Ba Duka Wanda Ke Da Ciwon Dake Warkewa Ba Ne Yake Warkewa

0
567

An karɓo Hadisi daga Aɗa’u ɗan Abi Rabah ya ce Abdullahi ɗan Abbas Allah ya yarda da shi ya ce: “Da ni bana nuna maka wata mace daga cikin ‘yan Aljanna ba? Sai na ce: Eh, nuna min, ya ce: Wannan baƙar matar ta zo wajen Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ta ce: Ana kifar da ni in faɗi, kuma ina yin tsiraici ka roƙar min Allah Maɗaukaki.

Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “In kin so ki yi haƙuri ki dace da samun Aljanna, in kuma kin so ina roƙa miki Allah Madauƙaki ya ba ki lafiya.” Sai ta ce, zan yi haƙuri (don na sami Aljannar). sai ta ce: Amma fa ina yin tsiraici ka roƙar min Allah (ko an kifar da ni) kar in yi tsiraici, sai ya yi mata addu’a”. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.

Bayan haka, cutar da ta zama ta tun asalin halittar bawa, ba ta magantuwa, kamar wanda aka halitta babu yatsu, ko rangwamen hankali ko rasa wani sashi na jiki.
Gaɓar da wata cuta ta lalata jijiyoyin da suke kai saƙo gare ta, kamar ido ko kunne a dalilin ƙyanda ko sanƙarau.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin A Kula Da Lafiya wanda Abubakar Abbas Ibrahim ya wallafa shi. Domin karanta cikekken littafin danna koren rubutun nan

labarin da ya wuceMu Ɗin Su Wane Ne?
Labarin na GabaYadda Ake Yin Sabulun Wanki