Ranar 27 ga watan Rajab, rana ce da Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya yi Isra’i da Mi’iraji.
Isra’i: Shi ne tafiyar da annabi ya yi daga Makka zuwa masallacin Aƙsa.
Mi’iraji: Shi ne tafiyar da annabi ya yi daga masallaccin Aƙsa zuwa sama ta bakwai har zuwa wajen da suka yi munajati da Allah (Subhanahu wata’ala).
Wannan ranar, ta kasance rana mafi daraja a wajen musulman duniya, saboda daga ita ne aka samu tabbatuwar salloli guda biyar, (wanda a farko guda hamsin ne).
Abubuwan da aka samu a wannan rana:
1. Salloli guda biyar.
2. Tabbatar aure.
3. Rabon gado.
4. Hanyoyin samun aljanna.
5. Tsarin gudanarwar rayuwar mutane.
Da sauransu
Danna nan don karanta Ranar Isra’i Da Mi’iraji
Edita; Rumasa’u M. Kallamu