Yadda Halittar Lokaci Da ƙarewarsa Yake

0
1066

Ƙudurar Ubangiji  kadai itace wanzanjjiya. Domin kuwa tun farko babu jiya babu yau, ba nan ba can , babu gaba  ba baya.

Ba a san nisa da kusanci ba, balantana kuma ko banbanci, kamshi ko wari babu su, dare da rana babu zuriyarsu, lissafi da kwatance ba mai tunani su.

Domin babu sama, ba ƙasa, ba  halitta. Sai ALLAH ya halicci sarari da lokaci sannan ya samar da halittu da rayuwa da mutuwa da ma’auni Ayoyi masu zuwa na ƙarfafa wannan ma’ana:

Sannan ya daidaita zuwa ga sama alhali kuwa ita (a lokacin) hayaƙi ce,sai ya ce mata, ita da ƙasa ku zo bisa ga yarda ko akan tilas “suka ce muzo, muna Da’a
Sura fussilat-Aya 11

Wannan Aya na nuna farko halittar sarari (space) tun a farkon al’amari. Daganan kuma halittu suka bigire da matsuguni. Kamar yadda Ubangiji maɗaukaki  ke faɗa dangane da farkon halittar  Annabi Adamu a lokaci yana cikin aljanna da matarsa Hauwa’u:

Kuma kuna da matabbaci da ɗan jin daɗi izuwa wani lokaci a bayan ƙasa (doron duniya)’’. Sura Bakara Aya 36

Rayuwa ɗan-Adam a doron ƙasa ba zata yiwu ba, ba don Ubangiji yahore tagare shi ba. Ubangiji na cewa:

kuma yahore muku rana da wata dawwamammu da kuma dare kuma ya baku dukkan abinda kuka roƙe shi. Da zaku ƙirga ni’imomin Allah (Maɗaukaki) ba za ku iya ƙididige su ba

sura-Ibrahim:33-34

Ubangiji Maɗaukaki na cewa:

shi ne wanda ya sanya rana mai haske wata kuma mai haskawa. Ya gwargwaje shi a masauki don ku san ƙididdigar shekaru da lissafi. Allah (MAɗaukaki) bai halicci wannan ba  sai don gaskiya yana rarrabe ayoyi ga mutane masu sani.
“Yunus-Aya 5

Saboda kimar lokaci kuwa ubangiji maɗaukaki ya yi rantsuwa da shi a wurare da yawa cikin Alqurani:

  • (Ina) rantsuwa da lokaci (zamani)…………………..
  • A wani gurin yace (Ina) rantsuwa da alfijir…………………………….
  • Wata ya yar kuma (Ina) rantsuwa dada lokacin walaha……………….
  • (Ina) rantsuwa dada Dare……………………………

Malam tafsir na cewa idan Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da wani abu to akwai ishara izuwa ga irin girman wannan al’amari da tasirinsa da amfaninsa. Lokaci na shuɗewa ne ta yadda mutum ba zai  Ankara ba har sai ya zagayo, wata ya wuce shekara ta zo ta tafi.

Wani mai hikima na cewa.
  • Ɗaya ta wuce biyu ta biyo ta:
  • Uku na nufin cin didigenta
  • Hudu ko kamar na rarako ta:
  • Zancen ya shekara ba wuya
  • Ka san da ranar haihuwarka:
  • Yau ga shi ka zama ɗan gidanka:
  • Domin gudu nata duniya

Ka lura da kyau daga ƙuruciyarka zuwa yau din nan, zaka ga kamar sati ne ya wuce. Babban misali a nan shine: ɗaukar ciki da haife shi. Yaye  da shayi Gama karatun firamare da sakandare. kammala ilimin jami’a. Ga shi yau har ka yi aure ka zama magidanci. Ashe dai lokaci gudu yake yi amma ba mai gani sai mai idanuwan zuciya da lura.

LOKACIN RAYUWA KAMAR ZAREN KASET NE

Lokaci rayuwa ga kowannemu ya danganta da irin yadda Ubangiji Maɗaukaki ya ɗeba masa. Manzon Allah (SAW) na cewa rayuwarmu shekaru sittin ko saba’in kadan ne ke wuce wannan.

Mu ɗauka wasu za su kai shekaru casa’in wasu ɗari. Wasu kuwa talatin wasu arba’in ko hamsin da sauransu. To ka ga kuwa rayuwarmu tamkar kaset ne mai 60 ko 70 ko 90 ko 100 ko 30 ko 40 ko 50 gwargwadon yawan shekarun da aka qaddara mana ba daɗai ba ragi.

Da zarar an haifi jariri sai  kaset ɗin rayuwarsa ya fara naɗe bayanan motsinsa da ayyukansa masu kyau da munana. Hatta minshari da kakaki da ihu  da ashariya da ibada, kaset ɗin zai cigaba da juyawa cikin zaren lokaci ba tsayawa. Ruwan mutum ya kama tasbihi ko karatun Alƙur’ani ko barci ko ya shiga kakaci da batsa, kaset ba zai tsaya ba. Kuma ba zai dena naɗa ba har sai ya je ƙarshe.

Da yaje ƙarshe kuwa mutum zai bar duniya ko da shiri ko ba shiri. Jama’a mu lura a kowanne lokaci zaren rayuwarmu ƙarewa yakeyi kullum cikin daƙiƙa. Mu ribaci lokutanmu don in ya tafi ba zai dawo ba. Ubangiji Maɗaukaki Na cewa:

Lallai ajalin Ubangiji Maɗaukaki in ya zo ba a jinkirta shi. Da kun sani (hakan)”. Sura munafiƙun-Aya-11

Game da gaggauta ayyuka na gari kuwa Ubangiji Maɗaukaki na cewa:

“Ku ciyar daga abinda muka azurta ku tun kafin mutuwa ta zo wa dayanku. Sannan ya ce Ubangijina ina ma ka jinkirta min izuwa ɗan lokaci na zamo cikin nagartattu.”

Allah (maɗaukaki) baya taɓa jinkirtawa wata rai idan ajalinta ya zo. Kuma Allah (maɗaukaki) Mai bada labari ne game da abinda kuke aikatawa”-Sura Munafiƙun: Aya 10

KIMAR LOKACI A RAYUWAR ƊAN ADAM

Manzon Allah (SAW) ya ce: Ka ribaci abubuwa biyar kafin abubuwa biyar (suzo)

  1. Quruciyarka/kafin tsufanka
  2. Lafiyarka kafin rashin lafiyarka
  3. Wadatarka kafin talaucinka
  4. Faragarka kafin shagaltuwarka
  5. Rayuwarka kafin mutuwarka

Bugu da Ƙari Manzon Allah (SAW) yace:” Ƙafafun Ɗan adam ba za su gushe ba a ranar alƘiyama har sai an tambaye shi game da abubuwa huɗu:

  • Rayuwarsa ta yaya ya ƙarar da ita?
  • Quruciyarsa ta yaya ya ƙarar da ita?
  • Dukiyarsa ta ina ya same ta, kuma ta yaya ya kashe
  • Iliminsa ya yayi da shi?

Akwai hadisi da Bukhari ya ruwaito Manzon Allah (SAW) ya ce: “Ni’imomi biyu ana yiwa mutane da yawa kumunga a cikinsu”. Ma’ana suna tozarta su cikin abinda ba zai bayar da amfani ba. Lafiya da samun dama”.

domin samun cikkekken littafin danna koren rubutu

labarin da ya wuceYadda Musulmi Zai Ribaci Lokutansa Na Rayuwa
Labarin na GabaYadda Za A Gabatar Da Aiki Mafi Muhimmanci