Manhajar Tsangayar Gwaji

0
251

Ya kamata manhajar wannan tsangaya ta gwamnati ta fuskanci cimma manufofin ingantaccen imani, da samun rayuwa ta dogaro da kai, da wayewar zamani.

Wannan manhaja za ta yi ƙoƙarin cimma koyarwar Shehu Usmanu Ɗan Fodiya, wadda ke komawa kan ilmi da noma da kiwo. Sauran tsare-tsare za su iya shiga sannu a hankali.

Wajibi ne manhajar ta cimma:

1. Samar da ingantacciyar haddar Alƙar’ani ko tilawa mai ƙarfi.
2. Koyar da almajirai wani abu na ilmin Fiƙhu da Hadisi.
3. Cusa son Larabci da magana da shi da ilmin lissafi da Hausar boko, don gogayyar rayuwar yau da gobe.
4. Ƙarfafa tukuri da musaffa da sauransu.

Albashin Malamai
1. Hafizi – GL 09
2. Dattijon Alaramma – GL 12
3. Gwani – GL 13
4. Gangaran – GL 15

Domin karanta cikakken bayani a kan Gudunmawar Mawadata Da Ɗaiɗaikun Jama’a Ga Tsangayu danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Gudunmawar Tsangayun Alƙur’ani Wajen Cigaban Al’umma danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihinsu Da Zamantakewarsu Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceSamar Da Tsangayun Gwaji Na Gwamnati
Labarin na GabaAbubuwan Da Suke Hana Karɓar Gaskiya