Yadda ake Yiwa Jarirai Hudubar Haihuwa

0
33

Akwai hanyoyin biyu da za a iya yiwa jarirai huduba wanda suka tabbata a suna bisa tsarin addinin musulunci kamar haka:

Hanya ta farko.

Yana daga cikin abin da yatabbata a sunna idan aka haifi jariri sai mahaifinsa ko wani wanda mahaifin sa ya wakilta,ya dauki jaririn ya kara bakin sa adaidai kunnen sa na dama,ya kira sallah, yadda ake kiran sallah da kalmomi guda (19) kamar haka:

Idan da maimaici kenan,ko guda (17) idan babu maimaici kenan,ga misali na guda (19)

“Allahu Akbar Allahu Akbar, Allahu Akbar Allahu Akbar,

Ashhadu an Laa iLaaha illal Laah, ashhadu an Laa iLaaha illal Laah

Ashhadu anna muhammudur rasulul Laah ashhadu anna muhammadan rasulul Laah,

Hayya alal Salah hayya alal Salah

Hayya alal falah, Hayya alal falah

Allahu Akbar Allahu Akbar,

Laa iLaaha illal Laah.”

Sannan ya kara bakin sa a daidai kunnen sa na hagu,nanma sai ya tayar da iqama kamar haka

“Allahu Akbar Allahu Akbar

Ashhadu an Laa iLaaha illal Laah,

Ashhadu anna muhammadan rasulul Laah

Hayya alal salaati, Hayya alal Salah,

Qad qaamatus salaatu, qad qaamatus salah,

Allahu Akbar Allahu Akbar

Laa iLaaha illal Laah.”

Sannan sai yace sunan ka wane,kamar misali sunan ka/ki (Ahamad ko Zainab).
Toh kuma daga nan Idan mahaifin yana so sai yayiwa yaron (tahaniki) abin nufi da (tahaniki)shine kasa dabino a bakin ka idan ka gatsa shi sai a sakawa jariri a bakin sa kafin a bashi wani abinci, amma ba hakan yana nufin uwa baza tabashi ruwan nono mai kauri kalar rawaya da ake kira daKushi da harshen hausa ba.

Zata bashi idan jariri na bukata sannan sai a bashi dabinon da aka gatsa ya tsotsi ruwan wannan shima yana cikin abinda akewa jariri da zaran an haife shi.

Hanya ta biyu:

Za ayiwa jariri (tahaniki) idan mahaifin sa naso sannan yace sunan wane, misali yacewa jaririn sunan ko sunan ki(Ahamad ko Zainab) ba tare da yin kiran sallah a kunnen dama da tayar da iqama a kunnen hagu ba.

Domin karanta yadda zakai tarbiyar yaro danna nan 

labarin da ya wuceNau’in Jinkiri Guda Uku Da Suke Sabbaba Mace-macen Mata Masu Naƙuda a Nigeria
Labarin na GabaMenene Amfanin Folic Acid Ga Mata Masu Juna Biyu
Lawan Bello
Abu muzaffar Malami ne masanin ilimin zamani da na addini bisa tsaren Ƙur'ani da tafarkin manzon Allah sallallahu alaihi wa sallam, mai hangen nisa a addini da kuma alummma, shugaban Abu Muzaffar foundation.