Addu’ar Komowa Daga Tafiya

0
5

Abdullahi ibn Umar, Allah ya yarda da shi, ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance idan ya kama hanyar dawowa daga tafiya wani yaƙi; ko aikin hajji ko umara, idan ya hau tudu sai ya yi kabbara sau uku; sannan ya ce:

“Laa ilaaha illallaahu wahdahu laa shariika lahu, lahul mulku walahul hamdu, wahuwa alaa kulli shai’in ƙadiirun, aayibuuna taa’ibbuna, aabiduuna li rabbinaa haamiduuna, sadaƙal laahu wa’adahu, wa nasara abdahu wa hazamal ahzaaba wahdahu”.

{Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaɗai; babu abokin tarayya a gare shi. Mulki nasa ne (shi kaɗai); kuma shi mai iko ne a kan komai. Mu masu komawa ne, masu tuba, kuma masu godiya ne ga Ubangijinmu. Allah Ya gaskata alƙawarinsa, Ya taimaki bawansa, Ya ruguza rundunonin kafirai shi kaɗai}.

Domin karanta cikakken bayani akan Yin Kabbara Da Tasbihi Yayin Da Ake Tafiya danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.

Edita; RMK

labarin da ya wuceAddu’ar Mazaunin Gida Ga Matafiyi
Labarin na GabaYadda Ake Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.