauta. Mutumin kuwa ya karɓi naman ya ci. Da ya je garin ya yi kashi sai aka kama shi. A maimakon a ba shi wani abin arziki sai suka kashe shi a zaton shi ne ya yi kashin nan na kwanan baya. Ita kuma tsohuwa ta koma ƙauyenta lami lafiya. Ta ɗauki
    alƙawari cewa ba za ta ƙara karambanin zuwa ziyarar ‘ya’yanta ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Wanda bai ji bari ba ya ji hoho.
    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Wajibi ne ga baƙo ya saurari gargaɗin masu masaukinsa.
    • Kowane tsuntsu, kukan gidansu yake yi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Dogarawa Uku

    Edita@rumasau-kallamu