Tarihin Malam Muhammadu Na Ta’ala

0
46

Malam Muhammadu Na Ta’ala ɗaya ne daga zuriyar Sheikh Abdullahi Alkanawi, almajirin Shehu Usman kuma jakadansa. Asalinsa mutumin Kano ne daga jinsin Gyanawa. Ya koma Sakkwato a lokacin da ya samu labarin bayyanar Shehu.

Daga nan kuma ya cigaba da taimaka masa a Sifawa. Bayan an dawo Sakkwato, Shehu ya ba shi fili inda ya gina gidansa da makarantarsa; wadda aka fi sani da Gidan Kanawa. Bayan rasuwarsa sai ɗansa Halliru ya zama halifansa. Daga nan kuma sai ɗansa Umar, shi ma kuma ɗansa Ibrahim Dasuki ya gaje shi.

Bayansa ne sai ɗan’uwansa Muhammad Na Ta’ala ya zama halifa. Wannan makaranta ba ta gushe ba ƙarƙashin ‘ya’yansa su Alhaji Bashir Muhammad Na Ta’ala da ɗan’uwansa Malam Ahmad Zaruƙu; inda suke cigaba da ilmantarwa da wa’azi.

Domin karanta cikakken bayani akan Malaman Mabera A Sakkwato Waɗanda Ke Tara Almajirai A Tsarin Tsangaya danna nan.

Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Kano Kashi Na Ɗaya(1) danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceIngantattun Hadisai Kan Falalar Ranar Ashura Da Azumin Ranar
Labarin na GabaYin Amfani Da Maganin Sauro Na Ƙonawa