Auren Sayyadi Abdullahi Da Sayyada Aminatu

0
39

Abdullahi ɗan Abdulmunaf shi ne mafi soyuwa a gurin Mahaifinsa, ya auri Aminatu ‘yar Wahabu ‘yar Abdulmanaf ‘yar Zuhra ‘yar Kilabu, lokacin yana ɗan shekara goma Sha-takwas (18) a duniya.

A lokacin da Abdullahi ya auri Aminatu ita ce mafi fifiko a cikin matan zamanin a cikin ƙabila Ƙuraishawa da dangantaka mai kyau, yayin da Abdullahi ya shige ta, sai Allah (Subhanahu wata’ala) ya ba ta rabo na manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam), da wata biyu, sai mahaifinsa bai jima a duniya ba, ya yi wafati aka rufe shi a garin Madinah a gurin ‘yan uwansa Banu-Aɗiyyu bin Najar. A wannan lokacin ya kasance ya tafi kasuwanci zuwa Sham (Siriya), sai Ajalinsa riske shi a garin Madinah a kan hanyarsa ta dawowa gida.

Yayin da lokacin haihuwar Aminatu ya yi, sai ta haifi annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam), an yi bushara da haihuwar wannan babban abin halitta, wanda ya yi dai-dai da ranar litinin, tara ga watan rabi’ul- auwal (Nurul yaƙin shafi na 8) ko kuma goma sha biyu ga watan rabbiyul-Auwal wanda bai yi dai-dai da ashirin ga watan Afrilu ba, shekara ta ɗari da saba’in da ɗaya (571) miladiyya, wanda ya yi dai-dai da shekarar farko ta giwaye.

Daga ƙarshe, aka sanya masa suna Muhammad, wanda ya ba Labarawa mamaki sosai, saboda a lokacin babu wani mutum mai irin sunansa a zamanin, Saboda Allah (Subhanahu wata’ala) ya nuna matsayinsa ga halittunsa, da dai sauransu.

Sannan a lamba ta huɗu (4), Yace; “Ummul-Aimana ta raine shi, to a nan ƙa’ida ta raino ga wacce ta ke so ɗanta ya zamo mai hazaƙa, to dole a kanta ta kiyaye irin abincin da za ta ci sannan ta dinga cin halal, sannan ta dinga kula da ɗanta shigarsa da fitarsa haɗi da mu’amala ta gari, Saboda ɗabi’a tana kwaikwayen ɗabi’a ne.

Danna nan don karanta  Yadda Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) Yake Shan Ruwa

Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

labarin da ya wuceAmfanin Aya Wajen Samar Da Lafiya A Jiki
Labarin na GabaTsarin Tazarar Haihuwa Mara Amfani Da Magani