Falalar Sallar Tahajjudi

0
750

1) Allah Ta’ala ya ce: “Kuma bayin Allah su ne waɗanda suke tafiya cikin nutsuwa a bayan ƙasa, in wawaye sun yi musu magana sai su ce, “Aminci ya tabbata a gare ku”. (Wato Allah ya ba ku haƙuri). Su ne waɗanda suke kwana suna sujjada suke tsayawa ga Ubangijinsu” (Suratul Furƙan: 63 – 64).

2) Allaha (Subahanahu wata’ala) ya ce: “Haƙiƙa masu tsoron Allah suna cikin Aljannata da ƙoramu. Suna masu karɓar abin da Ubangijinsu ya ba su, haƙiƙa sun kansance masu kyautatawa kafin wannan. Sun kansance suna yin barci kaɗan a cikin dare, kuma a lokacin sahur suna istigfari”.

3) Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam)ya ce: “Ya ku mutane, ku yaɗa Sallama, ku ciyar da abinci, ku sadar da zumunci, ku rinƙa sallah da daddare a lokacin da mutane suke barci; za ku shiga Aljanna cikin aminci”. (Tirmizi 1855, Ibn Majah 1334 Ahmad 751).

Ana iya yin ƙiyamul laili a farkon dare ko a tsakiyar dare ko a ƙarshen dare; ƙarshin daren shi ne mafificin lokaci.

Domin karanta cikakken bayani a kan Adadin Raka’o’in Sallar Asham danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceSallar Ƙiyamul Laili (TAHAJJUD)
Labarin na GabaAdadin Raka’o’in Sallar Asham