Fassarar Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 17 Rajab 1446 AH 17 January 2025

0
45

Mai Huɗuba:
Sheikh Dr Abdurrahman Al Sudais

Mai Fassara:
Dr Usman Azzuhri

Shugaban Shashi
Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

TAKEN HUƊUBA: GWALA-GWALEN KALMOMI GAME DA KARIYA DA GARKUWA
17 RAJAB, 1446H

Huɗuba Ta farko:
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode Masa, muna neman taimakonSa da gafararSa, muna tsarkake Shi tare da gode Masa; Ya ƙaddara al’amura kuma Ya zartar da su, kuma Ya haramta ɓarna da abin da ya yi kama da ita.

Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Ma’abocin girma, kuma duk wanda ya zama ma’abocin godiya da gode Maka, to, haƙiƙa ya haɗa ababen yabawa. Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, irin yabo da ba ya ƙididdiguwa ga maƙididdigi, shin akwai mai iya ƙididdige tsakwankwani da tsirrai da yashi da ruwa mai mamako.

Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, shaidawa da take kare jikkuna daga tawaya da ke lulluɓe su. Kuma ina shaidawa lallai shugabanmu Annabi Muhammadu shi ne mafi alherin halittu kuma mafi tsarkakarsu, Allah Ya yi daɗin salati da sallama da albarka a gare shi, da alayensa da sahabbansa, zaɓaɓɓun halittu kuma mafiya matsayinsu, waɗanda suka kai maƙura a matakan kariya da garkuwa, da Tabi’ai da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa Ranar sakamako.

Bayan haka:
Ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah, ku ji tsoronSa a sarari da ɓoye, duk wanda ya lazimci tsoron Allah, to, haƙiƙa ya amsa wa mai kira zuwa ga Allah, ya kuma yi tsauri ga ababe masu ɓatarwa kuma ya gagare su, kuma zuciyarsa da ruhinsa sun tsarkaka.
Tsoron Allah shi ne rabautar mutum a kodayaushe, kuma da shi ake ƙetare wahalhalu masu girma.

((Ya ku waɗanda ku ka yi imani, ku ji tsoron Allah kuma ku faɗi magana wacca take daidai () Zai gyara muku ayyukanku, kuma Zai gafarta muku zunubanku, kuma duk wanda ya yi wa Allah da ManzonSa biyayya, to, haƙiƙa ya rabauta rabauta mai girma)).

Ya ku taron muminai:
A cikin wannan zamani da ke cike da masifu da ƙalubale, da ɗimuwa da koke-koke, yaro na fatan ya girma, tsoho na burin ina ma ya koma yaro, mara aikin yi yana fafutukar neman aiki, ga ma’abocin aikin yi kuma ya ƙosa da aikin nasa, ma’abocin dukiya na cikin gajiya, shi ma matalauci na cikin gajiyar.

A cikin wata al’umma da ayyukan sihiri da tsaface-tsafacen shaiɗan ke yaɗuwa, da cututtukan kambun baka da annobar zukata, da abin da ke samun musulmi daga haka na damuwa da jinya, ko tawaya na rayuka da dukiyoyi, da kuma abubawa da Allah tsarki ya tabbata a gare Shi Yake ƙaddarawa na jarrabawa ga ɗaiɗaikun mutane da al’ummomi.

Kuma ita jarrabawa tsani ce na samun darajojin kamala ga wasu mutane, ga wasu kuma, kaffara ce daga munanan ayyuka, amma shi lamarin musulmi alheri ne gaba ɗayansa, idan bala’i da ƙunci suka sauko masa ((Kuma zai iya yiwuwa ku ƙi wani abu alhalin shi alheri ne a gare ku, kuma zai iya yiwuwa ku so wani abu alhalin shi sharri ne a gare ku. Kuma Allah Shi yake da sani, ku ba ku sani ba)).

Ya ku masu Imani!
Tunatarwa game da maudu’in kariya da garkuwa na daga cikin mafi mahimmancin abin da mutane suke buƙata, musamman ma a wannan zamani da cututtuka masu yawa suke game rayuka kuma suke kutsawa cikinsu, suke fuskantar su da matsaloli kuma suke ratsa su, na farfaɗiya da shafan aljanu da tsafi da kambun baka, da ƙullata da hassada masu kai wa ga mutuwa.

Haƙiƙa ayoyin Alƙur’ani sun haskaka da manyan hujjoji, Hadisan Annabi da mafi kyawun bayani, da shaida na gani da ido cewa su ne magani da waraka daga kowace gagararriyar cuta, Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: ((Ka ce shi (Alƙur’ani) ga waɗanda suka yi imani shiriya ne da waraka)).

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Ku bijiro mun da ruƙiyyoyinku, babu laifi a ruƙiyya matuƙar ba shirka ba ce). Muslim ne ya rawaito.
Sau da yawa za ka ga mara lafiya da yake dab da halaka da mutuwa, wanda manyan asibitoci da ƙwararrun masana da likitoci su ka gagara magance masa cuta, sai ya nemi waraka ta hanyar ruƙiyya ta Shari’a, sai Allah Ya tabbatar masa da lafiya da waraka.

Imamu Ibnul-ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce: “Alƙur’ani shi ne waraka cikakkiya daga dukkan cututtuka na zuciya da na jiki, idan mara lafiya ya kyautata yin magani da shi, ta yaya ma daman cututtuka za su iya turje wa maganar Ubangijin ƙasa da sama, maganar da da za ta sauka a kan duwatsu da ta rududduge su, ko a ƙasa da ta keta ta”. Allahu Akbar.. Madalla da wannan yaƙini tabbatacce.

Lalle tofi saboda guba ko kambun baka, idan ya kasance da tsantsan ayoyin Alƙur’ani ko sunnar Annabi ne, to wannan yana daga shiriyar Annabi da Shari’arsa, kuma wannan babu saɓani cewa Sunna ne.

Ya ku al’ummar Musulmi!
Kariya da garkuwa hanya ne da ake bi don nisantar cuta da jinya da rashin lafiya, don haka ya ku bayin Allah ina horon ku da kare kanku da ‘ya’yanku da gidaddajinku da wuridodi na Shari’a, da zikirai na safiya da maraice, da zikiran shiga gida da fita, da na ci da sha, da na bacci da farkawa, da wasunsu cikin zikirai da suka tabbata daga Shugaban halittu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, saboda su ne garkuwa mai kariya da izinin Allah, tare da tawakkali mai ƙarfi ga Allah Majiɓinci Mai gani da ji, da mai da lamari ga gudanarwarSa mai tsari da kyawu, kuma yaƙini da Allah shi ne mafi girman ƙudurori, kuma shi ya fi haske a cikin duhun ɗimuwa: ((Yanzu Allah bai ishi bawanSa ba?).

Na yarda da Ubangijina, kuma na mayar da lamurana gare Shi, kuma Ya isa Ya kasance Mai taimako na. Kada ka yanke tsammani saboda masifun zamani, lallai yaƙini na da Allah shi ne makarina. Bukhari ya rawaito a cikin Sahihinsa daga Hadisin Ibn Abbas Allah Ya ƙara masa yarda cewa: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana yi wa Hasan da Husaini addu’ar neman tsari yana cewa: (Lalle mahaifinku yana yi wa Isma’il da Ishaƙ addu’a da wannan addu’ar ta neman tsari: ‘A’uzu bi kalimatillahi at-tammati min kulli shaiaɗanin wahammatin wa min kulli ‘ainin lammah).

Kuma ya zo a cikin Sahihu Muslim, daga Hadisin Abu Umama Al-Bahili Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Ku karanta Suratul Baqara, domin lallai karanta ta albarka ne, kuma barinta hasara ne, kuma matsafa ba a datar da su ga koyonta).

Imam Ahmad ya rawaito a cikin Musnad ɗinsa daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Kada ku sanya gidajenku su zama kaburbura, domin shaiɗan yana guje wa gidan da ake karanta Suratul Baqara a cikinsa), musamman ma ayatul Kursiyyi da ayoyin ƙarshen surar, da Ƙulhuwallahu da Falaƙi da Nasi kamar yadda hakan ya kasance shiriyar Manzonku.

Ya ku taron Musulmi,
Saboda rashin kulawa daga yawancin musulmi wajen neman kariya ga kansu, da ‘ya’yansu, da gidajensu, tare da raunin imani da aƙida ga wanda shaiɗan ya shafa da wasiwasi ko wasu abubuwa masu kama da haka, ko wanda aka shafa da kambun baka ko hassada, wasu daga cikinsu suna tunkarar sihirce-sihirce da tsubbace-tsubbace da tatsuniyoyi, da tsafi da damfara da aikata laifuka, suna faɗawa hannun wasu daga cikin masu raya yin ruƙiyya, ko waɗanda suke raya warware sihiri da makamantansa.

Sai ka ga mai ruƙiyya yana rubutun da ba a ganewa kuma yana yin laya, wani kuma yana magana mara ma’ana, wani kuma yana tabbatar da cewa cutar kambun baka ce, kuma wanda ya yi kambun bakan a cikin dangi yake, wani kuma ba ya rabuwa da yin duka mai cutarwa, kuma mafi yawan waɗannan masu ikirari suna ɓoye haƙiƙanin lamarinsu ta hanyar bayyana siffofin mutane masu hankali da taƙawa, amma su ba komai ba ne illa mayaudara waɗanda suke cin dukiyoyin mutane, suna neman dukiya ta hanyar aikata rashin gaskiya, kuma ana iya bijiro da shi da wasu siffofi don yaudarar talakawa, musamman ma ta hanyar amfani da tashoshin talabijin da shafukan yanar gizo da kafafen sada zumunta, har ma da wasu manhajoji.

Ya ku bayin Allah!
Sannan shi kariya da garkuwa ba ya buƙatar wahala ko tsananta wa kai, ko faɗawa cikin tarkon maƙaryata, bari da, shi amintuwa ne daga waɗannan gaba ɗaya, mutum zai iya yi shi da kanshi, haka tare da iyalanshi da ‘ya’yanshi. Kuma yana taimakawa wajen kiyaye ɗaiɗaikun mutane da al’ummomi, da kishi wajen ba da kariya ga daɗaɗɗar aƙida, da ƙayatattar Shari’a.

A’uzu billahi minash-shaiɗanir-rajim: ((Kuma daga Alƙur’ani muna saukar da abin da yake shi waraka ne da kuma rahama ga Muminai; ba kuma zai ƙari azzalumai da komai ba sai taɓewa)). Allah Ya albarkace mu da Alƙur’ani da Sunna, Ya kuma amfane mu Ya ɗaukaka mu da abin da ke cikinsu na ayoyi bayyanannu da hikima.

Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema mana gafarar Allah Mai girma da sauran Musulmi daga kowane kuskure da zunubi, don haka ku nemi gafararSa kuma ku tuba zuwa gare Shi, Lallai Ubangijina Mai gafara ne Mai jin ƙai.

Huɗuba ta biyu:

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah bisa ni’momi da Ya yi, tsarki ya tabbata a gare Shi Ya yi wa bayinSa baiwa mai yawa. Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya.

Kuma ina shaidawa lallai Annabinmu Muhammadu shi ne abin koyi ga masu tsoron Allah, tsira da aminci da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa masu tsarki zaɓaɓɓu, da Sahabbansa masu biyayya da tsoron Allah, da Tabi’ai da waɗanda suka bi tafarkinsu har zuwa Ranar Alƙiyama. Bayan haka:

Ya ku bayin Allah!
Ku ji tsoron Allah ta hanyar bin umurninSa, da kuma guje wa haninSa da jan-kunnenSa, saboda Shi Allah Maɗaukakin Sarki Yana tsinkayar al’amarin da yake ɓoye ko bayyane, da abin da ke ɗarsuwa a zukata da abin da suke ɓoyewa.

Ya ku taron Muminai!
Jarabawowi da masifu da tashe-tashen hankula da fitintinu da damuwowi da bala’o’i, da ke samun al’umma ba su ɓuya a gare ku ba, waɗanda suka jawo mata rashin jin daɗi matuƙa. Saboda haka, lallai daga cikin mafi mahimmancin nau’ukan kariya a wannan mawuyacin hali shi ne: Kare hankulan matasa ta fuskar tunani da kuma aƙida.

Wannan nauyi kuwa ya rataya ne akan malamai da masu wa’azi da iyaye da malaman tarbiya da saita tunani, da kafafen yaɗa labarai da fitattun marubuta. Don haka ya wajaba a kansu gaba ɗaya su ba da gudumawa wajen kare matasa ta ɓangaren tunani da kuma aƙida, da kuma kwaɗaitar da su ga komawa wajen malaman al’umma masana, da kuma yin gargaɗi dangane da fatawowi waɗanda suke bauɗaɗɗu da masu ingiza mutane da kuma masu dilmiyarwa.

Da kuma faɗakar da su game da ƙalubalen da ke fuskantar su, a wannan zamani da fitintinu na son zuciya da shakku suka yawaita, tashe-tashen hankula suka shiga tsakanin ma’aurata da iyalai da al’umma. Da kuma yin riƙo da hannayensu daga aukawa cikin ramukan gurɓatattaun tunani, tare da wayar da kai ta hanyar bayyana shirin maƙiya da daƙile hanyarsu ta cimma munanan muradansu.

Allah Ya kiyaye matasanmu da al’ummarmu daga dukkan sharri da munanan abubuwa, Ya kare mana tsaronmu da zaman lafiyanmu da aƙidarmu da shuwagabanninmu, Lallai Ubangijina Makusanci ne kuma Mai amsa addu’a. Ku saurara! Allah Ya yi muku rahama- Ku yi salati da sallama ga shugaban Manzanni da Annabawa, jagoran masu tsoron Allah kuma tsarkaka, kamar yadda Ubangijin talikai Ya Umarce ku da hakan inda Yake cewa:

(Lallai Allah da mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati. Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi masa salati da kuma sallama mai yawa). Kuma ya zo a cikin ingantaccen hadisi: “Duk wanda ya yi min salati ɗaya, Allah Zai yi masa salati goma.”

Lallai yin salati ga Annabi babbar riba ce…duk wanda ya same ta, to, ya samu matsayi kuma ya mallake shi. Ku ribaci wannan dama ku riƙa yin salati ga Annabi, kuna masu cewa: Allah Ya yi masa daɗin tsira da aminci, har abada. Ya Allah Ka yi salati da sallama ga Annabinmu Muhammad da Iyalansa masu tsarki da tsarkaka, da Sahabbansa masu haske da ɗaukaka, da Halifofinsa shiryayyu Abubakar da Umar da Usman, da Ali da dukkan sauran Sahabbai gaba ɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa Ranar sakamako.

Allah Ka haɗa mu tare da su cikin falalarKa da kyautarKa da karamcinKa, ya Mafi karamcin masu karamci. Muna neman kariyar Ma’abocin mulki da iko, mun yi riƙo da Ma’abocin buyawa da ƙarfi, mun dogara da Mai rai wanda ba ya mutuwa.

Muna neman kariya da cikakkun kalmomin Allah waɗanda nagari ko fajiri ba su iya ƙetare su daga dukkan wani shaiɗani da dabba mai guba, muna neman kariya da cikakkun kalmomin Allah daga sharrin abin da Ya halitta da wanda Ya ƙaga da wanda Ya samar, da sharrin abin da yake sauka daga sama da sharrin abun da yake fitowa daga ƙasa da ma sharrin kowacce dabba wanda Kai ne Kake riƙe da ita, lallai Ubangijina a kan tafarki madaidaici Yake.

Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kare shingen addini, Ka sanya wannan ƙasa ta zama mai aminci da kwanciyar hankali, da yalwa da wadata, tare da sauran ƙasashen Musulmai. Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, ka datar da shuwagabanninmu da jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma Jagoranmu da gaskiya da dace.

Ya Allah ka datar da Shugabanmu Hadimin Masallatai biyu masu alfarma da Mataimakinsa ga abin da yake ɗaukaka ne ga Musulunci da kuma gyara ga Musulmi, da kuma abin da yake alheri da shiriya ga mutane da ƙasa. Ya Allah ka datar da ɗaukacin jagororin Musulmi.

Ya Allah, Ka taimaki jami’an tsaronmu da masu dako a iyakokinmu. Ya Allah duk wanda yake nufatarmu da Musulunci da Musulmi da wani sharri, Ka sa ya shagala da kansa, Ka mayar da mugun nufinsa a kansa, Ka sanya dabararsa ta zama hallakarsa, Ya Maji roƙo.
Ya Allah, Ka haɗa kan al’umma akan Alƙur’ani da Sunna, ya Ma’abocin kyauta da falala da baiwa.

Ya Allah ba a iya karya rundunarKa, ba a saɓa alƙawarinKa. Ya Allah Ka taimaki ‘yan’uwanmu a Falasɗinu, ya Allah Ka tarwatsa maƙiyansu Ka wargaza taronsu, Ka sanya su su zama izina ga masu lura. Ya Allah, Ka tsara wa wannan al’umma lamari na shiriya, wanda zai ɗaukaka ma’abota biyayya da imani, kuma ya shiryar da masu bijirewa da yin zunubi.

Ya Allah, muna da ‘yan’uwa waɗanda ɗari da talauci suka shafe su, ya Allah, ya Mai biyan buƙatu, ya Mai kawar da talauci, ya Mai agaza wa wanda ya ke cikin ƙunci, Ka saukar musu daga ɗumin jinƙanKa, Ka wadatar da su da falalarKa da albarkatunKa, ya Maji roƙo, ya Mafi jinƙan masu jinƙai. Ya Allah, Ka ba mu alheri a duniya Ka ba mu alheri a Lahira, Ka tsare mu daga azabar wuta.

Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Manzanni, godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai.

Danna nan don karantasahihin sirrin iza ja’a

Edita; Rumasa’u M. Kallamu

 

labarin da ya wuceRijistar CAC Da Muhimmancinta
Labarin na GabaBirkicewar Tsarin Jijiyoyin Jiki