Amsa: Abubuwan fili da suke karya azumi su ne:
Cin abinci ta hanyar tauna ko haɗiya.
Shan ruwa ko wani abin sha mai kama da ruwa.
Kwanciyar aure ga masu aure.
Fitar da maniyi ga wanda ba shi da aure ta hanyar kallace-kallace a fili ko mujalla ko wayoyin hannu ko talabijin.
Sauraran labaran batsa, ko na motsa sha’awa kai tsaye daga wani ko ta hanyoyin sadarwa da gangan.
Hujja: “Wanda yaci, ko ya sha, ko ya kusanci iyalinsa, ya karya azuminsa”.
Marawaici: Abu Huraira, littafi Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim, Sunan Abu Dawud, Sunan Turmuzi, Sunan Nassa’i Sunan Ibn Maajah.
Domin karanta cikakken bayani akan Waɗanne Abubuwa Ne Ke Lalata Azumi A Ɓoye? danna nan.
Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Azumin Watan Ramadana 2 danna nan.