وَفِيكَ بَارَكَ الله.
Wa fi ka barakallah
Kai ma Allah ya yi maka albarka.
Karanta Addu’a Ga Wanda Aka Zo Biyansa Bashinsa
Edita@rumasau-kallamu
Yadda ake amfani da WikiHausa

وَفِيكَ بَارَكَ الله.
Wa fi ka barakallah
Kai ma Allah ya yi maka albarka.
Karanta Addu’a Ga Wanda Aka Zo Biyansa Bashinsa
Edita@rumasau-kallamu

Sauran Ƙabilu
Akwai wasu kuma a yankin Filato waɗanda suka haɗa da Birom da Angas da Ganawuri da Sayawa da sauransu. A jihohin Bauchi da Gwambe akwai wasu ƙananan ƙabilun kamar Gerawa da Terawa da Jerumawa da Ganjuwa da Denawa da Kanakuru da Tangale da Waja da dai sauransu. A ƙasar Hausa ta yamma akwai wasu ƙananan ƙabilun da suke zaune a yankin Yawuri da Kwantagora waɗanda suka haɗa da Dakarkari da Kambari da Kamuku da dai sauransu.
Akwai daɗaɗɗiyar dangantaka a tsakanin Hausawa da waɗannan ƙananan ƙabilu masu maƙwabtaka da ƙasar Hausa. Mafi yawa daga cikin waɗannan ƙananan ƙabilu sun zauna a ƙarƙashin mulkin sarakunan ƙasar Hausa waɗanda suke maƙwabtaka da su. Misali, ƙabilun da suke kudancin jihar Kaduna sun zauna a ƙarƙashin mulkin Sarkin Zazzau tun cikin ƙarni na goma sha takwas, wanda shi ya sa a yanzu ake kiran su da sunan ƙabilun kudancin Zariya (Adeleye, 1975:593).
Ta wannan hanya ce al’ummomin waɗannan ƙananan ƙabilu suka riƙa hulɗoɗi da Hausawa. Ta hanyar waɗannan hulɗoɗi mafi yawa daga cikin al’ummomin waɗannan ƙabilu da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa koyon harshen Hausa wanda ya zama harshe na biyu gare su bayan harshen da suka gada.
Haka kuma harshen Hausa ya zama harshen da kowa da kowa daga cikin su yake amfani da shi wajen sadarwa da kasuwanci da addini da sauran ma’amalolin rayuwa na yau da kullum a tsakaninsu da sauran al’ummomin da suke cikin ƙasar Hausa da kuma waɗanda suke maƙwabtaka da su. A sakamakon wannan dangantaka ne, a yanzu harshen Hausa yake ƙoƙarin mamaye waɗannan ƙananan harsuna da suke maƙwabtaka da ƙasar Hausa.
Idan muka juya kan shigowar al’ummomin waɗannan ƙananan ƙabilu cikin ƙasar Hausa, za a ga mafi yawancinsu sun shigo a cikin ƙarni na ashirin. Wannan kuwa ya faru ne a sakamakon kafuwar mulkin mallaka wanda ya haɗa waɗannan al’ummomi wuri ɗaya a ƙasa ɗaya.
Kamar yadda wasu daga cikin waɗannan al’ummomi suka shigo cikin ƙasar Hausa, akwai wasu Hausawa da suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka shiga ƙasashensu. Misali, a sakamakon samun kuza da kwaranda a ƙasashen da suke kudancin Zariya da yankin Filato tun cikin shekarun 1920, an sami Hausawa waɗanda suka yi ƙaura daga Kano da Katsina da Zariya da Sakkwato suka koma waɗannan ƙasashe.
A wuraren da suke zaune sun riƙa yin hulɗa da al’ummomin wuraren, wannan ya sa sun auri mata ‘yan ƙasar suka mayar da su Hausawa (Hira da GMW, a garin Godo- Godo da kuma MIM, a garin Kafanchan, a ranar 24/8/2004).
Sauran baƙi a nan ana nufin ƙananan ƙabilu waɗanda suke maƙwabtaka da Hausawa daga kudu da kudu-maso-gabas da kuma kudu-maso-yamma da ƙasar Hausa. Dangane da wannan bincike an duba ƙabilun Dakarkari da na kudancin jihar Kaduna da kuma ƙabilar Tera a jihar Gwambe.
A nazarin da aka gudanar a waɗannan ƙabilu an fahimci nauyin al’adunsu cikin wanzanci ba shi da yawa. Wannan kuwa ya faru ne saboda yadda al’adun Hausawa suka taushe al’adunsu ta yadda a wannan zamani wasu daga cikin al’adunsu sun fara ɓacewa na Hausawa na maye gurbinsu. Amma duk da haka ga ɗan abin da aka samu.
Hausawa sun sami wasu magunguna daga wurin Dakarkari mazauna ƙasar Zuru a cikin Jihar Kebbi. Ire-iren waɗannan magunguna sun haɗa da na ƙarin ƙarfin azzakari. A wannan magani ana samo sauyoyin wani icce da ake kira jan yaro, sai a taho da su gida a sanya aska ko wuƙa a kankare su sosai.
Daga nan sai a ɗebo gero daidai gwargwadon wanda idan an yi kunu da shi mutum zai iya shanye shi, sai a sanya wannan bayan sauyoyin jan yaro da aka ɗebo a cikin tukunya a tafasa a dama kunun salala. Wannan kunu ne mutum zai yi ta sha sannu a hankali zai ji azzakarinsa ya yi ƙarfi sosai.
Wani magani da Hausawa suka samu daga Dakarkari shi ne, na nuna buwaya. Ana samun ƙanzon tuwo da aka yi a gidan wanda zai yi amfani da maganin, sai a ɗebo sassaƙen iccen gamji a daka shi.
Daga nan sai a haɗa garin wannan magani da ƙanzon tuwo a sa a ruwa a cakuɗa su a yi mulmule uku, za a riƙa cin mulmule ɗaya a kullum har zuwa kwana uku. Idan aka yi haka mutum zai buwaya a duk duk wurin da yake. Idan aka yi kuskure aka ci sau huɗu, to mutumin zai zama maye (AGMSAZ, 21/5/2005).
Tera wata ƙabila ce wadda ake samu a wuraren da suka haɗa da garuruwan Gwani ta gabas da Gwani ta Yamma a Ƙaramar Hukumar Yamaltu-Deba a Jihar Gwambe. Al’ummar Tera tana tafiyar da al’adun wanzanci kamar yadda Hausawa suke tafiyar da nasu. Wannan dalili ya sa aka sami kamanci da bambanci dangane da yadda suke tafiyar da wannan sana’a a tsakaninsu.
Haka kuma akwai fahimtar juna a tsakaninsu wadda ta haifar da musayar al’adu. A saboda wannan dalili ne wanzaman Hausawa suka sami maganin ƙurajen aski daga wurin Terawa.
A lokacin da aka yi wa mutum aski don maganin ƙurajen aski, sai ya sami buri na hura-hura wadda ‘yan mata suke talla, ya shafa a wurin da aka yi masa aski. A duk lokacin da aka yi masa aski idan ya shafa wannan gari ƙurajen aski ba za su fito masa ba (MYHW, 13/8/1998).
A taƙaice kamar yadda aka gani wannan babi an yi bayani ne kan nason da al’adun baƙi na kusa waɗanda suka haɗa da Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa da ƙananan suka yi a kan wanzanci.
An duba rawar da al’adun waɗannan baƙi suka taka wajen kawo wasu sauye-sauye dangane da yadda Hausawa suke gudanar da al’adunsu waɗanda suka shafi aski da cire belun-wuya da na mata da kaciya da tsaga da kuma magungunan gargajiya.
Karanta Nason Al’adun Yarabawa A Kan Wanzancin Hausawa
Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA
MAYU 2009/JUMADA ULA 1430
Edita@rumasau-kallamu

Majalisar Tarayya da Zargin Naira Miliyan Uku
Majalisar Tarayya ta daɗe tana fuskantar tuhuma. An taɓa zargin budget padding a shekarar 2016, wato ƙara wasu abubuwa a cikin kasafin kuɗi domin aljihun wasu. Haka nan ana yawan sukar constituency projects, inda kuɗi ke ɓacewa ba tare da an yi ayyukan da ya kamata ba. Wannan sabon batu na naira miliyan uku ya zo ne ya ƙara girgiza martabar majalisa.
Idan har wannan zargi gaskiya ne, to abin yana da matuƙar haɗari. Domin ya nuna cewa ba za ka iya gabatar da ƙuduri ba sai ka biya kuɗi. Wannan ba wai kawai cin hanci ba ne, har ma zalunci ne ga jama’ar da suka zaɓi wakilan su da fata cewa za su kare muradunsu. A irin wannan yanayi, ƙudurin da zai gabata ba lallai ya zama na amfani ga jama’a ba, sai dai na masu kuɗi.
Idan aka ce EFCC da ICPC za su binciki batun, wannan dama ce gare su su nuna cewa suna aiki ba tare da nuna bambanci ba. Amma idan suka yi shiru, jama’a za su ƙara yanke ƙauna daga gwamnati da tsarin doka.
Dimokuraɗiyya tana hannun jama’a. Idan aka ci gaba da zaɓen ‘yan majalisa da ake zargi da rashawa, to jama’a za su ci gaba da fuskantar wahala. Kuri’a ce kawai makamin talaka.
A yau, Majalisar Tarayya na fuskantar sabon jarabawa. Idan ta kasa kare kanta daga wannan tuhuma, martabarta za ta sake raguwa. Amma idan hukumomin bincike suka tashi tsaye suka tabbatar da gaskiya, hakan zai taimaka wajen dawo da ɗan ƙaramin imani ga al’umma.
Cin hanci shi ne cutar da ta fi kowace lalata Najeriya. Duk wani batu da ya shafi majalisar dokoki ya kamata a yi masa duba sosai, domin a can ne ake tsara makomar jama’a.
Tarihin Dr. Yusuf Bala Usman danna nan
Edita@rumasau-kallamu

بَارَكَ اللهُ لَكَ فِي أَهْلِكَ وَمَالِكَ ، إِنَّمَا جَزَاءُ السَّلَفِ الْحَمْدُ وَالأَدَاء .
Barakallahu laka fi ahlika wa malika. Inna ma jaza’u salafil hamdu wal’ada’i
Allah ya yi maka albarka a cikin iyalinka da dukiyarka. Haƙiƙa sakamakon bashi shi ne godiya da biya.
Karanta Addu’ar Ƙin Shu’umci
Edita@rumasau-kallamu

Allahumma la ɗaira illa ɗairuka wala khaira illa khairuka wala ilaha gairuka
Ya Allah! Babu shu’umci sai abin da Ka halitta, kuma babu alheri sai alherinka, kuma babu abin bautawa da gaskiya ba Kai ba.
Ƙarin Bayani; Shu’umci shi ne mutum ya kudurce cewa wani abu mummuna zai faru gare shi saboda ganin wani abu ko jin sa. Wannan haramun ne, saboda abin da ke cikinsa na jingina tasiri ga wanin Allah, da kuma munana zato ga Allah. To wanda irin wannan ya afku gare shi, kar ya bar aikata abin da ya yi nufin yi; sai ya tuba ga Allah, sannan kaffararsa ita ce ya faɗi wannan addu’ar. [Bayanin mai tarjama].
Don karanta Addu’ar Wanda Ya Ji Wani Ciwo A Jikinsa danna nan
Edita@rumasau-kallamu

Kasancewar gidansu gida ne na ilmi da yaɗa shi, ya sa shi gadar wannnan sana’a ta koyar da Alƙur’ani da ilmi. Duk da cewa a halin yanzu Malam Attahiru shi ne Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato, duk da haka makarantarsa ba ta gushe ba ta na yaɗa addini a cikin garin Sakkwato tare da taimakon ‘yan uwansa musamman ma Malam Abubukar da Malam Ibrahim da Malam AbdurRahman da Malam Ahmad Zaruƙu.
Malam Attahiru Na Liman tsatson Alƙali Abubakar Ladan Rame ne, wanda ɗan Gwaggon Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo ne. Wannan zuriya mai albarka ta cigaba da jiɓintar koyar da addini da alƙalanci har zuwa kan Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato na yanzu).
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Buhari Siriddawa (Sarkin Malaman Sakkwato) danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

Haka kuma suna kiran wanda yake yin aski kawai da sunan ‘fari – fari’ ko ‘akola’. A saboda haka akwai wasu al’adun Yarabawa waɗanda suka yi naso cikin al’adun wanzanci na Hausawa.
A al’adar Yarabawa ba su damu da cire wa jariran da aka haifa masu belun-wuya ba, don irin wannan aiki ba ya cikin al’adunsu. Har ma idan an sami wata matsala makamanciyar wannan, sai su ba wanda yake fuskantar matsalar maganin gargajiya ya sha ko ya shafa a wurin da lalurin yake (YASASHL, 6/2/2006).
Irin wannan al’amari ya yi tasiri sosai a wurin wasu Hausawa waɗanda suka daɗe a ƙasashen Yarabawa, domin kuwa akwai waɗanda ba a cire wa jariran da aka haifa masu belun-wuya da belun-mata musamman a wannan zamani.
Wannan tasiri ya biyo wasu Hausawa waɗanda suka baro ƙasar Yarabawa suka koma garuruwansu na asali a ƙasar Hausa, don kuwa a nan ma ko da an yi masu haihuwa ba sa kiran wanzami domin ya cire wa jariransu belun-wuya ko belun-mata (UƊ da MBT da MAHD da MAA da MAMI da HZO da MASO da MAIA da HR, 7 da 8 da 9 da 10/2/2006).
Wannan al’ada ta Yarabawa ta yi naso a kan wanzanci ne saboda ire-iren waɗanda suka yi koyi da ita ba sa bari wanzamai su je gidajensu don yin ayyukan wanzanci. Wannan al’amari ya shafi yadda ake gudanar da wannan sana’a yadda wasu wanzamai suke rasa ayyukan yi.
A al’adar Yarabawa ba dole ne a yi wa jaririn da aka haifa aski ba, idan ma ta kama a yi, ba dole ne a yi shi a lokacin da aka haifi jaririn ba. A wurinsu ana yin aski ne a lokacin da ake da sha’awar yin sa ko kuwa a lokacin da suma ta yi yawa, kuma ba dole ne a yi askin ƙwaryar molo ba kamar yadda al’ummar Hausawa suke yi (MGAA, 30/9/2004).
Irin wannan al’ada ta Yarabawa ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasashen Yarabawa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda suke zaune a jihohin Lagos da Oyo da Ondo da Ekiti da Oshun da Ogun waɗanda ba sa yi wa jariran da aka haifa masu askin suna.
A maimakon haka, sai dai su sanya almakashi su daddatse sumar a lokacin da ta yi tsawo (YASASHL, 6/2//2006 da UƊSA da MBT da MAHD da MAA da MAMI da HZHO da MAS da MAIA da HR, 7 da 8 da 9 /10/2006) .
Wanzamai sun sami magunguna wurin Yarabawa. Daga cikinsu akwai na maganin ciwon ela. Ciwon ela yana kama yara ƙanana ne da jarirai waɗanda ba a yaye ba. Yanayin wannan ciwon shi ne, za a ga tsakanin cinyoyin yara sun sale sun yi jawur.
Idan kuma mace ce har cikin farjinta da gefensa duk sai ya sale ya yi jawur. Wurin da ciwon yake zai ta yi wa yaran ciwo da ƙaiƙayi wanda yake tilastawa yaran su soshe wurin, a wasu lokuta a lokacin da yaran suke susar wurin sai ya riƙa fitar da jini.
Maganin ela wanda Hausawa suka samu daga wurin Yarabawa shi ne, sai a sami sabulun salo a riƙa wanke wurin da ciwon yake, daga nan sai a sami attarugu ƙwaya ɗaya a wanke bakin yaron da yake da matsalar. Bayan nan kuma sai a sami sauyoyin bini-da-zugu da ganyensa a dafa su da ruwa, idan ya huce sai a sanya yaron a cikin ruwan ya ɗauki wani lokaci a ciki.
A lokacin da aka fito da yaron daga cikin ruwan, sai a sami ƙyalle mai kyau a shafe ruwan da yake wurin ciwon, daga nan sai a sami man ja a riƙa shafawa a wurin. Za a yi ta yin haka kullum har lokacin da yaron ya warke (YASASHL, 6/2/2006).
Karanta Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa
Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA
MAYU 2009/JUMADA ULA 1430
Edita@rumasau-kallamu

بِسْمِ اللهِ
ثلاثاً
Bismillah. Da sunan Allah (nake neman waraka). (sau uku)
Sannan ka ce:
أعُوْذُ بِاللهِ وَقُدْرَتِهِ مِنْ شَرِّ مَا أَجِدُ وأَحَاذِر
(سبع مرات)
A’uzu billahi wa ƙudratihi min sharri ma ajidu wa uhadir
Ina neman tsari da Allah da kuma Ikonsa daga sharrin abin da nake ji (na ciwo) kuma nake jin tsoransa (sau bakwai)
Karanta Addu’ar Tafiya (Wadda Matafiyi Yake Yi)
Edita@rumasau-kallamu

Allahu akbar, Allahu akbar, Allahu akbar, subhanallazi sakkara lana haza wama kunna lahu muƙrineen wa ina ila rabbina lamun ƙalibun allahumma ina nas’aluka fi safarina haza al-birra wattaƙwa, wa minal amali ma tarda, Allahuma hauni alaina safarana haza wadwi anna bu’udahu, Allahuma anta sahibu fil safari wal kalifatu fil ahli allahuma inni a’uzubika min wana’i safari wa kabatil wanzari wa su’il mun ƙalibi fil mali wal ahli
Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma. Tsarki ya tabbata ga (Ubangiji) Wanda ya hore mana wannan (abin hawa); ba mu kasance masu ikon sarrafa shi ba. Haƙiƙa mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu. Ya Allah! Muna roƙon Ka nagarta da tsoron Allah a cikin wannan tafiya ta mu, da kuma aiki wanda Kake yarda da shi. Ya Allah! Ka sauƙaƙe mana wannan tafiya ta mu, kuma ka naɗe mana nisanta. Ya Allah! Kai ne Ma’abocinmu a cikin wannan tafiya, kuma Halifanmu a cikin iyalanmu. Ya Allah! Ina neman tsari da Kai daga wahalar tafiya, da abin gani mai sanya ɓacin rai, da kuma komawa mummuna ga iyali da dukiya.
Domin karanta Yadda Ake Addu’ar Hawa Abin Hawa danna nan
Edita@rumasau-kallamu

A halin yanzu mafi yawa daga cikin al’ummar Yarabawa suna zaune a kudu maso yammacin Nijeriya a jihohin Lagos da Oyo da Oshun da Ondo da Ogun da Ekiti da kuma a kudu maso yammacin jihar Kwara. Ana kuma samun su a ƙasashen Jamhuriyar Benin da Togo da Cote D’iɓoire da Saliyo.
Akwai daɗaɗɗiyar dangantaka tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa, wadda tun farko ta kasuwanci ce. An sami bayanan da suka nuna akwai dangantakar kasuwanci a tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa a cikin ƙarni na goma sha takwas. A wannan lokaci ne wasu ‘yan kasuwa daga Ogbomosho suka shigo Kano kuma suka zauna a cikin birni.
Wannan dangantaka ta ƙara ƙulluwa ta hanyar kasuwancin da aka riƙa yi a tsakanin mutanen ƙasar Hausa da na ƙasashen kudu waɗanda suke bin hanyar da ta bi Zariya zuwa ƙasar Nufe ta zarce zuwa ƙasashen Yarabawa. An sami ire-iren waɗannan Yarabawa a ƙasar Katsina da Zariya (Adeleye: 1975:592).
Da yawa daga cikin Yarabawan da suke zaune cikin ƙasar Hausa a yanzu sun shigo ne a cikin ƙarni na ashirin a sakamakon kafuwar mulkin mallaka. A Kano an sami al’ummomin Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo a farkon ƙarni na ashirin, kuma suna daga cikin mutanen farko waɗanda aka kafa unguwar Sabon Garin Kano da su.
Sun shigo Kano da Zariya don yin aikin ginin hanyar jirgin ƙasa wadda aka kawo Kano, ko kuwa don yin aiki a tashar jirgin ƙasa, ko don yi wa Turawan Mulkin Mallaka aikace – aikace, ko kuwa don yin aiki a kamfanonin da Turawa suka kafa a waɗannan wurare. Wasu Yarabawan kuwa sun shigo ne don yin aikace-aikacen addini na Musulunci ko na Kirista.
A sakamakon jin daɗin zama da suka yi a wasu garuruwan ƙasar Hausa musamman a Kano da Zariya da Katsina da Gusau da Sakkwato, sai wasu Yarabawan da suka shigo a matsayin ma’aikata bayan sun ajiye aiki suka yanke shawarar ci gaba da zama a waɗannan garuruwa. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon jin daɗin zama da al’ummomin waɗannan wurare da suke zaune da kuma samun damar yin kasuwanci ba tare da fuskantar wata matsala ba.
Misali, Alhaji Abdul’aziz Kehinde wanda yana ɗaya daga cikin al’ummar Yarabawa da suka fara shigowa Kano a cikin shekarar 1911, ya zo a matsayin ma’aikaci a tashar jirgin ƙasa. A shekarar 1925, sai ya ajiye aiki ya shiga harkar kasuwanci a nan Kano. Akwai ire-irensa masu yawa cikin garuruwa da ƙauyukan ƙasar Hausa, waɗanda bayan sun ajiye aiki, sai suka ci gaba da zama a wuraren da suke cikin ƙasar Hausa (Baƙo: 1990:104).
Fitattu daga cikin Yarabawa ‘yan kasuwa waɗanda suka shigo Kano a farkon ƙarni na ashirin sun haɗa da Alhaji Muhammadu Salihu Olowo wanda ya zo daga Ilesha a cikin shekarar 1903. Da farko ya fara zama a unguwar Ayagi daga baya sai ya koma Sabon Gari cikin shekarar 1916. Yana daga cikin waɗanda suka taimaka aka gina masallacin Yarabawa na Sanmori – ad – deen a cikin shekarar 1925.
Akwai kuma Alhaji Sani Giwa wanda ya zo Kano daga Abeokuta a cikin shekarar 1920. A duk faɗin Sabon Gari da kewaye Yarabawa da waɗanda ba Yarabawa ba suna ganin mutuncinsa saboda dattakonsa da karimcinsa da riƙe alƙawarinsa. Wannan ne ya sa shi zama Sarkin Yarabawa na farko a ƙasar Kano.
Haka kuma akwai Mr.D.O.Sanya Olu wanda shi ma ya shiga Kano ne cikin shekarar 1920, kuma shi ne mutum na farko wanda ya fara kafa Otel a Sabon Garin Kano a shekarar 1939. Da farko sunan Otel ɗin Colonial Hotel, amma da aka sami ‘yancin kai, sai ya canja masa suna zuwa Paradise Hotel (Baƙo, 1990:) Waɗannan misalai ne kawai aka kawo don akwai ire-irensu masu yawa da suke zaune a cikin garin Kano da kewayenta.
A garin Gusau ma akwai Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo don yin harkar kasuwanci da sauran hulɗoɗi. An bayyana cewa tun kafin ƙarni na goma sha tara akwai Yarabawa waɗanda suke kasuwancin goro a ƙasar Hausa. A cikin ƙarni na ashirin musamman a cikin shekarar 1920 ne ake tsammanin Yarabawa masu yawa sun fara shigowa garin Gusau.
A lokacin wasu sun shigo domin yin kasuwanci, wasu kuma sun shigo domin yin aikace-aikace a kamfanoni da ma’aikatun da Turawa suka kafa irinsu tashar jirgin ƙasa da dai sauran wurare.Yarabawan da suka shigo garin Gusau suna gudanar da kasuwanci iri daban-daban, misali matansu suna sayar da man ja da sabulun salo da man shafawa irin wanda suke yi, ana kiran sa da suna “Mai Zubi”.
Su kuma mazan suna sana’o’i irin su gyaran kekuna da ɗinkin keke da ginin bulon siminti da yin aski da dai sauransu. Haka kuma wasun su sai suka shiga harkar sufuri. An bayyana cewa an ƙirƙiro yin hayar mota tasi a garin Gusau cikin shekarar 1969, kuma Yarabawa mazauna garin Gusau ne suka fara yin wannan sana’a. Daga cikin su akwai Alhaji Abdulatif S.Adegoke da Alhaji Afolabi da Mr.Ganiyu Raji (Usman, 2000:205, 206).
A sakamakon daɗaɗɗar dangantaka tsakanin Yarabawan da suka shigo Gusau da Hausawan Gusau, wasu Yarabawan sun yi auratayya da mutanen da suka tarar wanda yin haka ya haifar da musayar al’adu. A halin yanzu Yarabawan da suke zaune a garin Gusau suna zaune a unguwannin Sabon Garin Gusau da Canteen da Tudun Wada da GRA da Sabon Fegi da Birnin Ruwa da Bakin Kasuwa da sauran wurare a cikin garin Gusau da kewaye (Usman, 2000:205).
Kamar yadda Yarabawa suka shigo ƙasar Hausa, an sami Hausawa masu yawa waɗanda suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka shiga ƙasar Yarabawa, kuma sun yi fiye da shekaru ɗari a wannan ƙasa.Ire-iren waɗannan Hausawa suna zaune a unguwannin Alaba da Agege da Obalande da Hausa Line a Lagos da kuma a Sabo Ibadan da Sasa a Ibadan da kuma a Shagamu da Ilori da dai sauran wurare a ƙasar Yarabawa.
Daga cikin ire-iren waɗannan Hausawa mazauna ƙasar Yarabawa akwai Sarkin Hausawa Dogara wanda ya bayyana min ta hannun Sakatarensa cewa an haife shi a Lagos, mahaifinsa ma a Lagos aka haife shi. A halin yanzu yana daga cikin fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Lagos, don kuwa daga cikin matansa akwai wadda ‘ya ce ga Oba na Lagos.
Bayansa akwai Sarkin Hausawa Alhaji Kabiru Garba wanda tsohon Hafsan Soja ne wanda ya yi ritaya, kuma yana zaune a Arewa House Ebute-Metta Lagos. A Ibadan akwai Sarkin Sasa Alhaji Haruna Mai Yasin wanda shi asalinsa mutumin Zakka ta ƙaramar hukumar Safana a jihar Katsina ne. A yanzu yana ɗaya daga fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Oyo.
Don karanta Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa danna nan
Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA
MAYU 2009/JUMADA ULA 1430
Edita@rumasau-kallamu