Tag: ilimi

  • Tarihin Mahiru Sharif Bala

    Tarihin Mahiru Sharif Bala

    An haifi Gwani Sharif Bala ɗan Sharif Musɗafa ɗan Sharif Muhammad a shekarar 1345; wadda ta yi dai-dai da shekarar 1934 a Unguwar Gabari cikin garin Kano.

    Mahiru Sharif Bala ya taso a gidan ilimi da wadata da karamci a inda ya yi karatu a wurin mahaifinsa tare da ɗan uwansa Sharif Ahmad. Mahiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani sau uku tun yana ɗan shekara goma sha takwas; kuma a dai-dai wan nan lokaci ne aka yi masa auren fari. Mahiru Sharif Bala ya kutsa fannonin ilmi inda ya karanci tafsiri da Hadisi da Fiƙhu a Unguwar Makwarari.

    Wani abin mamaki game da rayuwar Mahiru Sharif Bala ya yin neman Alƙur’ani shi ne: bai taɓa zuwa ko’ina ba kamar yadda abin yake wajen mafi yawan makaranta. Babbar baiwar da Mahiru Sharif ya shahara da ita baya ga ƙarfin tilawar Alƙur’ani, shi ne gwanintar rubutunmu na Magribi.

    Kwanciyar baƙaƙen AIƙur’ani irinsu “Kaulasan” da Lam’ara da tsaiwar Bayala shaida ce ga ficen da Mahiru Sharif Bala ya yi a wannan fage. Saboda irin baiwar rubutunsa da irin karɓuwar da yake da ita tsakanin makaranta Alƙur’ani ba a ƙasar Kano ba kawai; har ma da wasu sassa na Afrika ta Yamma; ta sa Mahiru Sharif Bala ya juyi littattafai a sassan ilman Musulunci da hannunsa irinsu:-

    – Asshifa
    – Dala’ilul Khairati
    – Ishriniyya
    – Alburda
    – Hamziyya
    – Risatul Anwar
    – Igasatul ibad
    – Risala
    – Iziyya da sauransu

    Babu shakka wannan ya sauƙaƙawa makaranta tsangaya waɗanda ba su saba da rubutun sharƙiyya ba, damar kutsawa fannoni ilmi.

    A taƙaice za mu iya cewa hannun Mahiru Sharif Bala da tasirinsa a tsarin tsangaya ya zama “hantsi leƙa gidan kowa”; domin kuwa ya ratsa kowane loko da saƙo na makaranta.

    Ma’ana dai, in almajiri bai je gabansa ya yi karatu ba to kuwa ya kwaikwayi irin salon rubutun hannunsa; tun daga kan Juzi’i biyar ko goma har zuwa ashirin.

    Yaɗuwar da Alƙur’anin Mahiru Sharif Bala ya yi ya zarta yaɗuwar mafi yawan Alƙur’anan da aka rubuta da hannu; domin kuwa ya rubuta Alƙur’ani hamsin da hannunsa. An buga bakwai daga cikinsu, kuma an ɗabba’a su fiye da sau dubu ɗari biyu: waɗanda duk sun yi fice da fitar da harji da meram da falalar kowace sura.

    Game da taimakon yin magani da ayoyin Alƙur’ani kuwa, Mahiiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani don sha fiye da sau ɗari; Suratul Yusuf sau dubu ɗaya, Bisimilla da Wallahu ya ‘asimuka da Sanuƙ’ri’uka sama da miliyan guda.

    Farin jinin rubutunsa da baiwar da Ubangiji yai masa ta sa an buga:-

    i- Asshifar da ya rubuta da hannunsa sama da dubu talatin
    ii- Dala ilul khairati sama da dubu ɗari
    iii- Ishiriniya sama da dubu ɗari biyar
    iv- Alƙur’ani ɗan izu ashirin sama da dubu ɗari biyar
    v- Alƙur’ani ɗan izu goma sama da miliyan biyu
    vi- Alƙur ‘ani ɗan izu biyar sama da miliyan biyu
    vii- Ƙawa’idi sama da miliyan biyu
    viii- Ashmawi sama da dubu ɗari biyar
    ix- Risala sama da dubu goma
    x- Iziyya sama da dubu goma
    xi- Alburda sama da dubu goma
    xii- Ira’atul biladi sama da dubu goma.

    Har zuwa yanzu, Mahiru Sharif Bala bai gushe ba yana ba da karatu da ilimi a shahararriyar makarantarsa; tare da mataimaka sama da talatin da almajirai yara da manya, maza da mata sama da dubu biyar. Ubangiji Maɗaukaki Ya ƙara masa lafiya ya kuma sanya masa kyawawan ayyukansa a mizani.

    Tsokaci

    Akwai wasu malamai na Alƙur’ani fitattu a Kano da yawa – da ya kamata na gutsurawa mai karatu wani abu daga tarihin rayuwarsu, amma hakan ba ta samu ba.

    Cikinsu akwai Malam Na Mai Ganji da Malam Giwar Takwasa da Malam Husaini Ɗangurai da Malam Ɗangidimoni; da Malam Ɗayyabu Mai Saje da Malam Yahaya Malammadori da Gwani Tata Bunkure da Malam Ɗan Ringim; da Malam Mai Hafizai da ma waɗanda ban ambata ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Malamai a Katsina danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Wasu Daga Malamai A Katsina

    Wasu Daga Malamai A Katsina

    Malam Sani Hafizi Katsina

    An haifi Malam Sani a shekara ta 1916. Ya fara karatun Alƙur’ani tun yana yaro ƙarami. An kai shi gabas (Maiduguri) don ya sami ƙwaƙƙwarar tilawa. Ya zauna a Nguru a inda ya haddace Alƙur’ani sannan ya tafi katagum yankin Guddiri daga bisani kuma ya isa Maiduguri. Ya zauna wurin Malam Ɗan kutama a Bazamfareri a inda ya Gyara tilawarsa.

    Malam Sani ya koma Katsina a shekarar 1994, wato shekarar guda Bayan rasuwar sarkin Katsina Muhammad Dikko. Malam Hafizu ya kafa tsangayarsa kusa da babban Masallacin juma’a da ke Katsina.

    Malam Salisu Gidan Liman Kurfi

    Malam Salisu ya shaharar da karatun Alƙur’ani a garin kurfi. Makarantarsa na karɓar baƙuncin ɗaruruwan almajirai a inda suke hadda ce Alƙr’ani. Mafi shahara daga ɗalibanta su ne Liman Ɗayyabu da Malam Daudu.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Fitattun Malaman Alƙur’ani A kurfi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Buɗe Karatun Alƙur’ani Da Bismillah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Daga Fitattun Malaman Alƙur’ani A Kurfi

    Wasu Daga Fitattun Malaman Alƙur’ani A Kurfi

    Waɗannan Malamai sun haɗa da:

    Malam Umar Saulawa da Malam Sule Unguwar Maraɗi da Malam Yahaya Tsoho da Malam Abdu ƙofar Igi da Malam Ibrahim ƙofar Fada da Malam Dauda da Malam Sa’idu Nasarawa da Malam Musa Mahaddaci da kuma Malam Jume.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Malaman Ƙasar Zariya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wajibcin Karatun Fatiha A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Matsayin Malamai Kan Kashe Husaini (Radiyallahu Anhu)

    Matsayin Malamai Kan Kashe Husaini (Radiyallahu Anhu)

    Malamai sun kasu gida uku dangane da kashe Husaini (Radiyallahu Anhu); biyu a gefe ɗaya a tsakiya:

    1. Ɗayan na gefe: suka ce an yi dai-dai da aka kashe shi, saboda ya fito ne dan ya raba kan musulmai, Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce: “Duk wanda ya zo yana son ya raba kawunanku, alhali kuna bin wani shugaba guda ɗaya, ku kashe shi”. Suka ce Hussaini ya zo ne ya raba kan mutane, alhali suna ƙarƙashin shugaba ɗaya.

    2.Ɗaya gefen kuma suka ce shi Husaini shi ne shugaban Musulmai a lokaci wanda ya wajaba a yi wa biyayya, kuma imani ba ya cika sai da yarda shi ba za a yi sallar jam’i ko jama’a ba sai a bayan wanda ya naɗa, kuma ba za a yi jihadi ba sai da izininsa.

    3. Su kuwa waɗanda suke a tsaka-tsaki su ne Ahlussuna, ba su goyi bayan waɗannan ɓangarori biyu ba, abinda suke cewa Husaini an kashe shi ne bisa zalunci, kuma ya yi shahada, amma a lokacin ba shi ne shugaba ba, shi kuma wannan hadisi (Na ‘yan tawaye) bai shafi Husaini ba. Saboda lokacin da ya sami labarin kashe ɗan baffansa Muslim bin Akil, sai ya bar maganar halifanci ya nemi a ba shi dama ya tafi wurin Yazidu, ko ya tafi jihadi ko ya koma gida, amma suka ƙi, suka ce sai dai ya yarda a kama shi, yin hakan kuwa bai zama wajibi ba a kansa.

    Ya ɗan uwa musulmi mai neman gaskiya ka ga dai matsayin Ibn Taimiyya a kan wannan mas’ala shin ina alamun ƙin Ahlul Baiti (Radiyallahu Anhuma) ko goyon bayan abinda aka yi wa Husaini da iyalansa a cikin waɗannan bayanai?

    Ya kamata duk wanda ya ce maka Ibn Taimiyya ya ce kaza, to ya kawo maka littafin kuma a karanto maganar tun daga farkonta har ƙarshenta, ba wai a ciccizgo maganganun nan da can ba. Yaa Allah ka fahimtar da mu gaskiya ka ba mu ikon bin ta. Ka ba mu ikon yin adalci ga wanda muke so da wanda ma ba ma so, ka fitar da gaba da riƙo daga zukatan mu. Amin.

    Yanzu kuma ga maganganun wasu fitattun ɗaliban Ibn Taimiyya:

    Shamsuddin Bn Kayyimul Jauziyya Rahimahullah (A.H.S 691 Y.M.S 751)

    Shi kuwa kuwa shaihin malami Ibnul Ƙayyim Muhammad Ibn Abubakar, babban almajirin lbnu Taimiyya (Rahimahullah) ga abinda yake cewa:

    Yana daga cikin hadisan ƙarya, hadisan falalar sa kwalli da yin ado, da yalwatawa iyali da yin wasu salloli ranar ashura da wasu falaloli da ake faɗa, waɗanda ko hadisi ɗaya bai inganta ba a kansu.

    Abinda kawai ya inganta shi ne yin azumi a ranar banda shi sauran duka ƙarya ne. Hadisi mai ɗan dama-dama a kan wannan shi ne hadisin yalwatawa iyali a ranar ashura (cika-ciki) shi kuma Imam Ahmad Rahimahullahu ya ce bai ingata ba”.

    Amma hadisin falalar sa kwalli da shafa mai da sa turare ranar ashura, haƙiƙa maƙaryata ne suka ƙirƙire su, sai kuma wasu (‘yan bidi’ar) suka ƙirƙiri nuna alhini da ɓacin rai domin su ƙalubalance su, duka su biyun ‘yan bidi’a ne, sun saɓawa sunna.

    Su kuwa ahlussunna, suna aikata abinda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya yi umarni da a aikata a ranar, suna nisantar bidi’o’in da shaiɗan ya yi umarni da su’.

    Ibn Rajab Al-Hambali (Rahimahullah) A.H.S 735 Y.M.S 795

    Babban malami Zainuddin Abul Faraj Abdurrahman Ibnu Rajab Al-Hambali ya Ce:

    “Dukkanin hadisan da aka rawaito a kan falalar sa kwalli da yin ƙunshi da wanka ranar ashura, ƙarya ne ba su inganta ba” amma an rawaito daga Abdullah ɗan Amr Ibnul As ya ce: “Wanda ya yi azumi ranar ashura za a ba shi ladan azumin shekara guda, wanda ya yi sadaka a ranar za a ba shi ladan sadakar shekara guda” Abu Usa Al-Madini ne ya fitar da shi.

    Maganar cika-ciki kuwa an tambayi Imam a kan wannan hadisin ‘sai ya nuna cewa bai inganta ba. Sai da Ibnu Uyaina yace shekararsu hamsin suna jarraba yalwatawa iyali ranar ashura, kuma suna ganin buɗi. Amma dai hadisin bai inganta ba.

    Amma ɗaukar ranar a matsayin ranar baƙin ciki da zaman makoki kamar yadda Rafilawa (‘yan shi’a) suke yi saboda a ranar ce aka kashe Husaini (Radiyallahu Anhu) wannan aiki ne na ɓatattu amma suna ganin dai-dai suke yi; saboda Allah da Manzonsa ba su yi umarni a mayar da ranar da musibu suka afkawa annabawa ko ranar mutuwarsu ranar makoki ba, ballantana, waɗanda suke ƙasa da su”.

    Al-Hafiz Abul Fida Ibn Kasir (AH.S 701 Y.M.S 774)

    Babban malamin hadisi, malamin tafsiri kuma malamin tarihi; Al-allama lbn Kasir (Rahimahullah) shi kuma ga abinda yake cewa:

    “Ya kamata dukkanın musulmai su yi baƙin ciki da kashe Husaini (Radiyallahu Anhu). Saboda shi yana daga cikin shugabannin musulmai, kuma yana cikin sahabbai malamai, ga shi jikan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) na wurin ‘yarsa mafi daraja, kuma shi mai yawan ibada ne jarumi karimi.

    Amma duk da haka, abubuwan da ‘yan shi’a suke yi suke yi a ranar ashura na nuna raki da baƙin ciki wanda wani abin ma feleƙe ne kawai da riya, ba shi da kyau, a shari’ance. Saboda babansa (Sayyidina Ali Radiyallahu Anhu) shi ma kashe shi aka yi a ranar Juma’a 17 ga watan Ramadan a shekara ta 40 daga hijra ya fito zai tafi sallar Asuba, amma ba su mayar da ranar, ranar makoki ba.

    Haka kuma Sayyidina Usman (Radiyallahu Anhu) wanda a wajen ahlussunna ya fi shi. Tsare shi aka yi aka hana shi fita daga gidansa tsawon kwanaki, a cikin kwanakin aikin hajji a shekara ta 36 daga hijra, amma ba a mayar da ranar juyayi ba.

    Ga kuma Sayyidina Umar (Radiyallahu Anhu) wanda ya fi Usman da Ali (Radiyallahu Anhuma) daraja, yana sallar asuba yana tsaye yana karatun Al-ƙur’ani a masallacin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) aka kashe shi, amma ba a yin komai idan ranar takewayo. Su kuma dukkan su Sayyidina Abubakar (Radiyallahu Anhu) ya fi su falala, amma ranar mutuwarsa ba a mayar da ita ranar makoki ba.

    To kuma ɗungurungum shugaban taliƙai (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya koma ga Allah kamar yadda annabawan da suka gaba ce shi suka koma ga Allah, amma ba a aikata bidi’o’in’ da ‘yan shi’a suke aikatawa idan ranar kashe Husaini (Radiyallahu Anhu) ta kewayo. Kuma babu wani wanda ya ce a ranar rasuwarsu waɗansu abubuwan mamaki na keta al’ada sun faru kamar yadda rafilawa suke cewa wai sun faru ranar mutuwar Husaini (Radiyallahu Anhu).

    Abu dai mafi kyau shi ne duk lokacin da aka tuna waɗannan musibu da makamantansu sai a ce; “lnna lillallahi wa Inna ilaihi raji’un” kamar yadda shi Husaini ya rawaito daga kakansa (Salallahu Alaihi Wa Sallam) cewa: “Duk wanda ya tuna wata masifa, komai tsawon lokacin faruwarta, ya ce: “Inna lillallahi wa inna ilaihir raji’un.” Za a ba shi ladan kamar a ranar masifar ta faru. Imam Ahmad da lbn Majah ne suka rawaito wannan hadisin. Kuma Ibn Kasir (Rahimahullah) ya ce:

    “Kuma a zamanin daular banu Buwaihe (daular ‘yan shi’a, a tsakankanin shekaru na ɗari huɗu daga hijra, Rafilawa sun kasance a ranar ashura a Bagdad suna fitowa tituna suna ta kaɗe-kaɗe, suna watsa toka da ɓuntu a kan hanyoyi da kasuwanni, suna maƙala ƙyallaye a jikin rumfuna, Suna koke-koke, wasu ma a daren ba sa shan ruwa, wai suna kwaikwayon ƙishirwar da Husaini ya sha ranar da aka kashe shi.

    Haka matansu ma suke fitowa, fuskokinsu a bayyane, ƙafafuwansu ba takalma, suna kururuwa suna marin fuskokinsu, suna dukan ƙirajensu, da dai bidi’o’i munana, wai kawai don su baƙantawa banu Umayya saboda a zamanin mulkinsu ne aka kashe Husaini (Radiyallahu Anhu).

    A gefe guda kuma waɗansu masu adawa da Ahlul Baiti (Nawasib) a Sham su kuma a ƙoƙarinsu na su ƙalubalanci ‘yan shi’a. sai su yi girke-girke a ranar, su yi wanka, su sanya sababbin kaya, su sa turare, su yi ta nuna farin cikin kamar ranar salla, wai don su ɓatawa ‘yan shi’a rai.

    Waɗansu sun yi tawili dangane da kashe Husaini da aka yi suka ce ai yana ƙoƙarin rarraba kan mutane ne, da yi wa shugaban da mutane suka zaɓa tawaye, wannan kuwa abu ne da manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya hana ya faɗi irin azabar da za a yi wa mai aikata hakan kamar yadda ya tabbata a Sahihu Muslim, to wannan tawili ne na jahilci, kuma bai kamata a y kisa a kansa ba. Da tun farko sun yarda da ɗayan abu uku da ya nuna a yi da shikenan, amma suka ƙi suka kashe shi.

    To kuma wannan ba zai zama hujjar da za ta sa a yi ta la’antar gaba ɗayan al’umma ba; saboda laifin wasu ‘yan tsiraru marasa kirki. Saboda mafi yawancin shugabanni sun yi tur da abinda ya faru tun wancan lokaci har ya zuwa yau. Babu wanda ya goyi bayan kashe Husaini (Radiyallahu Anhu) sai wasu ‘yan tsiraru daga mutanen Kufa; waɗanda su ne suka gayyato shi amma da suka ga abin duniya suka yi watsi suka rabu da shi; wasu ma daga cikinsu suka koma bayan masu yaƙarsa.

    Kuma koda a cikin wannan runduna ba dukkansu ne suka goyi bayan kashe shi ba. Kai koda shi Yazid ɗan Mu’awiyya (Radiyallahu Anhu) bai goyi bayan kashe Husaini (Radiyallahu Anhu); a bisa kyakkyawan zato da shi ne ya kama shi, da ya masa afuwa, kamar yadda shi da kansa ya faɗa. Sannan kuma har tsinewa Ibn Ziyad ya yi, amma kuma duk da haka bai tsige shi daga kan muƙaminsa ba bai kumayi masa komai ba Allah shi ne masani.

    Har ila yau shaihin malami Ibn Kasir (Rahimahullahu) ya yi bayanin matsayi da darajar Husaini (Radiyallahu Anhu); da kuma kyakkyawar alaƙar da take tsakaninsa da Abubakar da Umar da Usman da kuma Mu’awiyya (Radiyallahu Anhuma); inda yake cewa:

    “A taƙaice dai Husaini ya yi rayuwa da Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) kuma sun rabu lafiya; sai dai yana ƙarami lokacin wafatin Manzon Allah(Sallallahu Alaihi Wa Sallam).”

    Bayan nan Sayyidina Abubakar da Umar da Usman (Radiyallahu Anhuma) suna mutuƙar girmama shi. Ya rayu tare da mahaifinsa (Sayyadina Ali Radiyallahu Anhu) kuma ya yi riwaya a gurinsa; ya kasance tare da shi a dukkanin yaƙe-yaƙen da ya yi na Jamal da Saf’in. Sannan ya masa biyayya har zuwa lokacin da aka kashe shi.

    Lokacin da ɗan uwansa Hasan (Radiyallahu Anhu) ya zama halifa ya yi nufin yin sulhu da Mu’awiyya; ya nuna rashin amincewarsa, shi yana ganin gara a yi ta yin yaƙi. Shi kuwa Hasan (Radiyallahu Anhu); ya nuna ɓacin ransa ga wannan matsayi na ƙaninsa har ya yi barazanar ɗaure shi a kurkuku.

    A lokacin halifancin Mu’awiya (Radiyallahu Anhu) Hassan Da Husaini (Radiyallahu Anhu) suna yawan zuwa wurinsa; yana kuma matuƙar girmama su, yana yi musu kyauta ta girma; akwai ma ranar da a lokaci guda ya ba su dinarai dubu biyu har yace; “ku karɓa daga ɗan Hindu kyautar da ba ku taɓa samun irinta ba, haka kuma ba za ku sake samun irinta ba”, shi kuma Husaini sai ya ce; “kai ma ba za ka sake yin kyauta ga waɗanda suka fi mu daraja ba, kuma ba za ka taɓa yin irinta ba’.

    Bayan rasuwar Hasan (Radiyallahu Anhu) Husaini (Radiyallahu Anhu) ya ci gaba da zuwa wurin Mu’awiya; kuma Mu’ awiya ya cigaba da girmama shi da yi masa kyauta ta karamci. Yana ma daga cikin mujahidan da suka yi yaƙin Kustantiniyya a shekara ta hamsin da ɗaya a ƙarƙashin jagorancin Yazidu’.

    To ɗan uwa ka ga fa yadda ‘ya ‘yan asali tsarkaka suka yi mu’amala ta mutunci da girmamawa da Mu’awiyya da sauran sahabbai; amma a yau masu cewa tafarkinsu suke bi ba su da aiki sai ƙin jini da La’antar waɗannan sahabbai waɗanda su ne abokai; aminai, surukai, mataimaka na Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da ‘ya ‘yansu da jikokinsa (Ahlul Baiti Radiyallahu Anhuma).

    ‘Yan uwa a sake tunani a yi biyayya ta gaskiya da koyi na gaskiya ga Ahlul Baiti da sahabbai. Raditallahu Anhum Ajma’in) Allah ka ganar da mu.

    Imamuzzahbi Abu Abdullahi (A.H.S Y.M.S 748)

    Imamuz Zahabi MashahurIn masanin ilimin hadisi ne da tarihi da sauran fannoni; ga irin yabo da kirari da ya yi ga Imamu Husaini (Radiyallahu Anhuma) inda yake cewa; “Shi ne shugaba, sharifi kamili, Jikan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) kuma abin ƙamshinsa; abin ƙaunarsa a duniya, baban Abdullahi ɗan sarkin Muminai baban Hasan Aliyu ɗan Abu Talib; ɗan Abdulmuttalib. ɗan Hashim, ɗan Abdul Munaf, ɗan Kusayyu, Bakuraishe, Bahashime”.

    Kuma yana cewa: Shugabanmu Aliyu yana cikin halifofi shiryayyu; waɗanda aka yi wa albishir da aljanna, muna matuƙar ƙaunarsa; amma ba za mu ce shi ko Abubakar Siddik ma’asumai ne ba. ‘Ya’yansa Hasan da Husaini jikokin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ne; kuma su ne shugabannin samarin aljanna, sun can-canci halifanci.

    Bayan haka, ga kuma Imamus Suyuti wanda kowa ya yarda da shi, saboda ɗimbin iliminsa da tsoron Allah.

    Imam Jalaluddin Assuyuɗi (A.H.S 849 Y.M.S. 911)

    Imamus Suyuti Rahimahullahu ya ce; yana daga munanan bidi’o’i abinda wasu yan bidi’a suke aikatawa ranar ashura na ƙin shan ruwa; da nuna ɓacin rai da nuna alhini, abubuwan da Allah bai shari’anta su ba. Haka ma Manzonsa (Sallallahu Alaihi Wa Sallam), ko wani daga magabata ko a cikin Ahlul Baiti, ko a waninsu; saboda kisan Husaini (Radiyallahu Anhu) wata musiba ta faru tuntuni kuma ta wuce.

    Kuma abinda ya wajaba shi ne a karɓeta da faɗin; “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un” da kyakkyawan haƙuri kamar sauran musibu; amma ba a nuna raki da azabtar da kai ba, da yaɗa labaran ƙarya; da cin mutuncin sahabbai waɗanda ba su ji ba ba su gani ha, kamar dai yadda ‘yan bidi’a suke yi.

    Ibn Majah ya rawaito daga shi kansa Husaini ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma) ya ce; “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce; “duk wanda ya tuna wata musiba da ta same shi, (sai ya sake mai-maita) “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’ un”; Allah zai ba shi lada kamar a lokacin musibar ta faru komai daɗewa kuwa da ta yi da faruwa”.

    Amma ɗaukar ranar ashura a matsayin ranar makoki da ɓacin rai; wannan sam ba musulunci ba ne ya mafi kusa da maguzanci. Kuma su masu yin wannan bidi’ar suna yi wa kansu asarar lada da falalar da ke cikin yin azumin wannan ranar.

    Waɗansu kuma sai suka ƙirƙiri bidi’o’i saɓanin na waɗancan su ne na yin wanka, da ƙunshi; da sanya kwalli da gaggaisawa da juna, wannan munanan bidi’o’i da aka gina su kan wani hadisi na ƙarya. Abinda kawai ya tabbata a sunna shi ne a yi azumi a ranar. Hadisin da aka rawaito wanda yake bayanin falalar yalwatawa iyali ranar ashura rarraunan hadisi ne.

    Tana yiwuwa masu wuce iyaka wurin girmama ranar ashura; suna yin haka ne domin ƙalubalantar ‘yan shi’a to yin hakan dai ba dai-dai ba ne; saboda shi shaiɗan burinsa dai ya ga ya ɓatar da mutum ta kowane hali. Ya kamata dai ‘yan bidi’a su guji bidi’a kawai ba wata Magana”.

    Ya ɗan uwana mai neman gaskiya; ka dubi wannan hadisi mai girma wanda shi da kansa Imamu Husaini (Radiyallahu Anhu) ya rawaito shi daga kakansa. Ka ga duk masoyinsa mai goyon bayansa ya wajaba ya yi aiki da shi ta hanyar faɗin; “Innalillahi wa inna ilaihir raji’un” a duk lokacin da ya tuna da shahadarsa a Karbala illa iyaka; ba wai ya yi ihu da zage-zage ba. Allah ka ganar da mu.

    Shin mai imamai suka ce?

    A wannan gaɓa ina so mu yi nazarin maganganun da suka fito kai tsaye daga bakin shugabannin Ahul Baiti; waɗanda ake cewa saboda su ne ake yin ibadu da bukukuwan ashura domin mu tantance tsakuwa da tsaba; mu san gaskiyar addinin da suka koyar da kuma saɓaninsa.

    Da farko bari mu fara da shi kansa Imamu Husainni (Radiyallahu Anhu); mu ji wasiyyar da ya yi wa ‘yar uwarsa Zainab (Radiyallahu Anha) dab da zai yi shahada:

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasiyyar Imamu Husaini (Radiyallahu Anhu) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Azumin Tasu’a Da Ashura danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Malaman Ƙasar Zariya

    Malaman Ƙasar Zariya

    A ƙasar Zariya, neman ilimin Furu’a ya cuɗanya da neman ilimin Alƙur’ani. Wannan ya sa makarantun Alƙur’ani a Zariya da Sakkwato zama tamkar makarantun ilimi ne “Zaure”.

    A wasu lokuta, ɗalibai masu neman ilimin lugga ko Fiƙhu kan rubuta baikutan karatunsu a jikin allunansu; kamar yadda ake rubuta Alƙur’ani a allo a Kano da Barno.

    Tarihin yaɗuwar ilimin Alƙur’ani da ilimi a Zariya; kafin ma bayyanar Shehu Usmanu ba zai manta da zuriyar Juma do Kona ba. Waɗanda aka ce su ne na farko wajen kafa makarantun.

    Don haka za mu ayyana wasu cibiyoyi da Malamai shahararru a Zariya da kewayenta; musamman ma daga ƙarni na ashirin zuwa na ashirin da ɗaya. Waɗannan Malamai sun haɗa da:

    Malam Na’iya da Malam Inuwa Na Magajiya da Malam Muhammad Gali ƙofar Doka; da Malam Nuhu Ladan da Malam Auwal Kusfa; da Malam Usman Babajo Marmara da Muhammad Auwal Ƙaura da Malam Yakubu Kakaki da Alƙali Shu’aibu Kakaki; da Malam Alhassan Yawuri da Malam Haruna da Malam Junaidu Rimin Danza da Malam Umar Ƙwarbai.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Malamai Allori danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Samun Nutsuwa Da Kwanciyar Hankali Da Wadatar Zuciya danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Haƙƙoƙin Mabiya A Kan Shugabanni

    Haƙƙoƙin Mabiya A Kan Shugabanni

    Su kuwa mabiya suna da waɗannan haƙƙoƙi a kan Shugabanninsu:

    1. Tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi da mutuncin mabiyansa. Wajibi ne ya kula da tsaron kan iyakoki, ya yi maganin ‘yan fashi da ɓarayi da ‘yan ta’adda. Ya kula sosai da jin daɗin jami’an tsaro da iyalansu ta yadda za su samu ƙarfin gwiwa da kishin kare ƙasa.

    2. Kulawa da addini da bunƙasa shi ta hanyar jan managartan malamai a jiki da neman shawarwarinsu da fatawoyinsu da sauraron karatuttukansu da wa’azin su.

    Kada ya bar kafirci ko bidi’a ko lalata da masu yinsu su samu sakewa har su kafu a inda yake da iko. Ya ƙarfafa koyar da ingantacce sahihin addini bisa koyarwar ƙur’ani da sunna da fahimtar magabata na ƙwarai.

    3. Wajibi ne shugaba ya kula da al’amarin musulunci, kada ya yi sakaci da salloli biyar a cikin jama’a ya ringa halartar sallolin juma’a da na idi, ya kula da yadda limamai suke gabatar da huɗubobi, da karatuttukansu, ya kula da ladanai da kiran salla daidai.

    4. Ya naɗa alƙalai masana masu adalci da tsoron Allah da kamewa, ya sanya idanu sosai a kansu, saboda sai an tuhume shi kan duk shari’un da suka yi, zai kuma samu lada kan adalci da taimako da suke yi wa mutane.

    5. Wajibi ne a kan shugaba musulmi ya ringa fita jihadi da kansa, sannan kuma ya tura mujahidai suna yi a ƙalla sau ɗaya duk shekara. Gwargwadon ikonsa. Koda kuma ya yi sakaci da sauran nau’o’in jihadin.

    6. Aiwatar da Shari’ar Allah da hukunta masu laifi ba sani ba sabo kamar yadda Allah ya shari’anta da manzonsa, kada ya kuskura ya yi wani hukunci da ya saɓawa shari’ar Allah Ta’ala.

    7. Ya kula da tattalin arziƙin mabiyansa da jin daɗinsu da walwalarsu. Ya tabbatar yana bin hanyoyin da shari’a ta yarda da su domin samun kuɗin shiga kamar zakka, ganima da jizya, ya kuma sarrafa su ta hanyoyin da shari’a ta yi izini a sarrafa su.

    8. Kafa hukumar kula da waƙafi da tsara al’amarinsa ta yadda kowa zai amfana da shi, mutane kuma su samu ƙarfin gwaiwar bayar da kafa waƙafin.

    9. Yin adalci wajen rabon arziƙin ƙasa da gudanar ayyukan ci gaban al’umma.

    10. Wajibi ne shugaba ya kasance mai gaskiya da riƙon amana ya guji zalunci da nuna son kai da bambanci tsakanin mabiyansa.

    Shahararren malamin nan masanin siyasar musulunci Abul Hassan Almawardi Rahimahullahu ya faɗa a cikin sanannen littafinsa ‘Al- Ahkamus sultaniyya cewa akwai haƙƙoƙi goma a kan shugabanni.

    A taƙaice su ne;

    1. Kiyaye addini daga gurɓata.
    2. Tabbatar da doka da oda da bai wa kowa haƙƙinsa.
    3. Tabbatar da tsaro a birane da ƙauyuka.
    4. Tabbatar da hukuncin Allah ba sani ba sabo.
    5. Tabbatar da tsaron kan iyakoki.
    6. Yin jihadi domin ɗaukaka addinin Allah Ta’ala.
    7. Tattara kuɗin shiga da sarrafa su ta hanyar da shari’a ta yarda da su.
    8. Rabon arziƙin ƙasa da biyan ma’aikata albashinsu.
    9. Naɗa amintattu mutanen kirki masu gaskiya a kan muƙamai.
    10. Sanya idanu a kan dukkanin al’amuran mabiyansa da wanda ya naɗa su kula da ɓangarorin gudanarwa kada ya bari kowa yake cin karensa ba babbaka.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Halaye Da Siffofin Shugaba Nagari danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

     

  • Wasu Daga Malamai A Ilori

    Wasu Daga Malamai A Ilori

    Malam Musa Akalanbi

    Shi ne mashahurin Malami, Musa Ɗan Abubakar Ɗan Hassan Alkasinawiy. An ce iyayensa sun je Ilori daga Katsina don yaɗa Addinin Musulunci. An haifi Malam Musa a garin Ilori.

    Ya yi karatu a wurin mahaifinsa har ya haddace Alƙur’ani kuma ya shiga fannonin ilmi har ya tumbatsa a fannin Tafsiri da Hadisi. Makarantarsa cike ta ke da ɗalibai sama da ɗari Uku. Bai gushe ba yana koyarwa har ya rasu a shekarata 1970.

    Malam Muhammadul Ghali Ilori

    An ce zuriyarsa sun zo daga ƙasar Mali. An haifi Muhammad Ghali a garin Ilori kuma ya yi karatu a hannun mahaifinsa har ya zama malami masanin Alƙur’ani. Malam Ghali ya yi tafiye-tafiye Izuwa ƙasashen Yarabawa kamar Ibadan da Ikirun don koyar da Addini. An ce mafiya yawan Malaman Yarabawa sun yi karatu a hannunsa, kamar su Alhaji Ibrahim Giɗaɗo da Alhaji Sulaiman Limamin Juma’a Na Ikirun. Malam Ghali ya rasu a shekara ta 1974.

    Alpa Anla

    Shi ne Alhaji Abubakar Alkasinawiy, Wanda aka fi sani da Alpa Anla, ma’ana, babban Malami. An haife shi a cikin shekara ta 1913. Ya haddace Alƙur’ani tun da yarintarsa. Har ya zama hamshaƙin malami. Ya cigaba da koyarwa har rasuwarsa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin

    Misalan Malaman Nufawa A Ƙarni Na Ashirin

    Malaman ƙarni na ashirin sun haɗa da:

    – Alhaji Umar Egan Bidda

    – Alhaji Alpa Darajta Bidda

    – Alhaji Umaru Banwuya Bidda

    – Alaramma Malam Zubairu Kuba Bidda

    Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Malaman Yarabawa A Ƙarni Na Goma Sha Tara danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Falalar Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)

    Falalar Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam)

    Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; wanda ya yi salati ɗaya a gare ni, Allah zai yi salati goma a gare shi’.

    Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘kada ku mai da ƙabarina idi; ku yi salati a gare ni ko ina kuka kasance’.

    Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Marowaci shi ne wanda aka ambace ni a wurinsa amma bai yi mini salati ba’.

    Kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Allah yana da waɗansu mala’iku matafiya a bayan ƙasa; suna isar mini da sallama daga al’ummata’.

    Sannan kuma Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; ‘Babu wani wanda zai yi mini sallama face Allah ya dawo mini da raina na amsa sallamarsa’.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Yaɗa Sallama A Cikin Al’umma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Ya Raɗa Wa Manzon Allah(S.A.W) Suna Muhammad? danna nan.

     

  • Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyali suturar mutum, iyali suturar gida. A bisa yanayin zamantakewar bil Adama da aljannu, cikar ɗa, mutum namiji ko ‘ya, mutum mace ita ce yadda Allah ya hore musu, ya ba su dama, suka assasa zuriya ta kankin kansu.

    Ta haka za su sami nutsuwa, da samun ayyukan yi a duniyarsu da lahirarsu, musamman ma idan suka yi aiki da hukunce-hukuncen addini da matakan zamantakewar rayuwa bisa kyakkyawan zaɓi da dacewa. Haka kuma aure yana a kan gaba wajen tsayar da usra ko iyali da za su iya zama ƙwarara, ina ma a ce an bi sharuɗɗa da kyawawan dangogi na yin sa.

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo wanda aka fi sani kuma ake kira da Maradun, ya sami jagoranci na iyaye wajen yin matar farko 21. A yayin zaman Ɗanƙwairo a doron rayuwar duniya bayan matarsa ta fari, ya auri mata da yawa kuma wasu daga cikinsu ne suka haifa masa ‘ya’ya har goma sha bakwai (17).

    Matan Aure na Musa Ɗanƙwairo

    Mata waɗanda Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya aure a rayuwarsa ta duniya su ne:

    i) Hauwa Taladan
    ii) Hajiya Hadiza (Ikka/Tashikka)
    iii) Amina
    iv) Tumba
    v) Rabi (‘Yar Zuma)
    vi) Maryam (Amarya)
    vii) Hauwa
    viii) Maimuna

    ‘Ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maza da Mata

    Ga tsarin sunayen ‘ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ta bin ɗakunan iyayensu mata da suka haɗa da:

    i) Ɗakin Hauwa (Taladan)

    ii) Ɗakin Hajiya Ikka (Tashikka)
    a) Muhammadu Ɗanmakaɗa, Dauda na ɗaya (1)
    b) Alhaji Garba, Zwacin Kiɗi, Marafa, Daudu (2)
    c) Audu Adodo, Wakilin Kiɗa
    d) Zulaihat
    e) Habiba

    iii) Ɗakin Amina
    f) Ummaru Ka-ji-Dama (Makaɗin Noma)
    g) Amina (Kassu): Tana aure a Maradun

    iv) Ɗakin Tumba
    h) Sanin Ɗanƙwairo, Zakin Murya

    v) Ɗakin Maryam (Amarya)
    i) Sa’adatu
    j) Muhammadu Balarabe
    k) Umaru

    vi) Ɗakin Rabi’a (‘Yarzuma)
    l) A’ishatu (Indo)
    m) Malam Musa Tunau (Malamin Makarantar Allo)

    vii) Ɗakin Hauwa
    n) Abubakar, Ciroman Kiɗa
    o) Amina, Ige
    p) Ibrahim Ɗan’auta22

    viii) Ɗakin Maimuna
    Ba ta Haihu ba.

    Bishiyar Iyalin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun

    Kaka Maiganga
    Usman Ɗankwanagga = Yarnunu
    Musa Ɗanƙwairo23 Amina Binta (Maryam)

    = Hauwa = Haj. Hadiza =Amina = Tumba = Maryam =Rabi = Hauwa =Maimuna
    (Taladan) (Ikka Tashikka) (Amarya) (‘Yar Zuma)
    Malam Musa Ba ta
    Tunau haihu ba
    Umaru Amina (Kassu)
    (Ka-Ji-Dama) Tana Aure Sa’adatu Muh Umaru
    a Maradun (‘Yabbata) Balarabe
    Muhammadu Sani (Zaƙin Murya)
    Ciroma Amina Ibrahim Ɗan’auta
    Abubakar (Ige) (Harkokin
    Magaji na (2) Kasuwanci)
    Muhammadu Garban Audu Zainabu Habiba
    (Ɗanmakaɗa) Ɗanƙwairo (Adodo)
    Magaji na (1)

    = Salame = Baraka
    Muhammadu Muh Tamaikiɗi
    Ɗanjimma Basiru
    Magaji na (3)

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kiɗa da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Kiɗa da Makaɗi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.